bai cikin hayyacin sa , tabbas shi da kan sa ya ji mutuwar yarinyar , kome kuma ya kunce masa , zuciyar sa kuma ta raurawa ,
Kayi hakuri yaro mutuwa na kan kowa bari na ƙira a kawo maka ɗiyar ka , ƙanwar ta ma ta zo ku gaisa ,"
Waya yayi cikin gidan akan a zo da Falmata da baby mama ,"
Ya maida hankalin sa kan su Youssouf da tafeeda yana nazartar su , akwai tambayoyi dayawa da yake son yi musu ba wai dan bai yarda da su ba , sai dan a farkon kawo yarinyar gidan Hamza ya sanar da shi mijin yarinyar ya mutu boko haram sun kashe shi , sai kuma ga shi yanzu ya ga jami'in tsaro a matsayin mijin ta ko daman ɓata yayi ba mutuwa ba tsawon wannan lokacin ?
Shigowar Falmata riƙe da mama tare da rahima , shi yasa biyamuradi Youssouf ɗago kan sa ,"
Idanun sa so suke su ga ɗiyar , so yake ya samu rangwame ta hanyar fahimtar bashi da alaƙa da ɗiyar da aka samar ta hanyar banza wacce zuwan ta yayi sanadin mutuwar mahaifiyar ta me tarin rashin galihu , bai so lamuran sa su sake munana ,
Sai dai wani yanayi da ya tsinka jinin jikin sa lokacin da hasken fuskar ƴar jaririyar da ya ɓanɓare daga hannun falmata ba tare da ya jira sun ƙarasa shigowa falon ba yayi tattaki da sassarfa ya taro su ,
Yanayin mai ƙarfi ne da bai taɓa jin kwatankwacin sa ba da ɗai duniya ,
Jin sa yayi a wani yanayi wanda ya so ya saɓawa wanda yake cikin sa kafin ɗora idon sa akan ƴar da yaji ya gaza gane wacce matsaya yayi mata a halin da yake ciki ,
Kallon ta yake tamkar yana son ganin abun da ke lulluɓe cikin fatar jikin ta , kallon da yake mata ya sa duk wata suffa tata jeruwa cikin tunanin sa tana juyawa tare da girma mataki-mataki har zuwa lokacin da kammanin ta da mahaifiyar sa suka gama fitowa tsaf , tamkar kobo da kobo ,
Bai san lokacin da idanun sa suka samar da ruwan hawaye ba sai kawai ganin ɗigar su yayi akan fuskar ta , wanda ya nutsar da idanun sa kai babu shakka yana iya kallon ƙofofin gashin jikin ta ,
Sauƙar ruwa a fuskar ta ya sanya ta buɗe idanun ta a hankali ta wara su akan sa , fes ! da shi ma ya sake ware nasa idanun tare da ɗage duk girar sa biyu abun da ya kan yi idan yana cikin yanayi na shauƙi ,
Yamutse fuskar ta tayi cikin salon su na rikicin jaririyar zata yi kuka ,
Da sauri ya ɗago ta zuwa dai-dai fuskar sa ya sanya kan karan hancin sa yana goge mata ƙwallar sa dake kan kumatun ta da yake zaton ita zata sa ta kuka ,
Ai kuwa tamkar ya kunna ta sai kuwa ta sa kuka ,
Kukan ta ya zo dai-dai da fashewa da kukan falmata wacce da kyar Rahima ta banbare hannun ta daga cukumar da tayi wa rigar Youssouf , cewa take wanene anan ?
Rahima waye ya kwace min baby ?
Ka bani ita dan Allah ka bani ita kar ka sa ta kuka ? Kai waye , ? Rahima kika ce min Baba ne yake ƙiran mu ,? To waye ne ya karɓe min Yakaka na ?
Muryar prof ta sa ta ɗan samu nutsuwa har ta sassauta riƙon da ta yiwa youssouf , rahima ta samu nasarar janye hannun ta ,
Amma kukan yarinyar da take jin sa kamar ɗigar narkakkiyar dalma ya sa ta kasa tsayar da kukan ta , "
Ganin kukan ta yayi yawa ya sa Tafeeda tasowa ya dafa kafaɗun Youssouf , yana kallon fuskar sa , muryar sa babu ƙarfi sakamakon halin da ya ga Youssouf ɗin ya shiga tunda ya ɗaura idanun sa kan ƴar , yana nufin ɓullowar wani gagarumin lamari Masarautar Maradi .
