wanda zai zo mata da sauyi daga JAHILA ZUWA MALAMA .
Gidan malama Maryam bayan layin gidan samy baby ne , ɗan madaidaicin gida ne inda suke rayuwa ita da mijin ta da ƴaƴan su uku , babbar ƴar ta lubna zasu iya zuwa sa'anni da yakaka , sai maza biyu faruq da sadiq , a halin yanzu Lubna tana ss2 , faruq yana ss1 sai sadiq da yake jss3 , mahaifinsu ƙaramin ma'aikaci ne da yake aiki da wani company ,"
Rayuwar gidan Malama maryam abun sha'awa ce duba da yadda suke masu ƙaramin ƙarfi amma rayuwar su cike take da wadatar zuci , soyayya da shaƙuwa gami da tausayin juna a tsakanin iyayen da ƴaƴan su ya yawaita , da hakan ya zama abu mafi muhimmanci da ya haifar da ingantatciyar tarbiyya a wajen ƴaƴan su ,
tare da taimakon tsayayyar uwa da suka samu , malama maryam mace ce wacce ilmin addini ya wadace ta , take kuma aiki da shi, a yanzu matakin karatun ta degree ne a fanni Arabic And Islamic Studies , sai dai mai fadadawa tare da zurfafawa cikin neman ilmi ce musamman ma na addini, a bangaren bokon ma ba baya bace ,
Yanayin ɗabi'un ta su ke sanya take birge duk wasu mutanen da suka mu'amalance ta , komen ta cikin tsari da nutsuwa take yin sa , bayan wadatatciyar tsaftar da ta bayyana kan ta agare ta a duk inda ta kasance ,
A tun ganin farko da Malama Maryam tayiwa Yakaka yadda ta tarar yara na yi mata dariya , ta ji tausayin yarinyar ya tsirga mata , ta san babu shakka wani shamaƙi mai girma ne ya tauye yarinyar ya hana ta samun ilmi akan kari , dan haka ta ƙudiri aniyar jan ta a jiki , ta yadda zata tunga taimaka mata tare da ƙarfafa mata akan harkar karatu ,
Ganin suna kaiwa har kusan magariba kafin su dawo gida idan ta tsaya yiwa yakaka lesson saboda nisan dake tsakanin makarantar da unguwar su , yasa ta cewa yakaka su dunga komawa gida tare idan kowaccen su ta je gida tayi sallah ta ci abinci , sai yakaka ta zo har gidan ta suyi lesson ɗin , wanda lokacin da take ɗauka tana yi mata lesson ɗin ma ya zarce awa ɗayan da makarantar ta sharɗanta mata ,
Sannu sannu saboda nacin karatu irin na yakaka da kuma samun fuska da tayi wajen malama maryam da take kira ,"anty," wacce ta sake mata sosai babu tsangwama ko kyara a yayin da take koyar da ita , ya sa har ranakun da babu makaranta ma yakaka zuwa take su ɗauki lokaci ana mata lesson ko na arabi ko na boko , wanda malama maryam ta lura yakakar tafi kafa naci akan na bokon tamkar dai tana da wani lulluɓaɓɓen burin da take son cikawa ta hanyar karatun bokon , babu laifi ƙwaƙwalwar yakaka tana da saurin fahimta hakan ya sa take jin daɗin koyar da ita ,
A hankali sabo ya fara shiga tsakanin yakaka da lubna wacce take yarinya mai tsananin wayo , hankali da manyance , cikin abunda bai fi sati uku ba da fara zuwan yakaka gidan su ƙawance ya ƙullu tsakanin su kasancewar halin su na nacin karatu da ya zo ɗaya , saboda lubna mai naci da ƙwazon karatu ce duk kuwa da cewa makaranta mai sauƙin kuɗi suke karatu ita da ƙannen ta , amma saboda kaifin ƙwaƙwalwar su , da kuma tsayuwar iyayen su akan fannin karatun su ya sa ko yaran da suke karatu a shararrun makarantu kuɗi baza su fi su ilmi ba ,"
Nacin karatu biyu ta haɗu dan haka bayan lesson ɗin malama maryam , lubna ma ta na koyawa yakaka wasu abubuwan da suke ma sunfi matakin karatun ta , a cewar lubna lokacin da yakakar zata kai matakin ta riga ta koya baza ta ji wahalar karatu ba ,
A wani yammaci lubna da yakakar suna zaune kan ƴar darduma a tsakar gida bayan lubna ta gama koya mata karatu , suna ƴar hirar su kafin malama maryam ta gama ƴan aikace-aikacen da take yi a ɗakin baban su ,
Lubna ta dubi yakaka wacce ta duƙufa tana kwafar rubutu daga jikin textbook ɗin ta ,
Yakaka ku ƴan wanne gari ne ? Naga zane a fuskar ki , kuma hausar ki ma wata iri ?
