sai yanzu ya ɗauke ta a shirye take tsaf ta sha kayan sanyi irin na alfarma tayi kyau matuƙar gaya .
Ɗora mata ita yayi a jikin ta bayan ya ɗan ɗago mata gadon sai ya zauna tana jingina da jikin sa daga shi har ita tsurawa jaririyar ido su kayi suna ganin tsananin kamannin ta da Mama kamar lokacin da aka haife ta , marabar su kawai wannan tana da girma kuma tafi Mama gashi bayan hakan za'a ce Mama ce kawai Allah ya dawo musu da ita .
A hankali ta ɗago ta sumbanci kumatun ta dama da hagu da yasa ta motsawa a hankali tana ɗan yamutsa fuska irin na jarirai.
"Yakaka na ɗauke ta ,Yarinya ce mace Mai tsananin kama da Mama , Allah ya dawo mana da Mama Yakaka.
Daga can murmushi mai sauti Yakaka tayi tana jin ƙaunar 'yar da bata kai ga ɗora idanu akan ta ba na samun wajen zama na musamman a cikin ran ta a lokacin ji take kamar tayi tsuntsu ta je ta gan ta ta ɗauke ta ta riƙe a hannun ta ta rungume ta a ƙirjin ta ta gwada mata ƙauna a matsayin ta na uwa a gare ta ba wai Yayar uwa ba kawai ɗiyar Falmata ɗiyar ta ce halak malaƙ .
"Allah ya raya ta Falmata , Allah ya mata Albarka , Yaa Allah yasa ta amfanar da Al'ummar musulmai ajiye wayar ki ɗaga ta ki shayar da ita anjima zan sake ƙiran ki .
"Amin Yakaka .
Daga haka Doctor Hamza ya zare wayar daga kunnen ta ya kashe kafin ya jaa ta cikin jikin sa ya rungume ta tsam suna musayar jin ciwon rashin nasu gudan jinin da suka yi .
Sumbatar goshin ta da Youssouf yayi bai sa ta janye idanun ta daga kallon fuskar 'yar ta ba da take jin wani abun da ya zarce a ƙira shi da So sannan kuma ya wuce ƙauna tasiri yana bin duk wani sarari na ran ta yana dasa wani al'amari mai girma ji take kamar ta tsaga ƙirjin ta ta sa ta .
Wai yau ita Falmata ce take riƙe da 'yar ta ta cikin ta babu shakka Allah shine mafi girman Abun Godiya "Alhamdulillahi Yaa Allah .
Ta furta hakan a sarari tana jin wata ƙwallar farin-ciki na cika mata gurbin ido .
A hankali Youssoufa ya kai hannu yana ɗauke 'yar daga jikin ta bata yi wani yunƙuri ba illa bin su da tayi da ido cikin ran ta bata mamakin yadda ya iya ɗaukar jariri saboda tun akan Mama ta san ya ƙware .
Addu'o'i ya shiga yiwa 'yar sa tsawon mintoci fiye da talatin dan tun Falmata tana kallon su har ta ɗan fara gyangyaɗi .
Hannun sa da ya shafa mata kumatu shi yasa ta buɗe ido da kyakkyawar fuskar sa tayi arba yana mata murmushi kafin sautin sa ya sauƙa a kunnen ta "Mon Bébé kina ji na ?
A hankali ta gyaɗa masa kai idanun ta cike da baccin gajiya suke lumshewa sai dai kalmar da ya faɗa ya sa ta wara idanun ta da sauri ta dube shi tana son sake jin me ya ce ?
"Wanne Suna kin ka zaɓarwa ɗiyar mu na bar miki zaɓi dan saboda kawai na gwada miki kaɗan dagga farin-cikin da nake ciki.
"Da gaske kake ?
Ta tambaye shi tana narkar da idanun ta cikin nasa .
"Da gaskiya Fatima na bar miki zaɓin sunan ɗiyar mu mai darajja '
" a sa mata Yakaka .
