biyu na ci abinci na saya da hansin ɗin safen kuma baba mai kayan miya ma ya saya min biski da miyar yakuwa naci ɗazu da la'asar ,' anjima da dare kafin muyi bacci sai mu ci wannan ɗin , yanzu ni sallah nake so nayi ,!
******
Dare ya tsala yakaka ta gaza yin baccin kirki daga ta fara sai ta farka, sai juyi take yi ta tattake a cikin abun rufuwar ta tayi matashi da jakar kayan ta ,
Ba kome ne ya hana ta bacci ba illa ciwon baya da kai , ga kuma matsanancin tsoron karnuka da take jiyo kukan su kurkusa da inda suke , zuciyar ta sai dakan lugude take ,
A hankali ta zira hannu ta lalubi wurin da falmata ke kwance , wayam ta ji bata nan , sake baza hannun ta tayi , ba shiri ta bankaɗa abun rufuwar ta gami da miƙewa zaune , duhu ne bakikkirin a cikin rumfar har ba'a iya ganin tafin hannun , murya ƙasa-ƙasa ta kira sunan falmata ,"
Shiru ta ji
Da ɗan ƙarfi ta sake kiran sunan tana mai miƙewa tsaye ,
Haske ta ga ya ratso rumfar kafin ta ga shigowar falmatan tana lalube , da sauri ta taka ta kamo ta zuwa cikin jikin ta ta riƙe , murya ƙasa-ƙasa tace
Falmata ina kika je ? Meyasa kika fita ? Ke bakya tsoron dare ne ?
Yakaka fitsari na ɗan je baya nan nayi ba nisa sosai ba
Meyasa baki tashe ni ba ,? Kar ki sake irin haka , ba a cikin gida muke ba a bakin kasuwa muke bakin titi cikin rumfa , babu kowa sai mu kaɗai !
Toh ta amsa mata
Daga haka suka kwanta ƙwaƙume da jikin juna ko yaya ɗayan su ya motsa ɗayan zai iya ji ,"
Asubar fari suka tashi suka yi sallah suka ɗan sake kwanciya zuwa lokacin da gari zai ƙarasa wayewa ai kuwa waɓi daddaɗan barci ya kwashe su tare da taimakon sanyin asuba ba su suka farka ba sai da hayaniyar jama'ah da ƙarar motoci ya fara yawa wuraren takwas da rabi ,
Yakaka mun yi bacci dayawa , cewar falmata
Mu wanke baki mu ci abincin ALLAH ya sa bai lalace ba , ilai kuwa suna buɗe robar warin lalatatcen wake da shinkafa da miyar ya bigi hancin su ba shiri suka maida murfin ,
Bari na fita na sayo mana abin karyawa me zaki ci ? Fanke ko ƙosai ? Ko doya ko masa ?
Ni kawai duk abinda zaki ci yakaka , ki nuna min wurin da zanje na zubar da abincin nan na wanke masa kwanukan ?
Kwanci tashi suka yi kwanaki a bakin kasuwa suna gudanar da al'amuran su cikin jin dadi , ƴanci tare da walwala , sosai rayuwar da suke yi a bakin kasuwa ta fiye musu duk wata rayuwar da suka taɓa yi a cikin birnin maiduguri daɗi da kwanciyar hankali , zasu ci su sha kuma su adana ƴan kuɗaɗen su , babu ƙyara babu tsangwama ,
Ka'in da na'in yakaka ta kama aikatau ɗin ta ta riƙe kullum a chan take yini tana aiki chan take cin abincin rana , sai yamma lis take komawa gida , tayi wankan ta fes a banɗakin wurin aikin ta , a hanya zata ɗan saya musu ƴan kayan gwari da ake yayin su lokacin , karas ,lemo ,cashut da sauran su ,
Falmata kuwa har ta gane hanya daga wurin barar ta zuwa ƴar rumfar kwanan su , dan haka ta daina jiran yakaka ta zo ta mayar ta , daga ta ji kasuwa ta fara alamun watsewa sai ita ma ta tafi bakin rumfar ta jira zuwan yakaka , a hankali har suka fara sabo da jama'ar kewayen wurin ,
Yau an tashi garin a ɗan hargitse sakamakon kwana da aka yi ana ɗauki ba daɗi da ƴan tawayen boko haram da suke neman shigowa garin ta karfi ta wani yanki , sai dai basu samu nasara ba dakarun soji sun tarwatsa su wanda hakan ya jaa dayawa daga cikin su sun fantsama cikin gari da hakan kuma yake babbar barazana ga rayukan al'umma .
