Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mayar da ita ga aikata zunubin da tayiwa ubangijinta Alƙawarin ta daina baza ta sake ba ! Ƙuka take da hawaye wani na korar wani , tana jin yadda tsoro ke mamaye ran ta , tsoron kowa da kome , tsoron sake yin zina ta hanyar tirsasawa , Takurewa tayi ta sanya fuskar ta tsakanin ƙafafun ta , sanyin ruwan da ya ɗan sake dawowa da ƙarfin yana ratsa ta ta hanyar jiƙa kayan jikin ta . Assalamu Alaykum . Gaisuwa tare da fatan Alkhairi a gare ku baki daya! Nagode.                            [9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikra writers association MAFARI ( Hargitsin Rayuwa ) umm'muaz 30 Babu kowa a harabar barikin sai masu gadi da suke daga kowacce kusurwa  , sakamakon dare da ya raba tsaka 2am , sai Biyamuradi youssouf da ke kai kawo a cikin hunturun sanyin da yake ratsa har ɓargon mutum gami da iska mai ƙura da take toshe ƙofofin hancin ɗan adam , a tsaye yake tsakiyar filin ya sunkui da kan sa jikin sa sanye da ƴar baƙar riga mai gajeren hannu da dogon wondon uniform ɗin su na soji , Ya zurfafa a tunanin makomar Auren da yake shirin karɓarwa kan sa nan da wasu ƴan awanni zuwa wayewar gari ,     Ina zai dosa da auren yarinyar ?? Yarinya ce ƙanƙanuwa , sannan kuma miskiniya , ta wacce hanya zai fara tallafar ta , domin ƙwarai take buƙatar matallafi cikin rayuwar ta da bata da kowa sai ƴar jaririyar sa ,     Me zai cewa iyayen sa su fahimce sa da dalilin sa na auren ta? Wanne irin hukunci maimartaba da hajiya umma zasu yanke masa idan suka ji ainahin abunda ya aikata da har ya kai shi ga auren yarinyar ?? Zasu su yi fushi mai tsanani da shi irin fushin da baya fatan ya gitta tsakanin sa da iyayen sa duk tsawon rayuwar sa ,     Me zai wakana tsakanin sa da gimbiya maimunatu lokacin da ta san ya auri wata mace kafin ita , Yana riƙe da auren wata bayan ita ? Zata iya yi masa kallon mayaudari kuma munafuki , a ƙarshe soyayyar su zata gurgunce da zai iya datse alaƙar su shi da ita , bai fatan haka saboda ya shaida irin tarin ƙaunar da zuciyar sa ke yiwa gimbiya maimounatu, Kalaman prof ya tuno inda yake ce da shi ,     Madallah tunda ka amince da auren Fatima , ka zo da wakilan/waliyan ka, a gobe zan baka auren ta , daga nan idan kana buƙata a goben zaka iya tafiya da ita tare da ƴar ka ,    A lokacin ya amsa masa da     Toh na Amince Har ya tashi zai tafi prof ya tsaida shi , To amma akwai wani lamari guda ɗaya , lamarin kuwa shine bazan iya ɗaukar yarinyar nan na baka ita , ka tafi da ita, ita kaɗai ba dole zan haɗa ka da mutum ɗaya wanda za ku tafi tare chan ƙasar ta ku domin a gano inda zaku zauna saboda sha'anin duniya , ta ka zo ta kan zo ko watarana wasu daga cikin dangin su zasu ɓullo su zo neman sanin inda ƴar su take , da fatan ka fahimceni da kyau kuma ka amince ?    