Ba tare da ta ɗago ba tace
Ni ƴar maiduguri ce !
Su maman ku da ƴan uwan ku duk suna maiduguri ne , ? Kin ce nan da antyn ki kike zaune ,
Tsam yakaka tayi ta bar rubutun da take ,"
Ganin shirun ta ya ɗauki lokaci ya sa malama maryam fitowa daga ɗaki da duk hirarrakin nasu daman a kunnen ta yake ,
Lubna tashi maza ki ɗora girki , yakaka kawo textbooks ɗin ki mu fara karatu ,
Babu kuzari tare da walwala a gare ta suka yi karatun suka gama da bata wani fahimta ba ko kusa , da malama maryam ta lura da kyau ma sai ta ga taruwar hawaye a gurbin idon yakakar lokacin da suke yin sallama zata tafi gida , bata ko jira rakiyar lubna da take raka ta kofar gida ba , tayi tafiyar ta ,
Tana fita malama maryam ta ƙira lubna ta zaunar da ita tayi mata faɗa sosai akan bincikar mutum game da abunda ya shafi rayuwar sa kai tsaye ba tare da shi wannan mutumin shi yayi ra'ayin kan sa , ya bata labari ba,
Nan tayi ta ba wa mamar ta hakuri tace baza ta sake ba, malama maryam tace ita ba ita zata bawa hakuri ba , yakaka zata ba wa ,"
nan tayi alƙawarin gobe idan yakaka ta zo zata bata haƙuri ,
Tun a hanya yakaka take kuka shaɓe shaɓe da hawaye har ta ƙarasa gida , tana shiga kai tsaye ta wuce samy baby tare da ƙawayen ta da suke baje a falo suna hirar su , kowacce ta bararraje kai ba ɗankwali sai tilin izgar roba da aka yi musu kitso da shi a ka ,
Chan lungun gado ta samu ta Zauna gami da haɗa kan ta da jikin gadon ta fashe da kuka me fidda sauti , kukan tausayin rayuwar da ta bari a baya , kukan ƙewa da famuwar ciwon da ke binne a ƙasan ran ta , kukan tunowa da iyayen ta , ƴan uwan ta ,garin ta , asalin ta , kukan rashin kowa na ta da tayi ,
Yaks kukan me kike haka ? Cewa nake yanzu lokacin kuka ya wuce a wajen ki ? Ashe har yanzu baki san cewa kuka baya maganin kome ba ? Baya sawa bare ya hana ?
Ko kuwa wani abun malamar ta ki tayi miki yanzu na je na ci mata mutunci ? Ki min magana mana ?
Idanun ta jazur ta ɗago kai , anty samy na tuno da su mama , baba , falmata da baby mama , bani da kowa anty samy , ni bani da kowa !
Da wata irin murya mai ɗauke da tausayi , samy baby tace ,
Kina da ni yaks , ni zan cike miki gurbin su , har zuwa lokacin da zaki koma musu ,
Wasu sabbin hawaye ne suka zubowa yakaka ,
Falmata fa ? Waye zai zama madadi na a wajen ta ? Falmata bata da kowa ita ma idan gidan su rahima suka gaji suka kore ta ina zata je ita da baby mama ? Anty samy ina son komawa na zo da su ,!
Babu wanda zai kore su a gidan su doctor , doctor da baban sa mutanen kirki ne , ki kwantar da hankalin ki , ba yanzu bane lokacin da ya kamata ki ɗauki nawin su lokacin na nan zuwa kin ji ko ?
Naji anty samy ,
Yauwa ko ke fa ? Yakaka matar Yarima ta furta hakan tana juyawa ga barin ɗakin ,
Da wani irin kallo yakaka ta bita ,
Yarima
Ta maimaita !
