yace "ita da kan ta za ta fito kyale ta .
"Zuba mana abincin mu ci ina sauri Wafaa.
Cikin nutsuwa ta zuba musu soyayyan dankalin da ƙwai hadi da soyayyar ayaba , sai kuma farfesun marara zallah da tayi masa dafuwa irin na mutan Ndjamena (shurban) a ƙasa ta ajiye musu abincin a tsakanin su .
Suna ci Doctor Hamza yana ta santi , jin sa yake kamar ya dawwama a haka yana kallon fuskar ta da take cike da annuri .
Bayan sun gama cin abincin ya goge bakin sa da tissue "Wafaa ya ƙira sunan ta.
"Unmh
Ta amsa tana ɗago kan ta hannun sa da yake miƙa mata wani kwali mai kyau ta bi da kallo ba tare da ta karɓa ba ta daga idanun ta ta mayar kan sa da sigar tambaya?
" karɓi mana , sabuwar waya na saya miki ta hannun ki bata da wani amfani koyaushe na ƙira ba kya ɗauka kamar jiya kam ma a kashe ta wuni , bana jin daɗin haka na fi son na dunga jin ya kike ? Ko da bana gida .
Da yalwatatcen murmushi tare da ɗan boyayyen zumuɗi ta karɓi kwalin kafin ta fara kici-kicin buɗewa bai dakatar da ita ba har sai da ta buɗe ta zaro sabuwar waya sumfurin iPhone8+ da take ta daukar ido .
"Masha Allah .
ta furta a sarari lokacin da take kallon sa with her light brown eyes that were deeply creased with smile line at the coners.
"Yaya Dakta Wannan wayar ta 'yan gayu tawa ce?
Ta furta hakan da zallar farin-ciki kafin ta ɗora da cigaba da cewa " Kai wallahi nagode sosai , ina nufin nagode dayawa Ya Dakta Allah ya daɗa ma buɗi da arziki mai Albarka...
"Wafaaa
ya ƙira sunan ta ƙasa-ƙasa yana jin yadda farin-cikin da ya hango tare da ita ya ke ba shi wani shauƙi na musamman
Kumatun ta ya ɗan shafa yana miƙewa tsaye bayan ya ɗauki briefcase din sa da murmushi yace " Wafaa I can bring the whole world to you if I have it.
A hankali ta dago kan ta rana ta farko da ta ji kamar tana son mayar masa da martanin tsadaddun kalaman sa tana so tace wani abu ko da kadan ne akan tarin alkhairin sa marasa adadi da ya wanzu yana hidimta mata, "to me zan ce ne? Ta tambayi kan ta, daga can ƙasan ran ta kalmomin suka haɗo kan su suka fito ta tsakanin laɓɓan ta ba tare da ta janye ƙwarar idanun ta da ke cikin na shi ba ta ce "I always cherish your company Yaya dakta for that I'll forever serve you and do anything for you here in Duniya insha Allah. Thank you for everything! I mean everything Yaya Dakta.
Ɗage girar sa yayi yana jin sa kamar mai yawo a sama kalmomin nata taƙaitattu ne amma masu faɗi ne a wajen sa da zai yi zama na musamman domin yi musu fashin baƙi ,
" I appreciate that and I cherish yours even more, integrity you're worth-valuing, worth-treasuring and worth-cherishing. Your value is such unfathomable Wafaa.
zamewa ƙafar Sofia tayi da ƙiris ya rage ta gangaro daga ƙafar bene, bata taɓa sanin ƙeyar mutum na da ido ba sai da ta ji tana taka matakalar bene ta baya , kalaman na mata amsa kuwwa suna mata rakiya har ɗakin baccin ta da ta na shiga ta zube a ƙasa kan ta na juya mata tana ganin kome na dakin yana tafiya da kafafun sa.
