samaniyar garin da dare ya riga yayi duhu sai walkiya da cida ,alamun ruwan sama gaf yake da fara zuba .
A hankali yakaka ta ɗago falmata daga jikin ta tana share mata hawayen da suke zubowa daga gurbin idanun ta wanda idan ba an fada maka ba ko kuma ka lura kaga yadda suke tsaye kem alamun basa amfani uwa uba kagan ta tana lalube , baza ka taba cewa bata gani ba domin tar idanun ta biyu suke a buɗe ,ko meye sanadin makantar ta ? Ko haihuwar ta aka yi da shi ?
Ɗaga kai tayi ta sake kallon sama tana tunanin ina zasu samu mafaka daga dukan ruwan saman da yake daf da tsugewa , da sauri wata dabara ta faɗo mata cikin dusashiyar muryar tace falmata muyi sauri muyi sallah kin ga ruwa za'a fara ke kuma kin san kina rashin lafiya idan ruwan sama ya doke ki "zazzabi da mura" dan haka idan mun idar da sallah sai ki koma cikin randar ki bani hijabin ki na haɗa da zani na na rufa a bakin randar sai na daura murfin "wani ƙuzajjen farantin kwano ne" na rufe ki a ciki zuwa lokacin da ruwan zai tsaya sai musan in da zamu yi .
gƴada kai kawai falmata tayi , cikin sauri-sauri suka yi alwala suka duddungura sallolin su wanda kana gani kasan akwai ƙarancin ilmin addini a tare da su, ko kafin su gama an fara yayyafi da karfi da ya sanya yagana yanke doguwar addu'ar da ta fara ta kama hannun ƙanwar ta tare da kama mata ta koma cikin randar .
ko kafin ta gama toshe mata bakin randar ruwan ya riga ya tsinke, cikin hanzari ta gama rufewa ta tsugunna a bakin randar daga ita sai rigar ta da ɗankwali sai kuma siket ɗin ciki, haka ta takure jikinta ruwan nan yana dukan ta , ta ɗaura kanta akan gwaiwar ta hawaye yana sauka a idon ta tare da zubar ruwan saman da yake sauka a fuskar ta yana wanken hawayen da yake sauka, bakin ta ɗauke da addu'o'i iri-iri da take yin su cikin yaren ta.
Ruwan saman sai yayi kamar zai tsaya sai kuma ya sake tsugewa , a hankali sai da tsakar gidan su ya cika taf da ruwa, " kamar yadda ya saba" cikin karamar muyar falmata ta ankarar da yakaka wacce ta yi nisa cikin tunani har bata jin yawan ruwan da ya haura idon kafar ta ,"ruwa ya fara shigowa cikin randar yakaka,' cikin tashin hankali da sauri ta zame dankwalin kan ta ta matsa ruwan jiki ta sa dankwalin ta toshe hudar jikin randar da ruwan ya ke tsiyaya ciki ta ɓulin,
Ta sake tsugunnawa gami da takure jikin ta cikin jin matsanancin sanyi da wani ciwon kai da suka dirar mata lokaci daya , hakoranta sai karo da junan su suke tsabar karkarwa,
a hankali ruwan ya fara tsagaitawa bayan kwashe kimanin awa daya da kusan rabi ana tsugawa , sai iska me karfi da matsannancin sanyi ne yake busawo tare da sauran feshin ruwan saman .
*************
*MARAƊi Niger République*
Jihar maraɗi itace cibiyar kasuwanci a kasar Niger wacce Allah ya albarkace ta da masana'antu , masu kudi, da ma'aikata sanan kuma tana daya daga cikin garuruwa na kudancin Niger karkashin manyan garuruwan kasar hausa kuma ta kasance karkasin mulkin katsina shiyasa ma ake mata lakabi da katsinar maradi domin katsina ta mulke ta tun lokacin yakin kasar hausa kuma hasalima yanzu idan za a kira sarautar maraɗi sai ance sarkin katsinar maraɗi.