Ɗan ouwa bada ɗiyar nan ga mariƙiyar ta , ga ta sai kuka take , !
Dauke idanun sa yayi da kyar daga fuskar ƴar ya mayar kan Tafeeda , da wata muryar da bata da amo yace ,"
Ɗiya tawa ce Tafeeda , wagga Ɗiya jini na ce , Ɗiya ta ce , A yau ni Uba ne , Uba ne ga wagga ɗiya da tsautsayi tare da kaddarar zuwan ta duniya ya sa kome ya faru kamar yadda ya faru ,"
Ɗan satar kallon prof , Tafeeda yayi yaga yadda hankalin sa baki ɗaya ke kan su , amma kasancewa falon me girma ne da ƴar tazara a tsakanin su ,
Wallah ka lura Ɗan ouwa idan ba hakka ba kana iya ɓata mouna kome ,
Hannun sa ya kai da nufin karɓe ƴar daga hannun sa , wata irin zamiya Youssouf ɗin yayi ya janye ƴar jaririyar sosai zuwa cikin jikin sa ,"
Baka ganin kuka take ?? Ka bari na lallashe ta ,
Haɗiye firgicin sa Tafeeda yayi , ka bada ita Yarima uwar goyon ta zata mata lallashi , akwai abubuwa dayawa a gaban mu ,
Ina uwargoyon ta ?
Yace yana mayar da duban sa kan su Falmata da duk budurin da tayi na cukume sa da kalmomin ta duk bai ji su ba , ruɗanin da yake ciki ya toshe masa kunnuwa daga barin jin hayaniyar ta ,
Da ɗan yatsa Rahima ta nuna masa Falmata wacce tayi shaɓe-shaɓe da hawaye sai ajiyar zuci take ,
Ga ta nan ,
Matsowa yayi , ya miƙa mata ƴar
Karɓe ta , ki kula da ita kar ki bari kome ya cutar da ita , kar ki bari tayi kuka ban lamunta ba ,"
Hannun ta miƙa saitin inda take jin hucin sa , ta karɓi ɗiyar tana jin wani sanyi na ratsa zuciyar ta yana kore tunanin da zuciyar ta ke son kawo mata akan kamar ta taɓa jin amon murya kwatankwacin wannan ,!
Da kallo Rahima ta bi shi , kamar shine ? Kamar fa shine na jikin hoton cikin kayanYakaka , babu shakka ma shine ,"
Ku koma ciki Rahima , prof yace ga su ,"
Toh ,
suka ce suna kama hanyar barin falon ,"
Youssouf zai magantu , Tafeeda yayi saurin yunƙurowa yana faɗin ,
Mun gode Mun gode Baba , Allah ya saka da Alheri ya bada ladan Taimakon da kayi mana , yanzu zamu koma saboda a bakin aiki muke amma muna dawowa cikin kwanaki biyu masu zouwa da yardar Allah ,"
Ameen toh babu kome Allah ya nuna mana kwanaki biyu masu zuwa Allah ya ƙara muku haƙurin jure rashi, idan kun sake dawowa zamu yi magana ,..
Youssouf zai yi magana ,
Tafeeda ya sake katse shi yana jan hannun sa
Ɗan ouwa tashi mu tafi ,
Jaan hannun sa yayi suka fito daga gidan suna fitowa Youssouf ya zare hannun sa daga na Tafeedah ,
A tare suka haɗa baki wajen tambayar junan su ,!
Ɗan ouwa meye haka kake shirin yi ?
Kana nufin nan zan tafi na bar ƊIYA TA ?
Hannun mutanen da ban san su ba ?
Kallon baka da hankali Tafeedah ya yi mass kafin ya fara taku ya nufi wajen motar su , ',kazo muje muyi magana a tsanaki ,
Ran sa bai so ba ya faɗa motar ya shiga Tafeeda ya fara ƙoƙarin tada motar lokacin da yake magana da sojojin nan akan su bar su madam saly an samo inda yarinya take ," ya sauƙe wayar yana hawa kan titi ,
Da fitar su Prof ya ɗaga waya ya ƙira Doctor Hamza bayan sun gaisa , yace
Yanzu mijin yarinyar nan ƴar gudun hijira mai rasuwa ya bar nan gabana tare da ɗan uwan sa , ka ga ikon Allah ashe shi bai mutu ba , ya zo ya ga gan ta tare da ƴar sa yana...