Sautin da ya taso daga ƙasan ran ta ya subto akan laɓɓan ta .
Shiru yayi yana kallon ta kafin yayi magana ta katse shi ta hanyar cigaba da cewa "indai dai har ka bani zaɓi to a sa mata sunan Yakaka Yayata .
"Babu shakka ta cancanta domin kuwa ita ce Mafarin silar haɗuwar sa da Fatima-zahra ba domin ita ba da bai samu Fatima ba bare har ta haifa masa 'yar da yake riƙe da ita yanzu a hannun sa a ƙarshe kuma ita ɗin uwa ce ga 'ya mafi soyuwa a gare shi da har abada baya zaton za'a samu mafiyin ta wajen matsayi a cikin 'ya'ya .....
Tunanin sa bai yanke ba ya juyo yana fuskantar Falmata riƙe da Babyn a hannu yace "Meye Sunan ta na ainashi..?
Cike da zumuɗi Falmata tace "sunan ta Amina.
Bai ce ƙala ba sai ya sake mayar da kai ga yiwa 'yar sa addu'a kafin bayan ɗan gajeren lokaci ya ɗago kan sa yana mai ɗora mata 'yar a jikin ta yace
" Sunan 'yar mu Amina riƙe ta da kyau 'ya ce a gurin ki sannan kuma 'yar uwa.
Da hannuwanta biyu ta rungume ta tana jin yanayin da yafi na ɗazu yana danne ta ta kasa tsayar da hawayen farin-cikin da yake sauƙa fuskar ta kamar yadda ta kasa ɗauke ido daga fuskar Amina .
Haka ma Biyamuradi Youssouf da yake tsaye akan ƙafafun sa hannuwansa duk biyu a zube cikin aljihun sa yana murmushin da yake bayyana haƙoran sa ya kasa janye ganin sa daga kan su kamar yadda yake jin ƙaunar su biyun tana fisgar sa tamkar wanda guguwa ta riska a tsakiyar rairayin hamada .
***
Daga nan ɗakin da Falmata zata cigaba da zama kafin a sallame ta aka kai ta bayan nan Hajiya Umma da har yanzu bata tafi gida ba ta shiga inda suke ta mata sannu sannan ta sake mata addu'a ita da Amina kafin ta bar asibitin .
Sai kuma ta fara amsar waya daga Iyaye da dangin ta na Nigeria har dai zuwa lokacin da likitoci suka buƙaci da a bar ta ta samu hutu mai yawa kar a takura ta.
***
Daga lokacin da Doctor Hamza ya ga har dare yayi bai ji wani labari ba daga iyayen sa sai ya fahimci Sofi ta rufe zancen duk abunda ya faru bata faɗa ba .
Dan haka shi sai ya yanke shawarar sanar da iyayen su da kansa dan haka a daren ranar bayan sallar isha'i ya hada conference call da Baba Prof da Amne da Khaalty Rahima da Momy Kori da shi kan sa Baban Sofi.
Bayan duk ya gaishe su sai ya nemi da su bashi dama zai musu bayani.
Nan ya shiga basu labarin duk yadda kome ya wakana a tsakanin sa da Sofi tun daga farko har ƙarshe .
Kafin ya gama Sallallami da kukan Momy kori tare da Amne ya cika wayar .
Sai da kyar Baba Prof ya sa suka yi shiru domin shi da kansa Baban Sofi ya gaza cewa kome kawai kamar ruwa ya cinye shi saboda tsabar shiga razana da muzanta shi da Sofi tayi.
Ɗan taƙaitatcen Bayani Baa yayi akan lamarin da ɗari-cikin-ɗari ya goyi bayan hukuncin da Hamza ya ɗauka ya ɗora da cewa "tunda har dai abu ya zama da neman aikata kisan kai to babu shakka ba amfanin zaman rabuwar ita tafi dacewa.
