tsakanina da Mahaifinku babu daɗi , nema yake ƙarfi da yaji ya raba Rahima da gidan sa wanda nasan zugar 'yan uwansa ne da ni kuma ko kusa bazan lamunta ba , idan Rahima ta bar wajena ina zata ??
"har zuwa safiyar wata rana da na wayi gari Rahima kin yi gaban kan ki wajen barin Rayuwata , kin tafi kin barni cikin tashin hankalin da ya tunkuɗo min da naƙuda ,
"kika tafi ba tare da kin yi tunanin me hakan zai haifar ba cikin rayuwata ,
"duk wani wajen da nake tunanin zaki je Rahima naje neman ki har ms da wuraren da baza ki ba naje neman ki ,
" a cikin halin nan na matuƙar tashin hankali na haifi jaririyata da tun lokacin da na haife ta na shaidawa mahaifinku sunan ta Rahimatullah .
" da ɗanyen jego na dunga fita kusufa-kusufa neman ki da hakan ya tunzuro Al-Mustapha yace muddin na sake fita neman ki da kaina a bakin auren mu ,
" a wannan ranar nima zuciyata a taurare take da zafin rashin ki dan haka nima na taso masa , a take a wajen na nemi da ya sawwaƙe min auren sa tun a nan domin kuwa fita neman ki yanzu na fara har sai ranar da na ganki ,
"shima da alokacin yake ganin zallar laifin ki na cewar ai ke da kan ki kika ga damar tafiya dan haka zaki dawo ,
"a fusace a wajen ya datse igiyar auren mu ba tare da yayi la'akari da irin raunin dake tare da ni ba ,
"Ban kwana a gidan ba na tafi tare da jaririya Rahima , na bar masa Hafsa da Zainab Hamza kuma yana makaranta,
" nayi neman ki Rahimatullah har N'Djamena naje an tabbatar min da baki zo ba ƙarin tashin hankalina shine duk sauran ƙannena a cikin matsanancin talauci suke ,
" Na tattara musu duk wasu 'yan kuɗaɗen da na tafi da su na basu , na sake dawowa Nigeria , tare da taimakon ƙawayena biyu Hajiya Hadiza da Hajiya yaana , na sayar da tarin sarƙoƙi da ƴan kunnayena zuwa wara-waren zinare da nake da su , na sayi gidannan da muke ciki , na ɗora neman ki daga inda na tsaya saboda na tabbatar kina Nigeria wataƙila gari kika sauya , meyasa kika min haka Rahima ????
"aina kika rayu ? Ina mijinki kina da wasu 'ya'ya ne bayan wannan na cinyar ki ? Idan kina da su suna ina ??
Amnee ta ƙarasa bada labarin rayuwarsu da ɗora tambaya ga Khaalty Rahima wacce idanun ta yayi jazir tsabar kuka ,
Tausayin yayarta ya cinye zuciyar ta , ashe haka ta shiga damuwa akan rashin ta ??
ƙasa take son sharewa tayi rubutu ,
Amnee ta miƙe ta kawo mata takarda da biro , ta sanya hannu biyu ta karɓa ,
taƙaitatcen rubutu tayi a jikin takardar ,
" tsoron kar na zama sanadin rabuwar auren ku da Yaya mustapha yasa na tafi daga gareku ukhtee Amina ki yafe min , bansan ba zan zama sanadin tarwatsewar jin daɗin rayuwar ku .
"Mairambiri shine sunan ƙauyen da na rayu tsawon lokaci a cikin sa kafin zuwan yan tawayen boko haram su tarwatsa garin su kashe mijina da manyan yarana biyu mata da suma nake zaton sun mutu , Amina da Fatima shekaru shida yanzu da mutuwar su .bayan su ina da wata 'ya da ita ma harsashi ya same ta ta mutu , a yanzu Bulama shine kaɗai ɗana .
