da ƙwallar da take ji tana cika mata ido taƙi yarda ta sake kallon Sashin da Biyamuradi yake tsaye duk da cewa tana jin idanun sa na yawo a kan ta.
chauffeur ya buɗe ƙofar motar Siyama da Yumna suka shiga ganin haka yasa a hankali ta juya tana ɗaga takun ta dan barin wajen.
" Fatima .
ya ƙira sunan ta .
Chak ta tsaya ba tare da ta jiyo ba , ɗan taku yayi ya matso kusa da ƙofar motar cikin amon sa mai ƙarfi yace "je t'aime tellement Et tu me manqueras.
Har cikin ran ta ta ji kalmomin sa a hankali ta runtse idanun ta hawayen da suka cika gurbin idon suka gangaro kan ƙuncin ta .
Muryar ta na rawa ta furta "Allah ya kiyaye mu ku hanya ya kai ku lafiya Amin .
Da sauri kamar ba ita ce ke ɗauke da wannan tirtsetsen cikin ba ta ƙarasa barin wajen idanun ta a rufe da ruwan hawaye .
Youssouf da yake tsaye ji yake kamar ya bita ya riƙe ta ya hana ta tafiya amma ya san idan yayi hakan zai ɓata goma ne ɗaya bata gyaru ba .
Lokacin da ta ɓacewa ganin sa dan kansa ya shiga motar direba ya jaa suka ɗau hanyar barin-gidan suka kama hanya ɗoɗar zuwa Birnin Tahoua inda yake aiki .
Lokacin da Falmata ta koma sashin ta abu na farko da ta fara yi bayan ta ci kuka har ta bawa aku lada ta ji idanun ta sun fara raurawa suna mata alamun ciwo '
Lallaɓawa tayi ta ɗau wayar ta wacce take ji tana ta ɗaukar kiɗa da ko bata duba ba ta san Biyamuradi Youssouf ne ke kira
A hankali ta shafa wayar ta kashe tana zunɓuro baki kamar yana ganin ta tace "Na fasa yin Appel vidéo ɗin da kai .
****
Duk da cewa tafiyar bata yiwa Siyama armashin da ta so ba amma hakan bai guntule mata jin daɗi da ɗokin ta ba sai hira take yi masa wani ya amsa wani kuwa yayi shiru yana shafe-shafen waya da sarai ta lura da wacce yake faman ƙira Fatima ce .
Ko da suka isa jahar Tahoua da gefen Azahar a share a tsaftace suka tarar da gidan dan haka aikin da tayi ba mai yawa bane ba illa kayayyakin su da tayi musu ma'ajiya a muhallin da ya dace ta sake yin wasu 'yan gyararraki da ba'a rasa ba.
Kafin ta gama wani Soja da yake hidima da gidan ya zo da cefene dan haka kai tsaye ta shiga kitchen duk da cewa ba sabon ta bane yin girki amma bata gagara iyawa ba dai-dai gwargwado ta zage-damtse dan farantawa Mijin ta tayi girki mai kyau da daɗi Yumna na taya ta da ɓarna .
Youssouf kuwa tunda suka zo da aka sauƙe su shi wucewa direba yayi da shi can babban ofishin su inda zasu yi wata ganawa shi da abokan aikin sa .
Ba shi ya samu damar komawa gidan ba sai bayan isha'i lokacin da ya shiga gidan tsit babu motsin kome sai na na'urori.
bai tarar da Siyama a falon ba sai fa wani daddaɗan ƙamshi da ya shaƙa wanda take ya tado masa da tunanin Fatiman sa domin kuwa ƙamshin irin nata ne a duk inda tayi bigire nan yake jin irin ƙamshin kewar ta mai yawa ya ji tana bin jikin sa , tunda suka taho yake son ya ji lafiyar ta amma taƙi ɗaukar wayar a ƙarshe ma ta kashe ta baki ɗaya kuma tunda ta kashe bata kunna ba .