Matsanancin kuka Momy Kori ta sa cikin rishin kuka take sanar da su cewa ita har kawo yanzu ma da ake wannan maganar bata ga Sofi da idanun ta ba Sofiya bata zo gida ba to ina ta tafi ?
"Ta tafi ko'ina ma Kori , ina mai tabbatar miki da cewa Safiya ba za ta zo ta zauna min a gida ba domin nima ba zan zauna da mashayiya kuma makashiya ba tunda irin rayuwar da ta zaɓarwa kan ta kenan to tafi duk inda za ta tafi tayi rayuwar ta amma ni dai ban amince ta zo gidana Alhaji ka shaida ni na cire Safiya daga cikin 'ya'yana' ku kuma ina mai baku haƙuri kan abunda ya faru ita yarinyar ma dan Allah a bata haƙuri ita da iyayen ta .
Daga haka Baban Sofi ya yanke ƙiran daga ɓangaren sa .
Duk son kai irin na Momy Kori yau sai ta gaza kare 'yar ta haka tana ji tana gani saki Uku ya tabbata tsakanin Sofi da Hamza sannan kuma dole ta bada haƙuri ga su Amnee da shi kansa Doctor Hamzan da ya rasa gudan jinin sa sannan ta ajiye wayar .
Daga nan suka cigaba da jimantawa tsakanin sa da iyayen sa inda Amnee ta nuna son Yakaka ta zo gida a kula da ita amma tun ma kafin ta gama magana Baba Prof ya nuna rashin amincewar sa hujja da cewa ai shi Hamzan likita ne dan haka zai fi kowa lura da ita dole Amnee ta haƙura ita kuwa Khaalty Rahima daman bata cewa kome sai addu'a kawai tayi ta danne duk wata damuwar ta saboda kara .
Daga nan aka yanke shawarar cewa jibi Amnee da Zainab za su tafi Abujan daga nan su haɗu da hafsa idan sun duba Yakaka da jiki daga nan sai su dawo Kano su wuce Niger gurin Falmata .
Su Hafsa zasu dawo bayan suna Amnee kuma za ta ɗan yi ko da sati biyu ne tana kula da Falmatan .
Kafin kwanaki biyu zance ya gama baza dangi kan abunda Sofi ta aikata na yunƙurin kashe kishiyar ta kuma ta gudu ba'a san inda take ba.
Amnee sun je Abuja tare da direban su a babbar motar da Amnee ta cika kusan rabin ta da kaya .
Sun kwana a gidan Doctor Hamza ta sake rarrashin takwarar ta Yakaka sannan ta bata kayan gyara da tarin wasu turarurruka sannan ta sanar da ita sakon Prof da yace cikin satin nan za'a zo a shirya mata kayan ta a gidan .
daga nan kuma sai suka wuce Maradin Niger da tarin kayan ƙamshi da gyaran jiki tare da kayan jarirai masu kyau da tsada da Amnee tayi tanadin su musamman domin Falmata da zata haihu kayan gyaran tafiyayyu ne daga Chad .
Can a Maradi suka ga tarba irin ta saraki sai nan-nan ake da su ana sauƙe musu kabbakin arziki.
Daga Zainab har Hafsa sai da suka yi santin kyaun sashin Falmata da irin gatan da ake mata babu abunda yafi burge su irin tarin hadiman da take da su da ko yaya ta motsa sai sun mata sannu girma irin ta sarauta sai gidan sarauta .
Lokacin da Yakaka ta samu labarin cewa jaririya Sunan ta ta ci har sai da tayi kuka dan farin-ciki .
Doctor Hamza ma ya ji daɗi ya kuma musu fatan Allah ya ƙara musu zumunci a ƙarshe yayi alƙawarin daga ya ɗau hutun sa nan da wasu watanni cikin shekara mai zuwa zai kai Yakaka har Niger ta gano takwarar ta .
Ranar suna kuwa Al'umma da suka taru ba'a ce Falmata bata da dangi a Niger ba.
