amsa yana jin wani sabon tirniƙin ɓacin rai na taso masa sam sam baya son wani abu ya sake haɗa shi da kome ƙanƙantar abu wanda ya shafi yarinyar nan , daren jiya kwana yayi bai yi bacci ba saboda yadda ran sa yake ƙuna game da abun da yarinyar tayi masa , juyi ya dunga yi yana mamakin halin MACE ,
Shi a son ran sa ya bar su a chan wajen Amne ɗin lokaci lokaci yana zuwa yana kai mata abunda zasu buƙata domin a zahiri shi fatima da jaririyar ma bai son ganin su ," gani yake ita ma ƙanwar tata ta san kome tare suka haɗa baki , " shi yanzu ya bar ganin ƙanƙantar su tare da musu kallon matausaya ," ya tsinke akan lamarin MATA
Ba yadda ya iya haka ya shirya kafin ya wuce aiki yaje gidan Amnen inda ya tadda ta tana yiwa baby wanka jikin ta duk a sanyaye ta kwana da zancen mutuwar yakaka sosai yarinyar ta shiga ran ta saboda yanayin kamanni sosai da take da ƙanwar ta Rahima ,
Bai yadda ya ɗora idon sa kan jaririyar ba suka gaisa da Amne tana sake jajanta mutuwar yakaka tare da yi mata addu'a ta ɗora da tambayar sa aina aka yi jana'iza
Kaucewar tambayar yayi ta hanyar cewa ina ita ƙanwar tata ??
Tana wanka tun jiya take abu ɗaya ,"kuka ," kuma har zuwa yanzu bata kai ga sanin mutuwar ƴar uwar ta ta ba , ban ma san wanne irin hali zata iya shiga ba idan ta samu labari ," sai dai ka san hanyar da zaka bi ka kwantar mata da hankali kafin ka sanar mata da mutuwar nan
Cikin ƙagauta Hamza yace
Wane rarrashi Amne kowa ai zai mutu ki gaya mata kawai yayar ta mutu , kuma ki bata baby ta zo mu koma gida Baba ya ce na mayar su gida ...
Ƙarar faɗuwa da suka ji shi yasa Amne fitowa da gudu bayan ta shinfiɗe jaririyar ,
Doctor hamza ko gizau bai yi ba hasalima tun tsayuwar falmata a gun ya gan ta , yi yayi kamar bai gan ta ba , da hikimar sa na son fahimtar ko falmatan ta san kome da ya faru ?
Ganin yaƙi fitowa yasa Amne kwala masa ƙira ,"
Ka fito ka ga abun da yarinyar nan take yi , kar ita ma ta mutu ," tace da shi cikin ɗaga murya
Shi da kan sa ya tsorata ya kuma ji tausayin yarinyar lokacin da ya fahimci ciwon ta na asthma ne ya tashi , gaba ɗaya numfashin ta ya siƙe yana neman ɗaukewa bata cikin hayyacin ta ,
Da taimakon Allah da dabarun sa na likita , numfashin ta ya dawo ,
Zumbur ta miƙe zaune tare da kufcewa daga riƙon da Amne ta mata , lalube take tare da faɗin
Ina yaya daktan , ina kake yaya dakta , Dan Allah Dan Allah ka kai ni wajen Yakaka , naji kun ce wai Ta mutu , wai yaya ta ta mutu , ai wasa kake ko ? Yakaka tana gida ko ? Yaya za'a yi yakaka ta mutu ta bar ni ? Alhalin ta san bani da kowa sai ita , bani da ƙarfi kun gani fa ni miskiniya ce Dan Allah kar ku min irin wannan wasan ,"
Yaya dakta ka min magana mana , tace haka lokacin da ta samu nasarar chafko rigar sa ta rike tamau ,
Yaya dakta Dan Allah
Ta sake cewa muryar ta tana wani irin harɗewa ,
Ji yayi wani mugun tausayin ta ya rufe shi yaji ina ma bai ambaci kalmar mutuwa ba , cikin ƙwarar makafin idanun ta da suks firfito suka sauya launi tamkar ba nata ba yake iya hango irin firgici tare da azabar da zuciyar ta ke ciki ,
Kukan da baby ta tsanyara shi yasa ta yunƙura da gudu tayi sashin da taji tashin muryar jaririyar , kafin su taro ta har ta faɗa ɗakin kasantuwar ɗakin da ɗan zurfi ya sa ta faɗa ciki sakamakon jefa ƙafar da tayi nan take ta gurɗe ta tafi ta faɗi , bata haƙura ba ta rarrafa da gudu sashin da take jin kukan jaririyar
dai-dai da shigowar su
da lalube ta ɗauke ta ta riƙe ta gam a cikin jikin ta , "
Idan ni bakwa tausayi na Dan Allah ku ji tausayin jaririyar nan ku kai ta wajen maman ta ni da yakaka mun yi Alƙawari zamu haife ta mu rene ta mu biyu mu bata kulawa mu biyu ,
Meyasa yanzu zaku ce Yakaka ta mutu ? WAYE NI DA BABY IDAN BA YAKAKA ? WAYE ZAI KULA DA MU ?