A narke Yakaka take kallon sa lokacin da yake furta mata kalmomin da suka mata zurfi wajen fassara har ya sunkuyo ya sumbanci goshin ta, " ni zan tafi Wafaa .
Ya furta haka yana ɗaga taku ya nufi hanyar ficewa daga falon har ya kai ƙofa ya waigo ta , kallon sa take da murmushin da yafi so a tare da ita a hankali ya ƙarasa ficewa a falon ran sa cike taf da ƙaunar ta fuskar ta tana zanuwar masa a cikin rai yana jin zata ishe shi farin-cikin yau har ya je ya dawo .
Ya tada motar sa a hankali yana ficewa a gidan zuciyar sa na daɗa hasko masa yanayin da ya bar ta a ciki " she's smiley, she is smile just like the sunflower. Ya furta hakan a sarari.
Cike da zumuɗi Yakaka ta kunna wayar da cikin sa'a ta tarar da sabon Sim a ciki , duk da bata taɓa riƙe babbar waya ta kan ta ba amma bata gagara sarrafa wannan ɗin ba saboda Lubna tana riƙe irin su a wasu lokutan tana karɓa tayi 'yan taɓe-taɓen ta saboda sosai manyan wayoyi suke burge ta dan dai kawai bata da damar mallakar su ne .
Ta kwashe tsawon lokaci tana wasa da wayar cikin taka tsan-tsan ta shiga nan ta fita can kafin ta miƙe tana riƙe da wayar duk hankalin ta na kai ta tafi ɗaki ta ɗauko tsohuwar wayar ta ta kunna ta cike da zumuɗi ta kwafi number Hajja akan sabuwar wayar ta ta fara ƙira da ɗokin son ta yiwa Falmata albishir .
Bugu ɗaya Hajja ta ɗaga tana ɗauka da ta ji muryar Yakaka sai ta sa dariya "Ah ka ga manya a baku naku daban Babba Uwar Mama uwargida kuma Amarya a gidan Babban likita , ai yau kwana uku kenan uwarɗakina tana nacin ƙiran wayar ta ki bata samu tun ranar da muka samu labarin kin tare da fatan ana Amarci yadda ya dace ?
'Yar dariya Yakaka tayi ta fara sabo da halin Hajja na jaan zaren magana tayi ta tsawo , "Hajja kenan muna lafiya ya ya wajen ku ?
"Mu ma lafiya ras muke bari na miƙawa gimbiyar wayar ku yi magana tana ɗaki .
"To Hajja nagode .
"Ince da kuɗi a wayar ta ki ? Kar ki katse yanzu zan ba ta
A zaune ta tarar da Falmata ta tasa cikin ta a gaba da cikin kwanakin nan yake wani irin girma na ban mamaki daga gefen ta faranti ne a cike da warmers ɗin da aka shaƙe cikin su da kayan cimaka .
Miƙa mata wayar Hajja tayi tana cewa "Uwar biyu ma za riƙe waya Babba Uwar Mama ce ke kai .
Zunbura baki Falmata tayi kafin ta karɓi wayar tana cewa "Hajja ina faɗa miki bana son sunan nan wai Uwar biyu dan Allah Hajja ki daina .
Ta ƙarasa zancen tana kara wayar a kunnen ta dariyar da Yakaka take yi ita ta fara sauƙa a kunnuwan ta da yasa ita ma ta saki 'yar sassauƙar dariyar jin daɗin sauraron tashin muryar 'yar uwar ta da cikin kwanakin nan take jin kewar ta matsananciya .
"Yakaka na .
Ta ƙira ta da dariya , bata jira ta amsa ba ta ɗora da cewa "wallahi nayi fushi Ya yanyi3 ki ka koma Abuja ba muyi Sallama ba kuma bakya ko nema na yaya Dakta ya mantar da ke ni ko.?
Dariya Yakaka tayi tana rufe bakin ta da hannu ta ce "Falmata sharrin da za ki min kenan ? Haba Falmata na tayaya zan mata da ke 'yar uwa rabin jiki , kiyi haƙuri tunda na zo bana cikin kwanciyar Hankali ne Falmata na ....
