? Mammadou ɗan uwan sa ne da yake kusa da shi a haihuwa cikin jerin 'ya'yan gidan mutane biyu ne kaɗai a tsakanin su Bilal da kouma Yacouba da suke ɗaki guda.
Hajiya Mama kouwa da ɗai ba zai yafe mata ba da ta zama jagora na lalacewar rayuwar sa da zama tsanin faɗawar sa a duk wasu munanan aiyuka da yayi a baya.
Muryar Hajiya Umma ta katse masa zurfin da yayi cikin tunani inda take miƙa masa 'yan mukullin ɗakunan sa tana cewa "Magarib ta gabato ka tai kayi haramar Sallah nasan Maimartaba zai nemi ganin ka doumin ku tattauna ya ji ra'ayin ka kan duk waɗanda suka maka ƙeta kada ka cutar da kan ka wajen hanawa a bi ma hakkin ka , ka yafewa wanda duk zuciyar ka ta amince da yi masa yafiya , kada kouma ka ɗaukarwa kanka aniyar zama da wanɗanda zuciyar ka bata aminta da su ba ka saukakewa kanka sake faɗawa ga hatsari irin wanda ka fito a baya Allah ya ƙara ƙiyaye mouna kai sannan ka tsanan ta addu'a .
"Amin Umma na kouma gode sosai Allah ya ƙara nisan kwana tare da lafiya .
Lokacin da ya fito mafi yawan 'yan uwansa sun watse sun tafi hidindimun su wasu kuma suna haramar sallah Ubbo ce kaɗai a zaune da ya fito dariya suka yiwa juna shi da ita yana wucewa tace " Fita kake yi Yarima ?
" zan tai Sallah , ya ce mata yana ƙarasa ficewa .
Bayan ya idar da Sallah gajiya duk ta taso masa tun yana sallar yake hamma dan haka bai tsaya sauraran masu son gaisawa da shi ba ya nufi cikin gida sashin sa ya tasamma saboda so yake yayi wanka da ruwa mai ɗumi ya ɗan huta kafin lokacin isha'i da yasan bayan sallar isha zasu gana da Maimartaba .
Masu gadin shiyar sa suka buɗe masa ƙofa ya shiga , haske ya wadaci harabar da taimakon security lights dan haka ya nufi sashin sa kai tsaye yana janye ganin sa daga shiyar da Maimounatou tayi zama da ƙoƙarin son raba zuciyar da damuwar da take rufto masa ya hau kan 'yar barandar sa ya kai hannu yana kunna wuta domin ya samu damar buɗe ƙofa .
Zuciyar da tai masa wani ɗan ƙaramin tsalle lokacin da ya lura da wanzuwar mutum kwance akan barandar kusa da ƙafafun sa ,
"Wanene nan ? ya tambayi zuciyar sa yana yin baya kaɗan cike da mamaki yana kure kallo zuciyar sa a dake da ƙoƙarin ganin fuskar ta da ta juya baya tana baccin ta hankali kwance
Motsin sa da yayi da ɗan ƙarfi yasa ta motsawa ta juya zuwa rigin-gine tana motsa idanun ta da suka yi nawi .
Saƙare yayi yana duban ta karo na farko da ya ji ya yarda cewa akwai Mafarkin ido biyu domin shi yake yi a yanzu.
. "Fatima-zahra ya ƙira sunan ta a can ƙasan maƙoshi bata amsa ba saboda baccin da yake son sake danne ta .
Tsugunno yayi a hankali kamar mai tsoron kar ya taɓa ta ta ɓace ya kai yatsun sa biyu kan fuskar ta ya shafa .
Da sauƙar hannun sa a fuskar ta ta buɗe idanun ta da suke luf-luf cike da rauni ta ɗora ganin ta akan fuskar sa da
"Fatima-zahra est-ce vrai ? Ehm ? est-ce vrai ? Ya furta hakan muryar na 'yar ƙyarma .
