ta dawo kusa da Falmata ta zauna , gani na farko da ta yi mata ta ji ta burge ta ,tana ƙaunar ta musamman da ta gan ta yarinya kamar ma zata girme mata .
"Nagode , Falmata tace tana 'yar dariya idanun ta ta sauƙe kan Yumna da aka mata Shimfiɗa da wani lallausan bargo daga gefe tana ta baccin ta da alamun gajiya a tattare da ita ,
" tayi bacci ne ?
tace da ƙaramar murya ,
Murmushi Siyama tayi tana cewa "ɗiyar ki tayi baccin gajiyar hanya bata saba ba , ga shi kouma baku ko gaisa ba da alama dai yau a ɗakin ki zata kwana da dare idan ta farka kun gaisa ...
"Da gaske ?
Falmata ta furta hakan tana dariya cikin zumuɗi ta ɗora da cewa
"bata ƙuiya sosai ko ? Ba zata yi rikici ba ko ? Tunda bata sanni ba Bana so tayi kuka .
Siyama tana murmushin jin daɗin ganin zallar ƙaunar 'yar ta a fuskar Falmata tace
" A haka zaku saba ai 'ɗiya ba ta ƙi mamar ta ba...
Kafin ta ƙarasa faɗin abunda tayi niyya Muryar Ammi ta katse mata zancen ta ta hanyar cewa .
"So kike tayi ta ihu kenan ? Wannan ai ɗaukar hakki ne ki bar 'yar ki a katarar ki sai yafi alheri .
Shiru wajen yayi na ɗan wani lokaci kafin muryar khaalty Rahima ta ratso wajen fuskar ta da ɗan murmushi tace
" gaskiya kam bare ga baƙunta ga baƙuwar fuska abun zai zama bibbiyu , gara ta zauna a wajen Mamar ta cikin Alheri .
" Yakaka da ta lura da sanyin da jikin Falmata yayi sai tace " Falmata da son yara kike wallahi, anya ma kuwa za ki yarda a ɗau naki , zamu gani ai lokaci kaɗan ya rage ke ma ki riƙe naki a hannu inshaAllah .
Mairamar sarki ma da abunda yayar su ta ta so yi ya ɗan sanyayar mata da jiki sai tace
" ai kuwa ni ce mai raino dole ma ta ba mu ɗan mu ko 'yar mu ko mon beau-père ?
Dariya Siyama tayi tana waskewa hararar da Ammi take jefo mata ta ƙasan ido tace
" ɗakina ai nan ne wajen ajiyar kayan sa , ni zan dunga shirya shi , kafin a yaye shi daga an yi yaye kuma zai dawo wajena gabaɗaya sai dai Mamar su ta kawo mana wasu kuma .
Amnee ce katse musu hirar da suke yi lokacin da ta ce , " Aisha raka ta ta gaishe da baƙi a sashin Baban su .
Bayan dawowar su daga gaishe da su waziri Falmata bata tsaya a falon ba ta musu sai da safe kawai ta shige ɗaki , tana warware lafayyar jikin ta zuciyar ta na ga tunanin bata gan shi ba ,Ina yake ? ko dai bai zo bane ?
Gabaɗaya sai ta nemi ɗan farin-cikin da ta tsinci kan ta ciki ta rasa da daman zuwa yanzu ta fahimci kusanci da shi da ta samu sanadin ganin 'yan uwansa da zaton ta tare suka zo zata gan shi shine ya sata murna .
A yanzu kuma da ta fahimci bai zo ba duk sai ta ji ƙunci na safko mata wani sashi na zuciyar ta taji yana raɗa mata , " Falmata ke fa kike damuwa da shi dan rashin zuciyar irin taki , shi bai damu da ke ba tunda ga shi ya ƙi zuwa wajen ki sai wasu ya turo wai su tafi da ke sai kace wata kaya , zuwan nasu da bai wani burge ta ba , a gurin ta da shi kaɗai tal yazo , ta gan shi suka yi komawar su tare da hakan ne zai sanyata farin-ciki akan waɗannn da aka turo ga shi tun a gaban iyayen ta ma wannan yayar ta shi sai wani hararar take , ko meyasa ta tsane ta ? Oho .