A gurin taron suna dangin suka dunga tsurkun tururuwar zuwa duba Hajiya Mama wacce jinya ta sarƙe ta sakamakon wasu munanan ƙuraje da suke feso mata duk a ƙafafun ta bayan hawan jini da ciwon zuciya da suka mata rubdugu bata ko iya tafiya gaba ɗaya rayuwa ta mata juyin waina a tanda .
Kowa ya fito daga sashin sai yayi gulmar sakayya ce take gani tun daga nan duniya .
Wacce irin ta Maimounatou ɗiyar sarkin Agades ma ta samu sakamakon mutuwa da Mahaifin ta yayi a tun jinyar da ya afkama sanadin mummunan abun kunyan da ta aikata kan yunƙurin kashe Mijinta a halin yanzu kuwa rayuwa ta mata atishawar tsaki batta ga tsuntsu batta ga tarko .
'Yayan Hajiya Mama kansu gaba ɗaya basu da sakewa a cikin taron sunan duk kuwa da cewa sun zo sun kuma kawo kayan jaririya da na uwa irin na alfarma .
Da kaya sai da Falmata ta rasa gurin zuba su tsakanin wanda Mijin ta tayi mata da wanda iyayen sa suka mata da wanda Iyayen ta suka kawo mata da kuma na 'yan uwan sa ga kuma na dangi da abokan arziƙa .
***
Bayan suna da Zainab da Hafsa da zasu koma kayan niƙi-niƙi aka haɗa Su da shi .
Ita kuma Amnee ta zauna kula da Falmata da ta dage tana lura da ita saboda haihuwar da tayi wani ɗam rami na musamman na turara jiki ta sa aka mata a cikin uwarɗakin Falmata kamar yadda al'adar su take su basu cika shan magungunan na mata ba sai gyaran jiki tsaftar sa da ƙyalƙyale fata suka fi bawa muhimmanci .
Gefe guda kuma ita ma Hajja ta dage da nata gyaran irin na matan ƙasar Hausa da su kuma suka fi bawa shan kayan ɗa'a muhimmanci .
Kafin sati biyu Fatar Falmata ta zama kamar bayan tarwaɗa yayin da wani fitinannan ƙamshi ya zauna mata a jiki 'yar kiɓar shayarwa da tayi ta amshi jikin ta sai ta koma kamar irin hamshaƙan matan nan da suke kan ganiyar ƙuciyar su duniya kuma ta juya hasken ta akan su tana haska su .
Bayan cikar sati biyu da kwanaki biyu Amnee ta koma Nigeria inda ta je ta tarar da labari mafi daɗi da Prof ya tare ta da shi kan ya samarwa da ƙanwar sa Rahima Miji .
***
Sheikh Mukhtar ɗaya ne daga cikin jerin ƙannen abokansa da bai yasar da zumunci ba ko bayan mutuwar wansa yake ziyartar sa lokaci zuwa lokaci muddin ya shigo garin Maiduguri daga can ƙasar Saudi-Arabia da yake aiki da zama tare da iyalin sa sama da shekaru ashirin da yayi aure.
Wannan zuwan nasa lokacin da Prof yake tambayar sa iyalin sa yake shaida masa ita matar tasa ta rasu shekarar da wuce .
Prof ya masa ta'aziyya bayan nan ya shawarce shi da kar yayi jinkirin yin wani auren saboda shi aure ibada ne sannan kuma kariya ne .
A lokacin Sheikh Mukhtar ya nuna masa cewa har kawo yanzu dai bai samu matar da ta kwanta masa ba wacce ya yarda da hankalin ta da zai iya danƙa mata amanar tarbiyyar 'ya'yan sa da matar sa ta mutu ta bar masa su huɗu .
Sannu kan hankali cikin dabara irin ta manya Prof ya gabatar masa da Khaalty Rahima cikin sa'a da ganin girman sa Sheikh Mukhtar ya nuna amincewar sa ɗari bisa ɗari muddin dai ita ma ta amince da shi .