Hannun sa da yake cigaba da mata yawa a fuska ta riƙe da nata hannun kafin ta fara yunƙurin tashi sai dai kwanciyar da tayi a kan floor ba tare da shimfiɗa ba yasa jikin ta yin ciwo musamman haƙarƙarin ta .
Lura da yadda ta kasa tashi farar ɗaya yasa shi tallafar ta gaba ɗaya ya zaunar da ita lokacin da shima yake yin zaman dirshan a ƙasa ya jingina ta da jikin sa kamar wanda ya tuno sai ya ɗaura dukkanin hannuwan sa biyu akan tudun cikin ta yana shafawa da buɗaɗɗiyar muryar sa yace
"Fatima ki min magana mana don Allah , kece kuwa ?
Kewar sa mai girma da take ta faman yaƙa tsawon watannin da suka yi basa tare ita ce ta taso mata baki ɗaya a yanzu ta kassara duk wata juriyar ta sai ta juyo a hankali rana ta farko da ta ɗaro hannuwan ta a fuskar sa ta riƙe shi da sanyi murya tace " Baban Mama est-ce vrai ? Meyasa ka tafi ka barmu tsawon lokaci baka neme mu ba ? meyasa ? Ka sa min ciwo a zuciyata ta , kasa kullum ina ta kuka . ƙarasa zancen tana janye hannuwan ta daga fuskar sa hawayen ta suka fara sauƙa .
Riƙo ta yayi lokacin da ya lura tana jaa baya daga kusan sa cike da tsoron kar ta sake tafiya ta bar shi ya shiga share mata hawayen ta yana cewa " ke kika bar ni Fatima kin manta ke kika tafi ba tare da izni na ba , baki ko min sallama ba kika bar ni ? Fatima ke ma bakya sona ko ?
Kan ta ta mayar kirjin sa da ƙarfi tana jin farin-cikin sake ganin sa tana jin kamar an bata maganin wata cuta dake cinye mata nishaɗin ta , ta kewaye shi da hannuwan tana riƙe shi ƙam-ƙam .
"Oshh , yace yana ɗan ɗaga ta daga jikin sa saboda raunin sa da ta fama .
"Fatima ina da rauni a jiki , baki san nayi jinya ba kou ?
Idanun ta suka yi rau-rau tana kallon a hankali ta motsa bakin ta tana faɗin "sannu ,
Da ido ya amsa mata da yasan ba lalle ta gani ba da nishaɗi cikin muryar sa yace "Ya babyn mu ? Lafiyar shi lau kou ? Naga yayi girma , ya zama babba alhalin bana ganin sa .
Bai jira ta ba shi amsa ba ya ɗaga ta suka miƙe tsaye yana ɗora faɗin " mu tai ciki ki bani labarin yadda kika zou nan kuma ki nuna min Baby na na gan shi sosai .
Ƙin motsawa tayi a hankali ta zare hannun ta daga cikin nashi kafin tace " nan ba shine masauƙin mu ba a can wajen Umma muka sauƙa can zan koma .
Sake riƙo hannun ta yayi ya ja ta jikin sa ɗan tunbin ta ya tokare haɗuwar fuskokin su muryar sa a ƙasa da wani irin yanayi yace "to ai nan ne gidan ki nan da muke tsaye nan ne shiyar gidana nan shine ɗakina ya mata nuni da ƙofar ɗakin su .
Cike da son samun haɗin kan ta ya cigaba da cewa ko kin koma yanzu tunda na dawo gobe nan za'a kawo ki , kin ga nayi rashin lafiya ma baki ko min ya jiki ba , muje ciki na nuna miki inda aka min fiɗa .
Da sauri ta ɗago kan ta muryar ta tana rawa tace "yanka ka aka yi ? Aina ? Amma ka warke yanzu ? Ni fa ban san kana rashin lafiya ba sai da suka je tahowa da ni suke faɗa .