Mts
Tayi tsaki lokacin da take zama bakin gado , tana ƙoƙarin ture tunanin sa dake damun zuciya da kwakwalwar ta .
" Falmata na , ai damuwa kuma ta ƙare tunda ga 'yan uwan sa sun zo tafiya dake , za a mayar da ke gun angon ki mu huta da jin kukan ki da ganin ƙuncin ki "oh su soyayya manya .
Yakaka ta furta haka da dariyar tsokana lokacin da take ƙarasowa cikin ɗakin ,
Yamutsa Fuska tayi ta kawar da kai gefe kafin tace " waye yake cika miki kunne da kukan Yakaka bana so .
"Rabu da ita en loi , jibi war hakka kina cikin masarautar mu bayun ki na miki hidima daɗa ai ke ɗin sarauniya ce matar Yarima ,
Murmushi su duk biyun suka yi da ganin shigowar Aisha da ta cigaba da cewa
" kun yi waya da Biyamuradi ko ? Ya jikin na shi da sauki kou ? Ni dai nan tunda munka tasso da mun ka baro shiyar ƙasar mu Téléphone carte sim pas de service .
A hankali Falmata ta ɗago kanta zuciyar tana sauya bugu , da wani yanayi a muryar ta tace " Daman ba shi da lafiya ne ? Me ya same shi ?
Da sauri Aisha ta dafe kai tunowa da tayi da farkon zuwan su a can falon Prof bayan Waziri ya yiwa Prof taƙaitatcen bayani kan rashin lafiyar Youssoufa da shine dalilin da ya kawo jinkirin zuwan su , amma zuwa yanzu lafiya ta fara samuwa gare shi da yardar Allah , a ƙarshe suka daɗa neman afuwa tare da neman iznin tafiya da Falmata a gobe .
Prof ya jajanta musu sosai ya kuma yi musu addu'o'i sannan sai shima ya shigar da neman Alfarma kan a ƙara masa kwana guda tal a bar tafiyar tasu zuwa jibi , sannan kuma ya nemi da a sakayawa ita Falmata batun rashin lafiyar Mijinta tunda bata riga ta sani ba saboda halin da take ciki da ba'a son abunda zai tada mata da hankali .
A take duk suka yi Na'am da shawarar Prof kan cewa za'a rufe rashin lafiyar Youssoufa har sai Allah ya masa dawowa sannan kuma zasu ɗaga komawar su zuwa jibi .
"Aisha daman Youssouf jinya yake ?
Yakaka ta tambaya tana dafa kafaɗar Falmata da ta lura ta shiga damuwa sosai .
Da ƙoƙarin sauya akalar zancen Aisha tace " eh ,Ah ah ba wani ciwo bane ya dai tafi india ne , kai Mutanen Maiduguri kun ji daɗin ku ko'ina turaren wuta yana ci
Ta ƙarasa zancen tana musu nuni da ɗan burner da take cin turaren wuta a hankali .
" yayi tafiya ? Kuma kika ce ba shi da lafiya ne , dan Allah ki faɗa min mana ,
Falmata ta furta haka tana jin wani gagarumin tashin hankali na rufar mata , muryar ta har 'yar ƙyarma take yi .
Da sauri Aisha ta zo gefen ta ta zauna , ta dafa kafaɗar ta sannan cikin taushin murya da alamar rarrashi tace ,
" en loi kadda ki damou Biyamuradi ya shiga haɗarin rayuwa ne Amma Allah ya fidda shi , doumin kouwa yanzu yana samun lafiya sosai , cikin watan ga mai kamawa shi ke dawowa da yardar Allah kin ji kou ?
