gashi sai ya ƙarawa kyaun kitson armashi .
Shafa kan nata yayi yana murmushi yace ,
wow c'est très beau ,
Da dariya ta bar jikin sa ta nufi Falmata tana zuwa ta fara kici-kicin buɗe mata kai ,
Mamaa ke ma ki nunawa papa kitson ki , yafi nawa ma chau ko papa ?
A hankali ya gyaɗa mata kai yana jingina bayan sa da jikin kujerar ba tare da ya janye ganin sa daga kan su ba ,
Ture hannun ta Falmata tayi ta ɗan ɗaga sauti ,
Ki bari mama ba na hana ki buɗe min kai ba ?
Ba tare da ta sauke hannuwan ta daga kan falmata ba tace
Ai papa ne zai gani .
Tsawa tayi mata lokacin da take son ta sauƙe mata hijabin a tilas ,
Firgita tayi ta ja baya ta rakuɓe tana ƙwalan-ƙwalan da ido tare da raba kallon ta tsakanin mamar ta da baban ta ,
A hankali wasu siraran ƙwalla suka silalo daga gurbin idanun ta ganin an mata abunda ba'a saba yi mata ba ba kuma tare da an rarrashe ta ba ,
Cikin ran ta taji shirun da tayi tare da sanin manufar sa , dagulewar zuciyar ta ya zo dai-dai da zubar hawayen Mama ,
Hannu ta ɗaga ta fara lalubar inda take jin tashin shisshiƙar kukan ta , ta jawo ta jikin ta tare da ɗaura ta akan cinyoyin ta ,
Kwantar da kan ta tayi da ƙarfi a jikin mamar ta gami da fashewa da kukan da tayi tanadin sa ,
Kamar ruwan maɗaci haka take jin ɗacin sautin kukan ta daga cikin zuciyar ta, dan haka ta fara aikin lallashin ta ,
Hannu ta kai ta zame hajibin nata , ƙananan kitson da aka mata yir-yir suka bayyana
Ta karya murya cikin kuikoyon muryar mama tace :
Papa ka ga kitso na yayi chau ??
A hankali ta ɗago kan ta daga jikin ta idanun ta jage-jage da hawayen rikici , ta washe ƴan haƙoran ta lokacin da take kama dogon jelar kitson shade ,'( me hawa biyu ) da aka tufke shi ya sauƙa kan dokin wuyan ta , ta waiga tana duban Baban ta wanda duk abunda suke yana bin su da ido ,
ransa cike taf da ƙauna tare da shauƙin soyayyar dake tsakanin uwa da ɗiyar ta .
Muryar ta kamar ba ita ke kuka yanzu ba tace ,
Papa ka ga kitson mamaa na yayi chau ko ?
Yunƙurawa yayi ya matso sosai gaban kujerar da yake kai ,
Yana ƴar dariyar yadda fuskar falmata take a ɗaure tana wani takurewa yace ,
Ai tayi nissa daga can bani ganin kitson nata , ta matso nan kussa na gani kou ? Ya ƙarasa zancen yana karya wuya .
Eh Mamaa ki zo ya gani ,
Ta jawo hannun Falmata , gudun rikici ya sa Falmata ta biye mata ta taso ta biyo ta , gaf da ƙafafun sa Mama ta zaunar da ita ,
Idanun sa ya sauƙe akan kitson da suke yir-yir kamar inji ne ya jera , ƙwarai kyaun kitson ya birge shi .
Basu yi aune ba ta jaa hannun Baban ta ta ɗora akan Falmata ,
Papa ka ga ni ?
Ta ce tana washe masa haƙoranta .
Kasa janye hannun nasa yayi daga kan ta , saboda wani irin yanayi da yake ji yana zagaya illahirin jikin sa ,
Tundaga kan yatsar kafar ta taji tashin tsikar jikin ta , da wani yanayi da ya tsinka gudun jinin jikin ta , irin yadda bata taɓa ji ba a rayuwar ta , bakiɗayan jikin ta babu kuzari ,
Ganin shirun su ya tsawaita ya sa Mama ta raba ganin ta a tsakanin su , kafin ta ɗan turo baki ,
Papaa , baka ce kitson mama yayi kyau ba ??