Wani mummunan cin birki da Doctor hamza yayi wanda hatta prof sai da yaji ,
Subahananlahi , Hamza ban hana ka ɗaukar waya alhalin kana tuƙi ba ? Da fatan dai baka yi haɗari ba ? kana jina ?
Muryar sa ƙasa ƙasa ya amsa bayan ya ɗauke kan motar zuwa gefen hanya bakin daji ya tsaya ,
Ina ji Baba , a bashi ƴar sa tare da ƙanwar matar sa ya tafi da su kar su sake dawowa Baba ,"
Jimm prof yayi ,
Kafin yace
Toh babu kome idan sun nemi hakan ai sai a basu daman ai hakan ya kamata , ka dunga kula hamza ka daina ɗaukar waya alhalin kana tuƙin mota , kana ina ne yanzu ?
Ina jigawa Baba , insha Allah zan kula baba , ka min addu'a baba , zamu yi magana idan na isa .
Toh Allah ya tsare hanya daga ka isa ka sanar da ni ,
,"To ," yace yana sauƙe wayar
Cije gefen leben sa yayi , watau dai kome gaskiya ne , ga shi nan duk yadda suka shirya yana faruwa daki-daki , watau har sun yi auren ta turo shi ya zo ya ɗau ƴar sa da ƙanwar ta ,
Zuciyar sa tayi duhu , me na miki da zaki yi wasa da zuciya ta irin haka ? Ashe sakayyar da zaki min kenan ?
Wani irin kishi mai ɗaci yake ji a ran sa , shan alwashi yake daga yanzu bai ƙauna sake jin ko me suna irin nata , bai ƙaunar sake jin duk wani abu da ya shafe ta , bashi da wani sauran uzuri da zai iya bata kariya da shi , ya yarda ya amince ta yaudare shi .
Tada motar yayi a hankali ya hau titi , yana nisawa cikin tunanin mace a yau !
Sojojin nan basu bar su madam saly ba sai da suka sake chasa su yadda ran su ke so ," Ah soja birgimar hankaka ne fa ?
Suka yi ficewar su suka hau motocin su wasu a tsaye a bayan hilux wasu a zamne , suka yi tafiyar su ,"
illahirin gidan a ruɗe yake da kururuwar matan da aka lallasa , sai ɗuruwa ake ganin su ana tambsyar me ya faru ? Me suka yiwa sojoji ?
Ɗan liti wanda muryar sa ta dashe saboda tsabar ƙwarmato , ya dubi madam saly wacce bakin ta ya kumburo yayi suntum sakamakon haƙorin ta ɗaya da ya fita ,"
Cikin dusashiyar muryar sa yace saly fara yau wacce rana ce ? Kuma a wanne wata muke nawa kuma ga watan ??
Da ido kawai madam saly ta bi shi tana jin yadda raɗaɗi yake ratsa tsokar jikin ta ta ko'ina gefe guda ga bakin ta da take ji kamar an cusa garwashi ,"
Ya cigaba ,
Na rantse ki rubuta ki ajiye ido na idon wannan tsinannan yarinyar yagana sai dai uwatta tai naƙudar wata , wai ace kana zaune da makashin ka baka sani ba ? Ashe tuntuni ita ta san ana nan ana shirin far mana da yaƙin basasa ,amma tayi funfurus ta ƙi faɗa mana bare muyi ta kan mu ,ki tsoraci ɗan adam ƙuzazje mai tafiya da ƙafa biyu saly fara ,
wai yanzu ace tsawon lokacin nan ashe shegiyar yarinyar nan mai kama da takanɗa ta san inda yaran nan su yaks suke , shine bata taɓa yunkurin faɗa ba "ko daya ai yake hannun hagu ba baƙon duwawu bane ,"duk jirgi ɗaya ya kwaso su ," to ƙwaranƙwasa ba'a daki bulus ba, farautar ta zan shiga yi ba dare ba rana ," wayyo wayyo ni liti du mazauna na sun yi tsami sun ɗuri ruwa , saly gane min ko dai farfashewa mulamulai na suka yi ?