Langwaɓe kai yayi da son ta tausaya masa yace " nayi jinya iriyar wacce ban taɓa makamanciyar ta ba Allah shi ɗagga ni da war haka na daɗe a kushewata .
Ta buɗe buɗe baki zata yi magana suka fara jiyo muryoyi ana hira da dararraki ana kusanto su ,
A tsorace Falmata ta zare jikinta daga nashi a kunnuwan ta masu saurin ɗaukar sauti ta tsinkayo muryar Ubbo cikin masu maganar ,
Muryar ta tana ɗan rawa tace " ni ni zan tafi ga mutane suna zuwa kar a ganni ace kuma na biyo ka .
Yana ƙokarin sake riƙe ta taƙi yadda da sauri ta sauƙa daga barandar tayi bayan shuke-shuken da suke kusa da ita .
Da wani irin yanayi yayi tsaye hannuwan sa biyu zube cikin aljihun wondon sa har Siyama da Ubbo suka ƙaraso wajen bayan su bayu ne su uku suna bin su ɗayar saɓe da Yumna a ƙafaɗar ta biyun suna riƙe da manyan tire-tire da aka jera abinci bisa .
Kallon su yayi kafin ya ɗauke kai ya juya yana buɗe musu ɗakin
"Biyamuradi daman kana ta tsayuwa nan ? Ko kouwa yanzou kaima kake isowa ?
Ubbo ta tambaye shi ,
Bayun da suke gaishe shi ya amsawa gaisuwar kafin su wuce ciki Siyama na gaba tana musu jagora.
"Tun-tuni na zou Ubbo , ya amsa mata yana satar kallon inda Falmata take maƙale ran sa sam babu daɗi damuwar sa kar wani ƙwaro ya cije ta .
" To ni zan koma sai da Safe ku kula da kan kou .
Gyaɗa mata kai yayi lokacin da take juyawa Bayun da suka ajiye sakonni hannuwan su suna rufa mata baya bayan Siyama ta sallame su daga ciki .
Suna ɗan bada tazara ya sauƙo daga kan barandar da sauri ya nufi inda Falmata take kafin ya ƙarasa daga bayan sa Siyama tace " Baban Yumna wani wurin kake tahia ? Na haɗa ma abinci fa kouma ga wanka ma na tsumayen ka .
Juyowa yayi yana kallon ta ya ga yadda ta ƙarya wuya tana tsare shi da idanun ta , a dai-dai lokacin ya rasa takamaimai amsar bata yana ganin ta ta taho har gaban sa tana murmushi ta saƙala hannun ta cikin na shi .
"Ka bar koume zouwa gobe yanzou lokacin hutu ne Maimartaba da kan shi yace Umma ta sanar da kai ka huta yau sai daren gobe za ku gana .
Jan hannun sa tayi tana 'yar dariya ta sake cewa "mu tai ciki na kula da kai Vous êtes mon patient pour aujourd'hui et je suis votre médecin.( kai marar lafiyan da zan kula da shi ne a daren yau nice likitar ka )
Cikin idanun ta ya mayar da duban sa yana lalubo fassarar kalmomin ta a cikin su, murmushi ta sake yi masa tana kashe masa ido da yasa shi yin dariyar da bai shirya mata ba , cikin ran sa yana mamakin yaushe Siyama ta falle ya haka ? ya jaa ta jikin sa hannun sa riƙe da kugun ta suka juya tare muryar sa ƙasa-ƙasa yace mata " Fille, es-tu sûre que tu peux prendre bien soin de ça, ta patiente? ( Yarinya kin tabbatar za ki iya kula da wannan marar lafiyan naki da kyau ?
Dariya ita ma ta saki tana rufe fuskar ta da tafukan hannun ta cike da jin kunya gefe guda zuciyar ta na madallah da 'yar uwa irin Ubbo da duk wasu shawarwarin ta basa wuce akan yadda zata yi ta karkato da hankalin mijin ta kan ta.