Zama yayi akan kujerar falon yana sunce igiyoyin takalman sa , bai ji tahowar ta ba sai sauƙar kyakkyawan hannun ta da yasha adon ƙunshi ya gani ta ajiye akan hannun sa ta karɓe kunce takalmin da ya fara .
Sakar mata yayi yana bin jikin ta da kallo da ta sha ado da wata bugaggiyar shadda Boo ɗinkin bubu tayi ɗaurin ɗankwali mai ban sha'awa jelunan kitson ta da ta haɗa ta tufke ta haɗe cikin ƙaton ribbon ya taimaka wajen ɗago da ɗaurin daga ƙasa sai ya zauna ɗas a kan ta kamar hula .
"Siyama ma'abociyar kwalliya ce , daga can ƙasan ran sa ya aiyana haka .
Yana kallon ta har ta gama ta ɗago fuskar ta da bata cika fente-fente ba tana masa murmushi ta ce "Bienvenue mon amour et comment va le travail? Sannu.
Fuskar sa a sake da taƙaitatcen murmushi yace "ke za'a wa Sannu Maman Yumna da hidmar gida da kaɗaici , ɗakin taro mun ka hige sai yanzou munka kai ga hittowa.
bata amsa ba ta miƙe da ɗan murmushi a fuskar ta ta wuce ɗaki daga can ta haɗa masa ruwan wanka .
Ya shiga yayi bayan ya gama ya sako ƙananun kaya da basu cika nawi ba a jikin sa ya fito
Daga nan abinci ta kawo suka ci tare bayan sun gama ta tattara wajen ta dawo ta zauna daga gefen sa suna kallon TV tare duk da dai ita ba wani jin daɗin kallon take ba saboda tashar labarai ne shi yake ganin kayan sa .
Lokacin da ta ga ya ɗau waya sa sai da zuciyar ta ta doka tana satar kallon sa ta ga ya fara ƙira bugu ɗaya biyu , daga can ta ji computer na sanar da shi wayar a kashe take chajin wayar sa ya duba ya ga saura kadan ta mutu dan haka kawai sai ya kashe wayar ya sa a chaji
yana jin duk babu daɗi "meyasa Fatima za ta masa wannan horon ?
"Biyamuradi
Ta ƙira sunan shi
Da ido ya amsa mata yana kallon ta .
Murmushin yaƙe tayi kafin ta ce "tunda muka zo nayi ta neman wayar ƙamnata a kashe wayar....
Kafin ta ƙarasa Youssouf ya amsa mata fuskar sa na bayyana damuwa "nima itta nake ta ƙira amma ta kar wayar ko mai yassa tayi hakan ?
"Watakila batta so ta tsare ma aiki ne , Siyama ta amsa masa tana ɗan nazarin sa ta ɗora da cewa
"Amma ko za ka gouda kiran Hajja ne saboda a san halin da ta yini ciki.
"Hakka ya kamata, Amma itta telephoné na babu wutta cikin ta.
"Bari na ƙira ta da telephoné na sai ta sada mu da itta
Bugu ɗaya Hajja ta ɗau wayar ta tana ɗan gigin bacci tace "hallo waye anan ?
Daga can Siyama ta amsa mata tana jin muryar ta ta watsake suka gaisa faran-faran ta ɗora da faɗa mata dalilin ƙiran nan take Hajja ta yunƙura ta fita daga ɗakin ta ta nufi ɗakin Falmata cewa take "kada ma ki katse ƙiran ai yanzu zan kai mata idon ta biyu dan ban jima ba ma da barin ɗakin nata bayan mun gama hira .
"Hello Maman Yumna da fatan kun isa lafiya ? daga can Falmata da ta karbi wayar ta furta
Shiru ta ji anyi "Hello ta sake cewa.
Daga can ɓangaren da tunda ta ɗaga wayar Siyama ta miƙawa Youssoufa
"Fatima .