Kenan zamu iya cewa maraɗawa katsinawa , tun asali Maraɗi tayi yake yake sosai a kasar hausa inda taci nasarar wasu garuruwa wasu kuma su ka bata kashi amma dai tarihi ya nuna bamaraɗe jarumi ne kuma baya tsoro wanan shi yasa ta bunƙasa har zuwan turawan mulkin malaka a kasar hausa inda suka sha gwagwarmaya da turawa a wancan locakin ,a zamani sarkin katsinar maradi tsakanin shekara ta 1892 zuwa 1894 .
Bayan jihadin sheik usmanu fodio inda ya yaki sarakunan kasar hausa ya kuma jaddada addinin islama a wanan nahiyar ya kuma canza sarakuna da dama musaman wadanda suka bijirewa kaidodin sa maradi ta shiga cikin jerin kasashe da wanan abu ya ritsa da su
Kuma tasamu sarakuna 23 Tun daga kan Sarkin katsinar maradi Dan kassawa 1817, 1830
Har izuwa kan na yanzu .
Wannan kenan
Cikin Tafkeken falon wanda yake ɗauke da kayan ado da alatu , irin wanda ake samun su kaɗai gidan sarakai ,cikin masarautu irin namu na gargajiya ,
Mutane biyu ne cikin falon Mutumin da kallo daya za'a yi masa a hango girman cikar kamalar sa ,kasaitar sa da mulkin da ke gare shi yana zaune kan ɗunɗumemiyar kujerar da take ware daga tsakiyar falon tana fuskantar duk me shigowa cikin falon .
Gefe da gefen kujerar ƴan kananun teɓurin gilas ne dayan teburin saman sa ɗauke yake da ƴaƴan itatuwa nunannu lafiyayyu tun daga kan inabi,ruman ,zaitun,tuffa,tanjari, da sauran manyan ƴaƴan itatuwa masu daraja , ɗayan teburin kuwa ɗauke yake da wata kyakkyawar butar shayi da take kan wani babban farantin da suka zo tare ruwan zaiba tare da kananun kofunan ta da chokulan da daga gani du tare suka zo ,
Daga kasa kuma tsakanin kewayen manya-manyan kujerun da suka yiwa tafkeken falon ado , wani dogon saurayi ne wanda bayan sa kawai za'a kalla a gane tsawo da cikar halittar sa ta ɗa namiji kansa a sunkuye ,kafafun sa a tanƙwashe yayi zaman raƙumma gaban wannan mutumin yana sauraran duk wasu kalamomi da suke fitowa daga bakin sa ɗaya bayan ɗaya , da yake cewa ,
YOUSSOUFA na samu sakon bukatar da Ka zo da shi ,sai dai ina bukatar jin ƙarin bayani daga gare ka ,? Cikin kwantar da murya wanda aka kira da youssoufa ya ce ranka ya dade kamar yadda na fada wa jakadiya , wani aiki ne ya taso daga gwamnatin kasar nan wanda ta zabi sojoji kimanin dubu ɗaya da ɗari biyar, ta kuma wakiltani a matsayin shugaban su da zan jagorance su zuwa kai tallafin gaggawa ga yankin makociyar mu kasar Nigeria akan ƴan tawayen nan na boko haram da suka addabi yankin arewacin kasar wadda idan muka yi wasarere mu ma annobar tana iya shafar kasar mu nan Niger saboda boda da makoftakar da muke da juna ta kurkusa ,ya ɗan tsagaita gami da ɗaga kai ya kai kallon sa ga fuskar mutumin da ya zuba masa ido yake saurarar sa da dukkan hankalin sa.
Sake sunkui da kai yayi gami da cigaba da cewa shine nake neman alfarma akan a ɗaga biki zuwa lokacin da zan dawo wanda nake tunanin ba zai gaza nan da shekara ɗaya ba , do Allah ayi mini alfarma mai Martaba ,"ya karasa furta hakan cikin marairaicewa da kwantar da murya " ?