Cikin dai-daita nutsuwar sa ya janye hannun sa daga kan ta ya janyo Mama Zuwa jikin sa ,
Kitson Maman Mama yayi kyau sossai
très belle .
Batare da ta ƙara daƙiƙa guda ba ta miƙe , tana nufar hanyar ɗakin hajja , zuciyar ta na cigaba da tsananta bugu , cikin kowanne takun ƙafafunta take jin idanun sa na yi mata rakiya .
9:30pm
Falmata ta sake muskuɗawa tana rufe bakin ta daga gajerar hamma da take yi akai-akai saboda bacci da ya fara cin ƙarfin ta ,
Ita bata kaiwa dare sosai take yin bacci a yawancin lokuta ƙarfe takwas da rabi na dare sun yi bacci ita da Mama , shiyasa yau da hajja ta buƙaci son suyi magana ta zo kuma ta tadda ta tana shafa'i da wutiri , bayan ta idar kuma ta ɗora da addu'o'i , duk sai zaman jiran ya gundure ta bacci yake kawo mata samame ,
Falmata , Falmata . Ko kin yi baccin ne ?
Na'am hajja idona biyu .
To taso ki zo nan kusa da ni magana nake so muyi ,
a hankali ta taso ta taho inda take jin tashin muryar hajja ta zauna daga gefen ta bisa dardumar sallah .
Fatima ki nutsu da kyau ki saurareni , da kunnen basira , kin ga wannan tafiyar da za kuyi ke da Mijinki tamkar wata babbar dama ce Allah ya baki da za kiyi ƙoƙari ki dai-daita zaman ku ke da shi , ki ƙarbo martabar ki ta ɗiya mace , cikakkiyar matar aure , ke yanzu ba yarinya ƙanƙanuwa bace ba , da za'a zauna ana yi miki bayani dalla-dallah baƙi da fari akan aure , shekaru biyar ana cikin na shida da yin auren ku , lokaci yayi da yakamata ku kawo ƙarshen wannan zaman kai da ƙafar da kuke yi a tsakanin ku , ku haɗa kai ku rungumi junan ku cikin inuwa da alfarma irin ta aure ,
Ke kece mace bance ba ki bada kan ki ba , amma ki yunƙura kiyi hoɓɓasa cikin dabarun ki na ɗiya mace da Allah yayi miki baiwa da su , ki karkato da hankalin mijinki kan ki , tunda jajayen sawun ki , da sauran damar ki , kina kuma tare da makaman yaƙin da zasu taya ki karɓo kambun ki tun kafin damar ki ta kufce miki , futsanci , jin kai , halin ko inkula da miji ba naki bane , yanzu anwuce wannan zamanin , zamani ne muke ciki na tarairayar miji a gatata shi ta yadda za'a masa riƙon tsauri da kufcewa zata masa wahala , kin dai ji na faɗa miki .
turai zaku je , kiyi ƙoƙari ki sau jiki , ki shige masa , ƴan kananun kayan nan da yace ana saka su a can ki sa ya kawo miki su dayawa kullum ki dunga yi masa ado da su , daman ga ki da kyakkyawan jiki.....
Ƙananun kaya fa kika ce hajja ?
Falmata ta katse ta tana yamutsa fuska .
Eh su nace to meye ba mijinki bane ? Wani ma yayi rawa bare ɗan makaɗi ? Cewa nake kowa a garin su yake sawa ? To ke meye laifin ki idan kin yiwa mijinki ado da su ? Ji min rashin wayo .
