hannuwan nata ya sauƙe daga kan ta ,
Bata amsa ba illa riƙe hannun sa da tayi saboda yadda har yanzu take ji ba dai-dai ba a ƙwarar idanun ta .
Bayan likita ya gama dube-dube a ainashin cikin ƙwarar idanun ta ,
Biyamuradi Youssouf ya kamata suka dawo wajen zaman su suna fuskantar likitan da yake rubuce-rubucen sa cikin kwamfiyuta ,
Turo ƙofar ofishin akayi wata mace ta shigo , babu ɓata lokaci ta jagoranci su Youssouf zuwa wani sashi na daban inda aka yiwa Falmata hoton ƙwarar ido aka tura ga sakamakon ga Likitan ta ta kwamfiyuta kamar yadda ya turo musu da bayanan irin hoton da yake so su yi mata ta kwamfiyuta .
Kafin isowar su hoto tare da bayanan da duk suka dace sun riga sun iso masa , dan haka bayan ya kammala binciken sa , ya zunkuɗa yana mai gyara zaman gilashin idon sa , ya shiga yi musu bayani dalla-dallah cikin turancin sa yayin da su kuma pilot-in-ear yake fassara musu cikin faransanci ,
Iritis shine ciwon da ya haddasawa Falmata matsalar idanu da har ya kai ga ta rasa ganinta , shi iritis wata cuta ce da take samun ƙwayar baƙi/brown na tsakiyar idon ɗan adam , da take kumbura ƙwayar idon , sa ciwon ƙwayar idon da disashe gani ,gaza ɗaukar haske da sauran matsaltsalu da dama ,
wanda ake iya samun sa ta hanyoyin da suka haɗa da ƙwayoyin cutar maɗamfari ( infection ) , jin ciwo kai tsaye ga cikin ido , kamar bugu zuwa ƙwarar ido na daga kowanne irin abu , da kuma cutar da take kama ƙwayoyin halitta na jini tana kashe su.
Bayan dogon bayanin da likitan yayi musu ya ɗora musu da bayani kan matakin da cutar ta kai ga idon na Falmata wanda rashin samun maganungunan da suka kamata a kuma lokacin da ya dace , ya kai ga ta rasa ganin ta na tsawon wasu shekaru sakamakon mutuwa da wasu daga cikin jijiyoyin ƙwarar idon suka yi .
kai tsaye bazai yuwu ba ganin ta ya dawo kamar na sauran mutane masu lafiya , duk da cewa akwai yuwuwar kaso ɗaya bisa uku na ganin nata ya dawo tare da taimakon magunguna da allurai zuwa kan aiki na musamman da za'a iya yi mata a idon idan har magunguna da alluran basu taimaka yadda yakamata ba , wanda zai ɗora ta akai da zarar ya kammala binciken sa a yau .
Cigaba yayi da yi musu bayani har zuwa lokacin da ya tabbatar sun samu gamsuwa sun kuma fahimci duk bayanan da yayi musu ,
da kan shi ya jaa jinin Falmata ya fita da shi zuwa ɗakin gwaji saboda ya auna ya san irin magunguna da alluran da suka dace yayi mata bisa ga mataki na farko .
Basu bar asibitin ba sai da aka mata allurai biyu ta babbar jijiyar hannun ta tare da yi mata ɗaya a jijiyar da take daf da idonta na dama ,
Ba ƙaramar juriya ta nuna ba wajen tsayuwa da tayi cikin nutsuwa aka huda mata jikinta babu zilliya bare ihu da hatta shida kansa likitan sai da ta burge shi sanin da yayi allurar gefen idon tana da zafi ,
Ya dube ta bayan ya ƙare mata allurar gefen idon ,
" sorry It'll hurt but just for a few minutes .