ALLAH shine zai kula da ku Fatima , Amne ta ce tana sharar ƙwallar tausayin yaran , shi da kan sa hamza idanun sa sun kaɗa , tsanar yakaka na sake taso masa ,"
Wani irin kuka falmata take har tana tsuma ,"
Baba , Mama , yaana , Bulama Yakaka duk kun mutu ? Kun mutu kun bar ni ni kaɗai ? Ni meyasa ban mutu ba nima ??
Kiyi haƙuri Fatimah kowanne me rai zai mutu lokacin sa kowa yake jira , kiyi musu addu' a
Kawo baby na shirya ta ku tafi ," Amne ta furta hakan tana mai ƙoƙarin amsar jaririyar ,
Wani irin janyewa Falmata tayi da ƙarfi ta sake ƙanƙame yarinyar ,"
Ki bar min ita kar kowa ya taɓa ta bani da kome bani da kowa sai ita , ita ma haka , ita ce jini na kaɗai a duniya ita ce ƴar uwa ta madadin dangina gaba ɗaya , ita ce HASKEN da zan iya gani da ido na , kar kowa ya taɓa ta , kar kowa ya taɓa ta , kar kowa ya taɓa ta , ta dunga maimaitawa kamar bata cikin hankalin ta ,
Da ƙyar ta yadda Amne ta sanyawa babyn diaper tare da kayan sanyi tana riƙe a hannun ta ,
Wani irin yanayi take ciki , kamar ɗaukewar ruwan sama hawayen fuskar ta suka tsaya , ta kuma haɗe labban ta wuri guda bata cewa ƙala , sai ajiyar zuciya da take akai akai , lokaci zuwa lokaci laɓɓan ta na motsawa ,"
A haka suka fito Amne ta kama ta ta sanyata a mota tana rungume da jaririyar da ruwan ɗumi ya ratsa ta take ta baccin ta kasantuwar tun farar safe Amne ta cika mata ciki taf da madara ,"
Motar su tana tsayuwa Rahima wacce daman tana dakon jiran zuwan su , ta fito da gudun ta tana kuka ta rungume Falmata ,
Wacce take ƙiƙam bata kuka kuma bata ce ƙala ba , "
Sashin Baba ya kai ta , ta ɗurkusa guiwar ta biyu a ƙasa tana rungume da baby ,
Muryar ta chan ciki ta gaishe shi kan ta a sunkuye , ta'aziyya yayi mata kafin ya ɗora mata da nasihu , " a ƙarshe ya ɗora da shaida mata cewa ",Hajja mai wurya," dattijuwar dake yi masa girki ita zata cigaba da kulawa da jaririyar har zuwa lokacin da zata yi ƙwarai , bata ce kome ba kan ta a ƙasa ,
Rahima ƙarbo jaririya ki kawo ta nayi mata huɗubha , wanne suna kike so a sa mata ??