Sun kai kan barandar sa ya juyo yana sake kallon inda Falmata take a idanun sa ya ga motsawar ta a wajen .
Siyama ta jaa hannun sa zuwa ciki suka turo ƙofar .
A hankali Falmata ta fito daga inda tayi maɓoya idanun ta shaɓe-shaɓe da ƙwalla zuwa yanzu ta tabbatar ita 'yar karo ce a wajen sa da kaddara ta haɗa su marar yanci ce ita da koyaushe take duƙunƙune a gefe.
Siyama ita ce matar da take da 'yanci na yin duk yadda ta so da shi a lokacin da duk ta so amma ita ai a ɗosane take da kuskure kaɗan zata yi dangin sa su tunɓuke ta .
Idanun ta suna ruwa ta baro sashin da kyar saboda bayan ta da yake rirriƙewa sai dai lokacin da ta tasamma komawa masaukin ta sai ta rasa hanya ,
Sai lokacin ta lura da sashi-sashi ne a ainahin gidan da duk gine-ginen su iri ɗaya ne sai ka lura da kyau zaka iya tantancewa ko kuwa idan daman ka san gidan sosai .
A idanun ta da suke da rangwamen lafiya ga kuma duhun dare ba zata iya tantance ina ta fito ba sai dai tayi amfani da hagu da dama dan haka tayi hasashen sashin da yake hagu daga nan ta fito dan haka ta kama hanya .
Ko a tsarin harabar sashin bata ga sauyi daga wanda ta gani a ɗazu ba shiru sashin yake babu kowa duk hadiman sun kammala aiyukan su sun tafi ga makwantan su .
dan haka kan ta tsaye ta dunga ratsa falukan da ita take tura ƙofofin su da hannun ta har ta tarar da wanda ya mata iri ɗaya da nasu sai dai wannan ta lura kamar ba wancen ɗin bane saboda wannan babu kujeru sai wasu irin katifu da aka yiwa falon ƙawanya da su da ta tsaya da kyau ta lura sai ta ga kamar har labulayen falon ba irin waɗancan ɗin bane .
Tana ƙoƙarin juyawa ta nemi wanda zata tambaya ko nan ne sashin Umma kamar yadda ta ji ana ƙiran surukar ta da wannan sunan , dogon kunnen ta ya fara jiyo mata tashin muryar wata mace daga ɗakin da tayi zaton masauƙin ta ne dan haka ta ɗan taka gaba kaɗan zuwa kusa sa ɗakin tana saurarar kalaman matar da take yin su cikin tashin hankali da hargagi .
" Hafsatouwa ya zamo dole ki kouma wajen sa ki daɗa masa bayani da jaan kunne kada a samou watta matsala ga wannan karon wannan shegiyar ɗiya ta mutan agades da ta ɗora min jakar tsaba kaji sunka bini da tsattsaga ina buƙatar ya lalata min ƙwanyar ta , ta wanke ni ta wanke ɗiyana da bakin ta da ta min wannan sheri ta tona min asiri na da shike binne tsawon lokaci ina so ta lahe ɗoɗɗoyan aman da tayi da bakin ta .
" shi kouwa wannan taƙadarin yaro ɗan tamri Youssoufa da ake kome bisa kan sa ina so a sabunta min aikin sa yayi tsamri fiye da na baya a ƙara hargitse shi a gigitar shi ya fice hankalin sa , itta hegiyar ɗiyar da ya amro dagga Nigeria a sanya shi i mata shika ukku russ tunda na lura shina ƙamnar ta sosai hakan zai ci ran sa ya zaburar sa komawa ga ruwa ina so ya zama tamre wurin bibiyar mata a baya ya kwana da ya ya auri ƙamna gaba 'ya da uwa nake fatan ya haɗa kada kouma ya saurarawa barasa ya zuƙe ta tamkar nonon uwatai ya zama lalattace irin lalatar da zata sa iyayen sa su yahe shi dagga cikin 'ya'ya mutanen gari su masa korar kare dagga birnin Maradi .