Sautin sa ya doki dodon kunnen ta da yasa ta runtse Ido tana jin yadda gangar jikin ta ke sauyawa daga jin amon sa .
"Fatima me yassa kin ka kashe min waya unn ?
Shiru ta sake yi tana jin sa ya cigaba da cewa "kin sa na shigga damouwa , kar ki sake min ya hakka kin ji kou ?
"Fatima
"Mon bébé kina ji na ?
Sautin kukan ta ya ba shi tabbacin tana jin sa runtse ido yayi yana jin ciwon kukan nata ya fahimci Fatima tana da zafin kishi sosai da sosai da shi a ganin sa ba kome ya kawo hakan ba illa tsananin son da take masa.
Ajiyar zuciya yayi daga ƙasan ran sa ya fara harhaɗo kalaman da zai rarrashe zuciyar ta take cike da ƙaunar sa.
****
Bayan Awa Ɗaya da Rabi:
Rarrashi ya rikiɗe ya koma hira mai cike da raha da ƙaunar juna daga ƙarshe ma suka koma video call kamar ba sa rabu ba kafin daga ƙarshe ya sake wani rarrashin kafin su yi Sallama da alƙawarin gobe za ta gan shi a vidieo call a dai-dai wannan lokacin
Zuciyoyin Su cike da nishaɗi da begen juna suka yi Sallama bayan sun aikawa da juna Sumba ta iska .
Sai bayan da ya sauƙe wayar ya lura da yadda dare ya shiga wajen shaɗaya da rabi na dare.
Yawo yayi da idanun sa a falon sai dai ko alamun wacce yake dubawa bai gani ba , haka kawai ya ji wani irin yanayi na bin jikin sa yana ganin rashin kyautawa kan abunda yayi musamman da ya tuno da cewa da fa wayar ta su ka sha hira shi da Fatima , "anya kana adalci ? Zuciyar sa ta ƙwanƙwashe shi.
Cikin rashin kuzari ya miƙe bayan ya kashe kayan kallon ya rufe ko'ina ya nufi ɗakin baccin su '
A hankali ya turo ƙofar cike da son kiyayewa kada ya tada su a baccin da yake hasashen suna tsaka da yin sa .
Da shigar sa yayi turus kafin ya ɗan yi duru-duru saboda ido huɗu da suka yi shi da Siyama wacce take zaune daga ƙasa ta tasa laptop a gaba da alama karatu take yi .
Murmushin da ta jefe shi da shi lokacin da take zare gilashin idanun ta bai taimaka ba ko kaɗan wajen rage masa yanayin da yake ji a dai-dai lokacin da shi kan sa ya gaza fahimtar ainashin wanne irin yanayi ne ? .
"Ya Fatima da Bébé ? Duk suna lahia kou.?
"Suna lafiya , ya amsa mata kafin ya zauna daga kan kujera ɗaya tal da take ɗakin yana ɗan sosa ƙeya .
"Siyama .
Ya ƙira sunan ta yana kallon ta .
Cikin nutsuwa ta ɗago kan ta ba tare da ta amsa ba
Da taimakon hasken ɗakin ya iya hango yadda launin idanun ta suka sauya su ka yi jaa kaɗan .
"Ba kiyi bacci ba har yanzou ?
Ya tambaye ta .
Wani irin murmushi mai ciwo tayi tana kawar da kan ta , muryar ta babu ƙarfi sosai ta ce " Ban yi bacci ba Biyamuradi ina jiran ka shiggo muyi Sallama.
"Siyama
Ya sake ƙiran sunan ta bai jira amsawar ta ba yace .
"Duk lokacin da kin ka ji bacci kiyi ko da ina gidan ko bana nan ba sai kin jira mun yi sallama ba...''
"Saboda me ? Ta katse shi da wata irin muryar da take tsakanin harshe da wuyan ta
Kallon sa tayi ta ga yadda ya ke duban ta da rauni a cikin idanun sa , kafin ta ɗora da cewa .