Ɗan gyaran murya yayi kafin yace ,wagga lamari naka da ban mamaki ike kai youssoufa anya aikin taimakon ƙasa zai wucce raya sunnah ? ɗan jim yayi ɗaga bisani yace tashi kaje du shawarar da muka yanke tana iso maka ta hannun jakadiya ,
Ras-ras yaji zuciyar sa ta tsinke tun da Mai Martaba yace sai yayi shawara yasan bai gamsu ba bai amince da alfarmar da ya nema ba hakan yana nufin bazai amince masa ya tai zuwa nigeria wanda kuma hakan yake dai-dai da rasa aikin sa da tun da yayi wayo a duniya ya san soja ya kasance bashi da wani burin da ya wuce ya zama SOJA , duk da kasancewar sa ɗan sarki kuma BIYAMARADI , haka ya dunga kawar da duk wasu kalubalen da zasu shiga tsakanin sa da cikar burin sa ya shaa gwagwarmayar da ta kawo sa kan matsayin da yake na yanzu me amsa cikakken sunan COLÓNEL YOUSSOUF ABDOUL AZIZOU BASKORE !!!!!!!....
[6/24, 9:49 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association
*MAFARI.......* ( _HARGITSIN RAYUWA_ )
*Umm'muaz*
2
Cikin sanyin jiki tare da rashin kuzari yake takawa yana wuce zauruka da sashi sashi kamar yadda aka San tsarin ginin masarauta yake.
Jerun gwanon bayin sa su rai biyar suna biye da shi tun daga ƙofar fada inda ya amsa kiran Mai martaba , tafe yake cikin kasaitar da ta amshi tsarin zubin sa na ingarman namiji dogo da ya kere dukkanin mutanen da suke tare da shi tsawo a lokacin.
fuskarnan tasa a murtuke kitib ya fito a SOJAN sa sak kuma BIYAMARADI, baya ko amsa gaisuwar bayin da suke ta faman zubewa a ƙasa suna kai gaisuwar su tare da kirarin da suka saba yi masa.
Biyamaradi dan sarki mai jiran kujerar mulkin kassar mu
albarka, kayi gadon mai martaba. Biyamaradi jarumin jarumai, biyamaradi namijin, ayi yau ayi gobe sai gaskiya jibi rago ya kassa.
Dan sarki mai makaman yaki, Dan sarki mai ado.
Biyamaradi kai zaki ne mai watsar da taron maza Dan sarki mai tarin illimi to kayi ga arabi ga boko wallahi ka kure tunanin Masu tunani.
Allah.ya kare ka gwani na hattara biyamaradi. hattara biyamaradi. Hattara biyamaradi HATTARA BIYAMARADI
Sai dai ga Biyamaradi yousoufa a yanzu sam basa burge shi basa sanya shi nishaɗi , babu abun da yake sanya shi nishaɗi a yanzu irin karar kafafuwan sojojin da suke jaan tunga su ƙame masa idan sun hango shi , babu muryoyin da suke burge shi irin na amsawar sojojin da ke karkashin ikon sa idan ya basu umarni ,
Dai-dai ya zo shiga sashin sa da yake bangare guda ko kuwa ɗaula guda a cikin gidan nasu ya ga wani hadimin sa ,wanda yana karasowa wajen ya zube ƙasa yana ƙirari tare da kai gaisuwar sa , bayin da suke tsaye a bayan sa su suka amsa da " Biyamaradi ya amsa gaisuwar ka meke tahe da kai ? " yana daga durkushe yake isar da sakon dalilin tsayuwar sa anan "jakadiya" ce tace ya zo ya jira shigowar yarima ya koma ya sanar da ita .