Ya juyo mata duwawu ,
Kawar da kan ta tayi tana miƙewa da kyar ta nufi cikin gidan tana aiyana irin mummunan matakin da zata ɗauka akan Yagana , ai ita ba'a zubebeniyar ƙwaryar rashin mutunci da ita mutum ya kwashe ƙalau ,"
*****
Bayan komawar Biyamuradi Youssouf tare da Tafeeda ɗakin hotel , kowannen su shiru yayi yana saƙa cikin zuci ,
Ta bangaren Youssouf abu biyu ne zuwa uku , na farko mutuwar Yakaka da ta girgiza shi ta kuma bashi tsoro , ya wanzu yana tunanin da yanzu shi ne fa ya mutu ? Me zai cewa ubangijin sa akan tarin laifukan da ya wanzu yana aikatawa , tausayin ta yaji yana ninkuwa a ransa , tare da alwashi da yake ɗaukarwa kan sa na wanzuwa yana yi mata addu'a neman gafarar ubangiji har zuwa tsayuwar nasa numfashin ,
Ƙaunar ƴar jaririyar da kafin ɗora idanun sa akan ta suks tsara da shi da tafeeda akan cewa ko abun da aka haifa ya/ta nuna wasu alamu a halittar sa/ta dake nuna cewa nasa ne baza zai amince ya dangantar ɗa/ƴar da cewa jinin sa ba ne , kasancewar ya riga ya faɗawa Tafeeda yakaka ƴar talakawa ce sun san cewa ba wani tsananta binciken su gwajin jini a tsakanin sa da ɗa/ƴar da aka haifa za'a yi ba , dan haka suka tsara zasu barwa yakaka abunda ta haifa amma zasu taimaka mata tsayin daka kamar yadda tun farko Biyamuradi youssouf ya tsara ,
Sai dai fa kome ya sauya ya birkice masa lokacin da ya rungume ƴar sa a ƙirjin sa , ya ɗora idanun sa akan ta kamannin mahaifiyar sa duk suka bayyana kan su a halittar ƴar , ta buɗe idanun ta ta kalle shi , so irin na tsakanin ɗa da iyaye yayi tasirin sa cikin ƙudurar ubangiji , wani irin so mai yawa mai tafe da tausayi da tsantsar zallar ƙauna marar gauraye irin ta iyayen da suke da matuƙar ƙwalafaci da ƙawa zucin ƴaƴan su , suka taso suka lullube zuciya zuwa idanun YARIMA YOUSSOUF ABDUL-AZIZOU BASKORE
Yaji zai iya sadauƙar da kome da ya mallaka domin ya tsira da ƴar jaririyar ƴar da tayi rashin ɗumin uwa tun daga ranar zuwan ta duniya , rashin maihaifiya a tare da ita ya kassara illahirin gaɓɓan jikin sa , ji yake ina ma yana nan ranar da ta zo duniya alhalin uwar ta bata tare da ita , da tun daga ranar zai fara gwada mata ƙauna da tattali mai tudu biyu irin na uwar ƙwarai kuma jajirtattcen uba , tausayin ta yake , tausayin da bai taɓa jin yayiwa wani mahaluki irin sa ba , bai ƙi ba ace tun daga ranar haihuwar ta har zuwa lokacin da zata mallaki hankalin kan ta ƙirjin sa ya zama wajen kwanciyar baccin ta , so yake yayi mata rumfa ya zama mamar ta , kuma baban ta , ya zama ya cikace gurbi na duk wani makusanci da yaro zai nema cikin rayuwar sa na ƙuruciya , bai son ta tashi cikin maraici , tunanin hakan kawai na sauke ƙwalla a idanun sa , yana kuma katange tunanin sa daga duk wani ƙalubalen da kasancewar ƴar a rayuwar sa zai iya samarwa ,
kou yanzou baby ta daina kuka ?
Ya tambayi Tafeddah wanda ya rafka tagumi hannu biyu ya zurfafa cikin tunanin yanayin da ya hango da alamomin da suka bayyana kan su ga Yarima daga lokacin da ya ɗora idanun sa kan ƴar jaririyar da a yanzu yake hango alamun zamantowar ta barazana ga farin cikin mutane da dama da suke kewaye da yariman , shi yasan wanene youssouf ,
a lokuta da dama ba sai ya masa bayani ba yake fahimtar abunda ke cikin zuciyar sa , sai dai ya san wannan karon Yarima zai zo da wani Al'amari mai girma muddin ya nuna son ƴar ta tsaya tare da shi cikin rayuwar sa ,
Abunda hakan zai haifar ba abune mai daɗi ba , bai son ko tunawa , yau ace yarima youssouf ya doshi cikin masarauta tare da ɗiyar da ya haifa ba tare da amre ba , al'amura zasu rinchaɓe,
kai ka kawo yake cikin tunanin sa yana son samar da hanyar da zai bi ya dakatar da yunƙurin yarima ya bar ɗiyar nan a inda ya dace ta zauna,
Tunanin sa ya katse lokacin da yaji youssouf ɗin nayi masa magana ɗagowa yayi ya dube shi
Me kake faɗi yarima ban ji ba ?