Da sauri Falmata ta katse ta "Yakaka bakya cikin kwanciyar hankali ? Me yake damun ki ? Sofi ce ko ? Me take miki ?
"Falmata , abunda Sofi take min ba kyau ta takura min ta hana ni sakewa har fa kare take kawo min cikin ɗaki'....''
"Me ...? Kare ?
Falmata ta katse ta hankalin ta a tashe har tana wani ɗan yin zillo da hakan ya jaa hankalin Hajja da take shirin barin ɗakin dan ta basu dama suyi hirar su ta 'yan uwa ta ɗan dawo da baya tana cewa "Uwarɗakina ince dai lafiya ?
"Wallahi Falmata kare Sofi ta kawo gidan nan take kulle'....
Chak ta tsaya da bayanin da take sakamakon bugo ƙofar da Sofi tayi ta shigo a haukacen ta daga yadda take gama hanya na nuni da alamun ta shawu .
Cikin Yakaka yayi wani ƙugi ƙululu , ba tare da ta katse wayar ba ta sauƙe ta daga kunnen ta ta riƙe ƙam a hannu lokacin da take miƙewa ta tsaya akan ƙafafun ta .
Daga can Falmata ta ji shiru Yakaka ta katse zancen da ta faro yi mata zare wayar tayi a kunnen ta ta duba ta ga cewa Yakaka bata ajiye wayar ba , sanya wayar tayi a handsfree da zaton ko network ne da ɗan ƙarfi tace "Hello Yakaka kina jina ? Ki min magana..
Sautin da ta ji ya fara fitowa daga cikin wayar ya sa tayi saƙare tana kallon wayar .
"Yakakaakaa ko ? Ko Wafaaaa in Doctor voice ? Ko Aminaa Aminaa , whatever dan ubanki me na faɗa miki akan rayuwa ta da kika shigo kin manta alƙawarin da na miki dan me koyawa tsohuwar ki darasi ? Da har ki ka iya yin tsaurin idon yi min rashin kunyar da ta sa aka mare ni akan ki Kin yi kuskuren da ba zan bari ki maimaita makamancin sa ba .
Girgiza kai Sofi tayi kamar lokacin aka mare ta ta riƙe ƙuncin ta "Mari ni Sofi aka mara akan ki.?
Taku ta fara yi tana kusantar Yakaka wacce ko ba'a faɗa mata ba ta fahimci manufar Sofi , kuma tuni ta fara neman hanyar tsira .
Laɓɓan ta na rawa ta fara jaa baya tana cewa "Anty Sofi Dan Allah kiyi haƙuri walla.'..
Wata waftar da Sofi ta kawo mata ya sa ta daka tsalle ta tsallaka kan gadon ta hau ta tsaya..
"Zan kashe ki Yakaka na ga abunda zai faru ba dai kin gwada min naci ba ? Kin nuna a dole Mijina naki ne ko ? To sai na kashe ki kamar yadda na sha alwashi.
Daga can kuka Falmata ta sa ta yunƙura da ƙyar ta miƙe jikin ta na rawa ta miƙawa Hajja wayar da duk abunda Sofi take cewa a kunnuwan su muryar ta na rawa tace "Hajja , Hajja kin ji wai Sofi za ta kashe min Yakaka wallahi kuma za ta iya dan Allah ki bata hakuri Hajja.
Karɓar wayar Hajja tayi ta shiga cewa "alo 'Alo babba uwar Mama ba wa mahaukaciyar kishiyar ta ki wayar dan ƙunduƙurin ubata yau ji min tsinannana? Kishi hauka ne?
Jin shiru yasa Falmata ta sake rikicewa da muryar da take gaf da fara kuka tace ,
"Yakaka , Yakaka Dan Allah kiyi magana , Yakaka ki gudu dan Allah kar ta kashe ki..