Zare jaririyar Rahima tayi ta miƙewa baban su ,"
Ya sake maimaitawa wanne suna kike son a sa mata ,
YAKAKA ," tace da shi a taƙaice
Jimm yayi yana mai maida duban sa ga hamza , "
Wannan ba suna mai asali bane ki faɗi wani sunan Fatima ," Baba yace da ita ,"
YAKAKA , ta sake maimaitawa hawaye na kwararowa daga idanun ta ,
Shikenan za'a mata laƙabi da Yakaka, .
a take yayi wa jaririya huɗubha ya miƙawa rahima ta mayar ta hannun yakaka ,"
Suka miƙe suna barin falon ,
Abuja Nigeria
Ƙarfe shidda na yamma su Yakaka suka samu isa garin Abuja ," gajiya da ciwon kai da ciwon ciki irin na ssbuwar haihuwa, zazzabi tare da dumuwar da take cinkushe cikin zuciyar Yakaka suka haɗu suka yi ligi-ligi da ita , , ta zama marar lafiya sosai sai numfarfashi take , bata ko iya buɗe idanun ta sosai ,
Unguwar "Gwarimpsamy baby tayiwa tsinke , tana shiga unguwar bata yi nisa ba tayi parking a bakin wani ɗan madai-daicin gida mai ɗauke da ƙaramar ƙofa da ɗan madaidaiciyar ƙofar shigar da mota da mota ɗaya zata iya shigewa ," fita tayi ta sanya ɗan mukulli ta buɗe ƴar ƙaramar ƙofar ta shiga ta ciki ta buɗo ƴar babbar ta dawo ta tada motar tare da sanya shigar da motar cikin gidan , bayan ta kashe motar ta zagayo gami da bude ƙofar bangaren da yakaka take ta taimaka mata ta fito , "
Da kyar ta iya sanyo ƙafafun ta waje sakamakon yadda marar ta take karta mata , tana fitowa taji jiri na kwasar ta taku ɗaya ta iya yi jinin ya fara bin ƙafafun ta da gudu ,"
Wayyo Allah ciki na
Ta furta lokacin da tayi baya luu ta faɗi , da sauri samy baby ta taro ta tana ,"
Na shiga uku ke yaks meye haka ? Ni samira kar ƴar mutane ta mutu a hannuna daga zuwa ," abun arziki bai karɓi kare ba ,"
Kama ta ta sake yi ta mayar ta motar da sauri ta sake buɗe gidan ta fitar da motar ta kulle gidan gami da cilla motar a titi zuwa asibiti mafi kusa da ta sani tana tuƙi tana waiwaiyen yakaka wacce ta fara fita hayyacin ta ,"
Wani asibiti mai zaman kan sa ta kai ta inda tana zuwa aka karɓi yakaka ana tambayar samy baby meya same ta , nan ta shaida musu haihuwa tayi ɗazu da safe ɗan ya koma ,"
Nan dai suka shiga bata taimakon gaggawa bayan sun tsayar da gudun zubar jinin suka mata Allurai tare da ɗaura mata ƙarin ruwa , ba'a ɗauki lokaci ba ciwon ya lafa ta samu bacci ,,"
Agogon hannun ta Samy baby ta duba kafin ta jaa tsaki , har ƙarfe 7:40pm , wayar ta ta zaro daga cikin ƴar jakat hannun ta nan ta tadda miss calls ɗin samarin ta daban-daban , number da tayi wa suna da "Dude" ta bi bayan ƙiran ,"
Hello boo ya kake ?
Daga chan ya amsa mata , yana tambayar ta inda ta bar wayar nan ta sanar da shi ta zo da ƙanwar ta wacce ta gaya masa ɗin , amma bata ji daɗi ba ne ,"
Kuna wanne asibiti ya tambaye ta
Nan ta sanar da shi asibitin da suke ,"
Ba'a ɗauki lokaci ba ya iso asibitin , mutum ne magidanci da ya tasamma shekaru arba'in da biyar ,
Babu kunya samy baby ta mannu da jikin sa tana masa ƙwarƙwasa lokacin da suka haɗu , kafin ya nemi da ta haɗa shi da Casher na asibitin , nan tayi masa jagora ,"
ba ɓata lokaci ya dire naira dubu ɗari , aka rubuta takaddar shaidar biyan kuɗin aka ba samy tare da sharaɗin idan chanjin su ya rage zuwa lokacin sallamar marar lafiyar za'a mayar musu da ƙuɗin su , idan kuma su zasu yi ciko ma sai su ƙaro , "
Basu tsaya sauraran sauran bayanan nasa ba suka yi wucewar su samy baby tana manne da jikin sa ,"
Ɗakin da aka kwantar da yakaka suka je ,
Har yanzu Alluran da aka mata wanda akwai na bacci a ciki basu sake ta ba , dan haka suka tadda ta tana ta baccin ta ,"
Wani kallon ƙasan ido yayi mata ,"
Yane baby na kin san fa nayi shirin daren yau tare da ke , sai kuma ga marar lafiya mun samu ,"
Karkaɗa masa ido tayi ta wani rausaya ,
Boo yadda kake so haka za'a yi , zamu iya tafiya mu bar ta ai ƙarƙashin kulawar ma'aikatan asibitin , ni da kaina nayi tanadin daren yau domin ka , ta ƙarasa zancen tana kashe masa ido ,"
Wata shashar dariya ya sake kafin ya juya yana cewa
Baby na kenan shi yasa nake daɗa jin ki a cikin jini da tsoƙa ta , bari naje mu gama da ma'aikatan asibitin game da waɗanda zasu kula da ita , sai na dawo mu wuce ,"
Samy baby tare da farkan ta , basu yi tunanin a irin halin da ƴar mutane zata iya farkawa cikin dare ba , suka yi tafiyar su sheƙe ayar su suka bar ta ƙarƙashin kulawar biyu daga cikin nurses ɗin asibitin waɗanda Alhaji Gali ya danƙa musu hatimin nasara a hannun .
