ma zaki gan su ,
Ƴar fara'a Khaalty Rahima tayi , " duk da haka Ukhtee kin san fa irin aibun da yake tare da takwarar taki , ni gani nayi kamar an tauye shi da aka liƙa masa auren ta , kuma a yadda ma na lura yanzu ɗan nawa baya yi da takwarar taki ko da a baya ya nuna ra'ayin sa akan ta ,
Wucewa gaba Amnee tayi tana cewa " koma menene dai idan aka yi auren ai sa shirya kan su , so na gaskiya ai baya kankaruwa sai dai wani abu ya dusashe tasirin sa , ni bari naje na samu takwarata na shawo kanta ta amince ayi abun nan ranta na so , ba zan so ba a takuramin ita da auren dole ,
Ƴar ajiyar zuciya Khaalty Rahima tayi tana murmushi ta bi bayan Amnee zuciyar ta cike taf da ƙauna tare da farin-ciki marar misaltuwa da rabon ta da irin sa shekarun dayawa .
***
A ɗaki Amnee ta tarar da su ukun suna gwada ɗinkunan su , Falmata tana mitar burguza-burguzan riguna da siket ɗin da telan ya yi mata , " mai sunan Mama dan Allah ki ga wannan siket ɗin yadda ya min yawa ba ko fasali ni ɗai gaskiya a mayar ya rage min , naku ke da Yakaka cas-cas irin na ƴan mata amma ni shine ya min haka siket kamar buhu ?
Dariyar da tuntuni Yakaka take riƙewa ita ta ɓurtso kanta , cikin dariyar take cewa ,
" Kai Falmata gaskiya ba'a iyar miki , ke kome aka miki bai yi ba, yanzu da matsattsu aka miki cewa za ki yi sun matse ki sun hana Baby sakewa yanzu kuma anyi wanda Baby zai wataya kince an miki buhu , Allah kana gani dai , ka shirya min Falmata ,
" zunɓuro baki Falmata tayi dai-dai da shigowar Amnee da Mamar su ,
" Maama kin ga ku faɗa musu su daina tsokana ta kullum Rahima da Yakaka basu da abun yi sai tsokana ta, yanzu ku ga irin ɗinki da suka kai aka min ,
ta ɗaga siket ɗin ta ,
"ku ga kuma nasu ,
tace tana ɗaukar siket ɗin Yakaka ta nuno , ta ɗora da cewa " dan Allah Amnee za'a ce tela ɗaya ya ɗinka ? Nawa kamar wata gani garau , nasu kuma na yayi ?
Karɓar kayan Amnee tayi tana ajiyesu gefe , tace " sun yi girma kam , kiyi haƙuri za'a mayar ya rage miki wannan ɗinki ai ko a Niger ayi wanda ya fi shi tsari bare anan Nigeria gidan cancara ɗinki ,
Ganin ta ta mayar kan Yakaka da take kallon su tana dariya da haƙori ,
" Zo nan ki zauna takwara ta magana nake tafe da ita mai muhimmanci , duk ku nutsu ku bar shirmen nan ,
Amne ta furta hakan lokacin da take zama a bakin gadon , tana yiwa Yakaka nuni da gefen ta kusa .
A nutse Yakaka ta taho kusa da ƙafafun Amnee ta zauna a ƙasa maimakon gefen ta da ta nuna mata ,
Cikin nazari Amnee tace ,
" Takwara akwai wanda kuke tare ne ? Ina nufin akwai wanda kuka yi wata magana ta aure da shi ??
Dumm Yakaka tayi , zuciyar ta na sauya bugu , a lokacin ba wanda ya faɗo mata sai wannan mutumin da yayi ta nacin bibiyar ta shekaru kusan biyu tana zille masa a abuja , kafin barinta Abuja dai Lubna tace ta ba shi number ta Amma ko sau ɗaya bata taɓa riskar ƙiran sa ba , wataƙila daman wasa yake , ita kuwa bayan shi ai ba wanda ta taɓa saurara mafi yawan masu cewa suna son ta duk gani take fasiƙanci zasu yi da ita , domin tunda tasan illar zina da zunubin ta take jin tsoron maza ma gaba ɗaya .