"Ke jaa can ar kishiyar za ta guduwa ? Zancen banza ma kenan ,mugun nufi ai baya kashe ɗan barewa Babba uwar Mama zage ki taushe bakin akuyar wofi ki ɗaga ta sama ki doka ta da ƙasa kika yadda kika gudu ni da ke ne , nace ki zage ƙwanji 'yar nan ki kwaci 'yancin ki ta isa ne ma ta kashe ki ? Naushe ta a ƙahon zuci nace.
Hajja ta furta hakan har tana kaiwa iska duka tana cije baki cike da jin wani irin takaici na rufe ta .
Daga can kokawa tuƙuru ta sarƙe tsakanin Yakaka da Sofi da take neman shaƙe Yakaka amma ta kasa samun galaba abun mamaki wani irin ƙarfi ta tarar Yakakan na da shi da ko kusa ba ta yi zaton sa ba dan haka bata ankara ba ta tunkuɗa ta baya bata yi aune ba tayi baya ba shiri daɓas ta zauna da manyan mazauna ta akan wata ƙwalbar turaren da ta faɗo sanadin kokuwar da suke nan take kwalbar tace fusss! Ta fashe a take ta soki ɗuwawun ta.
Lokaci ɗaya wani irin raɗaɗi ya ratsa mata ƙwaƙwalwa da yasa ta saki ihu kafin ta dawo hayyacin ta Yakaka da daman matsera take nema ta tsallaƙe ta da gudu ta fice daga ɗakin bata tsaya ba ta buɗe ƙofar falon ta fita daga ita sai kayan jikin ta ƙafar ta ko takalmi babu sai fa wayar ta da take riƙe ƙam a hannun ta .
Sofi wacce bata saurari azabar da mazaunan ta ke mata ba ta fito gaba gaɗi tana ganin ƙofar falon a buɗe ta fahimci Yakaka ta fice a gidan abunda daman take so kenan .
Dan haka ta tura ƙofar falon da ƙarfi ba tare da ta kulle ba ta juya ta hau sama saboda raɗaɗin da take ji a mazaunan ta tana son ta duba irin raunin da ta ji.
Yakaka wacce take tsaye daga harabar gidan ta hango rufo ƙofar da Sofi tayi dan haka a galabaice ta samu waje daga gefe ta zauna baki ɗaya bugun zuciyar ta ba dai-dai yake ba .
Sofi ta kulle mata ƙofa ta bar ta a waje da tazarar tsakain ta da titi bai wani cika nisa ba sauran mutanen da suke makwaftaka duk za su iya ganin ta haka babu mayafin kirki wannan wane irin rayuwa ce take yi ?
Kiran wayar ta da aka yi yasa ta duba fuskar wayar sunan Hajja ta gani dan haka ta ɗauka tana ɗagawa daga can Falmata da ta kasa zaune ta kasa tsaye ta ce "Yakaka ke ce ? Bata mi ki kome ba ko.? D''
"Falmata ni ce eh na samu na gudo ki....'
"Kika gudu ? Gudu fa kika ce ?
Hajja take tambayar ta daga can kafin Yakaka ta ce wani abu Hajja ta karɓe wayar daga hannun Falmata tana cigaba da cewa
"Ke wacce irin Solobiya ce ? Kishiyar ke bin ki kina rugawa da gudu dan ragwanta da mutuwar zuciya kenan ko me ? Bakya tsayawa ki nuna mata banbancin ƙwarin jikin tsohuwa da na yarinya ? Wai ko ba wannan fantekar matar ta babban likita me jemammiyar fuskar nan ba ce ? Yanzu ita kike gudu ? Ita kike tsayawa tana cashe miki haka ba ki rama ba ? to wallahi kin rako mata 'yar nan ah lalle fa kina ina yanzu ?