Gyaɗa kai tayi tana jin yadda idanun nata suka yi nawi ga wani irin yanayi marar daɗi da take ji a idon ,
" Baban Mama , ta ƙira sunan sa tana lalubar hannun sa ,
Da sauri ya riƙo ta
" Na'am Fatima , sannu kina jin ciwou ? comment vous sentez-vous en général ? ( How are you feeling overall ? )
" Idona yayi jini ne ?
"bai yi jini ba Fatima , sannu .
****
Misalin ƙarfe tara na dare suka bar asibitin bayan sun ci abinci sama-sama daga kitchen ɗin cikin asibiti .
Suka yi bankwana da likita omer bisa ga yarjejeniyar sake dawowa asibitin nan da kwanaki huɗu masu zuwa , bayan ya haɗasu da mugunguna ɗore da dokoki da sharuɗɗan da ya gindaya musu .
Baki ɗayan su sun gaji Mama tayi bacci a jikin Babanta , Falmata kuwa tsukun da idanunta ke yi yana damunta wanda yake ta zubar hawaye , gaba ɗaya bata jin daɗin kome ,
damuwarta ta tayar da Hankalin Youssouf da yake amfani da kalmomin rarrashi iri-iri yana jera mata sannu , har suka dawo gida , kai tsaye ya zarce da mama ɗakin baccin su ya kwantar da ita ya lulluɓa mata bargo tare da kunna hutar ɗumama daki ya fito falo inda ya tarar da Falmata ta rufe fuskarta da hannu biyu , ta jingina kanta da jikin kujerar da take
A sanyaye ya ƙaraso wajen fuskar sa na nuna damuwa ƙarara ,
Zama yayi a kusa da ita jikin sa na gogar nata , ya kai hannu a hankali ya sauke hannun ta daga fuskar ,
Hawayen da idanun ke yi ya goge da hankicif ɗin da ya zaro a aljihunsa ,
"Fatima yaya ne ? Ciwo ne har yanzou ? Kou zamou koma ga doctorat ?
" Baban Mama idanuna ciwo suke kamar zasu fita , idona bai taɓa ciwo haka ba , bazan warke ba kar kayi asarar kuɗi dayawa , lafiyar Mama yafi samun lafiyar idona muhimmanci kuma ..
" Shittt , yace yana kai hannun sa kan ɗan bakin ta .
" Fatima baki ji abounda Doctorat ya faɗi ba ? Zaki warke ko ba du ba , waye ya faɗi miki zata zam asara doumun nayi jinyar ki daga jakka ta ?
" kiyi ta addu'a Allah shi sa a cimma nasara bissa ga neman lafiyar ki kin ji kou ?
Shiru tayi , ita ganin zancen likitan take soki-burutsu tayaya idanun ta zasu fara gani ? Bayan a iya sanin ta bata taɓa ganin hasken duniya ba .
Muryar sa ta katse tunaninta "
Kou baki so watarana ki ga fuskar mijinki ? Kou baki so watarana ki ga fuskar ɗiyar ki Mama tare da 'ɗiyan da zaki haifa nan gaba ?
Jin ya sosa mata inda ke yi mata ƙaiƙayi sai ta ɗago kanta , '
" inaso , amma nafi son na samu ɗa domin ya sadauƙar da ɓargon sa ga Mama , ta warke kamar yadda likita ya faɗa ,
Sai yayi shiru yana kallon ta da taimakon hasken da bai cika yawa ba da ya hasko daga jikin ƙwan fitilan dake ajiye saman teburin gaban su ,
zancen ta ya zo masa a bazata , ya ratsa ƙwaƙwalwar sa a jirkitatcen yanayi da ya kasa tantancewa .
Ita ma shiru tayi cike da fargabar kasassaɓar da tayi , kada dai tayi masa laifi ? Ko dai zantukanta basu dace ba ? Tayi masa tsaurin ido ko ?