"Saboda baka sona ? Baka ƙamna ta ? Baka amre ni domin so ba ? Ni matar cushe ce gare ka ?
"Siya...
Da sauri ta katse shi lokacin da ruwan hawayen ta ke sauƙa yana ɗiga ta cigaba da cewa
"Laifi zuciya ta tayi a doumin ta so ka ? Ko kouwa ni nayi laifi da na kassa jumriya akan ƙamnar ka har dai nayi kafiya kan Amren ka ? Da ka ke gwadan rashin ƙamna a fili kake watsi da sha'anin da duk ya shafe ni ?
Tasowa yayi ya dawo gaban ta ya zauna yana jin girman laifin sa na masa lulluɓi tunda ya kai girman da har ta kai yau Siyama ta ɗaga Muryar ta .
Hannuwan ta da suka ɗau sanyi ya riƙe yana lalubo kalmomin da ya musu ajiya mai nisa da basa taso da kan su sai fa akan wacce aka yi ajiyar su a domin ta yau so yake ya ƙalato su ya yiwa Siyama kyautar su wataƙila sa wanke mata zuciya su samar mata da nutsuwa a cikin hakan babu laifi domin ita ma ta cancanta.
"viens chérie yaya ki ke faɗin hakka ? Me yassa za ki ce bani ƙamnar ki ? Bani ƙamnar ki na amre ki har mun ka haihu ? Ina son ki mana Siyama...
Zame hannun ta tayi tana girgiza kai lokaci guda tayi wani murmushi mai ciwo muryar ta da 'yar dariyar baƙin-ciki tace .
"Kar ka jefe ni da kalmomin aro domin shi kayan aro ai basshi rufe katarar mai su , wannan kalmar ta so ba tawa ce ba ban taɓa samun ta ba ga gurin ka kai tsaye sai ko dan alfarma bani son jin ta domin ba'a halicce ta a zuciyar ka a domin ni ba .
Saƙare yayi yana kallon ta wata irin kunyar ta ya ji a lokacin tana tasowa tana danne shi har yana jin kamar bai iya numfashi mai kyau .
Ganin yayi shiru ya sa ta miƙewa bayan ta kashe laptop ɗin ta ta tura gefe , wani irin ciwo zuciyar ta ke yi so take ta samu waje tayi kuka yadda ya kamata .
Sai dai kafin ta ɗaga ƙafa ta bar gurin ya jawo hannun ta da ƙarfi ta taho gaba ɗaya ta faɗa masa yayi mata kyakkyawar runguma a ƙirjin sa .
Kukan da yake cin ta a rai shi ta samu damar yi ta shiga rairawa har jikin ta na tsuma .
Biyamuradi Youssoufa ya kasa cewa kome illa rungume ta da yayi tsam yana jin yadda kukan ta ke ratsa jijiyoyin jikin sa suna tsinka masa gudun jini tare da ɗarsa masa wani irin yanayi mai kama da tsoro-tsoro a cikin ran sa "tsoro yake ji na ɗaukar hakkin ta , tsoro yake kar Allah ya kama shi da laifin rashin adalci a tsakanin Matayen sa .
Sai da tayi kukan ya ishe ta har ta fara lafawa dan kan ta sannan ya kai hannu a hankali ya riƙo hannun ta ya ɗora shi a saitin ƙirjin sa muryar sa can a ƙasan maƙoshi yace .
"Kin ga nan , kin ji yadda zuciyata ke tsanan ta bugu a halin yanzu ? Akan ki ne Siyama tuhuma ta take yi meyasa na ɓata miki Siyama ? Zuciyata na ganin GIRMAN ki ke ABAR GIRMAMAWA kike a gareni , ina jin Kunya idan na ga na ɓata miki Siyama a nan duniya cikin 'ya'ya mata wace ta samu ƙima da girman matsayi kwatankwacin naki a gurina Siyama ? Amsar ita ce babu.'