Saboda ɗaukar mataki sai soji suka fantsama cikin gari , tare da sanya dokar hana zirga-zirgan motoci akan manyan titunan garin , kasuwar kan ta yau ba'a buɗe ta ba duk inda ka bi motocin soji ne suke kai kawo ,
Jugum-jugum falmata da yakaka suka yi , su sam basa ƙaunar wannan jiniyar ta motar sojoji , tsinka musu zuciya take ta tada musu hankula kamar yadda ya faru a yanzu tun safe sun gaza ko cin abinci sai faman wuri-wuri suke , ko ƙwaƙwarar magana sun gagara yi da junan su , illa hannun su da yake cikin na juna , lokaci zuwa lokaci yakaka tana ɗan leƙawa ta tsaƙanin labulen rumfar su tana ganin yadda garin yake shal tamkar an share .
Sun kwashe tsawon lokaci a haka , har zuwa lokacin da suka ji an kamo wasu gungun mutane an wuce da su ana ta dukan su ,
Basa fahimtar maganganun da suke tashi a wurin illa dai suna jin ana yawan ambaton kalmar boko haram , boko haram , boko haram !
Yakaka ta so leƙawa ta ga ko su waye ,? Amma sai ta ji falmata ta sake damƙe mata hannu , ƙasa ƙasa ta ji tace
Yakaka kar ki leƙa , tsoro nake ji , zuciya ta bugawa take , yakaka mu yi addu'a kar su gan mu su kashe mu .
Wucewar mutanen bai fi da mintoci biyar ba suka ji ƙarar fashewar bam da matuƙar ƙarfi har sai da rumfar da suke ciki ta girgiza ,
Harbe harben bindigogi ya biyo bayan tashin bam ɗin tare da guje -guje har ta gaban rumfar su suke jin takun gudun mutane tare da wucewar harsashi ,"
Iyakacin ruɗani tare da tashin hankali sun shiga kuka suke yi suna tsaye charko charko cikin rumfar ,"
Suna nan tsaye falmata ta ji wani ƙaƙƙarfan abu ya bugi kafaɗar ta ya wuce wanda sai da ya sa tayi baya da karfi ta bugu da jikin kofar shagon kafin ta silale ƙasa , cikin wani irin azabar raɗaɗi da take ji yana gauraya illahirin jikin ta takamaimai bata san ina ne yake mata ciwo ba ,
a razane yakaka ta jiyo jin yadda hannun falmata ya kufce daga cikin nata , abun da tayi arba da shi ya sa zuciyar ta ta tsaya da bugawa , bata san lokacin da ta zube a ƙasa ba tare da tallafo falmata wacce jini ke malala daga jikin ta , idanun ta suna rufuwa su buɗu da kan su , jikin ta kuwa babu inda baya rawa ,.'
Falmataaa
ta kira sunan ta da wata irin murya tamkar ba tata ba , wani irin ihu ta kurma lokacin da ta fahimci abun da ya faru ,.......!
Masha Allah ina gaida masoyan littafin mafari a duk inda suke !
Vote
Share
Comments
[6/24, 10:59 AM] +234 701 013 7848: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
umm'muaz
22
Da gudu ta tako ta fito daga ƴar rumfar , yanayin da ta ga falmata a ciki ya mantar da ita duk wani halin fargaba da tsoron soji da suke ciki ,
Tana kuka ta nufi bakin titin inda ta hango gungun soji da wasu mutane farar hula suna tsaye , tun kafin ta karaso gudun da ta taho da shi ya ɗau hankalin su ,tare da ihun da take faman yi
Tana ƙarasowa ta zube a gaban su ba tare da ta ji tsoron bakin bindigar da ta ga sojojin suna gyarawa ba tare da saita ta da ita ,"
Da rishin kuka take cewa kun harbi ƙanwa ta , zata mutu , kun kashe min ƙanwa ta me tayi muku ? Mu ba boko haram bane , meyasa zaku harbe ta wayyo Allah ƙanwa ta ,"
Wasu daga cikin su sun fahimci abun da tace dan haka wani daga cikin su fararen hula ya ɗan matso kusa da ita ,
Ina ƙanwar taki take ?