Gyaɗa kai kawai Falmata tayi daga haka ta miƙe daga tsakanin su , su duk biyun da kallo suka rakata har ta shige banɗaki .
Yakaka ta sauƙe ajiyar zuciya tana dawo da ganin ta kan Aisha , cikin yin ƙasa-ƙasa da murya tace .
"amma ciwon da yake damun sa ba mai tsanani bane ko ?
Ita ma cikin raɗa Aisha tace " ya fa fara samoun sauƙi nima dai baƙina ya subce min .
Miƙewa tayi tana ƙarasa cewa " bari na kouma ga masauƙin mu daman na tou yi muku sai da sahe .
" ku huta gajiya Aisha mun gode ,
Yakaka ta furta hakan da 'yar dariya ganin yadda duk Aisha ta ruɗe da ganin sauyawar Falmata .
bayan ta fita a sarari Yakaka tace "Hmm indai wannan 'yar rigimar ce ba ku ga kome ba .
" wa kenen ?
Falmata ta tambaye ta lokacin da take takowa cikin ɗakin kai tsaye ta nufi ɗan saƙon da suke yin Sallah ta hau Sallaya bayan ta zura dogon Hijab har ƙasa ta fara haramar tada iƙhamar sallar shaf'i .
" Ni kaɗai nake zance na Yaa Falta .
Yakaka ta furta hakan tana miƙewa ita ma ta tafi ɗauro Alwalar ta .
Washegari tun asuba masu aiki suka shiga hidimar abincin Baƙi Amnee da Khaalty Rahima basu zauna ba suna tsaye a kan su suna sa hannu a inda ya dace suna kuma gwada musu .
Kafin ƙarfe takwas illahirin harabar gidan har maƙota ya ɗau ƙamshin girki da sumfurin ƙamshi iri-iri na daga sunadaran ƙamsasa girki na mutan N'Djamena .
Mutan Niger sun ci sun gyatse sun kuma yaba sun zuba santi ba kaɗan ba domin kuwa Ɗan Malikin Maraɗi Mai ruwan kuɗi lokacin da ya gama ƙurbe shayin da aka cika masa 'yar butar shayi ( kettle ) cewa yayi " shi kuma wannan ruwan me sunan sa ? 🤔 ga shi dai yana wani zaƙi-zaƙi kamar tattaciyar zuma farar saƙa , ga kuma wani tsami-tsami da yake yi kamar matsatsen ruwan ɗan itaciyar inabi , ga kuma wani garɗi-garɗi da yake kamar ruwan zam-zam , ƙamshin da yake tashi a cikin sa ai mai samar da nutsuwa ne irin wannan idan kana shan sa kullum ai ka tsufa da ƙarƙon ka 😂
Amnee bata zauna ba ita ta shiga gyara Falmata ta sake goge mata jiki da sauran kayan gyaran jikin Amare da ya rage , kasantuwar bata iya zanen fulawa ba hakan bai hana bayan ta gama murjewa Falmata jiki ta kama kwaɓa lalle da turarurrukan ƙunshi irin nasu bayan ta jiƙa ganyen 'yar itaciyar "Sofan " ta ɗiga ruwan sa da yayi jawur a ƙwabin lallen ta ɗan ajiye shi ya jiƙu kaɗan ta kama ƙafafun Falmata ta rangaɗa mata lallen gargajiya a tafin ƙafar da kan yatsu .
Sha ɗayan rana Hajja ta iso da daman tun jiya Amnee ta ƙira ta a waya take sanar da ita batun zuwan dangin Mijin Falmata da zancen komawar su .
Da gama wayar su Hajja ta hau shiri ran ta cike da farin-cikin jin cewa Uwarɗakin zata koma ɗakin ta , daman bikin ya ƙare dan haka yau tun safe ta bi dangi ta yiwa kowa Sallama .