A sanyaye Yakaka tace "ina waje harabar gidan Hajja ta koro ni wallahi tsoro nake ta ɗau wuƙa ta soka min dan haka ta ce min wai wallahi za ta kashe ni kuma ni wallahi bana son tashin hankali Hajja ni fa ko musu na fatar baki ciwon kai yake saka ni bare danbe hajja....
"A ah ai fa lalle abun nayi ne wai an biyawa bazaura Hajji , na gani na kuma shaida haka waliyya to kina jina ko ?
"Ba dai ita ta ce 'yar iska bace? Zata hana ki rawar gaban hantsi ke da gidan Mijin ki da ke kuma ta same ki solobiya kike biye mata ?
"Hajja .....
"Yi min shiru 'yar nan barni da ita ke dai bin umarni ne na ki , ince dai can layi ta koro ki ?
"Eh Hajja .
"Da mutane a wajen ko kuwa ?
"Eh da mutane dai kaɗan .
"A yaya kika fito titin ?
Yakaka ta ɗan yi jim ita fa bata cika son biyewa subaɗaɗin Hajja ba muryar Hajjan ta katse ta da ta ji tana sake cewa
"Nace da kayan arziki a jikin ki ko kuwa ɗan diras ne a jikin naki ?
"Hajja da kaya a jikina .
"To yaga su
"Eh Hajja?
"Nace ki yage kayan ki musu mummunan yagu .
"Haba Hajja ya kuma za ki ce ta yaga kayan ta a waje fa take ?
Falmata ta furta hakan tana zaro ido da mamaki
" kar ki katse ni ki min shiru '.
"Babba uwar Mama kina jina?
"Ina jin ki Hajja ki saurareni da kyau 'yanci nake son taya miki ki kwato , shi maganin biri karen maguzawa dan haka duk abinda nace miki kiyi , kiyi kawai ina mai tabbatar miki daga yau bata sake chakumar ki da dambe bare har ta kora ki layi .
"Ince kina da layin wayar shi Hamzan ?
"Ina da shi Hajja
" You katse ƙiran nan ki ƙira shi ki tabbatar kina gunjin kuka za ki ƙira shi kice ya taho yanzu ga matar sa za ta kashe ki kina faɗin hakan idan kin tabbatar ya ji sai ki kashe wayar daga nan ki sake ƙira na.
Doctor Hamza ya gama round kenan misalin sha biyu saura ya ga ƙiran Yakaka , fuskar sa cike da annuri ya ɗaga ƙiran yana jin 'yar guntuwar gajiyar na barin jikin sa .
Sai dai me ? Muryar ta da ya ji cikin kuka ya sa zuciyar sa yin tsalle hankalin sa a tashe yake tambayar ta me ya faru ? Tana kuka ta fara masa bayani bai gama saurara ba ma ya katse wayar hankali tashe ya fara ƙoƙarin barin asibitin .
Yakaka tana sauƙe wayar ta ƙira Hajja da daman tsumayar ta take dan haka nan take ta ɗaga "na ƙira shi Hajja . Ta ce a sanyaye .
"Yauwa ta farka rigar ta ki ta waje-wajen wuyan sannan ta ƙasa ma ki yiwa zanin naki ko siket mummunan yagu ta wajejen cinyar kina jina ?
"Hajja dame zan ya ga ? ba zai ji daɗi ba idan ya gan ni haka jiki a buɗe a waje .
"Kin ci gidan ku ana son ƙwatar miki ƴanci kina gardama cewa nake fitinannar matar sa ta koro ki ? Yi maza ki yage kayan nan dan a kori gaba .
Ba yadda Yakaka ta iya haka ta ɗan yiwa kayan jikin ta rauni da ƙyar saboda ƙarfin su .
Hajja tana iya jin ƙarar ɓarkewar kayan tace "Yauwa to sai abu na gaba da kin dai-daici ya kusa zuwa ki cisge ɗankwalin kan ki ki yasar , kuka kuwa kar ki ƙaƙƙauta har sai kin ga nata hawayen ita ma ba dan kome nasa kiyi haka ba sai dan a kori gaba kin fahimta ko.?