Ɗiyar nan ko ta daina kuka yanzou ? Wacce iriyar madarar jarirai ake bata ?
Sasarere Tafeeda yayi yana kallon youssouf ,
Anya kou ranka ya dade yarima ba'a bar batun jaririyar nan haka nan ba ?baka gani Allah ne ya doube mu ya kawo hanyar da zamu samu masalaha akan wagga lamari ya kawar da uwar ɗiyar domin mu samu mafita ,"
abun da ni nake gani shine ka bar ɗiyar nan wajen masu riƙon ta tunda ba mu riga mun sanar da wani abu da ya shafi asalin mu ba ga mutanen nan ba, sai mu juya baya mu tahi abun mu ba tare da kowa ya san inda za'a same ka ba , ta iya yiwuwa ka dunga yin aike ta wata hanya mai nisa wadda zai dunga isowa ga ita ɗiyar nan , domin fa ka sani ita wannan ɗiya babbar barazana take a gare mu yarima da ma masarauta baki ɗaya , ko kouwa me kake tounani ne yarima ? Ko kouwa masalaha bata zou mana ba ??
Ya ƙarasa zancen yana kwantar da muryar ganin yadda Youssouf ɗin yake masa wani irin kallo mai karfi dake bayyana ɓacin ran da yake cikin ran sa ,
Tafeeda me kake faɗi haka mai kaushi , kana nufin na bar ɗiya ta jaririya nan nigeria hannun mutanen da ban sani ba ? ƙaƙa kake son rayuwar ƴa ta ta kasance cikin wahala tare da rashin galihu ? Baka tounanin tarihi zai maimaita kan sa ga ɗiya ta , rashin galihu yasa ta faɗa kwatankwacin halin da mahaifiyar ta ta shiga har ya zama silar faɗawar ta halin da ya zama silar samar da wagga ɗiya ? INA SON ƊIYA TA TAFEEDA , DOUNIYA ZATA KASSANCE TARE DA NI , DUK RUNTSI NI AI MAHAIFIN TA ,
A hasale Tafeeda ya miƙe tsaye
Amma ka san ita wagga ɗiya take ba ta halali bace kou ? Ita ɗin baka samar da ita ta tsafatataciyar hanya ba , ita ɗin barazana ce ga martabar iyayen ka da dangin ka baki ɗaya , barazana ce ga hawan ka ƙaragar mulkin masarautar mu , ƙazanta ce ita wacce ya kamata ka ji kunyar bayyana ta ba.....
tsawar da Yarima Youssouf yayi masa ya hana shi ,
Kome zai yanke tsakanin mu idan ka sake touzarta ɗiya ta Tafeeda , ita ɗin batta da laifin kome , ni ai nine za'a hukkunta , ita wagga ɗiya bata tare da dauɗar kome , ita ai abun a tausayawa ce ,
ita ce kaddara ta Tafeeda ina roƙon ka da Allah ka taimaka mouna ni da ɗiya ta , ka tsaya tare da ni bisa lamurran ta ni nasani me tarin laifuka ne , ka duba wnnan ɗiya mai tarin rauni ,
Yarima youssouf ya ƙarasa zance tare da share ƴar siririyar ƙwallar da ta sauko masa ,
So yake ya samu mai taya shi son ɗiyar sa , so yake a bashi karfin guiwar tsaya mata , tafeeda yana da muhimmanci cikin rayuwar sa bai son ya juya masa baya a wannan gaɓar ,
Tare da wani irin yanayi yake kallon sa , bai son tausayin sa da ya fara ji ya rinjaye sa har ya taya shi aikata abunda yasan zai cutar da shi mummunan cutarwa , zai kawo tsaiko akan cigaban rayuwar sa , idan yayi haka shi yasan bai kyauta ba Amintaka bata cika ba, kuma hatta shi fushin iyayen yarima sai ya shafe shi , kai shi fa basshi da ƙwarin guiwar da zai bada goyan baya ga yarima a wannan gaɓar ,"
Yarima idan ka ɗau ɗiya jaririya irin wannan ka tahi da ita zouwa ina ?