Tunanin ta ya katse lokacin da taji Amnee na maimaita mata tambayar , a hankali ta girgiza kai , " Babu kowa Amnee ,
" kin tabbata ? Ki fa faɗa min idan akwai ,
Amnee ta sake furta haka domin haƙaƙewa ,
Zuciyar Yakaka ta fara shiga ruɗu da son sanin dalilin da ya kawo wannan maganar ta sake cewa , " Allah babu kowa Amnee ,
" To Alhamdulillah , Aminatu kina jina ko ?
Bata jira ta amsa ba ta cigaba da cewa , " Baa Alaji , Baban ku na gidan nan ya yanke shawarar haɗa aure a tsakanin ku ke da Yayan ku Hamza , muna fatan ba za ki bijirewa Umarnin mu ba ?
A razane ta ɗago kan ta saboda yadda zancen ya zo mata baga-tatan , ta shiga raba ganin ta tsakanin Mamar su da Amnee cikin wani irin jirkitatcen yanayi ,
Ganin yadda fuskar ta ta nuna yasa Khaalty Rahima hanzarin tare ko wanne irin sakamakon da zai biyo baya ta hanyar cewa ,
" kuma har an riga an gama yanke magana za'a haɗa bikin ku rana guda da na takwarata nan da kwanaki goma sha biyu , babu sauran wata magana .
Ihun da Rahima ta sa tana tsalle ta taho ta rungume Yakaka shi ya katse zancen khaalty Rahima ,
" Alhamdulillah burin Big bro zai cika , Masha Allah Baa mun gode sosai wallahi , sai ta sake ta da gudu tana barin ɗakin tana cewa , " bari naje na taya bro murna wayyo Allah ,
Shiru ne ya ratsa ɗakin sai tashin sautin murmushin Falmata da farin-ciki mai tsanani ya bayyana kan sa a fuskar ta ,
" Takwara baki ce kome ba ? , Amnee ta sake katse shirun ,
A hankali Yakaka ta ɗago kan ta ta ɗan dubi Amnee muryar ta can ciki tace , " Shi ya yarda ?
Tambayar da ta karya zuciyar iyayen nata biyu har ma da Falmata , kafin Amnee ta amsa ta sake cewa , " Idan har shi ya yadda shikenan Amnee ni ai koyaushe mai muku biyayya ce Baa kuma nima Babana ne , nagode da duk abunda kuka min .
Hannuwanta duk biyu Amnee ta sanya ta ɗago ta , ta zarce da rungumeta a jikinta ,
" Allah ya miki Albarka takwarata Allah ya baku 'ya'yan da zasu muku fiye da irin biyayyar da kuka yi mana ,
Addu'o'i ta cigaba da yi mata Falmata na amsawa da ƴar muryar ta dake bayyana amon murna ,
Miƙewa Amnee tayi tare da cewa ," bari naje na sake sabunta tsari da shiri bikin ya zama biyu , kai wannan shekarar ta zo min da ɗinbin Alheru Alhamdulillah Allah nagode ma ,
Bata jira cewar su ba ta fita ta bar su , su ukun ,
Yakaka ta ɗago idanunta dake cike da ƙwalla damuwa ɓaro-ɓaro a fuskar ta take kallon fuskar Mamar su tana son ko yaya ta bata damar da zata ce wani abu ,
A hankali Khaalty Rahima ta tako ta zauna a inda Amnee ta tashi , bata yadda sun haɗa ido ba tace " Naji daɗi da kika nuna halacci baki yi butulci ba , abu na gaba shine ki ɗauko haƙuri da juriya akan duk wani ƙalubale da za ki fuskanta a gaba ki riƙe su a matsayin makamin ki , sannan a ko'ina kika tsinci kan ki cikin kowanne hali ki ji tsoron Allah , Allah ya miki Albarka Amina .
" Amin, Yakaka ta amsa hawayen idanun ta na sauƙa bisa ƙuncin ta ,
Miƙewa khaalty Rahima tayi saboda zuciyar ta ba zata juri ganin irin wannan damuwar mai tarin yawa da take hangowa daga Yakaka ba , abunda ta riga ta sani inshaAllah cikin auren nan nasu akwai alheri mai tarin yawa ,
Tasan abunda Yakaka take tsoro bai wuce illar dake tare da ita ba akan irin abunda ta aikata , ita ta ɗau hakan a matsayin kaddarar Yakaka, kuma inshaAllah a wannan gaɓar ta ƙudurci aniyar yakice kunya irin wacce iyaye mata ke nunawa ƴaƴan su , zata ɗauri ɗamarar gyara ɗiyar ta ciki da bai tare da mata darussa masu inganci cikin ɗan zaman da ya rage musu tare , da zai taimaka wajen sauƙaƙa mata duk wasu ƙalubalen da ka iya taso mata a gidan aure .