yana jin abin da bawan nan ya faɗi ya sanya kansa gaba gaɗi ya shiga gidan sa tare da yi wa bayin alama na kadda su biyo bayan sa , ( domin shi ya tsani taron bayun nan da suke zuwa du su zagaye shi su hana shi sakat ko wanne motsi yayi idanun su na kai suna yi masa surutun banza"kirari" a cewar sa)
babu wanda ya motsa daga inda yake cikin bayun nan domin idan da sabo yaci ace sun saba da tsarin halayyar BIYAMARADI"
Yousoufa shine ɗa na biyar a wurin mai martaba ɗa na huɗu a wurin mahaifiyar sa , kuma ɗa namiji na farko a gidan baki ɗaya , mahaifiyar sa ɗiya ce ga sarkin birnin gaoure, ita ce ƴa ta biyu cikin jerin ƴaƴan mai martaba Lamiɗo " Bafullatana ce gaba da baya kamar yadda kowa yasan birnin gaoure garin hullanin usul ne ,
Mahaifiyar yousoufa da mai martaba(sarkin maraɗi ) auren so da kauna suka yi , tun lokacin mai martaba bai kai ga hawa kujerar mulkin birnin maraɗi ba suka haɗu a wurin bikin yaye ɗalibai ƴan makarantar gaba da primary ta makarantar "École Bedir" da ke birnin Niamey a wancen zamanin da sai ƴaƴan wane-da-wane ke yin makarantar ,kanwar mai martaba " Zainab tana cikin ɗaliban da aka yaye a wannan shekarar ta alif dubu ɗaya da ɗari tara da saba'in da tara 1979, "wanda shi mai martaba Abdoul azizou ya wakilci mahaifin su wajen taron a lokacin shi ɗalibi ne a jami'ar Abdoul Moumouni Diof da ke nan cikin birnin Niamey"
Anan yaga safiyya , tana ɗaƴa daga cikin ƴan matan da aka zaɓa domin su gudanar da ƴar kwarya-kwaryar wasan koikoyo da akan yi lokacin bikin yaye ɗalibai , kallo ɗaya yayi wa ƴar fulanin yaji ta kwanta masa ya kuma ji cewar ya samu matar aure ,
Bai yi ƙasa a gwaiwa ba ya sanarwa zainab tare da gwada mata yarinyar daga nesa lokacin da aka kammala taron ana shirin watsewa nan take kuwa zainab ta shaida ta domin ta san safiyyah farin sani hasalima tamkar kanwar ta take domin koh lokacin da aka kawo safiyyah ajin farko a makarantar ita kuma tana aji na uku a lokacin ɗakin kwanan su guda su biyu ne rak a ɗakin kasancewar haka tsarin ɗakunan kwanan ɗalibai na makarantar yake, mutane bibbiyu ne a kowanne ɗaki , sun shekara guda tare cikin aminci har zuwa lokacin da ita zainab ta shiga ajin manyan ƴan secondry "aji huɗu" a lokacin ne aka sauya mata ɗaki ta koma saman bene a hawa na farko ,
Hakan ne yasa koh da yayan ta ya nuna ra'ayin sa akan safiyyah taji dadi sosai kuma ta wuce masa gaba ta gabatar da shi a wurin safiyyah duk da cewa dai ita a lokacin ne ma take aji na huɗu , Amma tayi na'am tare da maraba da bamarɗe Abdoul azezu .
Haka dai tafiya sannu-sannu suna tare cikin aminci da so da ƙaunar junan su har zuwa lokacin da safiyyah ta kammala karatun gaba da primary a shekarar mai martaba sarki Youssoufa Baskore mahaifin "Abdoul azizou ƴa tura da takardar neman aure da kayan nagani ina so ga masarautar sarki lamiɗo na barnin gaoure inda shima bai yi kasa a gwaiwa ba ya amsa cikin tsantsar farin ciki da lamarin "domin a garesu hakan babbar nasara ce kasantuwar kowa ya san sarautar maraɗi ita ce ta biyu a karfin mulki kaf kasar niger "
Aka tsaida ranar auren su sha biyar ga watan satumber na shekarar alif dubu ɗaya da ɗari tara da tamanin da ɗaya "15-sept-19981, rana ta zo aka sha biki amarya ta tare a gidan mijin ta sasahi guda a cikin gidan sarautar maraɗi .