Waiwayawa tayi tana nuno masa ƴar rumfar da suke ciki , tsabar kuka da ruɗanin da take ciki har numfashin ta sarƙewa yake yi ,
Su biyu suka nufi rumfar
Yakaka ta take musu baya
Nan take suka fahimci bullet ne ya samu falmata a kafaɗa cikin rashin sani ,"
Da gudu gudu suka koma wajen sojojin tare da neman taimakon su akan a kai yarinyar asibitin kurkusa , ba tare da gaddama ba soja ɗaya ya amince zai jaa su a motar su ta soji .
Dan haka suka ciccibo falmata wacce ta riga ta suma suka ɗora ta bayan hilux ɗin sojin tare da yakaka wacce idan banda sambatun kiran sunan falmata babu abun da take gaba ɗaƴa ta ƙanƙame falmatan a jikin ta .
Da isar su babban asibitin gwamnatin jaha ( general hospital ) wanda bashi da wani tazara mai yawa da bakin kasuwar , aka shige da falmata bangaren bada taimakon gaggawa ( Accident and emergency) nan suka tarar da mutane dayawa da suke cikin hali makamancin na falmatan wanda tarzomar jiya ta ritsa da su birjik , wasu sun ji munanan raunika , wasu babu hannu , wasu ba ƙafa , likitocin da suke kan aiki sai kai kawo suke , da alama sun gaji likis ga har zuwa yanzu akwai waɗanda ko kai ga fara basu taimako ba'a yi ba ,
Nan suka ajiye falmata akan dandaryar siminti bakin kofar domin duk gadajen da suke cikin ɗakin a cike suke ,
Bayan sojan ya shiga ciki yayi musu bayani , likitocin suka ce a ajiye ta kawai zasu zo kan ta domin aiki ya musu yawa , ko kuma idan likitocin safe sun zo su duba su tun da sun ce harsashin a kafaɗa ya same ta da sauki akan waɗanda bam ya tashi da su ,
Tsayuwar da bata fi ta rabin awa ba mutanen da suka kawo su suka yi , suka matso kusa da yakaka wacce har zuwa lokacin idanun ta zubar hawaye suke har sun kumbura ,
Yarinya mu zamu tafi , domin muna da aiyuka a gaban mu , su kuma likitocin nan ƴan walakanci ne basu da niyyar zuwa su duba ta , ki cigaba da jiran su , sannan ki dunga leƙawa kina damun su akan su zo su duba ta , idan kuwa ba haka ba har jinin jikin ta sai ya ƙare ta mutu anan indai likitocin nan ne babu abun da ya dame su , mu mun tafi ,
ga wannan ki rike a hannun ki ko zasu ce ki sayo wani magani ,suka miƙa mata dubu ɗaya suka kaɗa kan su suka yi ficewar su ba tare da sun sake kallon inda falmata take yashe a ƙasa ba ,"
Wani sabon kuka ta sake fashewa da shi tana tattaɓa fuskar falmata wacce tayi sanyi ƙalau ,"
Falmata na dan Allah kar ki bar ni , Falmata dan Allah ki tashi ,'
Kamar mahaukaciya ta yunƙura ta tashi ta bazama ta faɗa cikin ɗakin da ake duba marasa lafiyan ,"
Tana shiga nurses ɗin da suke taya likitocin aiki suka yi mata chaa ,"
Mata meye hakan ? Baki ga aiki muke ba zaki zo kan mu da ihu ? Ki koma daga waje ki jira a fito da marar lafiyan ku , ba'a shigowa nan idan ba mu muka kira mutum ba fita-fita dallah ,"
Kuka ta fashe da shi
falmata na zata mutu dan Allah likita ki zo muje ki duba ta jini sai zuba yake daga jikin ta jinin ta zai ƙare ta mutu idan ta mutu bani da kowa ,"
Kalaman ta suka doki kunnuwan sa yayi tsai daga aikin ɗinkewa wani mutum mummunan rauni da yake yi ,"
Tabbas ita ce , ita ce da kullum damuwar ta yake ga falmata ƙanwar ta ita ce da kullum hawayen ta yake zuba akan ƙanwar ta falmata , bata da wani abu mafi muhimmanci da ya wuce ƙanwar ta falmata , ita ce wacce ya kwashi watanni yana neman ta har ya zo ya haƙura ,
Cikin nutsuwa ya waiwayo yana duban inda take lokacin da nurse ɗin ta sanya wata security guard da take tsaye daga bakin kofa , tayi waje da ita domin tana son bata musu aiki ,"
Security guard ɗin ta cukuikuyo hijabin ta tana tura ta waje ,
Ita kuma tana sake ƙara karfin kukan ta tare da neman su taimaka mata ƙanwar ta kar ta mutu ,"
Hey jumai let her come in .