****
Kwanakin kammaluwar aikin Biyamuradi Youssouf Tare da komawa ƙasar sa suna sake kusantowa , aiki yana sake zafafa a gare su , inda cikin ƙasa da wata ɗaya aka samu asarar fiye da sojoji hamsin cikin rundunar sa , wanda hakan ko kusa ba abu ne mai dadi ba wajen su da ma gwamnatin ƙasar su baki ɗaya , duk kuwa da cewa aikin soja daman ya gaji haka , sadauƙarwa ne a bakin rayukan su ,
Dan haka duk yadda ya so ya samu damar zuwa sake ganin ɗiyar sa abu ya gagara dole ya haƙure har zuwa nan da kwanaki goma da wa'adin su yake ƙarewa ,
Baby mama sai girma take tana daɗa wayo , har ta wuce kwanaki arba'in tana neman cika watanni biyu , kome ƙin ka da jariri idan ka ga baby mama sai ta burge ka , ka ji kana son ɗaukar ta , idan kuwa ka ɗauke ta ji zaka yi ina ma a baka ita , ina ma ƴar ka ce ? Yarinya ce mai tsananin ruwan kyau bayan kyaun kan sa da take da shi , ƴar bul-bul da ita fara tas gwanin sha'awa madarar jariran da ake bata ta karbe ta ba'a ce jaririyar da ta barranta da shan nonon uwa bace ba ,
Bugu da ƙari kulawa da lelen da Falmata take yi mata domin duk da kasancewar falmata makauniya , tsafta yana daga halittar ta ce , dan haka ko yaya ta ji wani yanayi da bai gamsar da ita ba a tare da baby mama , take zata tuɓe ta ta goge mata jiki da wiper , ko ruwan ɗumi da tawul ta sauya mata diaper da kaya , bayan wanka sau biyu da hajja mai wurya take mata safe da yamma ," dan haka koyaushe baby mama cikin ƙamshi take da wankakkun kaya tsaf-tsaf ,
So da ƙaunar baby mama a bayan kowacce daƙiƙa sake ninkuwa yake cikin ran falmata , ta ɗauki duk wani so ƙauna da tausayi na duk wasu mutanen da ta taɓa so a rayuwar ta rashin su ya sa ta juye su akan ƴar jaririyar , tamkar ran ta aka taɓa haka take ji idan tace 'uhun' da sautin kuka ,
bata taɓa gajiyawa da hidimar baby mama , ta kan manta da yunwar cikin ta ko ƙishirwa idan ta shagaltu cikin tarairayar ta , son baby mama haɗe yake da bugun zuciyar falmata !
Waƙoƙi iri iri take rera mata da ƴar daddaɗar muryar ta cikin yaren su , sai kuwa ƴar jaririyar tayi luf , ƙulus a kwance tana kallon fuskar falmata da tunda ta fara kallon abubuwa ta himmantu gurin tsare fuskar falmatan da idanun ta a duk lokacin da take farke , ga alama bada jimawa ba zata haddace kamannin ta tare da ɗaukar yanayin ɗumin jikin ta , ta kuma gane warin jikin uwar goyon ta da ta buɗi ido tun ranar farko ta gan ta a matsayin UWA a gare ta ,"
******
Duk abunda aka sanyawa lokaci aka zana iyakar sa to fa babu shakka zai zo ya wuce tamkar da ɗai ba'a taɓa fara farkon sa ba ,
Yau shabiyu ga watan goma sha biyu ita tazo dai-dai da ranar kammaluwar aikin tawagar rundunar sojojin niger da suka kawo tallafi wurin yakar ƴan tawayen Boko Haram zuwa cikin yankin nigeria ta kan boda inda yankunan biyu suka haɗu na niger da nigeria ,