Kayan gyara kuwa daga nan har N'Djamena, zata ɗau hanya ta tafi domin ta ga ta yiwa ƴar ta gyara mai kyau da zai taimaka ko kaɗan ne wajen samar mata da ɗan matsayi ko yaya a wajen Mijinta, sanin da tayi tana da abokiyar zama ko kusa ba zata so ƴar ta ta walaƙanta ba . ( Khaalty Rahima nima ina da saƙo zuwa N'Djamena nan amma ni turaren wuta nake so 🙄🤐 )
Tana bada baya daga ɗakin Falmata ta taso da sassarfa ta isa inda Yakaka take zaune kamar an dasa ta ko motsin kirki bata yi , tana zuwa ta rungume ta tana ƴar dariya-dariya tace , " Yakaka na Alhamdulillah , kin ga Al'amarin Allah ko ? Allah baya bacci Yakaka nayi murna , nayi murna , a kunne ta ta raɗa mata ,"Félicitations Mme Hamza Mustapha Dilmari,
Kukan da tun-tuni ke cin Yakaka a rai shi ta saki lokacin da tashin hankali yayi nasarar lillisa zuciyar ta , " Aure ? Aure tsakanin ta da Doctor hamza mutumin da ya tsani kallon ko fuskar ta ? mutumin da yake zargin ta da tafiya yawon banza ? Mijin sofi ƙawar samy Baby ? Anya Mamaa ba zasu kaita inda za'a kashe ta bane tun kwananta bai ƙare ba , a gareta wannan ba gata bane ba .
****
Duk yadda Rahima ta dunga ƙwanƙwasa ƙofar falon Doctor Hamza bai taso ya buɗe ba duk kuwa da cewa yana zaune dirshan a ƙasa a falon sai dai damuwar da yake ciki ta toshe masa kunne daga jin hayaniyar Rahima , ya zurfafa cikin tunani .
Wani irin yanayi marar daɗi ya tsinci kansa a ciki , ko kusa da yasan abunda zai riska kenan a garin da bai zo ba ,
Yarinyar da ta gama yawon banzan ta bai sani ba ma ko ta maƙalo wata cutar ita ce dan kawai Baa yana son gyara wani shuɗaɗɗan kuskure sai ya laƙa masa auren ta ?
Wannan da bata ajiye kome ba sai tarin ƙarairayi da yaudarar banza , har ita ce ake so ya gatata ? To wanne gata zai mata da bai nuna mata sumfurin sa ba a baya ?
Shi ya sani a da ya so ta amma yanzu ko alama baya jin ɗigo na son ta sai ma baƙin-ciki da yake ji a duk lokacin da ya gan ta .
Babu yadda zai yi , bashi da wata mafita shiyasa ya amsa auren ta da aka liƙa masa , da ace ba Khaalty Rahima bace uwar ta da Wallahi da ko ta halin ƙaka sai ya cisge wannan liƙin da ake son yi masa ,
To amma kasancewar ta 'ya ga Khaalty Rahima ya sa dole ya amince , zai aure ta , su zauna a yadda yanayi ya zo musu shi da ita ..!
Assalamu Alaikum masu karatu
Da fatan kun wuni lafiya ? Ina miƙo saƙon gaisuwa tare da fatan alheri agare ku baki ɗaya .
To ga fa abun yazo , wai inji mai tsoron wanka , Ina nufin bikin Yakaka da Hamza 😂
sister J , da Raly Garba , ku ne fa masu rabon anko , sai dai kuma ga lokaci ya zo a ƙure kwana goma sha biyu kachal ai ya muku kaɗan. 🤔
[1/4, 12:40 PM] +234 816 886 5113: MAFARI
( HARGITSIN RAYUWA )
UMM'MUAZ
48
MAFI TSAWON DA BAI ZAMA KARSHE BA.