Jim yayi a ƙarshe ya sake amsawa da    NA AMINCE Waje ya samu ya zauna akan ɗaya daga cikin dakalin da aka yi su domin zama dake a watse cikin barikin , Da farko yayi niyyar idan ya ɗauke ta ya kai su Niamey gidan ubbo a matsayin ƴar gudun hijirar da ya taimaka ita da baby mama idan ya so su kasance ƙarƙashin kulawar ubbo tare da shi har zuwa lokacin da zai samawa kan sa hanyar da zai bi ya bayyana su ga dangin sa ba tare da abubuwa sun rinchaɓe masa ba , Sai dai batun haɗa su tafiya da wani ya rusa wannan nufin nasa domin ko kusa ba zai so a san wasu dangi nasa ba , ba zai so asan ko shi wanene ba saboda kar watarana kome ya bayyana , a biyo sawu ba tare da sanin sa ba , kome ya lalace masa a lokacin , Idan kuwa har ya nuna ƙin amincewar sa , hakan zai sa a dasa ayar tambaya akan sa , ayi masa zaton marar gaskiya , wanda zai iya sa pro ya tsananta bincike akan sa wataƙila a ƙarshe kome ya isa ga masarautar su , bai fatan haka , Idan kuwa haka ne dolen sa ya yarda ya tafi da su da me rakiyar su , Ƙaunar ƴar sa da Allah ya jarrabe shi da shi ya sa duk yana ƙoƙarin fuskantar duk wani ƙalubale , burin sa ya tsira da ita , dan haka a ƙarshen tunanin sa ya ture duk wani ƙalubale gefe ya amince da mallakar baby mama tare da uwar goyon ta a lokaci guda da me rakiyar su , Yana tsaye a wajen aka yi ƙiran sallan farƙo na karfe 3:30am , kai tsaye ya nufi babban masallacin cikin barikin ya ɗaura alwala da sassanyan ruwan da iskar hunturu ta gama hura sa ya shiga masallaci ya fara jero nafilfili , yana roƙon Allah ya bashi nasara akan manufar sa ya kuma rufa masa asiri ya kawo masa warwaruwar al'amuran sa a sauƙaƙe , "toh ameen," ALƘAWARIN UBANGIJI ( MATAR MUTUM DAGA GARE SHI TAKE ) Da misalin ƙarfe goma na safiyar ranar Alhamis ɗin karshen sati ,  ƴan tsirarun mutanen da prof ya ƙira na cikin unguwa da basu wuce goma ba tare da wasu ƙarin mutane biyar da youssouf ya kawo a matsayin wakilan sa wanɗanda a zahiri abokan aikin sa ne daga ƙasar su , suka haɗu suka shaida ɗaurin auren FATIMA DILMARI , tare da YOUSSOUF ABDUL-AZIZOU BASKORE , wanda ya sauya suna zuwa youssouf Garba Malbaza Uzine, Bayan ɗaurin auren babu ɓata lokaci su abokan aikin youssouf suka yi komawar su domin ɗaura shirin tashin su zuwa Abuja inda zasu wuce ƙasar su ta jirgin sama a yau ɗin ,,  da shi kuma youssouf ya shigar da neman iznin a bada mota guda cikin motocin su na soji tare da direba da zai tuƙa su zuwa Niamey ta hanya , ba'a tsananta bincike ba aka bashi izni tare da shaida masa ya tabbatar ya samu isa niamey kafin ranar litinin inda za'a yi bikin dawowar su tare da yi musu ƙarin girma , Hajja me wurya," ita ce dattijuwar da prof ya zaɓa a matsayin wacce zata raka fatima ɗakin mijin ta daganan ta gano garin da zasu zauna a niger , kasancewar ita hajja mai wurya dattijuwa ce da a ƙalla ta tasamma shekaru hamsin , sannan kuma a halin yanzu bata da wani jigo cikin rayuwar ta iyaye duk sun mutu dangin kuwa kowa ta kai ta kai yake sannan tun asali bata da haula ɗan ta ɗaya ne tal da ta haife shi a shekarun girma bayan aure auren da tayi ta yi domin neman haihuwa , tana tsakiyar fara cin moriyar ɗan nata da ya ɗan fara tasawa shekarun sa ishirin da huɗu , ƴan tawayen boko haram suka shigo har gida suka yanka mata shi , a cewar su yana zagin su tare da sukar akidar su , dan haka suka kawar da shi, Tun daga nan rayuwa ta fara yi mata wahala , ƙunci da talauci suka dirar mata , zamani ne da kowa yake gudun wahala ba'a duban zuminci , tunda ta fahimci haka ta daina yin raragefe gidan ƴan uwa ta bazama neman na kan ta sanin da tayi da ɗan sauran karfin ta bata zama ƙarƙashin dangina ana zuba mata sharar walakancin , aikatau ta fara a gidajen saida abincin ,kasancewar ta