ƙarƙashin jagorancin Colonel Youssouf Abdul-Azizou Baskore , a kuma yau gwamnatin ƙasar su ta bada umarnin su fara janyewa daga filin daga inda waɗanda aka turo su maye gurbin su zasu samu isowa bakin dagar a yau , ' dan haka baki ɗayan sojojin gurin idan ka dubi fuskokin su a yalwace suke da fara'a , inda dayawa daga cikin su suke ta ihu da wasanni a tsakiyar dajin domin bayyana murnar su a fili kan komawar da zasu yi ƙasar su cikin dangi da iyalan su , bayan kwashe fiye da tsawan watanni goma sha biyu da suka yi cikin daji ,
Colonel Youssouf ya bi jerin ƴan uwan sa soji wajen bayyana farin cikin sa bisa ga wannan nasarar da suka samu na tsallake hare-haren ƴan tawayen boko haram ɗin da suka sha far musu , da kuma nasarorin da suka samu wajen fatattakar ƴan tawayen boko haram ɗin ta hanyar kashe wasu tare da kama wasu da dama , hakan a gare su babban nasara ne da dukkanin su suke sanya samun ƙarin girman matsayi daga gwamnatin ƙasar su ,
Gefe guda kuma zuciyar sa cike taf da murnar sake ganin ɗiyar sa da zai yi a yau , sosai ya zaƙu yake kuma ɗora idanun sa akan fuskar ta , dan haka duk wani abunda yake cikin ƙuzari da karsashi yake yin sa ,
Sha biyun rana tawagar sojin da zasu karbi aiki suka iso ba tare da ɗaukar dogon lokaci ba bayan musayar gaisuwa da wasu bayanai na sirri irin na tsaro da ya shiga tsakanin manyan sojojin gurin da zasu tafi da sabbin da zasu maye gurbin su ,
Motocin da suka kawo sabbin sojin suka fara juyawa da tawagar masu komawa inda zasu ajiye su a babban barikin garin maiduguri zuwa gobe da zasu wuce ƙasar su ta jirgi da zai tashi ta abuja !
Biyamuradi Youssouf bai jira rana tayi sanyi ba , da isar su barikin maiduguri , wanka kawai yayi ya sauya kayan sa daga uniform ɗin soji ,
Ɗaya daga cikin direbobin su ya ja sa zuwa unguwar da ƴar sa take ,
Ƙarfe ɗaya na rana ta gota suka isa gidan nan ya tadda prof tare da wasu baƙin sa ,dan haka ya jira su har suka gama ganawa sannan ya shiga falon ,
Bayan gaisuwa da suka yi prof bai bari ya ɗora kome ba yace bari suyi sallah su ci abinci ,
Bayan sun ɗan taɓa abincin da ba sosai Biyamuradi Youssouf ya ci ba ,
Prof ya tattara hankalin sa ga Youssouf yana saurarar sa inda yake sanar da shi ,
Yana so gobe ya zo ya ɗauki ɗiyar sa saboda a goben yake son komawa ƙasar su domin aikin sa ya kammala ,'
Shiru prof yayi yana ɗan nazari
yayin da zuciyar yarima ta cika taf da taraddadi tare da fatan kar wata matsala ta taso domin zuwa yanzu ya gama tsara kome game da makomar rikon ƴar sa a tare da shi , ya gama tsara inda zai kai ta tayi rayuwa irin wacce yake so ƙarƙashin inuwar kulawar sa da kuma kariyar sa ,
dan haka baya jin akwai wani abunda ya isa ya hana shi ɗauke ɗiyar sa daga hannun waɗannan mutanen da bai kai ga sanin su ba basu kuma da kowacce irin alaƙa da shi da har zai iya barin jinin sa tare da su , ya shirya tsaf ko ta tsiya ko ta arziki zai tafi da ƴar sa !