Yakaka ba ita ta farka ba sai wajen ƙarfe uku na sulusin dare , ta tashi bata jin ciwon kome illah rashin ƙarfin jiki da kuma ƙirjin ta da take ji yayi nawi a sakamakon ruwan nono da ya zo ,"
Yawo tayi da idanun ta , ta tabbatar babu kowa a ɗakin sai ita kaɗai , miƙewa tayi ta zauna tare da zuro ƙafafun ta ƙasa tana bin ɗakin da take da kallo wanda yake wadace da hasken lantarki ,
Hotunan abubuwan da suka wakana tun daga safiyar jiya su suka yi ta dawo mata ɗaya bayan ɗaya , kamar a lokacin suke faruwa ,"
Wani irin kuka ta fashe da shi lokacin da tunanin ta ya kawo ta dai-dai wurin da take sanya ƙafafu tana wucewa ta gaban falmata ba tare da ta tsaya ta mata magana ba barw tayi mata sallama,damuwar da ta hango a idanun falmata a lokacin da ta waiwaye ta da kallon ƙarshe a jiya , ta tabbatar damuwar da take kwance idanun falmatan ya assasa ne ta dalilin rashin sanin halin da take ciki , ji tayi zuciyar ta ta kumburo da ta lalubi son sanin halin da falmatan take ciki har ta kwatanta a yanzu ,
Wayyo Falmata na ta furta a sarari tana dafe ƙirjin ta , yunƙurawa tayi ta tashi da sauri ta nufi ƙofar ɗakin , kamar wacce aka dakatar kuma sai ta tsaya , tsayuwar ta baya rasa nasaba da tunowa da tayi a bigiren da take a yanzu wanda yake da tazara mai tarin yawa tsakanin ta da inda ta baro Falmata ,"
Ruwa mau ɗumi ta ji yana kwarara ta cikin rigar ta da ya sata saurin janye rigar ta ga menene ??
Ruwan nono ne yake zuba ," tuno da ɗiyar ta da ta bari ba tare da ta kai ga ko ganin fuskar ta ba tayi , kukan da ta baro ta tana yi wanda ta tabbatar na yunwa ne sautin sa take iya jiyowa tamkar a yanzu take ji , wani irin tausayi ne tare da wani iri lamari mai girma da ya zarce nadama taji yana bin jijiyoyin jikin ta da gudu kafin ya zo ya watsu cikin zuciyar ta , "
Zubewa tayi akan guiwowin ta ta baje a ƙasa tana sake sakin wani ƙaƙƙarfan kukan da yake ɓullowa tun daga ƙarƙashin ran ta ,"
Ƙarfe shida na safe nurses ɗin da aka bawa ajiyar yakaka suka shigo ɗakin da take su biyu , ɗayar riƙe da magunguna tare da allurai .,"
Turus suka yi lokacin da suka ga gadon da take babu kowa , a tsorace suka ƙarasa shigowa ɗakin ," i
Ina take suka haɗa baki wajen tambayar junan su ??