gwanar girki iri iri ,musamman ma na ƙasar camaru da tayi farkon zaman auren ta a chan ,  amma sakamakon tsaurin ta da kuma tsayuwar ta kan gaskiya ya sa ba ta cika daɗewa a wajen aikin  ake sallamar ta , saboda bata zuru duk ta ga zalau sai ta tsinka ,"  daga baya ta koma aiki a gidajen masu hali nan ma gida biyu tana barin aiki saboda yadda take gwadawa uwargida iyakar ta a cikin gidan ta idan har ta ga abunda bai dace ba,  sai fa wannan karon da tayi dace ta samu aiki gidan Professor Mustspha dilmari  Allah ya tsawaita zaman ta a gidan da taimakon tarbiyyar yaran gidan da basu cika raini da walakanci irin na sauran ƴaƴan masu hali takwarorin su ba , babu kuma matar gidan shekaru biyu take nema da fara aiki a gidan a matsayin mai yin girki , musamman ma na shi prof . A jiya da prof ya ƙira su ita da falmata ya faɗa musu hukuncin da yake ƙoƙarin yankewa har ma ya tuntunɓi ita falmata akan jin ra'ayin ta , ta amince zata auri baban ƴar da take riƙo su tafi ita da shi da ƴar chan ƙasar sa ko kuwa ?? Ga mamakin sa ba tare da shayin kome ba Falmata ta amsa da ta amince zata auri baban baby ya tafi da ita tare da baby ,    Ƙwarai prof ya ji daɗin amsar Falmata domin da farko har yana fargabar ko yarinyar zata ƙi gatan da yake son yi mata na aurar da ita tunda ƙuruciyar ta , ga mutumin da yake iya hango nagartar sa a cikin yanayin sa da mu'amalar sa , yana hasashen mutum ne na ƙwarai ! A sarari ya nuna jin daɗin sa tare da yi mata addu'o'in samun nasara a rayuwa , sannan ya juya ga hajja mai wurya wacce ita ma take durƙushe daga gefen falmata , Hajja Alfarma zan nema a gurin ki akan ki raka fatima ɗakin mijin ta ki gano min wajen da zasu zauna ita da mijin ta a chan niger ɗin daga baya sai ki dawo. Da fatan zaki min alfarma ? Dariya hajja me wurya ta sa ! Babu kome Alhaji zamu tafi tare , me zaman aure ma ta amince bare ni ƴar rakiya ?? Ai ko gaba da binnin sin ne Alhaji ba na ƙi raka ƴar marainiyar Allahn nan ba , kai shima dai wannan dogon balaraben nijar ɗin Allah yayi masa Albarka da duk da kyan nan nasa da cikar zati irin ta ɗa namiji amma haka ya runtse ido ya ce ya amince zai auri wannan murɗaɗɗiyar bahaguwar yarinyar , ai dole ayi masa godiya bawan Allah . Nan dai Alhaji ya sallame su yana sake musu godiya akan biyayyar da suka ma sa , Kan hanyar su ta komawa hajja mai wurya tana riƙe da hannun falmata tace    Ke ƴar nan Allah ya dube ki ya tarfawa garin ki nono , irin wannan zankaɗeɗen miji da Allah ya wanke ya ba ki ?? Ai ko ɗiyar masu mulki ba ta ƙi shi ba , to zan fara faɗa miki tun wuri tun yanzu , ki zubar da waɗannan hargitsatsun halayen naki tun a nan nigeria kar ki ce zaki tafi gidan auren ki da su , saboda wannan dai miji naki wallahi kin yi sa'a wanke hannun ka taɓa Allah dai shi sa yadda surar nan tasa take halin sa yafi haka kyau , Ai bazan bar gidan nan naki ba sai na ga kamun ludayin zaman naki da shi , ato sai ki shirya ni ɗin dai da kika tsana kike ƙin bani riƙon jaririya , nice dai me miki zaman ɗaki sai dai muyi wacce za mu yi mahaukaci ya ɗau rigar kurma ... Zame hannun ta tayi daga cikin na hajja tayi gaba ta miƙa hanya , ƙalau tamkar me gani saboda yau da gobe ta fara haddace hanyar a ƙwaƙwalwar ta,    Sasakai hajja me wurya tayi    Au aikin banza kenan hanci