Ta mula kafin ta cigaba da cewa :
Ƴar rangwaɗa da kisisina irin ta mata dunga yi masa , ki raba kan ki da ƙwalafacin Mama ki fara tunanin hanyoyin da za ki bi ki faranta ran mijinki saboda kin ga dai dai-dai gawargado shi yana nuna miki kulawa ke kece kike ƙin bada haɗin kai , to ki sake zane tun dundumin ki da danshi , shi mijin mace huɗu ne .
Ga ƴan magunguna nan na karɓo miki su musamman a wajen uwar zainaba , ta tabbatar min da ingancin su su ma zasu taimaka miki ƙwarai da aniya .
Anya hajja idanun nawa kuwa magungunan nan zasu min aiki ? Amma dai ba na sawa a ido bane kin san fa a asibiti sun hana ni zuba magani a ido ,
Mts' ana raba ki da kiwon awaki kina kyalla ta haihu , wanne maganin ido kuma ?? Wannan maganin gyara tsakanin ku ne ke da mijinki , idan kika daure da shan su suma zasu taka rawar gani wajen karkato miki da hankalin sa .
Ni zan dunga sha ko shi ? Nifa bangane bafa hajja .
Yo ina kuwa zaki gane ana nuna miki gabas kina bauɗewa yamma , kina girma kina sake shiga daji ., maganin mata ne .
Maganin mata ?
Ta maimaita da sigar tambayar
Eh
hajja ta amsa tana dangwara mata kullin maganin a hannu ,
Karɓi ki sa a cikin akwatin tafiyar taku , da madarar ruwa ko ta gari ake shan su ,
Taɓe baki falmata tayi ,
Tana ciro Envelop daga hijabin ta ,
Hajja ga hotunan Mama din an karɓo ɗazu Baban ta ya bata ta kawo min,
Karɓar envelop ɗin tayi ta zaro ƴan madai-daitan hotunan Mama da aka ɗauketa kwanaki uku da suka wuce da zummar hajja zata tafi da su Maiduguri ta kaiwa mutanen gida su ganta domin rabon su da ganin hoton ta tun tana ƴar shekaru biyu ,
Kai ɗanɗashi hotuna kuwa sun yi kyau kamar a ƙirata ta amsa tar-tar da su , ƴar wayayyar fuskar nan ta fito , ai kin ga hakan yafi a tafi musu da hoton ta su ganta ko dan yadda Rahima da Alhaji suke begen ganin ta .
Murmushi tayi , jin daɗin Hajja ta yabi 'yarta
Hajja kar ki manta dan Allah da saƙon gaisuwata , ga Baba , Yaya dakta , Rahima , kai kowa da kowa dai hajja , ki miƙa musu gaisuwata tare da fatan alkhairi .
Insha Allah kuwa duk zasu ji Falmata , kin dai ji duk abubuwan da na faɗa miki ko ?
Eh duk naji Hajja ,
To ki dai yi amfani da cewa ta , idan Allah ya yarda za ki ga amfanin sa .
To Hajja .
Ƴar dariya Hajja tayi, to Allah shi sa idan kun dawo nayi farin ganin gamdakatar da sabon ango ko kuwa sabuwar ƙawa .
Falmata ta yunƙura ta miƙe tsaye , tana cewa
Aina kenan Hajja ? Ko daga can za'a kawo miki ɗan turawa ? kai kai kai Hajja baki da dama .
Saƙare Hajja tayi bakinta buɗe , sai kuma ta gallawa Falmata harara .
Kinci gidan ku da sauyawa zancena launi , ƴar nema ai nasan sarai kina fahimta ta da gangan kike bauɗewa , oho ni dai na faɗa miki kowa rai yayiwa daɗi ai bayan me shi ne .
tana ƴar dariya ta ƙarasa barin ɗakin , kalaman Hajja na kutsawa cikin tunaninta tana ɗora su a mizanin nazari .