"Naji Hajja .
"Madallah.
Ba'a rufa mintuna goma ba sai ga Doctor Hamza a guje da motar sa da Yakaka tana hango shi ta fara kukan da daman yana cin ran ta kan irin tozarcin da Sofi ke mata.
Ƙafafun sa kamar ba za su iya ɗaukar sa ba ya fito a motar idanun sa da suke bayyana tashin hankali akan ta yana bin duk saassan jikin ta da kallo .
Yana ƙarasowa Yakaka ta faɗa jikin sa shi ma ya riƙe ta gam da wani irin yanayi a muryar sa yace "wa ya mi ki haka ?
Tana shiƙar kuka tace "auntie Sofi .
Hannun ta kawai ya kama suka nufi ƙofar shiga gidan yana murɗawa ya ji ta a ɓude '
"Sofi Wacce take baje akan kujera tana zuƙar shisha daga ita sai 'yar doguwar rigar shan iska gefen ta Sam ne a kwance daga ƙasa ta tasa masa abincin sa a gaba yana ci .( irin ita Bosslady )
Lokacin da ta ɗago kan ta tayi zaton Yakaka ce sai kawai tayi ido huɗu da Doctor Hamza da yake tsaye yana mata wani irin kallo na tsana daga bayan sa kuwa Yakaka ce take rakuɓe .
Assalam Alaykum masu karatu da fatan alkhairi.
Ina dai neman afuwar ku yau da gobe ta fi ƙarfin wasa jiki kuma da jini .
Ina kaunar ku domin Allah.'
Nagode
[4/15, 8:07 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
......... HARGITSIN RAYUWA
UMM' MUAZ
54
MAI RABON SHAN DUKA
Ganin irin mummunan kallon da Doctor Hamza yake yi mata bai karya guiwar Sofi ba da zai sa har ta gaza yin wani yunkuri kare kanta ba .
Dan kuwa zuruf ta miƙe bayan ɗan taƙaitatatcen tunanin da ya gifta mata da bata yi ƙasa a guiwa ba ta fara ƙoƙarin tattaro nata makaman yaƙin "ai ba zata bari Yakaka ta ci ta da yaƙi ba haka nan take .ta aiyana hakan a zuciyar ta
"Doctor ka ga'.....
Wata irin tsawa Doctor Hamza yayi da ba ita Sofi kaɗai ba ,hatta Sam sai da yayi zillo yana ɗan kuka ya koma bayan kujera ya laɓe.
"Kar ki ce min kome Sofi , bana buƙatar jin ƙaryar ki ta banza abunda nake so kawai shine ...
Ɗan jim yayi yana kallon ta yadda ta wani irin saƙare cikin rashin madafa matsanancin tashin hankali gami da wani nisassashen yanayi shimfiɗe akan fuskar ta inda take bata motsa ba , ba domin tazarar dake tsakanin su na da ɗan yawa ba da babu abunda zai hana ya iya jin sautin bugun zuciyar ta..
"Ki tafi gida Sofi .
Ya ce da wata irin kakkaurar murya yana ɗauke ganin sa daga kan ta ya zagayo da Yakaka daga bayan sa yana sake bin jikin ta da kallo kamar dai yana yiwa Sofi nuni da mummunan laifin da ta aikat ,yana kallon fuskar Yakaka tamkar ita yake yiwa maganar ya ɗora da cewa.
"Ki je gida akwai buƙatar ki sake samun ƙarin tarbiyya irin ta masu hankali da cikakkiyar koyarwar Islama ko ɗaya ba zan iya sake jimirin ɗaukar salon haukar da kike yi ba .
"Ki tafi gidan ku Sofi.