Kwance tashi rayuwar su ta fara miƙawa cikin aminci fahimtar juna da tsantsar ƙaunar junan su , Allah ya Albarkace su da haihuwar ɗiya mace shekara ɗaya da auren su wacce ta ci sunan marigayiya mahaifiyar su Abdoul-azizou wacce ta jima da rasuwa tun su na yara ,"Halimatu'sa'adiyyah" ana kiran ta "Ammi"
Tsakani shekara biyu cif da safiyyah ta sake haihuwar ɗiya mace aka sanya mata sunan mahaifiyar safiyyah "Suwaiba" ana kiran ta "dada "
Bayan watanni tara da haihuwar "dada "
safiyyah ta sake samun ciki ta haifo "zainab" wacce ta ci sunan kanwar Abdoul-azizou sai ake kiran ta "ubbo"
Tun daga nan fa sai mai martaba sarki Youssoufa ya ce Abdoul-azizou sai ya sake aure koh ya samu magaji tun da ga alama matar sa uwar ƴan mata ce , babu yadda Abdoul-azizou bai yi ba akan ya fahimtar da mai martaba haihuwa kyautar Allah ce babu ɗiya mace koh ɗa namiji dukkaninnsu ɗaya ne har kullum masu albarka ake nema .
Sai dai fir mai martaba yaki saurarar sa domin a gefe guda "hajiya uwa " da takasance matar sarki ta biyu "wacce take matsayin babbar matar sarki tun bayan rasuwar mahaifiyar su Abdoul-azizou " a lokacin ta samu wuri sai daɗa hura wutar kiyayyar ɗiyoyi matan da ake haihuwa a gidan abdoul-azezu take " a cewar ta sarauta ta kama hanyar barin hannun Baskore tunda ga alamu Sarautar tana dakatawa ne akan Abdoul-azizou da yake a matsayin yarima a lokacin ,
Ba tare da neman shawarar Abdoul-azizou ba mai martaba ya nema masa Auren ƴar abokin sa kuma yayan matar sa "Hajiya uwa "Babban Limamin Maraɗi "Malam muhammadou" wacce ake kira "Saratu " .
Tare da sa hannun hajiya uwa wacce tayi ɗare-ɗare akan harkar bikin nan tayi uwa tayi makarɓiya , ranta ƙwal ! tana ƙitsimawa "idan sarauta ta kuskure masu ta wani wuri kasancewar ita bata taɓa haihuwa ba toh tabbas ga sarautar nan dawo masu ta wani hannu " tana da tabbacin daga saratu ta zo ta haifi ɗa namji shikenan sarauta ta zamto tasu.
Saratu ita ce ɗiya ta shiddah cikin jerin ƴaƴan Liman muhamdou , mahaifiyar ta tun tana ƴar shekaru biyu suka rabu da mahaifin ta "mahaifiyar ta ƴar Nigeria ce a can wani gari da ake kira zuru a ƙasar kebbi Nigeria , Saratu ta taso tsakanƙanin matan uba , babu irin izaya da wahalar da ba'a gana mata ba , shi ya sa ta tashi a kangare sannan me mummunar zuciyar da take cike da ƙudirin ɗaukar fansa,
Lokacin da ta shekara goma sha biyar ta kasance fanɗararriyar yarinya ce ta kin ƙarawa wacce tun da ta fara girma ta buwayi matan mahaifin nata da fitsara da raini uwa uba saratu ta kasance me matukar fasahar iya shirya zancen ƙarya da tuggu domin ta tada husuma a tsakanin matan mahaifin ta duk a cikin mummunan ƙudirin ta na ɗaukar fansa .