ASSALAMU ALAIKUM
'Yan uwa ina miƙo saƙon gaisuwata tare da fatan Alheri gare ku baki ɗaya , ina kuma mai yabawa bisa ga yadda kuke nuna ƙaunar ku ga littafin nan ,
nagode .
[11/15, 11:03 PM] +234 806 600 1491: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
39
Duk yadda Falmata take tunanin daɗin dake ga mallakar idanu ta tadda shi ya wuce haka , jin kanta take tamkar sabuwar halitta ,
Har bata so bacci ya shiga tsakanin ta da ganin hasken duniya , karambani kuwa babu irin wanda bata yi , har girki take karambanin yi Yousssouf kuwa yana taya ta ,
Shima a ɓangarensa baya gajiya da duk wasu tambayoyi da ko karambanin da zata yi , wani irin son ta yake yana riritata ,
Mama da kanta tasan cewa yanzu Mamarta ta samu waraka saboda wata kulawa na musamman da idanun ta sun hango mata wani ɗan datti a jikin kayan Mama zata yi maza ta gyara ta ta sauya mata wani ,
A kullum ta Allah sai ta miƙa godiyar ta ga Youssouf kamar yadda cikin duk wasu sallolinta sai ta ƙara godewa Allah akan wannan babbar kyauta da ya yi mata na dawo mata da ganin ta ,
Godiyar da take yiwa Youssouf ba a fatar baki kaɗai ta tsaya ba , har a aikace take gwada masa ta yadda take nuna masa ƙauna tare da ɗaukar buƙatun sa ba tare da gajiyawa ko ƙorafi ba .
Kamar yadda likita yace tana cigaba da zuwa ana dubata , babu wata sabuwar matsalar da ta ɓullo tunda aka yi mata aiki .
Idan tana da wata damuwa to ta lafiyar Mama ce wacce kwana biyu ciwon ta yake ƙoƙarin tasowa suna danne shi da tarin magunguna gami da ƙara ƙaimi wajen kulawa da ita , amma duk da haka kallo ɗaya za'a mata a iya hango tarin raunin dake tare da ita tun daga cikin raunanan idanunta da suka ɗan sauya launi zuwa ruwan ɗorawa har zuwa ƙafafunta da hannayenta da suka ɗashe suke yawan ɗaukar sanyi ,
Gaba ɗaya Falmata da shi kansa Biyamuradi Youssouf basa tare da walwala sosai ,
"Baban Mama ko dai za'a sake komawa asibitin nan ne maganar aikin Mama ,
Youssouf wanda yake shafa kan Mama wacce take kwance cikin jikin sa lamo , ya ɗago kan sa yana duban idanun Falmata da suke nuni ƙarara da damuwar da ruhin ta ke ciki ,
"Fatima duk wassu bayanai da zamu sake samu daga Doctora basu wucce batun baya da sunka faɗi muna , wanda kouma mun bar Lamari ga Allah zouwa lokacin da za'a samu damar yin aikin ,
Shiru tayi tana cigaba da kallon sa , cike da damuwa , so take yayi wani yunƙuri kome ƙanƙantar sa ,
Ji yayi gangar jikinsa na karban sakon dake fitowa daga cikin ƙwarar idanunta masu kyaun kallo ,
"idanun ki suna da kyau idan kina kallon Mutum da su Fatima , lokacin da basu da Lafiya kyan su bai kai haka bayyana ba , kina da sassanyan kallo Mai cike da nutsuwa ,
Murmushi tayi kaɗan , kafin ta ƙira sunan sa ,
"Baban Mama ,
Sai kuma tayi shiru ,
Kamo hannunta da yake kusa da shi yayi ya riƙe ,
"Ummh ina jinki menene ?
" daman nace ko zamu je ni ɗin a gwada ni ?
"gwaji Fatima wanne irin gwaji , akwai damuwa ne ga lafiyar jikin ki ?