"Daga nan na san baƙin-cikin haka shi zai kai Safiya ramin ta...tayi wata dariyar hango cikar buri .
Daga ƙasan ta inda tayi gurfano Hansatuwa da take sauraron ta tana taya ta dariya tace " Ranki shi daɗe maganin kukana ai wannan kullin magani da na kawo miki shi ita uwar ta su anka ce ana so ta ci domin barin ta haka nan tsakani yana lalata mussu aiki kin san ta da ibadar ganin ido .
" ar can kyale ta mu da muke ɗiyan liman ma munka saurarawa ibadar nan bare itta da haye tayi ɗaukar duman magaji da nishi dan kawai ace itta ta Allah , maganin ta nake yi wallashi sai na hana ta ga yin ibadar naga ƙaƙa ta ka yi ta lalata mouna aikin 'yar tselen uwa .
"Hafsatouwa muddin aiki shi tafi dai-dai da tsarin mu ki tabbata shekarar gaba ke ai babbar jakadiyar birnin Maradi doumin kouwa waccen kaucewa take ta baki guri da hannuna zan sallame ta da wani mummunan sharri ta yadda zuri'ar ta basu yin gadon matsayin ta sannan ban tsaya nan ba cikin jama'ar ki ɗai-ɗaya ne ba za su Makka ɗakin Allah ba sai fa wanda Allah bai ƙira ba .
Wata mitsi-tsiyar guɗa Ƙaramar jakadiya ta sake da hakan bai hana su jin motsin Falmata ba wacce a kokarin ta na yin baya ta ture 'yar randar da aka ajiye 'yar bishiyar fulawa daga sama kaɗan da inda take tsaye tana sauraron su tukunyar ta faɗo ta fashe .
A tare suka zaburo ƙirjin su na dakan tara-tara da jin tsoron ko dai an musu laɓe ?
"Idan kuwa hakane muddin ta kama mai mata laɓe sai ta sabauta shi kafin ta ɓadda shi ko wanene kouwa da dai ya fasa wannan sirri na ta mafi girma .Hajiya Mama ta aiyana hakan cikin ran ta lokacin da take nufar falon a ɗimauce .
ASSALAMU ALAIKUM MASU KARATU
DA FATAN KUNA LAFIYA TARE DA FATAN ALHERI .
KUYI HAƘURIN JINA SHIRU DA KUKA YI UZURIN DA YA GITTA MIN MAI GIRM ne .
A gaskiya bana jin daɗin ku masu karatu ta yadda bakwa musayan ra'ayoyin ku hakan ma na ɗaya daga cikin abunda ke duƙusar ni daga nayi yunƙurin yin typing sai nace "ah to yaya zan matsa kaina Alhalin ba'a nuna yabawa ? Sai kawai na ajiye na fuskanci wani lamarin da ya zarta haka , da fatan kun fahimceni za kuma kuyi duba izuwa koke na ?
Nagode '
[2/27, 9:35 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
(Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
51
Da baya-baya Falmata ta fara taku tana jin wani tsoro-tsoro daga ƙasan ran ta kafin ta juya da hanzarin son gujewa haɗuwar su da ita da mamallakan muryoyin da ta ji suna kitsa sharri da bata kai ga sanin su waye ba .
Sai dai taku biyu kawai tayi ta ji an fisgo rigar ta ta baya da matuƙar ƙarfi da ba domin rigar tana da faɗi ba da babu abunda zai hana ta yagewa bayan ta jefar da ita a ƙasa warwas .