Ya furta hakan da buɗaɗɗiyar muryar da yasa kuka tahowa Yakaka da sauri ta shige cikin jikin sa tana zagaye shi da hannunwan ta , matsanancin tsoro na ɗarsuwa a ran ta ganin ɓacin ran sa Mai tsanani irin wanda ta daɗe bata gani ba.
"Ga Sofi kenan matar son sa da ita ce ta kora ta layin.
ina ga ita kuma ? Da ta yaga kayan ta da kan ta ? Watakila idan ya gama da Sofi ya dawo kan ta "shikenan Hajja ta jawo mata .
Hannun sa da ya sauke a bayan ta yana ɗan buubbuga ta alamun rarrashi yasa ta ji nutsuwa ta fara dawo.mata da sauri ta ɗago kan ta tana kallon fuskar sa da shi ma ita yake kallo.
Zata yi magana ya hana ta ta hanyar jaan hannun ta zuwa hanyar ɗakin sa ba tare da yace ƙala ba
A ɗan tsorace ta dubi sashin Sofi har lokacin tana nan a tsaye inda take tamkar an dasa ta kallo ɗaya ta yiwa fuskar ta tayi saurin janye idanun ta tana jin yadda zuciyar ta ta doka da ƙarfi babu shakka ta hango wani lamari mai kaifi daga cikin idanun Sofi da suka tara ruwan hawayen da basu kai ga zuba ba '
"Ki tafi tare da dabban da kika kawo min gida bana so na fito na ga ɗayan ku .
Doctor Hamza ya furta hakan kafin su kai ga shiga ɗaki.
Wani irin tsuma jikin Sofi yake so take Allah ya kawo wani ya wanka mata marin da zai farkar da ita daga mummunan mafarkin da take yi "Doctor Hamza ne da kan sa yau yace ta fita ta bar gidan sa ? Razanar da ta tsinka mata gudun jikin jikin bai wuce dalilin korar ta ta ba " akan wannan kuchakar 'yar gudun hijirar 'Yar talakawa 'yar ƙauyen ne Hamzan ta ya kore ta?
Kai ina ƙarya ne lokaci yayi da zata farka daga gyangyaɗin da take yi da har yasa tayi saken da wankin hula ke shirin kai ta tsakar dare akan Yakaka.
Ihu take son kurmawa amma tana ganin a halin da take ciki babu lokacin ihu , da gudu ta taka ta hau sama ɗakin ta mukullin motar ta kawai ta ɗauka sai fa wani siririn mayafi da ta rufa akai ta fita daga gidan .
Wani irin gudu take yi a kan titi da ya zarce ka'ida tana yi tana dukan kan ta da hannun ta ɗaya .
Lokacin da ta shiga gidan su kai tsaye falon Momy kori ta zarce wacce bata san da shigowar ta ba sai da ta ji ana mata rotse a falo ta yunƙura daga kwanciyar hutun da take yi akan gado ta fito tana cewa "meye haka ? Meke...'
Sauran kalmomin sun maƙale ganin 'yar ta Sofiya ce take mata wannan aika aikar duk ta farfasa mata show-glass
Da gudu ta ƙarasa tana riƙo ta Amma sofi sai sake fisgewa take da alamun fitar hayyaci a tare da ita .
Hankali tashe take kiran sunan ta
"Sofi , Safiya ke Safiya meye hakan ? Kin yi hauka ne dan ubanki.? Nace hauka kike ?
Ganin taƙi saurararta yasa Momy Kori ta cire hannu ta wanke ta da marin da yasa Sofi wani irin juyowa a fusace ta tunkuɗa Momy kori tayi zaman dirshan a kujerar gefen ta .
"Momy ki rabu da ni wallahi sai na tarwatsa rayuwar Yarinyar nan yadda nake tarwatsa wannan show-glass din naki.
"Wallahi sai na kashe ta , kafin ta kashe min aure ta raba ni da Hamza a ƙarshe tasa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 104 Chapter of 111