Washegari
Da farar safiya direban da zai kai Hajja Nigeria ya iso , daman da shirin ta tsaf , dan haka babu wani jinkiri aka fito da kayanta aka sanya su cikin mota ,
Tare da rakiyar Biyamuradi , Falmata da Mama suka ƙaraso jikin motar sallamar bankwana suka yi , Hajja ta shige mota direba ya tada motar suka miƙa hanya Mama tana ɗaga mata hannu .
Allah ya kiyaye hanya Hajja ta
Falmata ta furta a sarari tana jin yadda kewar ta ke fara kamata , "sabo tirken wawa ',
Muje cikki Fatima kafin zouwar le chauffeur mu tahi I'aéroport .
Hannun ta cikin na Mama wacce take ta zuba surutu suka juya zuwa cikin gida ,
kai tsaye ɗaki ta shige ta zauna a bakin gado , tunaninnika suka yi mata dirar mikiya , kewar ahalinta na kassara duk wani karsashi nata , shekaru biyar ɗin basu zo mata da sauƙi ba , ba kuma sun rageta da kome ba wajen jin ƙauna tare da muradin sake ganin wani jinin ta a duniya bayan Mama ,
duk kuwa da cewa ita ɗin ta kasance daga cikin jajirtattun mutane masu yaƙi da damuwar su, tare da danneta su binne ƙarƙashin ran su , su yunƙura wajen gina rayuwar su a yadda ta zo musu ,
ba domin ƙarfin zuciyarta ba da tuni damuwar halin da ta tsinci kanta ciki sun kaita ƙasa .
A hankali irin nata akwai hangen wani ƙalubale da take yi wanda take hasashen zai iya ɓullowa cikin rayuwar su ita da Mama ,
daga dangin Biyamuradi , wanda har kawo yau da Mama tayi shekaru a duniya da yake dai-dai da shekarun auren su babu wani dangi nasa ɗaya da ya taɓa zuwa wajen su , ya gan su .
Shi kaɗai suka sani , duk kuwa da yana ikirarin cewa yana da iyaye da danginsa makusanta , to ina suke ? Meyasa basu taɓa zuwa inda suke ba ko su su ziyarce su ? Shin menene aboye wanda su basu kai ga sani ba ? Tsakanin ƙarya da gaskiya wa ake yiwa wasan ƴar ɓoye a tsakanin su da dangin sa ? Tabbas akwai lauje cikin naɗi .
Sai dai koma menene a shirye take tsaf da taryar sa , zata yi kome domin ta bada kariya ga Mama , ƙuɗirinta bazai taɓa sauyawa ba muddin tana numfashi ita zata cigaba da kasancewa garkuwa ga Mama .
Ya jima yana tsaye daga dokin ƙofar yana duban ta , a tsawon zaman su da shi da ita koyaushe yanayi ɗaya yake hangowa a fuskar ta idan bata san da wanzuwar sa ba a guri , "damuwa" tana da damuwa wanda yake danganta damuwar ta ta da kansa .
Yana sane da cewa shi da ƴar sa sunyi kutse tare da yin karan-tsaye cikin rayuwar ta , ba kuma tare da suna amfanar mata da kome ba .
Anya yana yi mata Adalci ??
Gyaran murya yayi da ya sa tayi firgit!
Tana gyara zaman hijabin kanta ,
Fatima tasso le chauffeur ya zou .
Jakar kayan su uku babbar ƴan kayan cimaka ne a cikin su da sauran ƙananan tarkacen matafiya , ƙananan biyun suturun su ne a ciki .
A shirye suke tsaf , Falmata tana sanye da doguwar riga ruwan sararin samaniya me ɗan nawi ta ɗaura mayafin rigar akan ta ( tayi ɗankwali da shi ) da ɗan madaidaicin hijabin ta , takalman kafafun ta marasa tudu sun shiga da hijabin ta kalar ruwan hoda me haske ( baby pink )
Mama anshirya ta cikin ƴar riga iya guiwar ta da dogon wondo kanta rufe da hular saƙa me nawi mahaɗin safar ƙafar ta dake sanye da rufaffun takalman yara .