Kamar ance su waiga suka hango ta zaune a ƙasa daga jikin bango ta takure ƙafafun ta ɗora hannayen ta bisa guiwowin ta gami da kwantar da kan ta akan hannuwan ,"
Kin tashi ne ? A ah ya kika zauna anan ?
Ɗayar nurse ɗin ta tambayi Yakaka suna matsowa kusa da ita ,
Ko gizau bata yi ba Duk da cewa idanun ta a buɗe suke ta kafe su a jikin bango ,"
Kallon juna nurses ɗin suka yi ,"
Patient da ke muke fa , ko bakya jin hausa ne ?
Motsa bakin ta tayi ƙasa ƙasa tace
Ina anty samy ?
baki da lafiya ne ? Kizo ki hau gado mu auna ki kisha maganin ki na miki allura kafin doctor naki yazo , yayar ki bata kwana a nan ba sun fita da mijin ta sun ce zasu dawo da safe ,"
Wasa gaske , ƙememe Yakaka taƙi miƙewa daga gurin da take takure a zaune , a ƙarshe dole suka haƙura suka bar ta a wajen suka yi tafiyar su shirye shiryen tafiya gida saboda masu aikin safe zasu karɓe su , suka rubuta a cikin folder nata taƙi yadda ta sha magani kuma taƙi yadda ayi mata allura ,"
Tara na safe ta gota aka turo ƙofar ɗakin aka shigo , samy baby ce ta shirye tsaf cikin wani ɗanɗasheshen yadi , hannun ta riƙe da ɗan kwando wanda ta zubowa yakaka abun ƙarin kumollo ,
Ita ma sai da zuciyar ta tayi tsalle da ba ta hango yakaka saman gadon asibitin ba ,
Chan gefe ta hango ta , da sassarfa ta nufi wajen ta tana
Yaks ya kike zaune a ƙasa lafiya dai ko ?
Tana jin muryar samy baby ta miƙe tsaye gami da takowa da gudu ta riƙe hannun samy baby ta shiga roƙon ta ,"
Anty samy Dan Allah kiyi sauri ki kaini wajen sa , ya mayar da ni gida na koma wajen su Falmata , ji nake kamar zan mutu ,
Da ido samy baby ta bita tana iya hango tashin hankali tare da ruɗani gami da tsantsar rikici a idanun Yakaka ,"
Ke yaks bana son shirme ki nutsu , haka kike so na ɗauke ki yarkace-yarkace daga gadon asibitin na kai masa ke ??
Ai wannan sai ya kore ki
Bazai kore ni ba anty samy shi zai kai ni a min gyaran jiki ,"
Mtss samy baby ta jaa tsaki ,
Ki zo kici abinci Yakaka tun jiya rabon ki da abinci , nurse ɗin sun baki magani tare da allura ? Ki ci abinci ki gyara jikin ki kafin likitan ya zo ,"
Warce hannun ta da samy baby ta riƙe tayi , ta durƙusa gami da haɗa hannun ta ta shiga yi mata magiya tana gunjin kuka akan lalle fa ita a yanzu zata kai ta wajen bature kam silum kuma a yau zata koma wajen su Falmata ,"
Tun samy baby na ƙoƙarin rarrashin ta tare da yi mata dabara har ta suƙe ta fara yi mata masifa ,
Faɗan da ta fara yi mata bai haifar da kome ba sai sake rikicewar Yakaka domin kuwa yunƙurawa tayi da gudu tana ihu ta nufi ƙofar ficewa daga ɗakin da nufin komawa gida ,"
Da gudu samy baby ta ruƙo ta kafin ta kai ga ficewa daga ɗaƙin , hankalin ya fara tashi ita ma , sam bata yi zaton yakakar zata birkice mata irin haka ba , " sai tayi da gaske tare da taka tsantsan idan ba haka ba zata jawo mata jangwam kowa ya san haƙiƙanin abun da ya faru daga ƙarshe ita ce zata iya faɗawa hannun hukuma ayi ram da ita ,"
Ke yaks Ke yaks ƴar iska meye hakan kike min ? Ina cewa da yardar ki da amincewar ki muka taho ? To shikenan gyara jikin ki ki sauya kayan ki da wannan rigar ta miƙa mata wata doguwar riga a cikin leda tare da audugar mata da sabbin panties , shirya mu tafi ,"