ba ƙafa , to ki fi ruwa tafiya , nace ki fi ruwa tafiya , wannan yarinyar sai na dage kafin ta shiga hanya ta ɗau haske ta san me duniya take ciki kan ta hayaƙi yake ,! Falmata ko sauraron ta bata yi ba hasalima ji tayi hayaniyar hajja me wurya ta hana kwakwalwar ta sakewa tayi tunanin da ya kamata shi yasa ta zame hannun ta ta rabu da ita ,    Aure da ita da shi ?? Wanene shi da yace baban baby ne ? Da gaske shine baban baby ? Wanne irin aure zasu yi ? Ina ne ƙasar ta su ? Idan suka tafi zasu dawo ? Bata son barin nan inda take , burin ta watarana dr hamza ya nemo mata maman su , to amma yanzu kuma ga shi zata tafi ta bar nan ɗin ,     Abun da ta sani zata yi kome , zata tafi ko ina zata kuma ta shiga kowannen wahala domin ta tsira da baby mama , domin ta tsaya tare da baby mama , domin baby mama kar ta sha wuya , naƙasun ta miskinancin ta , rashin idanu , da ace ita lafiyar ta ƙalau , bata buƙatar abokin tayi wajen gina rayuwar ƴar ta , da zata gudu da baby mama ta ɓuya wani waje tana kula da ita , to amma ita ɗin ma miskiniya ce dole ne ta bi baban baby da yace zai kula da mama ƴar sa ce ! Ƙarfe biyu cif aka fara fito da jakar bocco ɗin falmata wacce ta haɗe kayan ta da na yakaka kakaf a cikin babbar baccon yakakar , sai kuma kayan baby mama shima a cikin babbar jaka , duk aka zuba su a bayan dunƙulalliyar motar soji me ƙirar golf kofa biyu , Biyamuradi youssouf ya taka zuwa cikin gidan falon prof , suka yi sallama inda prof ɗin ya bi shi da kalaman godiya ya kuma ɗora da damƙa masa amanar fatima tare da roƙon sa akan ya kula da ita , ita ɗin abar a tausayawa ce , Nan youssouf ɗin ya amsa tare da ɗaukar Alƙawarin zai kula da ita , Yana zaune hajja me wurya da falmata rike da mama haɗi da rahima suka shigo , falmata tana shirye tsaf cikin sabuwar atamfar ta ruwan ganye da adon furanni farare,  ta saka farin hijabi har guiwar ta , Daga gefe suka tsugunna , nan prof yayi musu addu'o'i tare da ƴan nasihu ya sake ɗanƙa amanar falmata a hannun hajja me wurya har lau , Daga ƙarshe ya zaro kuɗin sadakin falmata naira dubu ishirin sabbin bandir ɗin ƴan ɗari biyu ,    Ungo Rahima , miƙawa fatima kuɗin sadakin ta hakkin ta , fatima ina me baki haƙuri akan yadda auren ya zo a ƙurarren lokaci ban miki kome ba da iyaye ke yiwa ƴaƴan su idan zasu kai su gidan miji , amma na miki alƙawari na kuma yi magana da shi mijin naki akan idan kun isa ya tura min account number zan tura da kuɗin da za'a saya miki kayan ɗaki da na amfanin gida a chan kin ji ko ? Ki riƙe wannan sadakin auren ki ne , Da sauri falmata wacce idanun ta suka kawo ruwan hawaye akan irin ƙaunar da prof ke musu tare da sanin cewa yau zata bar gidan shi zuwa wani waje da bata da sani akan me zata je ta tarar , tace   Baba na bar maka kuɗin ni babu abunda zan yi da su ,   A ah fatima ki karɓa nace hakkin ki ne , watarana zaki samu abun saya da su ,   Muryar ta na karkarwar kukan da ta soma tace   Baba to ka riƙe min idan na dawo zan karɓa , Ba shiri hajja me wurya ta zungure ta , tana satar kallon youssouf da yayi shiru yana sauraran ta ,    Ƙasa-ƙasa tace   Ka ji min sakarya auren da tun baki kai gidan ba kike fatan ki dawo , ?? Kawo ƙuɗin na riƙe mata Rahima, irin kunyar nan ce ta amare take gwada mana ,    Rahima da take murmushi a hankali ta miƙawa hajja me wurya kuɗin , Madallah Allah ya sanyawa auren ku Albarka Allah ya sa abokiyar arziki ce , Allah ya kauda shaiɗanun aljanu da na mutane a tsakanin ku , Allah ya sa mutuwa ɗai ita zata raba ku, Allah kuma ya baku zuri'a masu albarka irin wacce manzo Allah zai yi alfahari da ita !     