Sauƙar hannun sa cikin nata ya katse mata tunanin zucin da take yi ,
"Fatima mu tafi muyi sallar isha'i kiyi kwana (bacci ) dare yayi ,"
A sanyaye ta amsa da "To,
Har suka kwanta bacci babu wanda ya kuma magana kowanne a tsakanin su yana tunani,
Wayar sa ce tayi ƙara alamar shigowar ƙira , da azama ya ɗauka ganin wacce ke ƙiransa ya sanya shi miƙewa a hankali ya nufi ƙofar ɗakin , ya zo fita ya juya gami da kai kallon sa kanta da tayi lamo cikin bargo kamar mai bacci ,
ajiyar zuciya ya sauƙe ransa cike da tunaninnika barkatai ya fita gami da jaa musu ƙofar ,
Falmata wacce duk motsinsa a kunnen ta , ta miƙe zaune gami da yaye bargon , cikin ranta sam babu daɗi gani take kamar ta ɓata masa rai da maganganun ta tunda gashi daga lokacin bai sake cewa da ita kome ba , ko fushi yayi ?
Tashin muryar sa da yake magana kamar a gabanta "kasantuwar ta mai buɗaɗɗen kunne " ya sa ta saurarawa zagayayyar fuskarta na bayyana wani yanayi irin na wanda aka shammata lokacin da taji yana cewa ,
"bonjour ma princesse comment allez-vous aujourd'hui mon amour? ( Alo gimbiyata yaya kike yau masoyiya ? )
Cigaba yayi da cewa
"Je vais très bien et tu me manques aussi , ( ina lafiya lau nima nayi ƙewar ki )
Ƴar dariyar nishaɗi yayi , kana ya cigaba da cewa ,
" wannan kalma ke kin ka faɗe ta , ni kouwa gurina ba haka ne ba , duk wani bigeren da babu ke cikin sa wajena daɗin sa ragagge ne , babu kome anan sai matsanancin sanyi tafe da tarin nawi da wahalwalu bisa kaina ,
Murmushi yayi mai sauti ,
" a gida nake Yarima , ga gurin aikina kuma Mai muƙamin Major , nan kuwa ai ban wucce matsayin bawa dake hidima ga wassu rayukan ba ,
Gicciyewa yayi ya kishingiɗa yana me cigaba da sauraron ta ,
" ba domin yanayi da bashi yiwuwa na taho da ke ba, kin sani ban iya tafiya ga nissan duniya batare da ke gefena ba maimounatu ke ai sashi ce daga jikina ,
Falmata da take sauraran sa , sai ta koma ta kwanta tare da lulluɓuwa ta cure jikinta guri ɗaya ga barin sauraran zantukan sa , zuciyarta ke wani irin bugu da yake tafe da zallar tashin hankali ,
Sunan wacce aka ƙira da Maimounatu tare da irin Kalmomi masu daraja da aka mallaka mata , sun gaftare tare da ruguza duk wani ɗan guntun tunanin banza da ta fara yi ,"Ah to na banza mana , tunda 'yar kulawar da yake bata ya sa ta hasashen hawa wani matsayi da bata kai shi ba a wajen sa ashe ita ɗin ba kome bace face tarin nawi da wahalhalu .
Hawaye masu ɗumi suka gangaro daga idanunta suna ɗiga bisa hular sanyin kan Mama .
Maiduguri Nigeria
Tun ranar da Doctor Hamza ya gargaɗi Yakaka akan kada ya sake ganin fuskarta bata sake bari sun haɗu ba ,
Ko muryar sa ta ji yayi Sallama da shi bai cika shigowa ma sashin nasu ba , da sauri zata nemi gurin ɓuya , duk cewa tun daga ranar duk lokacin da ya buƙaci abinci daga Rahima ita take girka masa , sai ita kuma Rahima ta kai masa .
Yau Asabar ya shigo gidan da safe misalin ƙarfe tara shirye yake tsaf cikin shirin sa na zuwa ɗaurin auren ƙanin Abokin sa .