Prof ya nemi ganawa da Amnee tare da Khaalty Rahima bayan sun amsa ƙiran su ya tambaye su kan me da me ake buƙata da Falmata zata tafi da shi ?
Amnee tace " Baa Alaji ai lokaci ya ƙure na yin wani babban shiri sai dai kawai za'a ɗiba mata su turaren wuta a cikin na 'yar uwar ta ..
"Meyasa ita baza'a mata nata ba kada a taɓawa 'yar uwar ta kayan ta .
Prof ya katse ta , cikin kwantar da murya Amnee tace " to ai lokaci ne ya ƙure yau ne fa kawai ? Idan aka ɗibar mata kaɗan na Amfani idan ya so bayan sun tafi sai nayi waya can N'Djamena ayi mata nata a kuma ƙarowa Takwarata nata a tsanake idan Allah ya sauƙe ta lafiya sai mu tafi mata da kayayyakin ko kuwa ?
Ta tambayi khaalty Rahima . "Hakane Ukhtee ,
Prof ya ce to kayan ɗaki fa da na Amfanin gida ba za'a sauya mata wasu ba ?
"duk su ma idan ta haihu sai a mata sabbi tunda yanzu tafiyar ba ta shiri bace .
"Hakane to Allah ya kai mu kafin lokacin duk za'a tanadi kome ko ke da kan ki sai ki tafi Dubai yi mata sayayya .
Godiya mai yawa Khaalty Rahima ta yi masa bai amsa ba sai cigaba yayi da cewa a cikin ku biyun waccece zata raka ta ?
'Yar Dariya Amnee tayi kafin tace " da wai ni cewa nayi ko Zainab ma tunda ita take kusa anan sai ta kawo yaran idan Mijinta ya yarda sai su tafi tare tunda ga Hajja da daman tare suke , idan ta haihu mu sai mu je .
Cike da Amincewa Prof yace
"wannan shawara ce mai kyau bari zan ƙira shi Maigidan Zainab sai na nemi iznin sa da kaina , Allah ya kai mu .
" Amin Amin , Amnee ta amsa cike da jin daɗi
Bayan fitowar su daga sashin Prof a harabar gidan suka ci karo da Yakaka sai kai-kawo take a mamakance Khaalty Rahima tace " ke kuma me kike yi anan ?
Da sauri ta matso tana riƙo hannun Amnee ta ɗan rangwaɗa kai sannan tace " Amnee Dan Allah zan raka Falmata Niger ɗin ? Bana son ta tafi ita kaɗai nasan duk takura zata yi a tsakanin su tunda basu wani saba ba .
Kallon kin cika sakarci Khaalty Rahima ta mata kafin tace " Da iznin wa za ki tafi ? Kin san dai da Auren ki idan kuma gaban kan ki za kiyi to ,
Mayar da ganin ta tayi kan Amnee ta cigaba da cewa
" Ukhtee mai sunan ki dai sai kina yi kina taro ta sam bata da wayo .
Daga haka ta shige ciki ta bar su a tsaye , Amnee ta dubi Yakaka fuskar ta cike da murmushi tace ," takwara kema ai Amarya ce duk yaushe aka yi bikin ki ,? Ki bari idan ta haihu sai mu tafi tare .
" Amnee kawai raka ta zan yi fa Wallahi tausayin ta nake ji ace ta sake tafiya ita ɗaya , sai Hajja .
" Zainab ma zata raka ta .
Ta katse ta .
Zata sake yin wata maganar Amnee tace " ki tambayi iznin Mijin ki idan ya bar ki sai ku tafi tare .
"Ɗan tsallen Murna Yakaka tayi ta ƙanƙame hannun Amnee da yake cikin nata tana cewa "Nagode , nagode Amnee naa .