Gyaran murya prof yayi kafin ya ɗora da cewa ,
Ɗa na mai zai hana idan har ka amince ka bar jaririyar nan a hannun ƴar uwar mahaifiyar ta har zuwa lokacin da ta ɗan tasa tayi wayo shekaru biyu zuwa uku sai ka dawo ka ɗau ƴar ka , baka ganin yanzu idan aka raba yarinyar nan ƙanwa ga mahaifiyar ƴar , zata shiga damuwa me tarin yawa ganin cewa har zuwa yanzu ba ta kai ga gyagijewa daga ruɗanin da mutuwar yayar ta ya jaza mata ba ,bugu da ƙari bata da kowa nata a halin yanzu sai ita wannan ƴar ta ka , ka duba magana ta da kyau ,
Ya ƙarasa zancen da bada zaɓi ga Biyamuradi ,
Ba domin tun ganin farko da Youssouf ɗin ya yiwa prof ɗin ya riga ya cika masa ido da ƙwarjinin sa tare da cikar kamalar sa ba , sannan halin dattaku da mutuntaka da ya dunga nuna masa a kowacce haɗuwar su , mafi muhimmanci kula da rayuwar ƴar sa da yayi na wani lokaci ,
bayan haka da babu abunda zai hana ya kartawa prof rashin mutunci , ya kuma gwada ƙarfin ikon sa na soja , sannan da ƙafafar su ta sarakai da koyaushe abunda suka so shi ake mu su ba'a musa mu su , ya ɗauke ƴar sa yayi tafiyar sa , to amma girma prof nada yawa a idanun sa dan haka ya sassauta murya tare da saita nutsuwar sa yace
Baba nan ba kassa ta ba , sannan ni kuma ai ma'aikaci ne , idan na tafi na bar ɗiya ta nan hankali na basshi kwanciya , chan inda zan tahi da ita nan ai shi tushe da assalin ta , kayi haƙuri baba zan tahi da ɗiya ta na ɗau Alƙawarin zan wanzu ina kawo ta lokaci zuwou lokkaci ta ga innon ta da yardar Allah ,
Shiru prof yayi yana jin tausayin falmata na kawo masa , bashi da wani ƙarfin iko akan yaran , bai haɗa kome da su ba idan banda taimakon su da ya biyo ta hannun sa dan haka shi baya da ƙarfin hanawa Biyamuradi ɗiyar sa ,
Toh bari a ƙira ita uwar riƙon ƴar ta ji daga bakin ka , kafin gobe da zaka dawo ɗaukar ƴar ,
Rahima ce ta rako falmata a yau da kallo ɗaya za'a mata a gane gaf take da ɓarkewa da kuka saboda ƙiran da aka mata ta kawo baby mama
Daga gefe ta gurfana bayan ta gaishe da prof , tayi shiru ,
Fatima ga baban jaririya nan ya sake dawowa yau , miƙa masa ƴar sa ya gan ta ,
shiru tayi bata ce ƙala ba
A hankali Rahima ta zare baby mama daga hannun ta wacce take ta wasa da hannuwan ta idanun ta tar a buɗe , shirye take tsaf cikin jar riga ta jarirai mai haɗe da wondo da safa , kan ta lulluɓe da farar hular sanyi mai ratsin ado da fulawoyi jajaye ,
Hannun Youssouf har rawa yake lokacin da yake ƙarbar yar jaririyar , yana ƙarbar ta ya zarce da ita zuwa fuskar sa inda ya sumbanci kumatun ta zuwa goshin ta , bakin sa ɗauke da addu'o'i ya kama wannan ya Sake waccen ,
Farin cikin sa ya yawaita da har ya gaza boyuwa ya bayyana akan fuskar sa dake ɗauke da murmushi mai bayyana haƙora ,
maida ita ƙirjin sa yayi ya rungume ta rungumar da ke bayyana tsantsar so da ƙaunar da yake mata , ji yake kamar ya buɗe cikin ƙirjin sa ya ɓoye ta ,
Da dariya akan fuskar sa ya ɗago cikin cewa
Ɗiya ta girma sossai , hala wanni sinadarin ƙara wa jarirai girma da lafiya kuke bata ? Madallah Madallah da ku , "
Ɗan murmushi prof yayi , kafin ya maida ganin sa kan falmata wacce ta ƙagu a miƙo mata baby mama suyi tafiyar su ,
Fatima kina ji na ko ?
Ina ji Baba
Ta amsa da ladabi cikin muryar ta ,
Baban jaririyar nan ne ya zo yau yake shaida mana ya gama aikin sa da ya kawo shi nigeria nan ƙasar mu , dan haka gobe yake son komawa tare da ƴar sa , a shiryawa jaririya kayan ta kafin gobe ,
Tamkar kunnen ta ya toshe haka ta ji dumm , cikin kan ta , tana jin yadda kalmar a haɗa kayan baby mama za'a tafi da ita gobe yana bin duk wata gaɓɓa mai kuzari a jikin ta yana kassarawa ,
wanne azzalumi ne yake neman ta ƙarfi da yaji sai ya raba ta da jinin ta ɗaya tal da ta rage mata a duniya , ?
Da wani nisasshen yanayi cikin muryar ta ta ɗago kan ta tana saita idanun ta inda ta ji tashin muryar youssouf ɗin a ɗazu tace
Wanene kai ? Me muka maka kake son raba mu ? Aina kasan yakaka na ?meyasa kake ƙarya ?