Yana yin Sallama , Yakaka da take goge Falon bayan ta gama sharewa tayi saurin ajiye moper ( mofi ) ta tsallaka da ɗan gudu ta shige ɗaki ta rufo ƙofar ,
Hajja da take zaune a gefe tana karin kumallo ta harari bayanta ta wutsiyar ido kafin ta taɓe baki ,
" Ni hauwa'u naga abunda yafi ƙarfi na , ke kenan kullum a tsalle-tsalle da guje-guje ? Uwa wata tunkiyar da take rawar turke ? Allah ya kyauta .
Washe baki tayi tana dariya ,lokacin da Doctor Hamza ya shigo
" a ah kaga manya ɗiban farko , Babban likita ,
Fuskar sa ɗauke da murmushi suka gaisa , ba tare da ya zauna ba yace
"Hajja ina Rahima ?
" Yanzu ta hau sama , a ƙira ta ne ?
" a ah yi zaman ki Hajja idan dai ta fito ace ta min girki kafin dawowata ta kai min ɗakina .
" To babu laifi zan faɗa mata .
" Nagode Hajja .
Ya juyawa da nufin fita idanun sa suka sauƙa kan Hoton Mama da tun ranar da ya fara ganin hoton yake son tambayar Rahima 'yar waye ? Ƙwarai hoton yarinyar yake fusgar hankalin sa ,
Dan haka ya dawo da baya yana tambayar Hajja ,
" Hajja wannan 'yar waye haka aka samu kyakkyawa ?
Da dariya Hajja ta amsa masa
" 'yar wajen Fatima ce , Mama sunan ta ai sun ma yi tafiya ne can Amurka ita da iyayen nata .
"Fatima ?
Ya maimaita ,
" wacce Fatima Hajja ?
" Ƙanwar wannan yarinyar Yakaka take ko wa ?
'okay ,
Ya amsa yana barin wajen ba domin ya gane wacce ake nufi ba kai tsaye sai dan ƙiran sunan Yakaka da Hajja tayi .
ƙarfe biyu na rana suka shirya tafiya gidan Amne su Uku Rahima , Yakaka da kuma Hajja da itama tace zata je .
Shatar shatar adai-daita Rahima ta ɗaukar musu wanda ya tokare daga bakin hanya yaƙi gangarawa kwarin unguwar a cewar sa gargadar cikin unguwar zai ɓata masa mashin , dan haka dolen su suka sauƙa Rahima tana ta mitar wahalar tafiyar da zasu yi a ƙafa kafin isar su gidan .
Da wani tasowar sabon yanayi a zuciyar Yakaka take bin unguwar da kallo , unguwar da ta zama tushe na hargitswar rayuwar ta da bata tsinci kome a ciki ba illa wahalhalu da tarin abubuwan ƙi , unguwar da suka sha gwagwarmaya a cikin ta ita da ƙanwar ta da ƙawarta Yagana ko ina yagana take a halin yanzu ? Wataƙila ita rayuwa tayi mata kyau , tayi aure ta fara ginin rayuwar 'ya'yan ta .
tunaninta ya katse lokacin da Rahima ke cewa su gangara ,
Tana bin layin tana tuno da haɗuwar su da Doctor Hamza a bakin layin ana ruwan sama ,taimakon da yayi mata a ranar da ba domin shi ba da ta faɗa babbar kwatar taji mummunan ciwo ko ma ta rasa ranta ,
"Allah sarki yaya dakta ,
Ta furta hakan daga ƙasan ranta lokacin da suke miƙawa cikin layin .