A hankali Amnee ta zare hannun ta ta wuce ciki tana dariyar rashin wayon Yakaka , ita yanzu idan an bar ta sai ta sake kwasar ƙafa ta bi Falmata ita bata tunanin gina nata gidan auren da har yanzu bata da takamaimai matsugunni a cikin sa ? Ita kenan kome na rayuwar ta zai biyo bayan uzurin Falmata ne .
Jinjina kai tayi cikin ran ta ta kasa ƙiyasto iya adadin girman ƙaunar da Yakaka take yiwa Falmata , can sashi guda na ranta dariya take dan tasan ko kusa Hamza ba zai Amince da tafiyar Yakaka Niger ba bare kuma Prof .
Bayan wucewar Amnee Yakaka tsumu tayi a tsaye , ita sai yanzu da aka ce ta ƙira Doctor Hamza ne ma ta tuna ko number sa bata da ita a wayar ta , gaskiya tana son raka Falmata Niger ɗin nan saboda ko a hanya wannan ƙatuwar matar zata nemi ɓata mata rai ta tare mata .
Zama tayi akan dan dandamalin da aka yi shukar furanni ta cikin sa tana tunanin ina zata samu layin Doctor hamza , ita dai ba zata iya tambayar Amnee ba kunya take ji , ba kuma ta son ta tambayi Rahima ko da a waya ne tasan sai ta sille ta ta mata tsiya .
Wayar Mamar su ta faɗo mata a rai tasan babu tantama akwai number sa a kai , to ko zata ɗauka ta ƙira shi kawai ma ta wayar ta ta ƙila yafi ɗagawa da wuri fiye da idan ta layin ta ta ƙira da bai san layin ba .
Da sauri ta miƙe ta shiga ciki , ta hau sama ɗakin Khaalty Rahima da sa'ar ta babu kowa a ɗakin , daga gefen gado ta hango wayar , da sauri ta ɗauka ta shiga neman sunan sa cikin jerin sunayen dake kan wayar bata sha wahala ba ta samu sunan tare da number sa .
Shiru tayi ta gagara danna ƙiran , tana son tattaro kalmomin da zata yi amfani da su wajen yi masa magana ,
Idon ta ta kai kan agogon wayar ta ga sha biyu saura tasan dai duk tsiya yanzu ya tashi a bacci duk kuwa da cewa yau lahadi ce ba aiki .
Fargaba bai rabu da ita ba ta danna ƙiran layin bayan ta kai wayar kunne ta runtse ido gam tana jin wani yanayi mai ƙarfi na shigar ta , daga can ƙasan ran ta addu'ar samun nutsuwa ta fara yi .
Wural ta buɗe idanun ta lokacin da ta ji sautin muryar computer na bata tabbacin babu kuɗin da zai isa ƙira a wayar .
Dariya tayi da ƙaramin sauti , kafin tace " kai Maman mu sai a bar ta ko meyasa take barin waya ba kuɗi ? Ita kamar ma bata wani damu da wayar ba .
Numbers ɗin ta kwafa a wayar ta , sai da ta zauna a bakin gado sannan ta danna ƙiran .
ABUJA
Daga can Sofiya ce a ɗakin Doctor Hamza tana gyara gadon da basu wani jima da tashi a kai ba Doctor Hamza ya shiga wanka .
Tana gyara bargon su lokacin da wayar sa dake gefen gado ta ɗau kiɗa alamun shigowar ƙira .
Ba tare da ta dau wayar ba ta leƙa fuskar ta ga lambobi ne reras ba suna , ɗan yamutsa fuska tayi ta gatsina guntun hancin ta kafin tace "yau Sunday ma ba za ku bar mutum ya huta ba shi kenan cikin jigila tsakanin asibiti da gida yau kam rana ta ce sai na more lokutana da aka cinye na sauran kwanaki tsawon sati .
Har wayar ta gama ƙara bata ɗaga ba .