Biyamuradi ya riƙo hannunta da shima yake shirye cikin shigar kwat da wando ( suit ) ruwan ƙasa , ita kuma ta riƙe ƴan ƴatsun Falmata , sun sanyata a tsakiyar su suka fito farfajiyar gidan , Biyamuradi ya kulle ƙofofin gidan bayan ya kashe duk wasu na'urori masu amfani da lantarki .
tazarar ba wata me yawa bace tsakanin su da farfajiyar tashin jiragen sama na ƙasa-da-ƙasa ( Diori Hamani International Airport )
Dan haka cikin ƙanƙanin lokaci suka isa , bayan Bayan bin duk wasu tsare-taren da ya kamata matafiya masu tsallakawa ƙasashen ƙetere suyi tare da zaman jiran dai-daituwar jirgi da ya ɗauke su tsawon awanni uku da rabi ,
Biyamuradi Youssouf tare da Falmata da Mama suka bi sawun takwarorin su masu tafiya zuwa United States of America , a sawu na farko suka taka matakala , kafaɗar sa ta dama ɗauke da Mama wacce ta sarƙafo hannayen ta a jikin wuyan sa , ɗaya hannun nasa ya zare daga cikin na Falmata da tunda suka shigo airport ɗin yake kaffa-kaffa da ita yana riƙe da hannun ta , duk kuwa da yadda take yawan mutsu-mutsu da hannun tana son zamewa amma ya ƙi kulawa bare ya bata dama , ya maida hannun sa bisa ƙugunta tare da matso da ita jikin sa , a hankali yace da ita ,
Fatima ki kulla da kyau ki saurari takun ƙafa ta bissa matakala muke ,
ba tare da ta amsa ba ta gyaɗa kanta , tana jin yadda tsikar jikin ta ke miƙewa .
Cikin jerun kujerun first class suka yi mazauni akan kujerun su masu ɗauke da numbobin su da suke fuskantar juna , sai ɗan teburi a tsakanin su , bayan zaman su ya yunƙura tare da ɗaurawa Falmata seatbelt ɗin ta ya koma ya zauna tare da ɗaurawa Mama nata , bai tsimaya ba ya ɗaura nasa .
A hankali ya kai hannun sa ya kamo hannun Falmata da yake kan teburin gaban su , ya damƙe hannunta guda cikin nasa dai-dai lokacin da zazzaƙar muryar shugabar masu dauke da alhakin kula da walwalar mutanen cikin jirgin "Chief flight Attendant ," ta karaɗe cikin jirgin ɗauke da sanarwa da take cewa :
“Ladies and gentlemen, this is Rose jackson and I’m your chief flight attendant. On behalf of Captain Mike Abraham and the entire crew, welcome Turkish Airlines flight non-stop service from Niamey Niger Republic to Washington DC United States of America.
Our flight time will be of 9hours and 11minutes. We will be flying at an altitude of feet/meters 5612 miles .
At this time, make sure your seat backs and tray tables are in their full upright position and that your seat belt is correctly fastened. Also, your portable electronic devices must be set to ‘airplane’ mode until an announcement is made upon arrival. Thank you.”
Ta sake maimaitawa cikin yaren faransanci .
( Mesdames et messieurs, voici Rose Jackson et moi, votre agent de bord. Au nom du capitaine Mike Abraham et de l'ensemble de l'équipage, accueillez le vol sans escale de Turkish Airlines entre Niamey Niger Republic et Washington DC, États-Unis d'Amérique.
Notre temps de vol sera de 9 heures et 11 minutes. Nous volerons à une altitude de 5612 milles.
À ce stade, assurez-vous que vos dossiers de siège et vos plateaux sont dans leur position verticale maximale et que votre ceinture de sécurité est correctement bouclée. De plus, vos appareils électroniques portables doivent être en mode "avion" jusqu'à ce qu'une annonce soit faite à l'arrivée. Je vous remercie.")