Daga nesa ta fara jiyo hargowar sa muryar sa a sama yana rantse-rantse , domin ta tabbatar da shi ɗin ne ? Tayi saurin ɗaga idonta ta ɗora a kan sa shi da wata matar da kallo guda tayi mata ta gane yanayinta na matan banza ,
Da sauri ta ɗauke kai tana ɗan jawo hijabinta gaba kaɗan , zuciyarta cike da fatan Allah ya rufe masa ido ya wuce bai ganta ba bare ya gane ta.
cikin rashin sa'a hasken da take da shi ya riga ya ɗau hankalinsa kasancewar sa kawali idanun sa koyaushe akan wankakkiyar mace yake babu ruwansa da matsayinta na matar aure ko akasinta .
Sun ƙaraso gaf da juna ya jaa ya tsaya , kafin ya ɗau salatin da Hajja ta ƙarasar masa ,
Sauri yayi ya zagaya ta sashin ta ya dogare , yana kallon fuskar ta da taƙi yadda su haɗa ido ,
Dariya ya kwashe da ita yana tafa hannuwan sa alamun mamaki yace ,
"Ahayye nanaye ke duniya mai abun mamaki ? Yanzu duniya da gaskiya Yaks kƴa ga Ɗanliti ki ɗauke ido ki kawar da kai ? Lalle Yaks kin zama kaza ci ki goge bakin ki , Ko da yake ai kome kika yi ba mamaki tunda baki da shayin kowa .
Yakaka ta saci kallon Hajja wacce tayi saƙare tana bin Ɗanliti da kallon banza ,
" Ɗan-Ɗan liti ya kake ?
" Ras nake Yaks .
Yayi fari da ido kafin ya ɗora da
"Ke kuma fa ? Ya na ganki haka da Bargo yaro-yaro kina yawo kadda dai kice min kin yi ƙarkon kifi , ? Kin fito daga ruwa kin faɗa wuta ? Yo ai kuwa da kin ɗibga asara a duniyar nan Yaks ace dai wai mace hamshaƙiya kamar ke kina yawo a ƙuɗunɗune cikin hirami yake ko hijabi ko jallabiya ? Bani sunan sa ɗaya .
" Ubanka yake nace Ubanka yake shashasha , wofin wofiyo banzan banza , yau ga ɗa ya zama lalatatce bayan an kashe ragon suna , to Allah ya shirye ka , ke un-un Yakaka wuce muje .
Hajja ta furta hakan tana huci tare da yiwa ɗanliti daƙuwa da hannuwanta duk biyu , ta ƙarasa zancen da fusgar hannun Yakaka ,
Buɗe baki Ɗanliti yayi da mamaki ,
," Ke tsohuwa , ki kiyayeni ki kiyayen nace da zaki zo ki shiga cikin maganata dake nake ? Nace da ke nake ? Yo Allah na tuba ke a zamanin ki waye ya san irin tsiyar da kika shuka ta rawar banjo da kiɗan gurmi daga ke sai ɗan kanfai ? Ko da yake wannan baƙin naki uwa shuni ba wani tasiri kika yi ba ko a wajen su garbati mai kalangu . ,
",Na rantse kin ci darajar yaks domin ni na falle tsohuwa da marin da zai sa ta ga star abune mai sauƙi a wajena , gaba ki kiyaye kin ji na gaya miki .
tsaki Hajja tayi suna barin wajen ,
" Allah ya shirya ka zindiƙi .
Shima ya rama Hararar da tayi masa ,
" waye yake ta taki tsohuwar guzuma , Yaks Ki samu lokaci ki leƙo mu akwai labarai da hanyoyin arziki masu tarin yawa , af na manta na faɗa miki uwarɗakin fa bata da lafiya...
Bai ƙarasa zance ba yayi shiru ganin sunyi nisa ,
" ji min tsohuwar nan zata yaɓan magana wai nine zindiƙi ? Tsohon ki ne dai zindiƙi aikin banza .
****
Da sallama suka shiga gidan Amne , tana zaune kan barandar ta tana ƙunsa lalle a ƙafafunta da basa rabuwa da ƙunshi ,
Tayi mamakin ganin su saboda Rahima bata sanar da ita zuwan nasu ba ,
ta tare su da fara'a tana yiwa baƙi barka da zuwa , idanunta da hankalinta baki ɗaya akan yakaka .