Daga can Yakaka tayi jim da waya a hannun ta , cike da tsoron kar ta dame shi ta daure ta sake danna ƙiran a karo na biyu ,
Wannan karon har Sofiya zata fice a ɗakin sai ta dawo baya , ta ɗau wayar kai tsaye ta ɗaga ƙiran tana kara wayar a kunne tace " Hello who's on the line ?
" Mukut
Yakaka ta haɗiye yawun firgici , jim tayi kafin tace " amm ni ce Yakaka ina kwana ? bata tsaya ba ta zarce da cigaba da cewa "ki kaiwa Yaya doctor wayar .
Ba domin Sofiya tana shakkar kar Doctor Hamza da tasan kunnen sa yana iya jiyo ta ba da ba abunda zai hana ta ɗuɗɗurawa Yakaka zagi .
Baki ɗaya fuskarta tayi jaa a take tana huci tayi ƙasa da murya kafin tace " To akuya sarkin naci ana ƙorar ki kina daɗa naniƙewa , shugabar 'yan rashin zuciya Miji bai damu da ke ba sai ke ce ke neman sa jarababba , to ƙwalelen ki ke da Doctor sai gani sai hange daga nesa-nesa dan kuwa zaman ki kenan a inda kike 'yar .....
Ƙit !
Ta ji Yakaka ta katse ƙiran ,
Daɓas ta zauna a bakin gadon baki ɗaya ranta ya cunkushe har wani raɗaɗi take ji a hancin ta kamar ta shaƙi barkono ," wannan jarababbiyar yarinyar watau har ƙiran Mijinta take yi ?
" Sofi waye ya ƙira ni naji kamar kin ɗaga wayar ?
Da sauri ta waiga kafin ta miƙe tsaye ta ƙarasa zuwa gaban shi inda yake tsaye yana goge kansa da towel ,
Tana zuwa ta karɓi towel ɗin ta shiga goge masa jiki , bata yarda sun haɗa ido ba fuskar ta babu walwala tace , " Akuya ce ta ƙira ka ? 🙄
"Akuya fa ?
Ya tambaye ta yana duban ta da mamaki ,
Cike da bagararwa ta kai hannun ta ƙirjin sa tana ɗan tsikarin sa tace " eh dan kukan akuya nake ta ji tunda na ɗaga wayar ina Hello , Hello , Hello . Ba'a cewa kome sai Kukan Akuya .
Jawota yayi ya haɗe tsakanin su , yana kallon cikin tsakar idon ta yace " Sofi baki fa da kirki a wasu lokutan nasan daga Office ne aka ƙirani , Ni yanzu muje ki bani abinci na ci yunwa nake Ji ina son na fita akwai wani waje muhimmi da nake son zuwa yau .
Kicin-kicin tayi da fuska jin cewar zai fita yasa ta sake jin tasowar ɓacin rai da ya ɗan fara lafa mata sanadin haɗuwar fatar jikin su .
Bai kula ɓacin ran ta ba yayi shirin sa cikin wani yadi mai ɗan nawi ruwan zuma ya fesa turare tare da ɗaura agogon sa sai lokacin ya juyo ya dube ta da take zaune a bakin gado ta kumbura suntum .
Fushinta bai wani taɓa masa rai ba yace " mu je ki bani abincin ba daɗewa zan yi ba zan dawo nima so nake na huta yau ɗaya .
Bayan ya ɗan cac-cakali Omelet da kidney Sauce ya ɗan kurɓi ruwan tea ya miƙe a gurguje ya mata sallama yana barin gidan .
Da fitar sa ta yi jaɓar ' akan kujera tunanin ƙiran wayar sa da Yakaka tayi ya bata tsoro , ita da ta saki baki ta zauna malumman ta sun ce mata an yiwa Yakaka da Hamza farraƙu to tayaya Yakaka ta iya samun damar ƙiran sa ? Kada dai ace asirin nan bai ci ta ba ?