Sunkui da kan ta ta sake yi tana jin nawin zancen akan harshen ta , sai dai tana jin zata iya yin kome domin ganin Mama ta samu lafiya , muryar ta a ciki tace ,
"ko Allah zai sa a dace un-un ko wai a jikina akwai abunda da za'a iya amfani da shi wajen yiwa Mama maganin ,
Kiris ya rage Biyamuradi Youssouf ya kwashe da dariya , sai dai ya gintse saboda yana son jaan ta ,
" Fatima kin manta likita yace ke baki iya bada jinin ki ?
Cikin sauri ta katse shi ,
" ai ba jini na ba , wai a auna ko akwai cikin ?
" ciki aina ?
Yace da dariya a cikin sautin sa,
Ɗago kanta tayi tana iya hango hasken haƙoransa da yake dariya,
" un-un a jikina ko ?
Dariya ya kwashe da ita , cikin ransa ƙaunar ta na sake yawaita , kunya da kawaicinta yana burge shi haɗi da salon rashin wayewarta da baya sa ta fidda tsagoron ƙauyencin ta .
"Fatima ciki ai sai ya nuna Alamunsa tukun ake zouwa ayi gwaji , hakanan bai yiwuwa aje ga gwajji sai a mouna dariya ,
Shiru Falmata tayi tana ganin wautar kan ta , to ita ya zata yi ne ? Ta matsu Mama ta warke ta samu lafiya kamar sauran Yara , tsintar kanta tayi da addu'ar Allah ya nufe ta da samun ciki nan kurkusa domin lafiyar Mama ,
Daren ranar basu samu bacci ba saboda jikin Mama da ya tsananta idan banda nishe-nishe da ƙananun kuka babu abunda take yi , hankalinsu baki ɗaya a tashe , Falmata ta rungume ta anjima Youssouf ya ɗauke ta ya ɗora a jikinsa , haka suka yi ta fama .
Asubar farko a cikin tsananin sanyi suka nufi asibiti a take likitocin ta suka shiga bata kulawa ,
Ba'a fi awa guda ba ciwon ya lafa ta samu bacci , tana rungume a jikin Falmata
Ƙarar wayar sa ya sanya shi miƙewa daga kujerar da yake zaune ya ɗan taka zuwa wajen ɗakin yana ɗaga ƙiran da ake masa wanda yake daga Tafeeda ,
" Youssoufa akwai Al'amari maigirma da muni da yake tunkaro ka ,
Sune kalaman da Yaji Tafeeda ya furta masa ba tare da sun ko gaisa ba ,
Ji yayi ya cigaba da cewa ,
"Bayan tsawon shekarun da ka kwashe kana ɓoye kuskuren da ka aikata yanzu kome yana daf da bayyanuwa batare da ka farga ba mutanen da suka ɗau lokaci suna bibiyar sawun duk wani motsi naka ba tare da ka kai ga hankalta ba gaf suke da cimma nasara akan ka ,
"Ya zama dole ku dawo tare da kai da 'yar taka da matar da ka aurawa kan ka kafin kome ya lalace , mafi girman lamarin shine nan da kowanne lokaci Maimartaba tare da Hajiya umma zuwa kan iyalai tare da 'yan uwanka zasu iya sanin Mummunar Fuskar ka ,
" Maƙiya kuma zasu samu damar kassara ka , wanda kafi kowa sanin me hakan ke nufi ??
"Ta-Tafeeda , meke Faruwa ne yi gaugawar sanar min ,
"ni a matsayina na 'dan ouwa a gareka zan yi dukkanin bakin ƙokarina wajen ganin lamura basu munana fiye da ƙima ba , duk kuwa da cewa ni ai ba bakin koume nake gareka ba ,
Ɗut-ɗut !
Yaji ƙarar Alamun yankewar ƙiran
Tashin hankalin da ya zo masa a lokacin maigirma ne , me Tafeeda duk ya faɗa masa ??