A washegarin ranar da aka tabbatar masa da haɗin Auren sa da Yakaka nan da kwanaki goma sha ɗaya masu zuwa , Doctor Hamza ya tattara ya nasa ya nasa ya koma Abuja da sassafe , duk yadda Amnee ta dunga son shigo masa da zancen Yakaka tana son ta haɗa su , lokacin da ya shiga yi musu sallama ita da Baa , ƙi yayi , ko Khaalty Rahima sai ta wajen Amnee ya bar mata saƙon tafiyar sa .
Gaba ɗaya baya cikin nutsuwar sa garin ya masa wani irin zafi .
Prof da Amnee basu wani damu da yadda alamun ɗan nasu ya nuna dake bayyana bai yi farin-ciki da auren da ake shirin yi masa ba , suka cigaba da yin duk wasu tsare-tsare da shirye-shiryen yadda bikin zai kasance , an riga an buga katin auren Rahima har ma an rabar , ganin cewa bikin Hamza ba na farko bane ,na biyu ne ,ya kuma zo a ƙurarren lokaci , sannan abun nasu tuwona maina ne , saboda sune dangin uwa da na uba saboda a cikin baki ɗayan dangin Uban su Yakaka har yau an gaza samo ko guda duk kuwa da cewa sau uku Khaalty Rahima tana bin sansanin ƴan gudun Hijira ko Allah zai sa ta ci karo da wasu daga cikin tsirarun dangin Mahaifin su Yakaka duk kuwa da cewar tsawon zaman su ba zaman daɗi suka yi ba , saboda karan-tsana da suka ɗora mata ita da yaranta , haka siƙau , sai dai Allah bai sa ta gamu da ko wanda ya san su ba , kai ko mutanen ƙaramin garin nasu ma Allah bai haɗa ta da su ba .
Dan haka sai basu wani damu da a sanar da dangi ba kawai suka bar lamarin a tsakanin su .
Amne ta ƙarfafa da a rufe zancen auren a tsakanin su ne saboda tsoro da take yi kar danginsu suyi wani yunƙuri na hana auren sanin da tayi tun da can daman ba ƙaunar ta suke ba ita da Rahimar ta , tayaya kuwa zasu so 'yar Rahima ta auri Hamza ? musamman da ya kasance Hamzan ai tasu yake aure 'yar yar'uwar su .
Dan haka ta dage akan a rufe zancen har sai ɗaurin auren ya matso a yadda ta so ma sai sanarwar ɗaurin auren kowa zai ji ,sai dai da alama hakan ba mai samuwa bane , koma menene ita dai zasu tsawaita addu'a ita da Khaalty Rahima kan Allah ya tabbatar da lamarin nan tare da Aminci
Shiri suke sosai a tsakanin su , lokaci ne yanzu na wayar tafi da gidanka , da saƙo ke saurin isa inda ake buƙata , ta waya Amnee ta sanarwa da dangin su na can N'Djamena labarin bikin da ya zama uku ba ma biyu ba , watau Hamza ,Yakaka da kuma Rahima ƙarama .
Murna ta ishe su a can nan take suma suka shiga sabunta shiri , da daman suke tsakiya da yin sa , saboda dayawa daga cikin su ,wannan karon suna shirin zuwa saboda su gana da ƴar uwar su wacce ta ɓace shekara da shekaru har aka fidda rai da sake ganin ta ,
Cikin masu zuwan har da yayun su maza da matayen su da wasu daga cikin 'ya'yan su , sai kuma dangin su na wajen uwa da na uba duk gasu nan dai gayya guda ,
Nan take labarin auren ya sake bazuwa a tsakanin su , jin cewa har da na 'yar Rahima mace da Hamza ɗan Aminatu, da za'a musu haɗin gida, nan take suka yi sabon zama na musamman , inda suka sake ninka gudummawar su da zasu tafi da shi da daman turaren wuta ne da turaren jiki na ruwa ( Humra ) har ma da na wanka da mayukan jiki da na gashi , ( kulaccan da karkar ) suka ɗau nawin yiwa Rahima ƙarama gudummawar sa ,a matsayin su na dangin uwa sai suka sake ninkawa da wani haɗin turaren wutar da humran , su kulaccan da karkar makamancin wanda yake ajiye duk suka haɗa acikin manyan mazubai suka rufe ,
Sannan suka sake ƙarawa da kayan ƙamsasa girki da daɗaɗa shi irin nasu na can , haɗi da ingantattun ganyayyaki haɗin shayi ( tea ) da suke ƙara lafiya da kuzari tare da sanya nishaɗi, shima roba-roba suka keɓence shi .