" Yakanar ki ta sayo miki mafi ɗaukakuwar daraja a gurina shin ba za kiyi alfahari da hakan ba ?
A hankali ta ɗago kan ta daga cikin ƙirjin sa tana jin yadda ruwan hawayen ta ke ƙafewa zuciyar ta ke tsantsamewa kunnuwan ta ke buɗewa .
Kallon da take masa kallo ne na irin " sake faɗa na ji ? Da gaske kake ?
Da hannunwan sa biyu ya riƙo fuskar ta yana jin yanayin da yake ji a game da ita na sake ninkuwa har yana neman fin ƙarfin sa so yake kawai ta yarda da abunda yake faɗa mata .
"Siyama zuciya ta na girmamaki gangar jikina kuma na buƙatar ki ke ɗaya ce ke da wannan matsayin a guri na da alƙawari na miki watta ba zata samu gurbi ya irin na ki ba , watta ba zata ɗau wannan matsayin ba ki yarda da ni .
Ɗan bakin ta da ya faɗaɗa da murmushi yake motsawa da son cewa wani abu shi ya rufe domin a lokacin baya buƙatar tace wani abu .
"So , ƙauna , haƙuri , Yakana da kawaicin da ta kwashi shekaru tana gwada masa sun riga sun masa gamsarwar da bai buƙatar ta sake furta kowacce kalma a gare shi a domin wai ta maida masa martanin kalmomin sa lokaci ne yanzu yayi da ita ma zai kyautata mata gwargawdon girman da zuciyar sa ke bata .
"Ta gaza tantance a halin da take ciki tsawon lokaci ji take kamar mafarki take za ta farka , kalmar girma ta mata nawi wajen ɗauka kamar yadda zuciyar ta ta gaza wajen jurar irin farin-cikin da take ciki wanda da ɗai a rayuwa bata taɓa samun makamancin sa ba dan haka ta dunga maida masa martanin Soyayyar da yake gwada mata cikin nishaɗi da basu taɓa samun makamancin sa ba a duk zaman auren su .
"Shin me ya kai hakan martaba a ce Mijin ka wanda Allah ya umarta da ka girmama shi , da bakin sa yace shi ke girmama ka ?
"Ashe ba soyayya ce kaɗai abun nema a wajen Miji ba akwai abunda yafi soyayyar girma da martaba .
"Babu shakka daga yau za ta iya tutiya da matsayin da Mijinta ya ɗora ta akai matsayin da bata taɓa tarayya da wata akan sa ba nata ne mallakin ta ita kaɗai .
"Ina ma da mata zasu fahimci hakan a duk lokacin da hagu ta ƙi su a gurin Miji suyi amfani da Dama su samarwa da kan su ramin kan su ba tare da sun nace da suyi kafaɗa da kishiya ta fanni ɗaya ba.? Da kuwa gidaje da yawa an zauna lafiya a tsakanin kishiyoyi .
Siyama ke ayyana hakan a cikin ran ta bayan bacci ya ɗauke Biyamuradi Youssouf da ita kuma zallar farin cikin da take ciki a yau shi ya hana ta bacci .
A karo na biyu ta ɗaga kan ta duk da cewa da duhu a ɗakin so take ta sake ganin hasken fuskar sa ko da sau ɗaya ne kafin bacci ya ɗauke ta .
A daren yau son da take masa ya sake ninkuwa ne akan na daa har tana jin kamar ba zata iya ɗauka ba .
Cikin bacci ya mayar da kan ta jikin sa ya kwantar tare da sumbatar goshin ta kafin ya cigaba da baccin sa cikin nutsuwa .
Ɗan murmushi tayi ta sumbanci ƙirjin sa kafin ta rufe ido baccin da yafi daɗi da kan sa daɗi ya ɗauke ta.
****
Abuja
Cikin satika ukun da suka biyo bayan barin Sofi Gidan Doctor Hamza wata irin Soyayya mai daɗi da shaƙuwa mai girma ne ya ƙullu tsakanin ma'auratan biyu Doctor Hamza da Yakaka .