"Tayaya ya san cewa tare yake da Fatima da Mama ?
"Su waye maƙiyansa masu bibiyar rayuwar sa ?
"Fallasuwar Asirinsa a gurin iyayensa hakan na nufin ɗebe ƙaunar sa daga zukatan su ,
"wai shin me yake shirin faruwa ko kuwa ya ma riga ya faru ??
Ya zama dole ya koma gida ,
Da sauri ya shiga neman layin Tafeeda sai dai har ta gama ƙara bai ɗauka ba , ya sake gwada ƙira a karo na biyu nan ma ba'a ɗauka ba ,
Tashin hankalin sa ya yawaita da har Falmata ma ta kai ga Fahimta , damuwar sa ta ƙara mata damuwa , sau biyu tana tambayar sa ko me yake damunsa ? Yana ce mata ba kome .
Kafin dare Mama ta warware dan haka suka koma gida ,
"Falmata ta haɗa ruwa mai zafi ta yiwa Mama wanka ta shirya ta cikin jibga-jibgan kayan sanyi , kasantuwar cikin magunguna da Alluran da aka yi mata akwai masu sa bacci bata jima ba bacci ya sake ɗauketa ,
Itama wankan tayi ta shirya cikin wondo wide-leg da Rigar sanyi ribbed sweater ta ɗaura hular sanyi akanta ,
Ta fito ta cimma masa yana zaune a ƙasa ya jingina bayan sa da kujera , hannun sa biyu tallafe da ƙeyarsa ,
Babu wadatar haske a falon saboda duhun dare da ya shigo fitilar falon kuma ɗaya ce a kunne , kasantuwar idanun nata ba gani suke sosai ba , ya sa bata ma kai ga ganin sa a wajen ba sai duhu-duhu take gani ,
"Fatima ,
Ya ƙira sunan ta lokacin da ya ga ta kashe ƙafa daga ƙofar ɗakin , alamun tana buƙatar ɗan jagora ,
"zo nan ,
Yace da ita
Inda take iya hango duhun sa ta nufa a hankali ,
kallo yake bin ta da shi ganin yadda kayan suka karɓi jikinta musamman ɗan wondon da bai kai ga sauka ƙasa ba , daga ƙungunta ya zauna ɗas saboda ɗaura shi da tayi akan rigar .
Hannun ta ya kama ya ƙarasa zaunar da ita akan jikinsa yana jin yadda ƙamshin daddaɗan turaren da ta fesa yana ratsa hancin sa ,
Lamo tayi a jikin sa tana jin damuwar rashin walwalar sa na damun ta ,
" Alhamdulillah Mama ta samu sauƙi ko ?
Tace da shi da dabarar son jin maƙasudin damuwar sa ,
"Mama ta samu sauƙi Alhamdulillah ,
Ya ce yana ƙanƙameta a jikin sa ,
"Har hankalin mu ya kwanta , bana son ciwon Mama ina tausayinta ,
"Fatima zamou kassance cikin shiri zouwa wassu kwanaki nan gaba zamou koma gida ,
" ɗago kanta tayi da son ganin fuskar ko Allah zai sa ta fahimci damuwar sa ,
"Baban Mama na ɗauka sai an samu lafiyar Mama ?
Zai yi Magana wayar sa tayi ƙara ,
Ganin sunan Hajiya Umma a fuskar wayar ya sa zuciyar sa tsinkewa ,
Da sallama ya ɗau wayar , sai dai yadda ya ji ta amsa masa ya sa jin hankalinsa ya sake tashi ,
Sama-sama ta amsa gaisuwar sa , bayan nan abunda ta sanar da shi shine kawai duk me yake ya nemi izni ya taho gida cikin kwanakin nan kusa .
Shiru yayi bayan ya ajiye wayar , tabbas akwai abunda ke wakana game da shi a gida .
"Baban Mama...