Zan yi amre na bada riƙon ta ga maimounatou zata riƙa min ita ,"
Kana da tabbacin ƴar sarkin agades ɗiyan gata irin ta zata yadda tayi maka riƙon ƴa ?
nakan iya haƙourewa dagga amren ta muddin batta riƙon ɗiya ta.
Murmushin takaici tafeeda yayi
kace da maimartaba da hajiya umma , da ƴan uwan ka me ??
Kaddara ta ce ta zou a haka , nasan umma zata fahimce ni ta fahimtar da maimartaba ƴan uwa zasu min uziri da afouwa ,"
wanne irin tanadi kake tounanin maƙiya zasu yi ta hanyar ɗiyar nan su kawo naƙasu cikin rayuwar ka tare da lalata mana sunan masarauta ?
Maƙiyi shi ai kullum maƙiyi ne , shi kuwa jajirtatcen namiji badda maƙiyan sa yake ,
gƴaɗa kai tafeeda yake yana iya hasaso gingimemen rikicin da Toussouf yake neman tsunduma kan sa cikin rayuwa ,
Allah shi badda sa'a yarima
Amine !
yarima ya amsa yana jin daɗin ganin kamar tafeeda ya sauko zai goya masa baya ,
Yaushe zamou kouma ka ga ɗiyar nan ɗan ouwa ?
Gobe iwar hakka na hantse a ƙassa ta ta haihouwa ,
Gobe kake koumawa ɗan ouwa ?
toh zaman me zan yi a nan na baro aiki na ? Gobe da iznin Allah nake koumawa .
Allah shi kaimu ,
Yarima Youssouf yace yana ƙarasawa gaban window ɗakin ya yaye labulen yana kallon rana da tayi yamma take gaf da tafiya ,
Ran sa cike taf da son sake ganin fuskar ɗiyar sa ....!!!
[7/9, 4:43 PM] +234 803 559 8589: Fikra writers association
Mafari .......
Hargitsin Rayuwa .
Umm'muaz
29
TUN RAN GINI RAN ZANE
Washegari da misalin tara na safe , jirgi ya ɗaga da Tafeeda zuwa birnin Lagos inda ta chan zai wuce ƙasar su ,
Dukkanin su shi da Biyamuradi babu mai isashiyar walwala suka yi sallama , alhalin basu kai ga cimma matsaya guda kan matsalar su ba ,
Duk da cewa bangaren youssouf ya ji kaso sittin cikin ɗari na damuwar sa ta tafi , saboda ya bayyana ta ga aminin nasa , ya kuma san Tafeeda zai yi duk yadda zai yi ya ga ya dai-daita kome a gida kafin komawar sa , yanzu babbar matsalar sa ita ce rayuwar ɗiyar sa ,
A daren jiya kwana yayi yana dogon nazari akan yadda zai yi ya ga ya bata ingantatciyar rayuwa ba tare da gurbatatciyar hanyar da aka samar da ita ta zama ƙalulabe a gare ta ba , da mutum yana iya sauya kaddarar sa da a daren na jiya ya juya , ya gyaro hanyar da aka yi ƴar nan ta sa ta zo duniya , amma ya riga ya san bakin Alƙalami ya bushe ,
hakan ya sa ya ɗau ƙuɗirin zai jajirce akan duk wani ƙalubale da shi zai iya cin karo da shi cikin rayuwar sa wajen ganin ya inganta tare da kyautata rayuwar ɗiyar sa ta FARKO a duniya ,"
Tafeeda kuwa ya bar ƙasar ran sa cike taf da tunanin yaya zai yi yaga ya boyewa hajiya umma musabbin shiga damuwar yarima ? Ya zai yi ya boye mata irin mummunan aikin da yarima ya aikata ? Yaya zai boye mata samuwar wata haramtatciyar ɗiya daga tsatson ta ? Kome yana neman kubce masa , shi ya kasance a tsakiya ne , ɗan aike ne shi , sai dai saƙon da zai koma da shi a yau me nawi ne wanda ya fi ƙarfin fitowa daga kan harshen sa ,
Cikin awanni (2) da tashin jirgin su daga Murtala Mohammed International Airport Lagos, Ya samu dira a Diori Hammani International Airport Niamey , duk yadda ya so ya tsaya wajen 'ubbo' su gaisa kamar yadda ya tsara , ya gagara
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 42 Chapter of 111