A tsorace ta juyo da taimakon hasken lantarki suka yiwa juna kallon tsakar ido tsakanin ta da Hajiya Mama ,
Ba tare da Hajiya Mama ta saki rigar Falmata ba tana ƙanƙantar da idanun ta da suke cike da tashin hankali tace "wacece ke ? Me kuma kike nema anan ? Wa ya aiko ki ? Sannan me kika ji ana cewa ?
Falmata ta kif-kifta idanun ta da basu cika karfi ba kafin ta fara kici-kicin kwacewa cike da dakiya a muryar ta tace " Ni ce Falmata , matar unh ' Umh Yarima Youssouf Abdoul-aziz , kuma ki sake min riga ta na tafi .
Wani irin zillo Hajiya Mama tayi a take gumi ya karyo mata ta shiga juya kan ta daga ɓangaren hagu zuwa dama baki ɗayan jikin ta tsuma yake .
Idanun ta da suka fir-fito a halin yanzu su ta gwalalo cikin kufcewar nutsuwar ta ta shiga jijjiga Falmata da wata muryar da ta fi kama da raɗa take cewa "Annamimiya ke kuma salon ki kenan ? Da salon da kika zo kenan ?? Lalle kin yi kuskure mafi girma da da ɗai wallahi baki sake maimaita makamancin sa .
Juyawa tayi tana jaan ta ita kuma tana turjewa , cikin ɗakin da suka fito ta koma jaye da ita tana shiga ta ingiza ta ba tare da ta kula da cikin jikin ta ba da sauran ƙiris ta faɗa kan cikin ba dan ta riƙe gadon da ta samu damar ƙarasawa gaban sa ba.
Hafsatouwa da tuntuni bata samu damar cewa kome ba illa fargaba da ita ma ya cika mata ciki maƙil jin wacece Falmata , da matsayin ta a gidan da kuma alaƙa mai girma da take da shi da zancen da suke tsakiyar yin sa ita da uwargijiyar ta da babu shakka Falmata ta ji kome .
Tana shiga ɗakin ta rufe ƙofar ta murza ɗan makulli da hanzari ta juya jin sautin mari da ya karaɗe ɗakin .
Akan Falmata ta sauke ganin ta wacce ta durƙusa akan guiwar ta riƙe da ƙuncin ta da Hajiya Mama ta zage iya ƙarfi ta mare ta .
Sake chakumota tayi ta ɗaga ta tana sake chukui-kuiye ta tace "za ki faɗa min me kika zo yi nan wajen a dai-dai wannan lokacin kuma wa ya turo ki ? me kuma kika ji ina cewa ? ko kuma sai na shaƙe ki kin mutu ?
Falmata da zuwa lokacin hawaye ya gama wanke mata fuska zuciyar ta kuma ta cika da tsoro cikin rawar murya tace "wallahi ban zo yin kome ba kuma ba wanda ya aiko ni nan , mantuwa nayi na kasa gane hanyar komawa sashin da aka sauƙe mu saboda tunda muka zo ban taɓa fita ba kuma kin ga idona , idona wallahi bana gani mai kyau dan Allah kiyi haƙuri ku mayar dani sashin da Hajja take .
"Ƙarya kike yi munafuka , me ya fito da ke a daren nan idan da gaske dindimin kike yi ? Baki bani amsa ba me kika ji muna tattaunawa nace ? Kuma uban waye yace ki min laɓe ?
Mukut ! Falmata ta haɗiyi yawun tsoro cikin rashin sanin takamaimai amsar bayawar tayi shiru .
Cikin rashin sanin ta shirun da tayi shi ya basu tabbacin ta ji kome , abunda suke gudun kuma yana gaf da faruwa watau fallasuwar asirin su .
Falmata bata ankara ba taji sauƙar wani marin kafin tayi wani yunkuri ta ji sauƙar duka da dundu ta ko'ina kusan gabadaya Hajiya Mama bata hankalin ta dai duka kawai take kai mata .