Bayan haka matar baban wan su da ake ƙira Hajje khalsum ta ƙira Amnee tana sake tambayar ko akwai kuma wani abunda suke so a taho musu da shi daga nan N'Djamena ?
Nan Amnee tayi amfani da wannan damar take sanar da ita buƙatar ta na son a haɗo mata kaya gyaran jiki tare da magagungunan mata ,irin nasu masu ɗauke da sunadaran da suke ƙamsasa kowanne saƙo na jikin duk wata matar da take amfani da shi , bayan sun mata gyara ciki da bai .
Amnee ta cigaba da cewa a faɗa mata adadin kuɗin da zai isa a kawo kayan gyaran kashi uku , kafin ta gama bayani Hajje Khalsum ta katse ta , tana sanar da ita cewa ai wannan ta kawo cuta inda ake da tushen maganin ta , domin kuwa ƙanwar ta da suke uwa ɗaya uba ɗaya , ƙwararriya ce ta wannan fanni na gyaran mata ciki da waje , domin kuwa faɗin ƙasar su ansa da ingantattun magungunan ta , babban shago ne da ita anan babban birnin N'Djamena da taƙe sayar da irin waɗannan magungunan da kayan , har kuma ƙasa-da-ƙasa ake ɗaukar ta tana zuwa gyaran jikin , tare da haɗawa mata ingantattun magunguna dan haka kada ta damu , nan da kwanaki biyar inshaAllah zasu taho tare da ita .
Zuciyar Khaalty Rahima ta daɗa cika da ƙaunar 'yar uwar ta , domin ko bata faɗa ba tasan cewa dan Yakaka ne Amnee ta ƙira Mai gyara , da daman tuntuni take son tayi wani yunƙuri akai , amma kunya da kara suka hana ta ganin cewa duk wasu ragamar bikin na hannun Amnee , sai kuwa ga shi zata sa a gyara mata Yakaka ,
Duk abunda ake na zafafa shirye-shirye , Yakaka ta maida kan ta mai zaman ɗaki , daga kuma ta samu sarari sai ta shige banɗaki taci kukan ta , tsoro da damuwa sun hana ta walwala , tuƙuru tsoron rayuwar da zata riska nan gaba kaɗan take ,
Daga Amnee har Khaalty Rahima ba wacce ta bata sarari bare ta ji damuwar ta saboda sun riga sun san ko damuwar ta mecece ?dan haka suka kyale ta suna sabgogin su ,
Ganin bata yin wani shiri , ko alamun gayyatar ƙawaye koda na mutunci ne yasa suka fara lallashin ta kan cewa " yakamata ita ma ta gayyaci mutane , ranar auren ta rana ce mai ɗimbin tarihi wacce yakamata mutanen da duk tayi ko da zaman mutunci da su ne su shaida wannan ranar ,
Yakaka tace " ita fa bata da ƙawaye , ƙawarta ɗaya Lubna kuma tayi aure , bayan ita bata da wata ƙawa , da suka matsa mata ma kuka ta sa tana cewa " Amnee Mama kun san fa irin rayuwar da muka yi , ina mutane suka mu'amalance mu da mutuntawa bare har su kai mu kusa da su ? Da zamu iya ɗorar da zumunci idan bayan Malama Maryam da Lubna babu wasu mutane ta wajena ,
sai ta basu tausayi suka bar maganar , amma daga baya sai suka sa ta ƙira Malama Maryam ,bayan sun gaisa ta miƙawa Amnee wayar dan ita kunya take ji ta faɗi ranar auren ta da kanta , ta baki da baki Amnee ta shaida mata sanya ranar bikin 'yar ta kuma ɗalibar ta ,
Ba ƙaramar murna Malama Maryam tayi ba har ma tayi Alƙawarin halartar bikin ,
basu bi ta kan Yakaka ba wacce take faman ƙwalan-ƙwalan da ido tana son sake yin wani kukan , suka yi ficewar su daga ɗakin suka bar ta , dumuwar ba zai sa a fasa kome ba , domin na ɗan lokaci ne kuma gata ne babba ake shirin yi mata .
Cikin kwanakin nan Falmata sai ta fita walwala , domin ita labarin bikin Yakaka da Yaya dakta yayi awo gaba da kaso kusan talatin na damuwar ta , duk da cewa ba wai ta daina jin damuwa da rashin ji daga Biyamuradi bane , farin-cikin auren Yakaka ne yake saisaita mata damuwar ta .