Girgizan da jirgin ya ɗauka shi yasa ba shiri Falmata ta sake ɗora ɗayan hannun ta akan na Youssouf tana ƙanƙame sa hannayen su suka cure guri guda , kamar yadda zuciyoyin kowannen su ke ƙoƙarin jawo kusanci a tsakani .
Idanun sa a kafe kan fuskar ta dake bayyana tsoro ɓaro-ɓaro .
Cikin ikon Allah jirgin ya samu dai-daituwa a sararin subahana ya shilla da gudun gaske cikin tafiyar gaibu bisa iska a tsakanin sama da ƙasa .
Nigeria
Tafiyar kwana ɗaya da yini biyu ta sada Hajja da birnin Maiduguri , da la'asar sakaliya motar da ta kawota ta dakata a ƙofar gidan Prof .
Kai tsaye ta sauƙa ta shiga gidan , tarɓa ta musamman ita da direban suka samu daga sabbin ƴan aikin gidan guda biyu tare da Rahima da daman duk ansan da zuwan su .
Bayan magarib ta nemi iznin zuwa gaishe da prof da zuwan su a ɗazu suka tadda shi tare da baƙi , hakan ya sa basu samu ganin sa ba sai yanzu .
Bayan doguwar gaisuwa tare da godiyar da akayi musayar su tsakanin Prof da Hajja , taƙaitatciyar hira suka yi wanda duk rabin ta akan Al'amuran da suka shafi taɓarɓarewar tsaro ne tsakanin Niger ɗin da Nigeria da har kawo yau Ƴan tawayen Boko Haram basu saduda sun bar yin kisan mimmiƙe tare da ɓarnannaki tsakanin ƙanana da ma manyan garuruwan Niger da Nigeria ba .
Sannan kuma har kawo yau gwamanatin ƙasar Nigeria ta gagara kawo ƙarshen hare-haren ƴan kungiyar duk kuwa da cewa cikin ƙasar tushe da MAFARIN kafuwar ƙungiyar da ta jefa Dubunnan rayukan Al'umma cikin HARGITSIN RAYUWA yake .
Shin yaushe ne kome zai kawo ƙarshe ? Yaushe ne abubuwa zasu koma dai-dai ? Yaushe ne za'a ƙira ƙungiyar Boko Haram da shuɗaɗɗan lamari da ya zama tarihi ? Allah Shine Mafi sani .
Hajja ta miƙe ta ƙarasa gaban Prof tana miƙa masa envelop ɗin dake ɗauke da hoton Mama ,
Alhaji ga hoton Amaryar taka ta Niger ka ga yadda ta girma duk da ƙarancin lafiyar ta amma ta miƙe .
Miƙa hannu yayi ya karɓa yana dariya , dai-dai da shigowar Doctor Hamza wanda ya dawo daga Masallaci .
To toh Masha Allah , Babu kome ai kowacce cuta Allah yayi maganinta , sai dai idan har sanin ɗan Adam bai kai ga gano maganin ba .
Ƙwarai maganar ka dutse Alhaji .
Cewar Hajja .
ya zaro hoton yana gyara zaman gilashin idanun sa , bayan sun haɗa baki wajen amsa sallamar Doctor Hamza ,
ka ga Babban Likita , Likita bokan turai , ƙarshen ƙwaƙƙwafi da bincike sai likita , lalle tafiyata bana me sa'a ce tunda naci karo da kai , shekaru fiye da biyar rabona da na ganka .
Murmushi yayi yana zama daga gefen ƙafafun Prof .
Hajja sannun ki da zuwa , da fatan kin samu isowa lafiya ?
Lafiya ƙalau Likita ,yaya bayan rabuwa ? Ya iyalin naka ?
Duk kowa lafiya hajja .
To Alhamdulillah .
Masha Allah wannan Amarya tawa ai tafi kama da ƴaƴan nasara , ga dukkanin Alamu tana da wayo .
Prof ya furta haka yana mayar da hotunan cikin envelop ɗin .