Ya katse hanzarin ta
"Fatima zamou kouma gida , a gaba zamou dawo neman lafiyar Mama ,
Sai ta mayar da kan ta jikin sa tayi shiru , baki ɗaya walwalar da ta ɗan samu na murnar samun sauƙin Mama ta kau ,
Daren ranar babu wani armashi agare su musamman ma Falmata da damuwar da take ciki ta haifar mata da zazzaɓi da ɗan ciwon kai , dan haka washegari ta tashi haka sukuku ,
Karin kumallo ma sama-sama suka yi ,
Bayan sun gama karin kumallo su dukkanin su biyun sun yi shiru sai mama ce take ɗan wasan ta ,
" J'ai réservé notre vol, nous rentrerons à la maison le 18 le mois prochain , ( nayi mana tanadin jirgin komawa , zamu tafi ranar sha takwas ga watan gobe , )
Muryar sa ratso shirun wajen ,
"Allah ya kaimu Baban Mama , ko zaka sanarwar da Hajja itama ta fara shiri ko ?
"Eh zan sanar da ita idan ya ragge kwanaki goma mu tafi sai tayi shiru cikin kwanaki biyar , idan ya rage kwanaki biyar da tafiyar mu sai direba ya ɗaukota daga Nigeria ,
"To Allah ya kaimu ,
****
Wasa gaske cikin 'Yan kwanakin Youssouf ya gaza samun kwanciyar hankali tsoro ne cike taf a ransa , duk kuwa da cewa babu wanda ya sake neman sa kan wani batu sai dai yana tsoro ne kar ko tana ƙasa tana dabo .
Falmata har ta gaji da tambayar sa akan yadda ya zama koyaushe cikin tunani babu nutsuwar kirki , 'yar soyayyar da yake gwada mata mai sanyi da shiga zuci duk ya rage a wasu lokutan ma raba dare yake tunani , da juye-juye ,
Kasantuwar daman ita mace ce marar hayaniya mai kammalewa sai bata tsananta shisshige masa ba ta ɗan janye jikinta itama ta maida hankalinta baki ɗaya kan Mama ,
da kuma fama da kanta da take yi saboda wani ciwon kai marar daɗi da yake addabar ta tare da bugun zuciya fiye da ƙima duk tayi wata 'yar hidima sai ta ji mummunar gajiya da bugun numfashi sun taso mata ,
Mama da kanta ta san cewa Babanta ya rage kula da dararrakin ta sosai saboda duk ta dame shi zai samu ya zameta ya shiga ɗaki ya rufe ,
Ya rage sati biyu tafiyar su da ya ke tsawon kwanaki kusan goma da yin wayar sa da Tafeeda , wanda duk yadda ya so ya samu damar da zasu sake yin wata magana , Tafeedan yaƙi ba shi haɗin kai idan ya ƙira wayar sa ba bai ɗauka saƙonnin sa kuwa ya tura su babu adadi ta kan yanar gizo da kai tsaye ta hanyar saƙon karta kwana , nan ma ga shaidar an karanta sako amma babu amsa , dan haka shima ya zuciya ya daina neman sa .
Ya fito wanka da safe ya tarar da miss call ɗin Tafeeda , da hanzari ya ɗau wayar bai ko tsaya shafa mai ya sanya kaya ba ya ɗau wayar ya shiga neman layin sa ,
Sai dai kakarun Amai da ya jiyo daga Falon su ya sanya shi sauƙe wayar daga kunnen sa ba tare da ya kashe wayar ba ya fito falon hankalinsa a tashe ya ƙaraso ga Falmata wacce take durƙushe daga ƙofar kitchen ɗin su tana Amai ,
Da hanzari ya ƙaraso wajen ya riƙo ta zuwa jikin sa bayan ya ajiye wayar sa a ƙasa da aka riga aka ɗaga kiran daga ɗaya ɓangaren ba tare da ya sani ba ,
"qu'est-ce qui ne va pas avec toi chérie, es-tu malade? ( me yake damun ki ? Baki da lafiya ne ? )
Bata amsa ba illa yunƙurin Aman da ta cigaba da yi duk kuwa da babu kome a cikin nata ,
Shafa bayanta ya shiga yi yana ɗan bubbugawa tare da jero mata sannu ,
Mama wacce tashin ta kenan daga bacci ta jiyo muryar su ta fito , itama ta tsaya tana kallon su fuskar ɗauke da alhini da 'yar muryar tace
"Papa qu'est-ce qui ne va pas avec Mamma ?