Musamman da ya kasance daman 'yan uwan juna ne dan haka sai aka yi dace wasu daga cikin halayen su suka zo ɗaya kamar yanayin buƙatuwar halittar su da matsananciyar tsaftar su , yawan ibadar su , da rashin son hayaniyar su dan a wasu lokutan ma shiru gidan yake ɗauka suna gudanar da soyayyar su a aikace ko kaɗan basa gajiya da junan su kusan koyaushe cikin ƙoƙarin farantawa juna suke muddin dai suna tare .
A satika ukun har wata 'yar sirantatciyar ƙiba Yakaka tayi ta sake fari tayi fes da ita , yawan gyaran da take yiwa fatar ta kamar yadda Amnee ta koya mata bayan ta haɗo ta da kayan gyaran yasa kullum jikin ta kamar bayan ƙwai luwai-luwai .
Ga ƙamshi na musamman da ya zauna mata saboda turara da take yi gaba ɗayan jikin ta da hakan shi yafi kome sa Doctor Hamza ya liƙe mata kasantuwar sa ma'abocin son kamshi.
Ga girki da kullum take yi musu masu gamsarwa da ƙara lafiyar jiki saboda har ajin koyan girki ta shiga a whtsapp na musamman da shahararriyar ƙwararriyar mai koyar da girke-girken nan kuma Marubuciya Maryam Talba ta bude take kuma jagorar azuzuwan musamman domin koyar da mata girke-girke masu gamsar da Maigida,
Tare da goyon bayan Doctor Hamza da shi ma yake jin daɗin girkin ta dan haka ya amince ta faɗa ajin Koyan girki Na chef Maryam Talba
(wacce duk take da ra'ayin shiga ajin girkin Chef Maryam Talba duba da cewa Azumi ya gabato Uwargida kina bukatar sabbin darasi kan girke-girke domin gamsar da Maigida da iyalan ki , to kar ki ji kome yi maza ki min direct message insha Allah zan sada ki da Chef din da na san sai kin min godiya a gaba sannan babban abun farin-cikin da za ki tadda shine a kudi mai rahusa za ki fada ajin 👌sai kun zo👍)
*****
Yau ta wayi gari cike da burin gwada wani daddaɗan girkin da a jiya Chef Maryam ta gwada musu da yayi matuƙar burge ta .
Kamar yadda Chef Maryam ta kware a girke-girken mu na nan gida Nigeria har da na ƙetere ma ba'a bar ta a baya ba ta ƙware a girkin larabawa dan haka yau Yakaka tayi aniyar gwada dafuwar Maqluba wadda dafuwar shinkafa ce da kaza, dankali, ganyayyaki haɗi da sauran sinadaran girki .
Maqluba girki ne na mutanan gabas ta tsakiya wanda yake da matuƙar daɗi .
Cike da nishaɗi take aikin ta tana yi tana bin ƙira'ar Alkur'ani da ta sa a wayar ta.
Kafin ya bayyana ƙamshin sa ya sanar mata da wanzuwar sa a gurin zuwa lokacin da ya shigo kitchen ɗin ta ɗago kan ta a hankali tana jifan sa da wani tsadaddan murmushi .
"Habibi barka da tashi , gaskiya ka sha bacci.
Ta furta hakan ba tare da ta janye murmushin ta ba
Ƙarasowa yayi ya rungume ta ta baya yana ɗora kan sa a kafaɗar ta yace .
"Wafaa kin saɓa doka ta meyasa ?
Wara ido tayi tana ƙoƙarin juyowa ya hana ta a hankali ta ce
"Kayi haƙuri cikin rashin sani ne.
"Ba laifi kika yi ba Wafaa , amma ban ji daɗi ba da kika manta cewa na hana ki kiyi aiki ke kaɗai idan har ina gida ko da bacci nake ki dunga tashina muna yi tare .