Suka tsinkayi muryar babban likitan su da yake duty , ya bada umarni
A tare suka waiwaya da yakaka wacce jin muryar sa ya sa ta waiwayo da fatan son kasancewar shi ne da gaske a wurin ai kuwa tayi arba da shi jikin sa sanye da korayen kaya ,'ɗan siririn farin gilashin da yake ɗore saman karan hancin sa bai isa ya sa ta gaza gane shi ba ,"
Da ƙarfi ta fizge jikin ta daga riƙon da security tayi mata , ta tako da gudun gaske ta ƙurɗo ta tsakanin gadajen marasa lafiya tana zuwa ta kamo hannun sa da yake cikin safar hannu ta duba marasa lafiya ta shiga jaan sa tana cewa
Dakta ƙanwata falmata ai ka san ta ko ? Ita ce harsashin bindiga ya same ta , ta suma kamar ta mutu jini yana ta zuba a jikin ta , dan Allah ka zo muje ka duba ta ,kar ta mutu dan Allah ka taimaka min !
A hankali ya zame hannun sa daga riƙon da tayi masa , ya maida duban sa ga nurses ɗin da suke tsaye
Ku sa a shigo da ita !
Doctor bamu da gadon da zamu ajiye ta ,"
Yana mai komawa bakin aikin sa yace
A nemo gado a ɗaura ta akai yanzu zan duba ta ,'
Biyu daga cikin nurses ɗin suka fita tare da security guard ɗin , yayin da ɗaya ta aunawa yakaka harara ,
Ai Sai ki fita mata , domin ba'a tsayuwa anan ,'
Ba tare da ya juyo ba yace
Sister kalsum ki bar ta ta tsaya anan , yanzu za'a shigo da ƙanwar ta ,!
Tashin hankalin da ya hango a fuskar ta ya taɓa masa zuciya sosai ,"yana jin tausayin ta mai ƙarfi yana taso masa , ita kullum a cikin kuka da wahala take !
Mokaɗe baki nurse kalsum tayi ,
Cikin ran ta tana son sani alaƙar dactor hamza da wannan kucincinannar yarinyar ƙazama !
Cikin mintoci goma sai ga falmata an turo ta a gadon marasa lafiya an shigo da ita ," da hakan ya zo dai-dai da kammala aikin da yake yi ,
Ya tako ya zo gaban gadon falmatan ya duba ta tare da yin aune aune , nan ya fahimci ta zubda jini dayawa da ya sa dole sai anyi mata ƙarin jini , bayan an cire harsashin da yake cikin jikin ta
Dan haka yayi umarni a kare gadon falmatan a kuma sauya mata kaya zuwa na tiyata," sannan ya juyo da ganin sa ga yakaka , cikin tausasa murya tare da sigar lallashi yace ,
Ki nutsu ki daina kuka haka kin ji ko ? Ki samu wuri ki zauna a waje ,ki sayi ruwa ki sha ,insha Allah babu abun da zai samu ƙanwar ki , ɗan rauni kaɗan ta ji kuma yanzu zan cire mata harsashin na ɗinke mata wajen na sa magani zuwa anjima zata farka kuyi magana kin ji ko ?
Gƴaɗa kai tayi tana duban fuskar sa
cikin son samun tabbaci ta ce
" Ka ce zata samu sauki har ta tashi anjima koh ?