Lokacin da aka sanarwa da Khaalty Rahima batun Sheikh Mukhtar bata ƙi ba tunda dai iyayen-goyon ta sun amince ita kuwa me zai ta tayi gardama idan tana da damuwa ɗaya ce ji da tayi ƙasar za ta bari gaba ɗaya ta bar Bulama dan ta sauran 'ya'yan ta mata ta san Allah ya riga ya sanya mata su a hannun nagartattun Mazaje '
Damuwar ta Bulama ne da ya shaƙu da ita fiye da misali sannan babu wani dangin sa na uba da aka samu ɓullowar su har kawo yau duk kuwa da neman da aka ta yi saboda har kawo yau da ake ɗiban shekaru fiye da bakwai da tarwatsa musu gari da 'Yan tawayen Boko Haram suka yi alƙaryar su bata sake kafuwa ba an riga an shafe ta mafi yawan mutanen su kuma sun mutu da take hasashen ciki har da mafiya-yawan dangin Uban su Yakaka da daman ba wani yawa suka cika ba ƙaramar zuri'a ce da su masu gajeran baya .
Duk da ba wai shakkun Bulama zai wahala bane idan har ta bar shi a hannun Amnee sai dai tasirin tsakanin uwa da ɗa ne musamman waɗan da suka shaƙu ya haka raba tsakanin su ba ƙaramin abu bane sai ko Mutuwa .
Ga jin daɗin ta kuma lokacin da suka yi ganawar farko da Sheikh Mukhtar shi da kansa ma ya mata batun riƙon Bulama zai dawo hannun sa daga zarar sun yi aure .
Da yake lamarin ba wai na yara bane cikin satika uku har magana tayi ƙarfi inda nan da satika huɗu mai zuwa za'a ɗaura auren idan ya tashi tafiya nan da watanni biyu ya tafi da Matar sa da ɗan su .
Bayan watanni shida.
Maradi Niger
Siyama tare da Falmata ne tsaye suna Sallama a jikin motar da Biyamuradi Youssoufa yake lafe a ciki yana riƙe da Amina wacce Falmata ta mata laƙabi da ( Ukhtee ) take ƙiran ta haka da kuma sunan ya bi bakin jama'a kowa ma hakan ke ƙiran ta.
Jin Sallamar tasu taƙi yankewa yasa Youssoufa leƙo kan sa yana cewa "Siyama kin ka ce yau aikin rana kin ka tahi yanzou kouwa ga hantsi ta ɗagga ko kouwa kin fara wassa ne da aikin naki ko kouma kin gajiya ne za ki bari dagga farawar ki.?
Da sauri Siyama ta saki hannun Falmata da ta riƙe jin cewa Biyamuradi Youssouf ya sako maganar aikin da da kyar yarda ta nema ta fara zuwa har sai da Maimartaba ya sa baki yace aikin ta na ceton rai ne sannan tun tasowar ta burin ta ne ta zama likitar haƙora ƙaƙa zai hana ta bayan shi ya san daɗin samun cikar buri a rayuwa tunda shi ma babu wanda ya katse masa nasa burin na zama Babban Soja mai yiwa ƙasar sa hidima .
Ba yadda ya iya haka ya haƙura aka samar mata da aiki a babban asibitin jaha tare da sharaɗin ba ita babu bin sa jaharTahoua sai dai shi zai dunga zuwa kamar yadda suke yi a tun can baya .
Babu jaa Siyama ta amince saboda ranta ya afu ga son taimakon Al'ummar ta itama lokaci yayi da za ta bayar daga ilmin da Allah ya hore mata falalar sa .
Baya tayi tana jaan mayafin ta ta rufe cikin ta da ya fara girma da yake nuni da nan ba da jimawa ba Ukhtee za ta samu ƙani ko ƙanwa .
"Ƙamnata Allah shi kiyaye mukku hanya hirar mu ba mai yankewa ce ba ina dai sake faɗa miki dan Allah dagga kin koma ecole ki dagewa karatu kiyi zarra ga abokan karatun ki hakan zai zama abun alfahari ne a gare mu.