Laɓɓan Youssouf ne suka motsa a hankali da ,"Ameen .     Rahima ita ta raka su har bakin mota tana jin yadda kewar su take taso mata , ai anyi sabo zaman watanni tare , duk da cewa ta so tafiyar su tafi haka tsawo sai dai damar bata samu ba , amma ko babu kome tayiwa fatima murnar samun ɗanɗasheshen mijin da ya ƙere sa'an auren ta ta ko'ina hakkun fatima me sa'a ce .     Da wannan tunanin ta rufe musu ƙofar motar bangaren da falmata ta shiga inda suke zaune tare ita da hajja me wurya a bayan motar , Biyamuradi da direban sa suna gaba ," . ***** Tafiya ce suka ɗora ta miƙaƙƙiya tun daga maiduguri zuwa sokoto , inda basu samu isa sokoto ba sai cikin dare misalin sha biyu da rabi , alamun gajiya da suka bayyana baro-baro ga falmata tare da baby mama wacce ta ke yin ƙananun rikici na gajiya da rikon hannun ya sa youssouf ya kama musu ƴan ɗakuna a wani ƙaramin guess inn da yake cikin garin na sokoto zuwa wayewar gari sun huta sun kuma sake shiri sai kuma su faɗa yankin niger ta," ilela ," su ɗau hanya ta birnin N'konni da zai ɗaura su kan kodoben da za su sadu da birnin Niamey ɗin niger ....! Ba su suka samu isa Niamey ba sai ranar Asabat da misalin ƙarfe bakwai na dare duk kuwa da gudun da direban ya dunga shararawa tun da suka faɗa yankin niger kasancewar sun shigo ƙasar su , kowa yaga gilmawar motar su basu hanya ake , Kai tsaye direban ya wuce da su ( Radisson Blue hotel,) ƙarƙashin umarnin youssof , kasancewar shahararren hotel ɗin mafi yawan lokuta nan ne wajen sauƙar sa idan wani aiki ya kawo shi Niamey ɗin kasantuwar hotel ɗin kusa yake da manyan ma'aikatu masu muhimmanci na ƙasar da ke babban birnin Niamey , Babu ɓata lokaci ya kama musu ɗakuna inda hajja me wurya da falmata zasu zauna a ɗaki guda , (one bedroom Residence ) dake ƙasa shi kuma ya Kama nasa ɗakin a sama ( royal suite ) inda ya saba zama idan ya zo otel ɗin yayin da direba yayi tafiyar sa inda sauran abokanan aikin su suke ,  ya bar masa mukullin tare da motar , ' Bayan yayi wanka ya sallaci isha'i , misalin ƙarfe takwas da rabi ya sauko ƙasa , ɗakin da suke ya tasamma , ƙwanƙwas musu ƙofa yayi , Hajja me wurya tana sallar isha'i lokacin , falmata kuwa ta idar tana kwance bisa faffaɗan gadon ta sanya baby mama a gaba wacce take ta baccin gajiya bayan an cika mata ciki da madarar ta me ɗumi , Sake ƙwanƙwasa ƙofar yayi a karo na biyu yana sake kallon number ɗakin da take rubuce a jikin wani ɗan katako dake sakale a jikin ƙofar  ,"nan ne dai ɗakin nasu ," Miƙewa zaune tayi     Hajja kamar ana buga ƙofa ko ? Ƙyat ! Ƙyat    Hajja ta mata alama da hannu Oho sallah kike ? Sake bugun ƙofar aka yi da ɗan ƙarfi da ya sanyata miƙewa a hankali bayan ta zura hijabin ta , Ƙasantuwar ɗakin ba wani babba sosai bane taku kaɗan tayi ta isa jikin bango , dan haka ta fara shafawa bata sha wahala ba hannun ta ya sauka jikin ƙofar,     Waye ne ?    