Sosai kuwa insha Allah
ya bata ansa yana mai duban ƙwarar idanun ta da tsabar kuka ya sauya musu launi ,"
da jan ƙafa ta fice tana waiwayan inda falmatan take ,
Shi kuma ya juya ya ɗau wata ƴar takadda yayi rubuce rubucen sa ya kira ɗaya daga cikin ma'aikatan da suke tura gadajen marasa lafiya/kujerar marar lafiya , ɗauko file da sauran su , ya miƙa masa takkadar bayan yayi Signature ya buga Stamp .
Ka je blood bank ka kai musu , ka tsaya ka ƙarbo jinin ka kawo .
Toh sir
Cikin gwanancewa ya fara aiki ga falmata !
Bayan awa ɗaya ya kammala ya ɗaura mata jinin da aka kawo leda ɗaya bayan yayi mata allurai ,
Sai da ya sake jaddadawa nurses ɗin da suka karɓi aiki akan su kula da ita Ƙanwar sa ce , bayan yayi bankwana da likitan da ya ƙarbe shi a bakin aiki ya shigar masa da duk wasu bayanai akan marasa lafiyan da ya duba ciki har da falmata da ya roƙi Alfarma a lura da ita da kyau , abokin aikin nasa ya amsa da zai kula da ita sosai .
Cikin takun da yake nuna tsabar gajiyar da yayi ya fito daga ɗakin , yana goge ruwan hannuwan sa da ya wanke da farin ƙyalle .
Tana hango fitowar shi ta miƙe daga inda take durƙushe a jikin bango ta nufo shi ,"
Cikin nazari ya tsaida idanun sa akan ta tana tahowa yana son tabbatar da zargin sa akan alamomin masu juna biyu da yake gani tare da ita alhalin shi a budurwa ya san ta .
Dakta ta farka ? Tana magana ? Jinin ya daina zuba daga jikin ta ? Ko na shiga na gan ta ??
Bin fuskar ta da tayi jazur da kallo yake yana ganin yadda fatar bakin ta ta bushe idanun ta suka kumbura,
Bai amsa mata tambayoyin ba , yace mata
Zo muje !
Ta bishi a baya tana waiwayen ɗakin da falmata take ciki , so take tayi gaddamar bin sa sai dai ta kasa ,
A bakin wani ɗan shagon da ake sayar da kayan sanyi da kayan fulawa irin su Biscuits, cake , meat pie , donut da sauran su , suka tsaya
Duban sa ya mayar kan fuskar ta cikin kulawa yace me zaki ci marar nawi sosai ? Zaki sha Hollondia yogurt ? Ko juice kika fi so ? Cake zaki ci koh meat pie ?
Wani jirkitatcen kallo ta yi masa , falmata tana cikin yanayi irin wannan har shi yana tunanin zata iya cin wani abu ? Ai ita ko ruwa baza ta iya sha ba idan ba ta ga farkawar falmata cikin ƙoshin lafiya ba .
Sunkui da kan ta tayi daga kallon fuskar sa ,' cikin siririyar murya tace
Bana cin kome bana jin yunwa , dakta dan Allah ya jikin falmata ? Ta samu sauki , ka kai ni na gan ta dan Allah ,
Bai amsa mata ba sai ya maida ganin sa kan mai shagon da yake tsaye ta cikin ɗan shagon sa yana kallon su .
Bamu hollondia yogurt babbar roba ɗaya da Chii exotics babba ɗaya , meat pie guda uku , tare da ruwan roba guda ɗaya .
Suna tsaye ya haɗa a leda ya miko musu , dakta hamza ya karɓa gami da miƙa kuɗi aka bashi chanjin sa ,
A takaice yace mata
Mu tafi ! Yana mai yin gaba
Cikin ƙosawa ta bi shi a baya .
Wurin da motar sa take ajiye a wajen tsayuwa na musamman ya ƙarasa , gami da buɗe motar ya shiga
Ita ma yayi mata umarni da ta shiga bayan ya buɗe mata ɗayan bangaren ,"
Ta shiga ta zauna gami da mayar da kan ta jikin murfin motar ta kwantar tana jin wani irin yanayi marar daɗi yana taso mata , sam ita bata son takurar da yake yi mata a koyaushe idan suka haɗu ,!