"Princess Maman ki bata da lafiya ne, dauko min papier mouchoir dagga ɗaki na goge mata baki ,
"To ,
Ta juya da ɗan gudu zuwa ɗakin su ,
"Sannu Fatima ,
Yace cike da tausayawa ,
Daga can ɓangaren Hawaye masu ɗumi suka silmiyo daga idanun Hajiya Umma , ta zare wayar Tafeeda daga kunnen ta tare da miƙa masa wayar ,
Karɓar wayar yayi ya duba wayar yaga ba'a katse ta ba dan haka cike da tashin hankali ya kara a kunnen sa yana fargabar ko wani abu ne ya faru da Youssouf ɗin ,
Sai dai ya ƙarashi Maganar sa bai ji Youssouf ɗin ya amsa ba , sai muryar wata mace yake ji ƙasa-ƙasa , dan haka ya katse wayar waigo ga Hajiya Umma ,
"Umma Lafiya Yarima yake kou ?
"babu shakka lafiya yake ,
ta amsa da wata irin murya ,
Ganin yanayin ta ya sa Tafeeda miƙewa yayi mata sallama zuciyar sa cike da tunanin meye haka Youssouf ya faɗi wanda ya sa Hajiya Umma ƙwalla ?
Shi daman zouwa yayi ya gaishe ta tare da cigaba da kwantar mata da hankali bayan tashin hankalin da ta shiga a kwanaki sakamakon wani Al'amari mai girma da ya taso game da Youssouf ɗin ,
wanda shi yayi tsayuwar daka wajen ganin lamarin ya dai-daita da a yanzu yake mataki na ƙarshe na gyara kome wanda kuwa hakan ba zai samu ba sai da haɗin kan Youssouf ɗin ,
tunanin ko zai yadda da lamarin da zai je masa da shi a matsayin shawara ko ba zai yadda ba ya sanya shi yin jinkiri yana nazari dan haka nema yaƙi yarda suyi magana da Youssouf ɗin
Sai fa yau da Hajiya Umma ta sa ya ƙira sa a gabanta ta warware masa labarin mummunan ƙullin da aka so yi masa ,
Sai kuma ya ga Umma ta ƙare wayar ba tare da ta ce kome ba sai ƙwalla , lamarin da ya ƙulle masa kai kenan , koma menene zai ƙira Youssouf ɗin ya ji .
A ɓangaren Su Youssouf bayan Falmata ta gama Amai ya gyara wajen ya ɗau wayarsa bai lura da Shaidar an ɗaga ƙiransa ba saboda hankalinsa da yake kan Falmata wacce sai numfarfashi take saboda ƙaruwar bugun zuciyar ta tare da ciwon kai da ya haɗu mata ,
Ko sannu da Youssouf yake yi mata da kyar take amsawa ,
"Fatima ko mu tahi hospitalisé ne ?