Falmata tana murmushi ta amsa da "Insha Allah ba zan baki kunya ba Docteur Siyama nan da wassu 'yan shekaru ƙamnar ki zata zama diplômée.
"Allah shi badda sa'a ƙamna ta.
"Amin .
ta amsa tana shigewa Mota direba ya jaa suna barin gidan , Falmata ta waigo tana miƙa hannu domin ɗaukar Ukhtee da take ta tsalle a jikin Baban ta tana wasa girman jikin ta da wayon ta sun wuce na watannin ta shidda sai dai a kai ta watanni goma .
Noƙewa tayi tana ƙin zuwa ta faɗa jikin Baban ta da sauri tana ƙyaƙƙyala dariya irin ta yaran da lafiya da jin daɗi ya wadace su .
A lokaci ɗaya iyayen nata su ma suka sa dariya suna bin ta da kallon dake cike da ƙauna Falmata ta ɗan jaa kumatun ta "Ukhtee yau ni kike yiwa ƙyauya ? Ai anjima kaɗan za ki zo ne .
Shafa kan ta Youssoufa yayi wanda ya sha adon ribbons irin na yaran gata da ya dace da lallausar sumar kan ta mai tarin yawa da yake sake fiddo kyaun ta da ido bai gajiyawa wajen kallon ta.
"Ki rabbu da ita Fatima kin iya shigga tsakanin ɗiya da Mahaifin ta ?
Girgiza kai Falmata tayi tana mai matsowa jikin sa ta kwantar da kan ta ta ɓarin jikin sa na dama ita da ukhtee fuskokin su na kallon juna akan ƙirjin sa .
Haɗa su yayi ya rungume bayan ya sumbanci kan Falmata da yake ƙirjin sa. "Fatima-zahra ina son ku irin son da ba shi da iyaka.
"Biyamuradi Youssoufa mu ma haka muna ƙaunar ka irin ƙaunar da bata da iyaka.
Direban da yake iya jiyo sautin su sai ya ƙara volume ɗin radio da waƙar matashiyar mawaƙiyar nan camelia jordana mai taken mens moi take tashi cikin baitukan ta inda take cewa :
"Je rougis je rougis je rougis
Quand tu me souris
Ô tes yeux menthols
Me mentent et m'affolent
"Oh mens-moi si tu m'aimes
Mais me manque pas
Me manque pas
Me manque pas
"Je défaille à tes mots fous
Mots doux vaudous
Quand je suis dans tes bras
Hé dis, tu penses à quoi ?
Abuja
Sofi lokacin da ta bar gida bayan ta ci uwar wahala kafin ta samu ɗan tasi ɗin da zai yadda ya ɗauke ta taje ta sayar da ɗankunnen gwal ɗin da ya rage mata tal a kunnen ta ta biya shi kuɗin sa .
Daga nan wani ɗan ƙaramin hotel mai sauƙin kuɗi ya kai ta ta kama ɗaki ta shiga ta zauna a cikin dabarar ta da tayi niyyar ƙullawa na rufewa kowa maganar saki ukun da Hamza ya yi mata har sai zuwa lokacin da aikin boka ya ɗau wuta akan Hamza shi da kansa ta san zai fara neman ta daga nan idan ta gama wana shi ta rama duk irin cin mutumcin da ya mata sai ta nemi da su rufe zancen sakin a tsakanin su kada kowa ya ji su koma su cigaba da zaman su..
Tasha alwashin sai ta walakanta rayuwar Yakaka dan ta ma fasa kashe ta da wuri sai ta mata gashin ƙuma sannan za ta ƙarar da numfashin ta a doron ƙasa..
Kashe wayar ta tayi ta kwanta amma ta gagara bacci saboda tsamin da jikin ta yayi yana mata ciwo na fitar hankali .
Dole ta sa ta tafi asibiti aka bata magunguna ta zo ta sha .
Daren ranar haka ya ƙare mata tana surutan iska .