Shiru tayi tana jin yadda fitar numfashin ta ke sauyawa kafin ta ce cikin ƙarajin kukan da ya taho mata ,
ƙarya kake baby mama bata da BABA kai ba baban ta bane , yakaka ita kaɗai ta haifi baby mama , ina kake lokacin da yakaka take rashin lafiya akan cikin baby mama ? Ina kake lokacin da yakaka take shan wahala alhali baby mama tana cikin ta ? Aina kake lokacin da Yakaka na ta mutu sanadin haihuwar baby mama ?? Ƙarya kake kai mugu ne , ba kai bane baban baby kana so ne ka gudu da ita ,
rarrafawa tayi inda ta ji sautin baba prof yana ƙoƙarin son katse mata maganganun ta ,
Illahirin jikin ta rawa yake lokacin da ta dangana da jikin kujerar da yake zaune ,
ba-ba-Baba bani da kowa sai baby yakaka dan Allah kar ku bari ya raba ni da ita wallahi ƙarya yake yi maka , Baba ni miskiniya ce dan Allah kar ka bari ya zalunce mu ni da baby yakaka dan Allah Baba ,!
Wani irin yanayi me wuyar fassara prof ya tsinci kan sa a ciki ƙwarai da yana da iko da yau ya hana youssouf ɗaukar jaririyar nan ya bar ta a hannun yarinyar nan , "
Idon sa ya sauke akan Youssouf ɗin wanda kan sa yake sunkuye yana kallon fuskar ƴar sa ,tamkar bai san da bulayin da Falmata ke yi ba, sam baya so tausayin falmata da ya fara tsirga masa ya sanya shi barin ƴar da Allah ya jarabbe shi akan ta hannun mutanen da ba shi da tabbacin zasu iya riƙon ta har tsawon rayuwar ta ba , kar watarana ta walakanta ko ta sha wuyar rayuwa , ƴar sa mace ce ƙwarai tana buƙatar uba a halin tafiyar rayuwar ta nan duniya ,
shi ya barranta daga samari irin sa waɗanda zasu samu haihuwa ta haramtatciyar hanya su ƙarawa kan su zunubi ta hanyar yin watsi da abunda suka haifa ko ma su kashe baki ɗaya , yana so ya ubangiji ya yafe masa akan zunubin da yayi ma ta hanyar samar da ita baya fatan shaiɗan ya sake jaan sa ya aikata wani zunubin da yafi wanda ya aikata a baya muni ,
Mayar da ganin sa prof yayi ga Falmata cikin sigar rarrashi yace fatima ki daina cewa jaririyar nan bata da Baba , alhalin ga baban ta nan a zaune yana jin ki babu kyau haka , kiyi haƙuri ki bari ya tafi da ƴar sa yayi alƙawarin zai dunga kawo ta nan gidan gurin ki kin ji ko ?
sai lokacin Youssouf ya ɗago kan sa ya dube ta ,
Ƙwarai nayi alƙawari ƙanwa ta, zan dunga kawo ta zouwa gare ki har girman ta , ke ai har abada uwa kike a gare ta ,
Zumbur ta miƙe tsaye , cikin takun da kafafun ta ke harɗewa ta nufi inda take jin tashin muryar sa ,
Hannun ta duka biyu ta miƙa da zummar riƙe sa yayi saurin kaucewa yana sake boye baby mama cikin ƙirjin sa ,
Gefen rigar sa tayi wa wani ƙaƙƙarfan riƙo ba da wasa ba , Cewa take
Dan Allah ! Dan Allah ka ji tausayi na ka bar min baby , Dan Allah kar ka raba ni da ita , zan mutu idan ka ɗauke ta , dan Allah .....
Numfashin ta ne ya fara tsarƙewa dai-dai da ƙarasowar Rahima wacce prof ya yiwa umarni da ta janye Falmata , hawayen tausayin Falmatan suna zarya a kumatun ta ,
Luuuu ta tafi baya ta faɗi bisa jikin rahima suka ƙarasa bajewa a ƙasa tare babu alamun numfashi ga Falmata ,
subahannalahi innalillahi wa inna ilaihi raji'oon sune kalmomin da prof ke jerowa
Rahima ƙira direba maza a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 44 Chapter of 111