Jikin ta babu kuzari ta gyada kai ,
Cikin hanzari ya shiga ya shirya ya wankewa Mama jiki tare da goge mata baki , ya dawo ya tarar da ita tana baccin zomo ,
"Fatima mu je ki shirya ,
Shi da kansa ya taya ta ta gyara jikinta yana riƙe da hannun ta suka fito
" za ki iya tafiya da kan ki ko kuwa na ƙira taxi ,
"zan iya tafiya ,
Basu sha wata wahala ba kasantuwar daman tana kan ziyartar likita , dan haka suka samu ganin likitan ta inda shi kuma bayan tambayoyin da yayi mata da duk bayanan da ta ba shi , ya miƙa su ga wata likita daban , wacce ta sake yi mata tambayoyi ,
Daga haka ta yi mata gwaji , bayan bayyanar sakamako ,
da fara'a likitar take miƙa musu sakon taya murnar cewa Falmata tana ɗauke da ciki na tsawon sati huɗu ,
Duk da cewa Falmata tana jin yaren faransanci babu laifi , Amma a yau ji tayi sam bata Fahimci me likitar ke nufi ba , tamkar ta manta ma'anar kalmar ,
Sai da ta ga Biyamuradi Youssouf ya rungume ta , yana bayyana farin-cikin sa da lokaci guda Albishirin da likitar tayi masa ya wanke masa zuciya tare da yin awun gaba da duk wata damuwa tasa , "Ya'ya ai arziƙi ne .
"Fatima Tu es enceinte, tu portes mon bébé , Alhamdulillah
Ya ɗago fuskar ta ya sumbanci goshin ta ,
Hannunta ta kai kan nasa hannun da yake tallafe da kumatun ta , kyawawan idanun ta na bayyana farin-cikin dake maƙare da zuciyar da
"Baban Mama da gaske ina da ciki ? Zan haifi jariri daga cikina Mama Zata samu dan uwa , Mama zata wa....
Katse ta yayi ta hanya ɗora laɓɓansa akan nata ya sumbace ta ,
"Mama da Yumna zasu samu ɗan ouwa ko ƴar ouwa insha Allah nayi Farin-ciki Fatima .
Mama da take tsaye tana kallon su ba tare da ta san me suke yiwa murna ba , sai ita ma ta sa dariya ta taho ta rungumo su ,
Hannuwansa ya sa ya zagaye a jikinsa yana jin waɗannan rayukan guda biyu sun zama wani ɓangare na daga rayuwar sa ,
Da wannan farin-cikin me tarin yawa suka baro asibitin zuwa gida , bayan likita ta basu shawarwari tare da 'yan magungunan da zasu taimaka a matakin farko na zaman ciki .
Falmata Ji take babu wata rana da take kai wannan ranar farin-ciki a wajen ta , minti kaɗan zata kai hannu ta shafi cikin ta , farin-cikin ta biyu ne ,
Tana ganin cewa lokacin warkewar Mama yayi tunda gata ɗauke da ciki ,
Da shigowarsu gida wayar sa tayi ƙara Tafeeda ne ya sake ƙiran farin-cikin sa bai ɓuya ba a muryar sa suka gaisa da Tafeeda ,
Kafin Tafeeda ya ɗora da cewa ,
"Yarima magana nake so muyi kou ka bani dama ?
Jin haka sai ya miƙe daga jikin Falmata ya fita zuwa 'yar barandar gaban gidan ,
"ɗan ouwa na baka dama faɗi ina jin ka ,
Yace masa a taƙaice ,
"Magana ce zamu yi game da lamarin yarinyar nan da kake boyen sa gareni tsawon wannan shekaru , na riga nasan koume kan zaman ka tare da su da amren innan ita yarinyar da kake har gidan da kun ka tare a Niamey na shina Yarima ,
"To munin Al'amarin ba dagga gareni yake ba , sai fa dagga maƙiya waɗanda sunka dunga bin lamarinka , a cikin binciken da nai kai tamkar da sanya hannun su kome da ya faru ya kai ga faruwa ,
"Lamari ya munana ta inda zance ya taho ga Fada ya iske kunnen Maimartaba da Hajiya Umma bai tsaya nan ba har sai da ya iske mutanen cikin Fada baki ɗai ba'a kouma san waye ya fiddo maganar ba ,
"cewa Yariman Maraɗi yana da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 72 Chapter of 111