Murmushi mai bayyana haƙora tayi ta ɗan sauƙe ajiyar zuciya lokacin da ta kashe gas saboda girkin ta ya kammala .
Tana ƙoƙarin juyowa ya sassauta riƙon da ya mata ta juyo tana fuskantar sa.
"Hannun ta ɗaya ta ɗora a ƙirjin sa tana ɗan bubbugawa a shagwaɓe tace "wallahi har hankali na ya tashi ko wani laifin na yi ban sani ba.
Dariya yayi yana riƙe hannun ta yace "laifi kika yi mana meyasa za ki wahalar min da ruhina da kika san koyaushe yana nan ne a tare da ke , meyasa baki tada gangar jikin ba ? Anyi aikin tare da shi ?
Murmushi tayi tana kallon sa irin waɗannan kalaman nasa su suka ta dilmiye a cikin ƙaunar sa ba tare da ta ankara ba ko kaɗan baya mata ƙouron kalaman sa na soyayya kamar yadda baya ƙasa a guiwa wajen gwada mata ƙauna a zahiri bai kuma jinkirtawa wajen yaba mata a duk lokacin da tayi wani abun a yaba kome ƙanƙantar sa kuwa '
Maza irin sa sukan sauya akalar zuciyar kowacce mace cikin sauƙi .
Sauƙe idanun ta tayi ƙasa tana murmushi saboda wani irin narkakken kallo da yake mata , ita irin salon Soyayyar sa nawi take mata kunya take sa ta har ta dunga jin wani yarrr a jikin ta.
Ko kaɗan bata iya masa martanin kalaman sa , kuma bata jin daɗin hakan so take ita ma ta koya su dunga musayar ƙauna kamar abun zai fi armashi .
Sautin dariyar sa ta ji da yasa ta ɗago kanta da sauri tana kallon sa sai ta ga idanun sa bayan ta yake kallo .
Juya ta yayi yana mata nuni da wasu tattabaru Mata da Miji (aure ) , da suka sauƙa ta gaban tagar kitchen ɗin suna soyayyar su .
"Wow look at them Wafaa so lovely.
Ya furta hakan muryar sa kasa-kasa yana rungumeta ta baya.
Zuba musu ido tayi tana kallon yadda suke sumbatar junan su kamar sa cinye bakin juna, sun matukar birgeta tsuntsaye kenan ma suke wannan soyayyar ? Ba shakka soyayya aba ce mai daɗi.
Daga shi har ita shagala suka yi da kallon soyayyar tattabarun mai ban mamaki da Sanya sha'awa tare da nishadi a zuciyar ma'abota soyayya.
Basu Ankara ba Matar ta gayyaci Mijin dan Su cimma maƙurar soyayyar Su ganin haka yasa da sauri Yakaka ta ɗaga tafukan ta biyu tana rufe fuskar ta .
"Habibi mu bar su hakan nan zasu yi sirrin Su.
Ta furta hakan tana ƙoƙarin janye jiki daga wajen .
'Yar dariya Doctor Hamza yayi yana sauƙe mata hannun ta da ta rufe fuskarta da shi
Cike da zolaya a muryar sa yace "ki buɗe ido ki kalle su darasi za mu ɗauka mu ma anjima sai mu gwada.
tana buɗe idanun ta ta gan su a halin da ita bata so da sauri ta sake rufe ido ta juya tana shigar da kan ta kirjin sa har a cikin ranta kunya ta ji .
Rungume ta yayi yana dariya ƙasa-ƙasa kunyar ta na ɗaya daga cikin abunda yasa yake ƙara son ta ,kunya alamun imani ce bayan haka tamkar ado take ga ma'abota ita.
Ƙiran wayar sa da aka yi shi ya katse shirun nasu ya sassauta riƙon da yayi mata kafin ya zaro wayar sa daga aljihu.
Cikin ransa cike da addu'ar Allah yasa ba ɗaya daga cikin waɗan da yake zato bane .
Addu'ar sa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 106 Chapter of 111