Bayan sun gaisa ta dubi Rahima ,
" aina kika sake samo min mai kama da Rahima ta ? Da ace shekaru basu jaa dayawa ba zan iya cewa Rahima ta ce wannan ,
" dariya Rahima tayi , Amne baki gane ta ba ko ? Yakaka ce fa , 'yar gudun hijarar da suka zauna a gidan mu shekarun baya da akayi zaton ta rasu wajen haihuwa ?
duk da ba wani jimawa tayi da yaran ba amma sunan su ya tsaya a ƙwaƙwalwar ta ,
" Yakaka ke ce ?
" ni ce Amne ,
" Alhamdulillah ashe Yakaka kina raye ? Ina kika tsaya tsawon lokacin nan ? Ina ƙanwar ki tare da 'yar ki ?
hannun ta ta ɗora akan na Amne da ta miƙo mata su , fuskar ta ɗauke da murmushin jin daɗin zallar ƙaunar da ta hango a idanun Amne ta matso kusa da ita ,
"Falmata su na America wai .
Hajja tace ,
" Wai ne ma ? ai ya wuce wai .,
Amne bata tsananta tambayoyi ba ga Yakakar domin ta bata damar sakewa ,
Lallen da Amne take sawa ta karɓa , tare da cewa
" kawo na sa miki Amne .
tana murmushi ta miƙa mata 'yar robar da lallen ke ciki , ta shiga sanya mata sannu kan hankali ,
da sauri Rahima tace
"Daman kin iya lalle ne Yakaka ?
tana murmushi tace ,
" ko ban iya ba zan koya a ƙafar Amne .
Hajja da Amne suka cigaba da hirar su ,
zuwa lokacin da Rahima tace ,
" Yauwa Amne ki nunawa Yakaka Hoton Khaalty Rahima da kike cewa suna kama Yakaka tana son ganin ta...
"eh Amne ina son ganin Khaalty Rahima , Yakaka ta furta hakan cike da ɗoki ..
Assalamu Alaikum masu karatu maza da mta , ina miƙo sakon gaisuwa ta tare da fatan alheri , ɗauke da yabawa bisa ga yadda kuke bin littafin nan cike da bani ƙwarin guiwa nagode ƙwarai da gaske Allah ya bar so da ƙauna ( sunan wani littafi 😂 ) sharhin ku a fejin da ya gabata ya min daɗi matuƙa da fatan za'a ɗore da haka ? .
Ghost readers muna nan da ku , za'a ji kan mu watarana .
😡
Nagode .
[10/26, 11:28 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
37
Cike da zumuɗi Yakaka ta karɓi wani ƙaramin envelop ɗin da Rahima ta ɗauko mata daga ɗaki tana cewa
" Yakaka ga hoton Khaaltƴ Rahima duba ki gani, ita ce takwarata ai ina kama da ita ko ? .
Da murmushi bayyane kan fuskar ta , ta zaro hoton bayan ta goge hannun ta da yake da ɗan danshin ruwan ƙunshi .
Ƴar ƙaramar budurwa ce a jikin hoton na farko da baza ta wuce shekaru sha huɗu zuwa sha biyar ba , fara ƙal tamkar baturiya , ƙibabbiya 'yar dumur-mur jikinta sanye da doguwar rigar iya ƙwauri mai guntun hannu irin shigar su ta shuwa ,kanta ba ɗankwali sai manyan kitson guru da aka mata gwammon sa a ƙeya ,
" wai Masha Allah Rahima mai sunanki ta fiki kyau gaskiya ,
Ta furta tana 'yar dariya kafin ta zame hoton na bayan sa ya bayyana da bai kai wancen a tsufa ba domin a wannan ta ƙara girma ta zama budurwa da a lokacin zata iya kaiwa shekaru sha bakwai , da alama a makaranta ta ɗau hoton ganin jikinta sanye da uniform ,
Tsam , tayi tana ƙurewa cikakkiyar fuskar ta kallo da take dariya , tamkar dai tana rikiɗe mata zuwa fuskar da tayiwa sani na haƙiƙa ,
"fuskar wa ?