Washegari kuwa da farar Safiya ta dasa zaman ƙiran Samy Baby sai dai layi ya ƙi shiga wasa-wasa sai da ta shafe tsawon yinin ranar da waya a hannun ta tana ƙiran layin da Samy Baby ta ƙira ta da shi har wayar chaji ya ƙare ta mutu bata samu ta shiga ba
Ta lallaɓa ta sayo kan chaja ta zo tasa bata jira wayar ta cika ba ta dasa daga inda ta tsaya wajen ƙiran layin Samy Baby .
Kafin cikar kwanaki uku Sofi tayi ƙaramar hauka a ɗakin otel saboda dai babu wani saƙo daga Samy baby babu alamar sa kuma ita ta gagara samun ta sannan kuma ko alama bata ga ƙira daga wani nata ba da da har kashe wayar take dan kar a ƙira ta.
Doctor Hamzan da take hasashen aiki ya fara cin sa kuwa duk lokacin da taga alamun Kamfanin Sadarwa sun tura mata saƙo zato take shine .
Haka zata yini sambatun ƙiran sunan sa.
Kafin cikar Sati kuɗin hannun ta ya ƙare da daman fiye da rabi zama take da yunwa tana biyan kuɗin ɗakin da take kwana .
Ala tilas ta fita daga Otel ɗin kawo yanzu kwakwalwar ta ta ƙara birkicewa ta kasa yarda da abun da ya faru da ita yake kuma sake faruwa da ita .
Ciwon mazaunan ta da suka ɗuri ruwa tun ranar da ta yanke shi yafi kome ɗaga mata hankali saboda azabar da take sha kullum dare bata iya bacci .
Ba arziƙi ta kama hanyar gidan su a birkice kamar sabuwar mahaukaciya .
Da zuwa zata sake dasa sabuwar ƙarya ta tarar da ashe tuni kome ya jima da kwaɓe mata asirin ta ya daɗe da tonuwa kowa kuma yasan abunda ya faru abunda ta aikata da irin hukuncin da Hamza ya yanke mata .
Babban tashin hankalin ta yadda tana ji tana gani Baban su da ya dawo ƙasar kwanaki biyu da suka wuce ya kore ta a gidan bayan ya ƙare mata tanadi .
Gidan wata dangin dangau ɗin Hajiya Kori da take mata kore a can irin unguwannin kusa da ƙyaukan Abuja nan Hajiya Kori ta sa direba ya kai Sofi ba tare da sanin Mahaifin ta ba domin idan ta shi ne kawai Sofi tayi tafiyar ta Momy kori ta ce ta zauna a can kafin Baban ta ya huce ya saurare ta .
Bata haƙƙaƙe da babu wata sa'a da ta rage mata a rayuwa ba sai da aka shafe fiye da kwanaki arba'in tana ƙirgawa babu Samy Baby ba labarin ta .
Zuwa lokacin ta haƙiƙance cikin biyu ɗaya ne ko dai Samira ta yaudare ta ta mata damfara ta gudu a duniya ko kuwa ta gamu da mummunan hatsarin da ya rutsa da rayuwar ta a can india ba tare da an mata aikin da ta aiketa yi ba .
Ƙurunƙus sai gaba ɗaya mummunar zuciyar ta da shaiɗan da bai riga ya gama cika aikin sa akan ta ba suka cigaba da mata raɗa cewar ai babu wani amfanin da rayuwa za ta iya sake mata nan gaba .
Dan haka sai kawai ta afkama shaye-shayen miyagun ƙwayoyin da basu cika tsada ba sai mugun aiki dan da haka kaɗai take iya samu ta hasko kan ta a irin rayuwar da ta kwashi shekaru tana tsarawa a kan ta ita da Doctor Hamza.
Kafin wasu watanni ta yiwa rayuwar ta illa ga kuma ciwon da yake daɗa cin jikin ta gaba ɗaya ta sururuce ta koma
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 110 Chapter of 111