Ihun da Falmata ta buɗe maƙogoro ta rafsa shi yasa Hajiya Mama dakatawa daga dukan ta , idanun ta jawur ta juya ga Hafsatouwa tace "Hafsatouwa tai ki ɗauko min wuƙa mai kaifi ki kawo min .
Da gudu Hafsatouwa ta miƙe daga durƙuson da tayi ta fita .
Cak Kukan Falmata ya tsaya ta shiga wara idanun ta da ganin su ya sake yin ƙasa saboda kukan da take yi , ta fara taku tana laluben hanya so take tayi wani yunkurin tseratar da kan ta .
Fizgota Hajiya Mama ta sake yi ta warɓar da ita a bakin gado da muryar da take cike da bushewar zuciya tace "ƙwarmato kike yi min ? Kina son tara min jama'a ? Yarinya baki sanni bane , amma za ki sanni dagga lokacin da na guntule miki halshe .
Cikin neman agaji Falmata ta zube guiwar ta a ƙasa dai-dai da dawowar Hafsatouwa da take riƙe da wata sharɓeɓiyar wuƙar yanka dabba a cikin kuɓen ta
hawaye na tsiyayo mata ta haɗa hannuwan ta biyu da sigar migiya tana cewa "Hajja dan Allah kiyi hakuri ki barni na tafi wallahi duk abunda naji ba zan faɗawa kowa ba , wallahi bazan faɗa ba , kiji tausayina ki ƙyale ni ko dan abunda ke cikina .
"Ki min shiru hegiya , ina ruwana da hegen cikin ki ? Kar na kuma ji kin ƙira ni ba suna na Hajja ba .
"faɗa min me kika ji ana cewa ? Maimaita min idan kuwa kika min ƙarya sai na yanka ki billahil azim.
Tiryan-tiryan Falmata ta maimaita musu hirar su kamar yadda ta haddace akan ta ba kalma guda da ta manta duk a ƙoƙarin ta na son suyi mata afuwa bata tsaya da bayani ba sai da ta dire sannan ta ɗora da cewa "wallahi shikenan abunda naji kuma nayi Alƙawarin bazan faɗawa kowa ba .
Sai dai tunanin ta ya tsaya chak lokacin da Hajiya Mama tayi wata gajerar dariyar da ke bayyana irin halin ɗimuwar da take ciki.
"Bayan duk kin ji wannan sirrin nawa da mutane uku ne suka san shi bayan ni a din duniya ? Sirrin da 'ya'yan cikina ma basu san shi ba , sirrin da yake ginshiƙi na rayuwata baki ɗaya , da na ta'alaka duk wasu nasarorina akai , shine kike tunanin zan bar ki ki tafi ? Na barki ki tafi kiyi rayuwa a cikin gidan nan ɗauke da sirrina a hannun ki ? Ko a hankali irin naki na dabbobi hakan abu ne da zai yiwu ?
Wata dariya ta sake yi kafin tace "yarinya wannan ba mai yiwuwa bane dole nayi abunda zai sa na kuɓutar da sirrina da yake hannun ki ...
"Wallahi Hajja bazan faɗawa kowa ba .
Falmata ta furta hakan tana sharar hawaye da rigar ta .
"Ni da kaina zan goge shi daga kan ki ko da kuwa ace hakan ba zai samu ba sai na raba kan ki da gangar jikin ki ne '
"Hafsatouwa ban wuƙar nan .
Da sauri ta miƙa mata ta sake komawa tana Sake jaan labulen windows din dakin.
A hankali Falmata ta ɗago kai zuwa lokacin ta karaya cikin ran ta ta saddaƙar mutuwar ta ta kusanto ,
Idanun ta ta sauƙe akan Hajiya Mama , tana jin yadda zuciya da ƙwaƙwalwar ta ke adana hoton kamannin fuskarta , a matsayin matar da zata raba ran ta da gangar jikin ta .
Fitsarin da take riƙewa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 96 Chapter of 111