A take -take zata haɗa zantukan ƙarya ta ɗora mutum kome girman sa akai kuma ya hau ya zauna daram , saboda tsabar yadda ta iya shirin ƙarya , wasa-wasa sai da ta maida gidan mahaifin ta sansanin yaki a wurin matan gidan , kullum cikin faɗa ake kamar garken karnuka , ita kuwa ta koma gefe tana wake-waken ta ,bayan idanun su ta shiga ɗaki ta ci dariya son ran ta ta fito tsakar gida tana karya wuya tare da bai wa wacce ta zuga hakuri .(Saratu kenan , ƴar malam wacce taƙi halin malam )
A tsakanin matan mahaifinta su uku babu wacce ta kai ga fahimtar hallayar saratu na karya da munafurci "sakamakon rashin haɗin kan su tare da zazzafan kishin su tun asali " sai shi mahaifin nata ne da kan sa ya fahimci "saratu ita ce matsalar gidan sa " yana tunanin yadda zai iyi ya samu ya kawar da ita daga gidan sa "( ya aurar da ita ) .
Sai ga sakon kira daga mai martaba "Liman bai yi ƙasa a gwaiwa ba "ya amsa kiran da ya sanya shi kwanan farin ciki bibbiyu na farko dai farin cikin zai zama surikin yariman maraɗi a yanzu , kuma surikin sarkin maraɗi a gobe idan da rai , uwa uba zai rabu da annobar da ta ke sanya shi fargabar shigar sa gidan sa a kullum,
Dan haka cikin rawar jiki da murnar sa da ta kasa boyuwa ya amsawa mai martaba sarki youssoufa , ya bawa yarima Abdoul azizou auren Saratu koh gobe ake so a ɗaura ya shirya ,
cikin farin ciki da karamci da aka nuna masa Sarki youssoufa ya tsayar da ranar ɗaurin auren Abdoul azizou da saratu ranar ishirin da biyar ga watan sha biyu shekara ta alif dubu daya da ɗari tara da tamanin da biyar 25-Dec-1985 .
A daren ranar ya aika aka kira masa yarima abdoul azizou , in da ya sanar da shi hukuncin da ya yanke tare da bashi umarnin ya shirya gobe da Maraice ya je su ga juna shi da saratu ɗiyar liman domin kwanaki ishirin da ɗaya kachal suka rage a ɗaura musu aure ,
Ba tare da yarima Abdoul azizou yana fahimtar sauran kalaman bakin mai martaba ba ya amsa masa gami da yi masa godiya da sallama ya fito daga turakar mai martaban zuciyar sa cike da zogi da raɗaɗin bacin ran tashin hankalin da yake iya hango samuwar sa tsakanin sa da abar son sa "safiyyah "
Tabbas shi yasan yadda safiyyah take tsananin kaunar sa da kishin sa , yasan duk lokacin da ya je mata da labarin auren da aka riga aka nema masa ya kuma zama dole a gareshi ya amsa hannu bibbiyu , kasantuwar bai taɓa musantawa mahaifin sa ba akan duk wani hukunci da ya yanke a rayuwar sa domin shi mutum ne me ilmin addini sosai , yayi karatu sosai arabi da boko ya san irin haƙoƙin da iyaye suke da shi akan ƴa ƴan su hakan ya sa ya kasance ɗa mai tsananin biyayyah ga iyayen sa .
Dan haka a yanzu ma yayi aniyar karban auren da za'a yi masa da hannun aminci duk da cewa shi ba son auren yake ba asalima bai taba kawowa ransa sake yin aure nan kurkusa ba kamar yadda tun da yake bai taɓa son wata ɗiya mace irin son da yake yi wa safiyar sa ba kuma baya jin zai sake son wata ƴa mace irin son da yake yi mata " ya ajiye auren da za'a yi masa a karo na biyu a mizanin kaddara "
Sai dai babbar matsalar sa a yanzu tunanin hanyar da zai bi ya tunkari saffiyah da batun karin auren sa ,"a daren yau din domin baya son ma lamarin ya kwana ba tare da ya fitar mata da hakkin ta ya sanar mata ba a matsayin ta na matar sa da suke zaman aminci , kaunar juna da fahimtar juna " sai dai ya san mata idan aka zo batun kishiya ba dama ne '
Haka dai ya shiga gidan nasa baya sun natsa ya fuskance ta da maganar auren , sai dai ga mamakin sa ,' bata tayar da hankalin ta irin yadda yake zato ba hakan kuwa yana da nasaba da zancen ya riga shi isowa zuwa kunnuwan ta "
Abun nufi ta ji zance a cikin gida " abun ka da gidan sarauta da kuma yadda ya kasance hajiya uwa tana ta yamiɗiɗi da zance tana yada magana tare da fiffikar ta ta zata shigo gidan " da farko bata fahimci zancen ba sai da ta tambayi jakadiyar sarki ta wancen zamanin ita ce ta warware mata zare da abawa ta kuma kwantar mata da hankali tare da bata shawarwarin alkhairi da za su taimaka mata.