Ta tambayi kan ta da kan ta .
"Fuskar maman mu ," babu shakka dariyar ta da zubin haƙoranta irin na maman mu ne , sai dai maman mu bata da jiki da kyaun wannan mai kama da turawan,
Tunanin ta ya katse lokacin da ta tsinkayi muryar Amne wacce ita ma ta kafe ta da ido tana nazarin yanayin da take hangowa a tare da ita ,
" Yakaka ko kin san ƙanwata Rahima a wani waje ne ?
Kallon Amne tayi kamar zata ce wani abu sai kuma tayi ɗan yaƙe , tare da girgiza kanta lokacin da take ƙoƙarin mayar da hotunan cikin gidan su ,
" A ah Ban san ta ba Amne ,"
"Allah sarki , Rahima kenan ƙanwata da muke uwa ɗaya uba ɗaya jal a duniya , Yaa Allah ka san halin da na wanzu cikin sa tsawon shekarun nan akan rashin Rahima , Allah ka dawo min da Rahimatullah , ka sa muna da rabon sake ganawa a duniya .
"Amin Amne ,
suka amsa mata su duka fuskokin su na bayyana alhini , musamman Yakaka wacce ta shiga wani irin hali na ruɗani da ganin hoton khaalty Rahima ya jaza mata .
Ƙwarai fuskar ta tsaya mata a zuci da cikin tunaninta , Babu wadatar nutsuwa na sosai a tare da ita suka ƙarasa yinin su zuwa gefen La'asar suka kama hanyar komawa gida ,
Rahima ta dubi Yakaka bayan mai adai-daita ya sauƙe su a daf da ƙofar gida ,
"Yakaka ya naga duk kin yi wani iri , akwai damuwa ne ? Kafin mu fita a gida ba haka kike ba ,
Kafin Yakaka ta amsa Hajja tayi charaf ta amshe zance ,
"Ahaf zai wuce batun wannan ɗan banzan , ɗan hamsin yake ko ɗan daudu ? Idan har kika ce ƴar huɗubar wofin nan da ya wassafa miki zaki ɗauka ki aza a rai to kuwa kin kama kumfar teku , domin wannan da kike ganin sa rabon sa da alasambarka tun kwanansa bakwai ran suna , babu Alheri a tare da shi ko na aninin kobo atoh .
A ɗan kaikaice Yakaka ta dubi Hajja zata yi magana , aka buɗo babbar ƙofar gidan , Doctor Hamza ya turo kan motar sa , kallo guda ya yiwa gefen da Yakaka take ya ɗauke kan sa ,
Da sauri Yakaka ta wuce tana gyara zaman hijabinta , ta bar Rahima da Hajja suna gaisawa da shi , inda yake tambayar su daga ina suke ??
Suka sanar da shi daga gidan Amne suke , sosai ya ji daɗi tare da tambayar su yadda suka baro ta ? Suka amsa masa da tana lafiya ƙalau ,
Daga haka ya wuce yana satar kallon madubin motar sa inda ya hango Bayan Yakaka tana tafiyar ta a hankali dogon hijabin jikinta da yake kusan taɓa ƙasa bai boye salon takun tafiyar ta irin na barewa ba ,
Ɗauke kai yayi lokacin da yake dai-daita kan motar sa ya hau titi ya cilla zuciyar sa cike da zullumin tunani kan inda ya nufa ,
Kai tsaye ya tasamma unguwar da aka bashi tabbacin anan gidan da matar nan da yake zaton innar sa ce take aiki , duk kuwa da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 67 Chapter of 111