Ba musu yakaka ta karɓi rigar tana jan ajiyar zuciya irin na wanda ya ci kuka sosai , ta shiga banɗakin wajen ta gyaro jikin ta gami da sauyo kayan ta ,"
Kwandon abincin samy baby ta ɗauka suka fito daga asibitin ba tare da sun yiwa kowa sallama ba bare su bi ta kan chanjin su da samy baby ta tabbatar akwai ,"
Gidan da yake mallakin ta ne wanda ta fara kai yakaka jiya nan ta sake yada zango ,inda tayi wa yakaka umarni da ta fito ba musu ta fito , ta taka ta bi bayan ta zuwa cikin gidan inda ta sa ɗan mukulli ta buɗe wata ƴar kwatatciyar ƙofar madaidaicin falon suka shiga kai tsaye samy baby ta wuce jikin wata ƙofa da take daga gefen hagu a cikin falon ta sanya ɗan makulli ta buɗe kofar ta sanya kai ciki ,
Yakaka tana dogare daga bakin ƙofar falon ta ji muryar samy baby na ƙiran ta daga cikin ɗakin da ta shiga ,
cikin ɗakin ta shiga gami da durƙusawa daga baki-baki tace
Na'am Anty samy
Tashi ki ƙaraso yakaka nan ɗakin ki ne , na shirya miki shi tun kafin na kawo ki , ga banɗaki nan shiga kiyi wanka na haɗa miki ruwa mai zafi sosai da zaki gasa jikin ki , idan kin fito ga gado ki kwanta kiyi bacci idan ya so in kin farka kin cin abinci kin nutsu sai muyi magana ,"
Tunda ta fara magana Yakaka ta ɗago idanun ta tana kallon ta ,gama maganar ta ya zo daidai da silalowar ƙwalla daga idanun Yakaka , da kyar ta harhaɗo kalmomin da zata iya amfani da su
Anty samy cewa kika yi shi yace ki kaini wajen sa , na ɗauka tun jiya zaki kai ni ? Dan Allah ki kai ni bazan zauna anan gidan ba ,"
Kallon baki da hankali samy baby ta watsa mata ,
ai kuma sai kiyi tunda ke kunnen ƙashi ne da ke bakya jin maganar mutane , tace tana kewaye ta ta fice daga ɗakin har ga Allah ta fara ganin gangancin kan ta da ta ɗauko yarinyar nan ta zo da ita nan ba tare da ta mata bayanin haƙiƙanin gaskiyar manufar ta ba , kar fa ta zame mata matsala !
Zama tayi akan ɗaya daga cikin ƴan kananun mannanun kujerun da suka zagaye falon suka yi ɗas gwanin sha'awa ,
Ta ɗauki wayar ta da nufin ƙiran ƙawar ta ,"
Yakaka ta gani ta fito ta tsaya akan ta jikin ta sanye da dogon hijabin da ta bata jiya ,"
Ɗurkusawa tayi a gaban ta cikin wata irin murya chan ciki tace
KI MAIDA NI GIDA ANTY SAMY ,"
Da sauri samy baby ta miƙe tsaye
Ke Yakaka kar ki min iskancin banza da rashin kunya ,
To bari ki ji na faɗa miki Gaskiya ni taimakon ki nayi na tsamo ki daga cikin hallakar da wannan Doctor yake neman jefa ki ta hanyar ƙulla soyayya a tsakanin ku , alhalin ya san cewa sofi na nan na dakon soyayyar sa shekara da shekaru ,
ni nasan irin Alkaba'in sofi da Alwashin da take ci akan duk wata mace da ta raɓi Doctor Hamza , da bana fatan ko kusa ki faɗa cikin kaidi tare da masifar ta , shi yasa na zare ki daga cikin rayuwar doctor baki ɗaya na kawo ki nan waje na domin na inganta miki rayuwa na tsaya miki ta yadd watarana za ki zama macen da ire iren Sofi da waɗanda suka fi ta zama annoba ma basu isa ɗaga miki ɗan yatsa ba , amma dayake ke ƴar iska ce WAWIYA JAHILA ,kina neman butulce min akan wani sakaren makahon son abunda baza ki taɓa samu ba da kike yi ,
ki buɗe kunnen ki kiji da kyau ni ban san inda wani
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 39 Chapter of 111