Ledar da kayan da ya sayo suke ciki ya ɗora mata akan cinyar ta .
Bana son musu ko doguwar magana ki cinye kuma ki shanye duk abinda yake cikin ledar nan , ƙanwar ki na mata aiki na bata magunguna yanzu haka bacci take daga ta tashi zaki ganta insha Allah baza ta ɗauki lokaci mai tsawo ba zata warke, idan har kun zauna an bata kulawar da ta dace baku gudu ba !
Sanyin kayan da suke bisa cinyar ta suka haɗu da jin daɗin cewar falmata tana raye an yi mata aiki har ma tana bacci suka tayar mata da kishirwar da ta jima tana ji ,
Ba tace kome ba , ta buɗe ledar gami da ɗaukar gorar ruwan ta kunce bakin ta kafa kai ta fara sha bayan ta muskuɗa ta juya tana fuskantar murfin motar ta bashi baya ,"
Ajiyar zuciya ya sauke yana jin farin cikin sake ganin ta yana ratsa shi , ya zubawa bayan hijabin ta ido da duk jinin falmata ya ɓata , '
A garin yaya harsashi ya same ta ?
Ya jefa mata tambayar lokacin da ya ga ta gama shan ruwan ,"
Muna cikin rumfa ne a bakin kasuwa
Bakin kasuwa ? ya maimaita
Me kuke a bakin kasuwa a wannan yanayin da gari yake ciki na hargitsi ?
Daman anan muke zama
Ta amsa masa
Kamar yaya ? Yaushe kuka dawo garin ?
Ɗagowa tayi ta dube shi
Daman muna gari , a bakin kasuwa muke kwana a cikin rumfar mai shago !
Ji yayi kan sa ya wani irin juyawa , take alamun da ya gani na masu ciki a tattare da ita ya faɗo masa cikin rai ! Shi ƙwararren likita ne wanda ya san aikin sa ya kuma faɗaɗa tare da zurfafa bincike cikin duk wani ilmi da ya shafi lafiyar ɗan adam , ba sai wani ya faɗa masa ba ba kuma sai yayi gwaji ba babu shakka cikin kallon tsanaki da yayi wa yarinyar ya fahimci tana da juna biyu , toh amma ta yaya haka ta faru ?
Wani mummunan tashin hankali ya ziyarce shi lokacin da yayi hasashen abun da ya faru ga rayuwar yarinyar , da ta yadda aka yi ta samu cikin
Tare da waye kuke kwana a bakin kasuwa ya tambaye ta yana tsare ta da kallon tuhuma .
Mu kaɗai ni da falmata !
Bai san lokacin da ya birkito da ita tana fuskantar shi ba ,"
Wacce irin rayuwa kuke yi a bakin kasuwar ? Baki da lafiya faɗa min waye yayi miki ciki ?
a tsorace ta ɗago kan ta tana kallon sa , yadda taga jijiyoyin kan sa sun tashi idanun sa sun kaɗa sun yi jaa ya sa ta matuƙar razana ,"
Nan take hawaye suka ɓalle a idanun ta , ta sake maƙure kan ta da jikin kofar motar
Sakin hijabin ta yayi tare da yin baya da kan sa ya ɗora a jikin kujerar da yake zaune bisa ya runtse idanun sa , tunani iri-iri suka rikito masa ,
Wani ƙazamin ɗan iskan ya riga ya bata rayuwar yarinyar tun a ƙaracin shekarun ta , mutanen duniya mafi yawan su azzalumai ne , sun cutar da rayuwar yarinyar saboda rashin galihun ta , ji yayi zuciyar sa ta raurawa idanun sa sun kawo ruwa ," wani irin tausayin ta da ya danne tasirin bacin ran sa da zafin kishin da yake ji ,ya mamaye ruhin sa ,
Allah sarki talaka !
Ya furta a cikin ran sa ,
Murya ƙasa ƙasa yace
Ki koma ki zauna a inda mutane suke jiran ƴan uwan su marasa lafiya , zan je na dawo ki tabbatar kin ci abinci , kar ki zauna da yunwa ,
Kamar jira take yayi mata umarni ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 28 Chapter of 111