Doctor Hamza kuwa tun ranar da ya isa Abuja ya so sanarwa da Sofiya halin da ake ciki kan lamarin aure da ya taso masa , saboda hakkin ta da yake kan sa ya zama dole ya sanar da ita .
Sai dai yadda ta tare shi cike da ɗoki kamar wanda ya shekara rabon sa da ita ba kwana guda ɗaya tal ba , sai ya kashe masa ƙwarin guiwar sanar da ita labarin da yake tafe da shi sanin da yayi ba abun farin-ciki bane a wajen ta,
Sai yayi zaune kawai yana bin ta da kallon yadda take ta ririta shi tana tarairayar sa , tayi kwalliyar ta fes-fes cikin riga da siket , ta mammatse manyan kayan da yafi so tare da ita sun firfito ko yaya ta motsa suna rangaji tare da dusashe masa ƙarfin gani suna tayar masa da kwaɗayi .
Shi dan ta shi tuni ya haƙura da ya zauna tare da ita ,ita kaɗai saboda a halin zaman su na aure babu ta inda ta kuskuro shi sai ta wajen girki wanda shi kuma hakan bai wani dame shi ba saboda shekarun girma da ya fara shigo masa , a matsayin sa na likita shekara arba'in ya kamata ya fara kiyaye kansa daga ciye-ciye barkatai da sunan jin daɗi .
Rashin haihuwar su kaɗai ke ɗan taɓa ransa , kuma yayi-yayi da ita taje asibiti ya haɗa ta da kwararrun likitocin mata su duba ta taƙi , daga baya yayi watsi da ita lokacin da ya fahimci akwai wata matsala tata da take ɓoye masa , koma menene ita ta sani shi dai ya san lafiyar sa rass , domin a farko-farkon shekarun auren su yayi gwaje-gwaje da dama kan rashin haihuwar su domin gano ina matsalar take ? Ta haka suka tabbatar masa da ingancin lafiyar ƙwayayen halittar sa dan haka shi bashi da fargaban kome ,
Yawan ƙaunar da take gwada masa salo-salo yasa yake ɗaga mata kafa , domin kuwa ta san ta kan sa sosai bai wani cika murɗe mata ba muddin ta raɓu da jikin sa ,
Domin a yanzu ma kasa sanar da ita labarin ƙarin auren sa yayi , maimakon haka kawai sai ya ɓige da neman samun nutsuwar gangar jikin sa ya shiga shinshinata yana gwada mata soyayya irin wacce ita dai tunda take da shi bai taɓa yi mata makamancin haka ba , zuciyar ta ta ji ta kunburo tana daɗa tunbatsa da ƙaunar sa , gefe guda kuma wani irin tsantsar farin-ciki take ciki , "yau Doctor ne yake nuna mata zallar so tare da kalamai masu tausasa zuciyar masoyi ? Babu shakka masu iya magana suna cewa daɗewa a mabauta ma ƴanci ce ."
Shi kuwa a ɓangaren sa zuwa washegari ya tabbatar dai ba zai fa iya sanar da ita ba , sai ya kuɗurce zai tura ta can Maiduguri da wuri , su da suka rakito auren sa san yadda zasu yi su sanar da ita domin shi Allah ya sani ba zai iya ƙarawa kansa damuwar haukar da sofiya zata iya yi ba akan ta shi damuwar da yake ciki , gara tayi haukar ta acan idan yaso ma ta huce akan ita Yakaka , shi duk wannan ba damuwar sa bace tsuntsun da ya jaa ruwa .
Saɓanin yadda ya zaci damuwar sa zata zama ƙanƙanuwa sai lamarin ya zarce tunanin sa domin tunda aka yi batun auren su kullum tsaffin laifukan ta daɗa sabunta kan su suke a zuciyar sa , baki ɗaya sai ya susuce kamar farkon lamarin .
Ya zama ko office ya tafi baya wani taɓuka aikin kirki , har waɗanda ke tare da shi suka fara fahimta , Suleiman Amininsa shine ya fara farga da yawan damuwar da yake ciki ya kuma matsa masa da tambaya ? a farko Doctor Hamza ba shi da niyyar
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 87 Chapter of 111