Wayo kuwa na sosai Alhaji ai Mama sai godiyar Allah ba shakka tana da kaifin ƙwaƙwalwa da saurin ɗaukar abu
Allah shi rayata , ya bata lafiya , yayi Albarka cikin rayuwarta ita da sauran yaran musulmai baki ɗaya !
Ameen Ameen Alhaji
Hajja ta amsa tana sanya hannuwanta biyu ta karɓi envelop ɗin da yake maida mata , ta miƙe tana yi musu bankwana tare da barin falon ta koma cikin gida .
Baba , wacce yarinya ce hajja ta kawo maka hoton ta ?
Doctor Hamza ya tambayi Prof .
Ya buɗe baki da zummar bashi amsa shigowar ɗaya daga cikin dattijan unguwar da suke cin abincin dare tare da Prof ya katse musu hirar .
Abuja
Yakaka ce a zaune kan hannun kujerar falon Malama Maryam gabanta kuwa babbar jakar kaya ce da take shaƙare taf da kaya , daga gefen ƙafafunta ma wata ƴar matsakaiciyar jakar ce .
tana shirye tsaf cikin dogon hijabinta da yake har kusa da idon sawun ta , fuskar ta fayau babu ko kwalli , ramar da tayi ta fito sosai akan fuskar ta da idanunta da suka ɗan zurma ciki .
daga gefe a cikin falon Lubna ce a zaune tayi jugum tana kallon Yakaka wacce idanun ta ke kallon ƙasa , tayi shiru tamkar ba sune masu yin dararraki ba muddin suna waje guda .
Malama Maryam ce ta fito itama shirye take , ta kai dubanta ga Yakaka tana jin yadda tausayin ta ke sake narkar da ranta tabbas Yakaka tana buƙatar majiɓanci cikin Rayuwar ta .
Yakaka tashi mu tafi , lubna taya ta ɗauko kayan ku kai cikin mota Abban ku yana jiran mu , kar mu rasa motar farko ko ta biyu , saboda mu samu isa da wuri tafiya daga Abuja zuwa Maiduguri da tazara gara muyi sammako .
Jikin Lubna babu kuzari ta miƙe tana gyara zaman hijabin jikinta ta sunkuya ta ɗau ƙaramar jakar tare da kama gefen babbar ta taya Yakaka riƙewa ,
Sun zo tsakar gida Lubna ta jaa ta tsaya da hakan ya sa Yakaka waigowa .
idanunta cike taf da ƙwalla tace
Sahiba irin rabuwar da zamuyi kenan babu bankwana ? Shekaru biyar ba kwana biyar bane Sahiba ban so ba zaki tafi tare da maɗaukakiyar damuwa .
ɗan guntun murmushi Yakaka tayi ,
Sahiba kin san har abada kina cikin mutanen da bazan iya mantawa da su ba cikin rayuwata , cikin kowanne irin hali na tsinci kaina , nima zanyi kewar ki Lubna , ta ƙarasa zancen siririyar ƙwallar da bata shirya zubowar ta ba na sauƙa bisa ƙuncin ta .
Idan kika tafi a yanzu waye zata maye min gurbin ki ? Waye zata zama babbar ƙawata a bikina ? Da ke muka tsara kome Yakaka .
Idan Allah ya yarda zan dawo Lubna , zan halarci bikin ki na ɗau Alƙawari , amma dole na tafi a yau shekaru biyar Falmata tayi cikin rashina ,
Hon ɗin da aka matsa da ƙarfi shi yasa suka fara taku cikin hanzari ba tare da sun sake musayar wata kalma ba a tsakanin su .
Ƙarfe takwas da rabi na safe motar da su Yakaka tare da Malama Maryam suka shiga domin tafiya Maiduguri ta ɗau hanya ɗoɗar .
Tafiya ce me nisa ta tsawon fiye da awanni takwas tsakanin Babban birnin tarayya Abuja da Birnin Maiduguri dan haka a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 62 Chapter of 111