Ni ne buɗe min ƙofa     Ta shaida muryar sa   kama mariƙar ƙofar tayi ta murɗa sai dai bata ji alamun ƙofar ta buɗu ba , Ban iya ba   tace da shi cikin ƴar ƙaramar muryar ta ,    ,'Bata iya buɗe ƙofa ba ? Ya tambayi kan sa ,"   Hajiya batta cikin ɗakin ??   Tana sallah ,      ta ce masa   Bai ce kome ba ya gyara tsayuwa gami da jingina da jikin bangon ɗakin ,    Cigaba tayi da tsayuwa tana ɗan laluba jikin ƙofar ko zata ji wajen buɗewa ,    Ba'a ɗauki lokaci ba hajja ta idar da sallah ,     Ke kam wannan yarinya anyi bagidajiya , yanzu ace buɗe ƙofa ma kin kasa ? Ni gusa ki ban guri ,   buɗe masa ƙofar tayi ya shigo suka gaisa ,     Hajja akwai abunda kuke buƙata ne ?     Babu abunda muke buƙata ɗan nan , mun gode ƙwarai da hidima ,    Idon sa ya ɗora kan baby mama ,     Ta daina rigimou kou ? Ba ku buƙatar kome kou ? Shiru falmata tayi domin bata ma san da ita yake ba , Hajja ta ce fatima maigidan na magana       Wanne maigida hajja ?? Wata ƙatuwar harara hajja ta wurga mata , tamkar falmatan tana ganin ta  a ƙufule tace     Baban jaririyar ta ki A sanyaye ta ce me yace ? Wai zai tafi da baby ?   Da sauri youssouf yace Ban faɗi hakka ba fatima cewa nayi ba ku buƙatar kome ? Eh !    Ta bashi amsa tana zama bakin gado ta shiga laluben baby mama, hannun ta ya sauka bisa kan ta ta shiga shafawa a hankali , Ya juya ga hajja , ni zan shiga gari wajen aiki na , akwai yiwuwar gobe sai yammaci zan shigo , duk idan kun buƙaci wanni abu ku ƙira ma'aikatan otel ɗin ta kan wayar tarho ,   Ga ta nan ," ya nuna mata telphone ɗin dake ajiye daga saman ƴar durowar gefen gado  " madallah hajiya ina sake godiya Mune da godiya ai ɗan nan mune da godiya , to to babu kome Allah shi taimaka muna nan muna addu'a Ameen hajja sai gobe    Ya juya yana barin ɗakin Da sauri hajja ta zunguri falmata ,     Ke baki san ki gaishe da miji ko kiyiwa miji addu'a bane ? yau ni hauwa'u na ga abunda ya fi ƙarfi na me zan gani haka ? Yanzu ashe haka za ki dunga gwada rashin hankali a gidan auren na ki ? Ko kuwa taƙamar yarinta kike ? To bari ki ji na faɗa miki ni lokacin da aka min auren fari ma ban kai ki cika ba , kin fini ƙugu da ƙirji da sharaɓa da kome ke har shekaru ma domin ni lokacin da aka min aure ma sha huɗu nake ko nonon arziƙi bani da su , amma billahil azeem ban yi irin wannan haukar da na hango somi-somin ta a tare da ke ba ,     Ke kenan sai ƙwalafacin ƴa , alhalin kina gwadawa uban ta halin ko in kula , idan taƙamar ki son ƴaƴa ai sai ki kwantar da kai kema ki samu ki tara naki ba ki dunga gwada naci akan ƴar wasu ba ,    Falmata wacce ta fara jin haushin hajja akan takurar da ta ke mata,  muryar ta a cunkushe tace ,   To a ta ya zan tara nawa ƴaƴan ??     Sororo hajja tayi ,   Ah lalle abun naki na yi ne,  'an biyawa bazaura hajji , to sai ki cigaba da tambaya ta , ranar bada amsa tana zuwa , aikin banza yarinya sai sokonci kika iya ,.    Washegari biyamuradi youssouf bashi zaune bashh& har sai da ya samu wani ɗan madai-daicin gida irin wanda yake so a unguwar ,(Banifandou 2) ya kamawa su falmata hayar sa ya biya kuɗin shekara guda cif , Ƙarfe hudu tayi masa a shahararren company ƙera kayan katako da shirya gida ,(sunwe) inda ya faɗa musu buƙatar sa na son a kai masa kaya dai-dai da tsari da fasalin gidan sa , Basu yi ƙasa a guiwa ba suka tashi ma'aikatan su har

Chapter 53 of 111