Amma duk da haka bayan dawowar ta sashin ta yini tayi tana kuka tare da tunanin ƙalubalen da yake fuskanto ta "abu ɗaya ne ya rage mata jin zafi ji da tayi matar da za'a aurawa mijin nata ba ƴar wani babban sarki bace ko kuwa wani hamshaƙin attajirin da kasa ta san da shi ba "
Ƴar Limamin Maraɗi ce hakan sosai ya rage mata zafi kasancewar safiyyah irin ƴaƴan sarautan nan ce masu ji da kan su da nuna isa sosai jinin sarauta na ƙasaita , da iko suke yawo a jikin ta ta yadda take ganin duk wani wanda ba ɗan sarautar da ya kai ya kawo ba a matsayin kasasshe a wurin ta,
safiyyah tana son sarauta tana alfahari da sarauta tana kuma ƙaunar masu sarauta , bata daukar mutanen da basu da sarauta da wani muhimmanci a rayuwar ta .
Dan haka koh lokacin da ranar da aka yanke na ɗaurin auren Abdoul-azizou da saratu ya zo , aka kuma ɗaura auren cikin kwanciyar hankali tare da bakukuwa kamar yadda yake a al'adar su , sam safiyyah bata bayyana matsanancin tashin hankalin ta ba duk kuwa da cewar abun yana nuƙurkusar ta a karkashin rai !Saboda yadda take kaunar mijin ta sai ga shi a yanzu ya zama nasu ita da wacce take ganin bata kai matsayin ta haɗa kafaɗa da ita akan abun da take so ba .
Hakan ya sa bayan tarewar Saratu "a sashin ta da aka gina mata daura da sashin Safiyyah ta hannun hagu "Sam safiyyar bata shiga harkar Saratu "A ganin ta saratu bata isa tayi gogayya da ita ba " "iyakaci idan sun haɗu a cikin gida 'idan sun je gaishe da hajiya uwa da sauran matan mai martaba biyu "Hajiya mai karamin ɗaki da umma Amarya " " su gaisa da juna sama-sama, sosai ita saratu take jin zafin yadda safiyyah ta tattara ta tare da shirgin ta ta watsar a gefe take nuna kamar bata san ma da zaman ta a cikin gidan ba , "
Hakan yana kona ran ta , domin ita ta shigo gidan ne da nufin ta dunga bi ta ƙasa-ƙasa irin yadda ta saba ( a gidan mahaifin ta) tana tunzura safiyyah tana tada bala'i a tsakanin ta da Abdoul-azizu har dai tayi nasarar dusashe karfin soyayyar da ta lura Abdoul-azizu na yi wa safiyyah ,ta yadda ya kasance idan suna tare koyaushe bakin sa cikin ambaton Alkhairin safiyyah da kyawawan halayenta tare da yabawa safiyyar yake ,"
Sai dai bata samu damar hakan ba domin duk wata kafar da zata bata damar aiwatar da mummunan nufin ta safiyyah ta toshe "ta hana ta fuska "
A cikin hakan ta fara laulayin ciki bayan watanni biyu da auren su "wanda kuma kusan tare suka ɗau cikin da safiyyah " domin ita ma tana ɗauke da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 111