Wani irin huci take yi lokaci guda ta tashi da gudu ta hau sama ɗakin ta ta shige laluben wayar ta , ya zama dole ta sabunta aikin ta .😂
***
Doctor Hamza kuwa yana fitowa hankali kwance ya dai-daita motar sa akan titi unguwar su Malama Maryam ya tasamma da bata kasance ɓaƙuwar unguwa a wajen sa ba , ya sha kai sofiya gidan ƙawar ta Samira .
Tsawon sati biyu da yayi yana bin duk wasu Matakai daki-daki domin tabbatar da zancen da Suleiman ya sanar da shi game da Yakaka gaskiya ne ko ba gaskiya ba ? Duk da cewa yana da tabbacin Suleiman ɗin ba zai masa ƙarya ba amma yana da buƙatar samun ƙwararan hujjoji ko dan ya wanke zargin ta daga ransa da hakan shine kaɗai zai ba shi damar samun nutsuwa tare da ita da zai iya rungumar ta hannu bibbiyu , tun usul ƙaunar ta bata tunbuƙe ba daga ransa girgiɗi kawai tayi da a yanzu kuma ta dawo ta tsaya chak da ƙafafun ta ta kuma shiga kaiwa duk wasu gaɓɓan jikin sa mamaya .
ASSALAMU ALAIƘUM MASU KARATU .
Da fatan duku kuna lafiya ? Sakamakon saƙonnin da nayi ta amsa daga masoya masu karatu kan taƙaice ƙarshen MHR da wasu ke ƙorafi wasu kuma suka nemi Alfarmar na ɗan sake jaan zaren labarin nayi dalla-dalla ko da kuwa ban yi filla-filla ba , hakan yasa na karɓi ƙorafi na kuma ɗan jaa kaɗan ba mai yawa ba da nan gaba kaɗan mu kan iya rufe bangon littafin mu adana shi Insha Allah
A ƙarshe ina godiya sosai da sosai ga dukkanin makaranta MHR na fili da na ɓoye daɗa nasan na ɓoyen sun ninka na filin yawa "ghosts readers barkar mu dai ina gaisuwa fa 😜❤nasan kuna tare da ni domin ina ganin inuwar ku , ko da kuwa baku bani tukuici ba .
Nagode. [2/3, 9:34 PM] +234 803 083 8792: Mafari
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
50
Lokacin da Doctor Hamza ya isa unguwar su Malama Maryam dai-dai layi da gidan da Doctor Suleiman ya kwatanta masa sai ya ga ashe ma ya taɓa sanin gidan duk kuwa da cewa da dare ya taɓa zuwa amma bai manta da yarinyar da ya taɓa taimakawa ba a wani dare ana ruwan sama babu shakka a ƙofar wannan gidan ya sauƙe ta .
Kasancewar ana haramar sallar Azahar a lokacin dan haka a masallacin da yake kusa da gidan nan yayi Sallah .
Bayan ya idar sai ya matsa ya miƙawa Liman hannu suka yi musabaha , nuni ya yi masa kafin ya ɗora masa bayanin gidan da ya zo , to amma kasancewar an sanar da shi matar tana da aure ya zama dole sai da iznin Mijinta zai gana da ita , tunda ba sanin juna suka taɓa yi ba dan haka yake son sanin Mijin ta da farko , a zahiri wata buƙata ce ta son samun wasu bayanai daga bakin Matar da ake ƙira Malama Maryam yasa shi tasowa musamman domin ganawa da ita .
Dan jim liman yayi yana sake nazarin Doctor Hamza , kafin yace " bawan Allah lafiya dai ko ? Ba dai wani al'amari bane marar daɗi ya auku da har yasa kake neman Malama Maryam ?
Da sauri Doctor Hamza ya girgiza kai kafin yace ' ah ah ba wani abu bane marar kyau , kawai tambayoyi nake so nayi mata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 93 Chapter of 111