Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sun gaisa da hajja wacce take ta shi masa albarka har ma ta taya shi murnar ƙarin girman da ya ssmu wajen aiki , Dumm ! Yayi , ƙaƙa ankayi ta san an masa ƙarin girma ? Kamar ta san tunanin da yake cikin dariya tace ma sa    Ɗazu na gani a tv , gaskiya ɗan nan ka sha hotuna , anya hasken majigin hoto bai kashe ma karfin gani ba ? Yadda ka ƙware a rawar nan ta ku ta soji ka burgeni ai naso ita ma wannan matar ta ka tana gani ,da ta ga yadda kake shan juyi a fili nasan dole ka burge ta , hahaha Ɗan murmushi yarima yayi yana maida kallon sa ga falmata wacce take gefe a ƙasa riƙe da baby mama , alamun rashin kuzari duk sun bayyana agare ta ,    Fatima miƙo min ɗiyar ki na ga fuskar ta ko kouwa har yau kina mini rowar ta ne ?? Cikin sauri ta girgiza kan ta , "    Hajja miƙa ma sa ita ! Hajja me wurya ta karbi baby ta bashi ,   Ya karbe ta yana tambayar yanayin lafiyar jikin ta a yanzu ? Hajja ta amsa masa da samun tabbatuwar lafiya ga baby mama , ya shagaltu da yiwa ƴar sa wasa daga shi sai falmata da ke rakuɓe daga chan gefe , Hajja tana cikin kitchen tana aikin gyarawa tare da sanya duk wasu kayan abinci a inda suka dace , bata yi aune ba ta ji ƙarar bindigogi da sauti iri iri ya karaɗe falon da ya sa ta yunƙura da gudu tana neman wajen tsira , rashin sanin kan falon ya sa ta dunga cin karo da kujeru ,     Wani mummunan karo ta ci da doguwar kujerar falon da yasa tayi baya tare da sakin ihun da yasa biyamuradi miƙewa a zabari ya taro ta da hannun sa ɗaya , jin mutum a kusa da ita da ƙara kusantowar harbe harben da take ji ya sa ta ƙwaƙumewa a jikin sa ta zagaye dukkanin hannunwan ta biyu zuwa bayan sa , Hajja da ta fito da gudu saboda jin ihun falmata da ƙarar harbe-harben bindiga , sai ta ɗan yi turus tana yawo da ido neman bindigar take , Miƙa mata baby mama yayi ganin yadda take ƙoƙarin sanya kuka saboda ƙaƙƙarfar rungumar da falmata tayi masa ya sa ta firgita , Hajja ta karɓe ta tana cewa ƙarar bindiga nake ji ɗan nan ,  ince dai ba wai yaƙi aka soma ba ?? Bai amsa mata ba illa zaro wayar sa da yayi daga cikin aljihun sa bai duba waye ke ƙiran ba ya katse kiran ,   Hajja ku yi haƙuri sautin ƙiran téléphone ne hakka ba wani abou bane ya kai ga faruwa ba , Au to to , ai cewa nake yaƙin ne ya biyo mu har nan , ! Wucewa tayi da baby mama ɗaki tana neman abin goyo ,! Fatima    Sakar ni haka nan , na faɗi miki ƙarar talfo ne ...    Wayar sa da ta sake ɗaukar ruri ita ta sa falmata ƙara sanya ihu tana sake shigewa jikin sa idan banda ƙyarma babu abunda jikin ta ke yi , Sauri yayi ya ɗaga kiran ganin sunan me ƙiran na sa        princesse Allô ma jolie fille. Ya furta dai-dai lokacin da yake yin baya ya zauna akan kujerar da ya tashi tare da falmata wacce har lokacin riƙe take da shi tsam ta runtse idanun ta , Allo Mon amour ! tu me manques mon amour comment vas-tu aujourd'hui?   Gimbiyar maimouna ta amsa masa cikin salon sautin ta na gogaggun matan da suke tsakiyar ganiyar su , Je vais très bien et tu me manques aussi,      Ya amsa mata yana jin yadda daɗin sautin ta yake ratsa jikin sa ,         Ma princes , Albishirin ka ?    Tace da shi  . Ɗauke da amon murmushin da ya bayyana har a fuskar sa yace  ,    Gorro farare gimbiya ! Ko kassan yanzou jakka ( jakadiya )  ke sanar mouna saƙo ya taho dagga masarautar ku maigirma , ɗauke da gorron tsayar da ranar amren mu , gomma ga wata me kamawa , tabbas sa'a zata tabbata gare ni ranar da anka ɗamra amren mu da kai biyamuradin maraɗawa ! Wani irin daɗi ne marar misaltuwa ya ji yana ratsa zuciyar sa , tabbas zuciyar sa na ƙaunar maimounatu fiye da kowacce ɗiya mace , samun ta kuma nasara ce maigirma saboda a ta suffa da ƙawa tayiwa sauran mata zarra a wajen sa ,     Cikin shauƙi ya sake riƙe wayar sa da kyau yana ɗan bubbuga bayan falmata wacce ta fara dawowa hayyacin ta , da ɗayan hannun nasa , Wannan albishir naki mai girmou ne tauraruwar Agades , votre histoire a fait son chemin dans mon cœur, s’enfonçant dans mon âme. tamkar Falmata ta ji abunda ya faɗi , sai ta ɗago kan ta daga jikin sa , a hankali ta zare jikin ta daga nasa , ta miƙe tana taku sannu-sannu da ƙoƙarin barin falon , zuciyar ta shaƙare da haushin sa , ita shiyasa ta tsani soja , kome na su akwai sumfurin mugunta a ciki bayan haka tayaya sautin ƙiran waya da ta san ƴar ƙara ce mutane ke sawa a wayoyin su amma sai ga shi ta shi wayar ruwan alburusai take har da tashin boma bomai ," Cigaba yayi da hirar sa cikin nishaɗi yana jin yadda albishirin da tayi masa yake ƙara masa kuzari , lalle maimartaba yayi masa attaque par surprise       Fiye da mintoci ishirin suna hirar su sannan suka yi sallama ya aje wayar sa ,        Bankwana yayi da hajja wacce har lokacin tana kitchen goye da mama tana girka musu ɗan abinda zasu ci kafin kwanciyar bacci ,         Har ƙofa ta raka shi tana masa addu'a da godiya     Inda yake sanar da ita gobe zai wuce garin su zai iya kaiwa sati biyu zuwa kwanaki ishirin idan ya tafi saboda haka zuwa goben su masa lissafin abubuwan da zasu iya buƙata baki ɗaya ,     Bayan fitar sa ta kulle ƙofar ta dawo ciki zuciyar ta cike da wasi-wasi akan hirar da ta ji youssouf ɗin na yi da wata wacce bata kai ga sanin wacece ba , sai dai cikin hirar su da mafi yawa da faransanci shi youssouf ɗin yake bada amsa , ta fahimci mafi yawan maganganun nasa na soyayya ne saboda zaman da tayi a ƙasar kamaru , kurtun ɗan sanda ne mijin nata a bariki suka yi rayuwar su dan haka sosai take tsintar wasu kalmomin faransanci duk da dai shekaru ya sa ta manta yaren sosai ! A fahimtar ta youssouf yana da wata mace wacce yake tsanananin so da a kowanne lokaci zata iya cuso kan ta cikin rayuwar sa ta mallake shi wanda hakan yake babbar barazana ga rayuwar auren sa da yarinya falmata miskiniya ,    Hodijan ! Kai tsaye ɗakin da falmata ta shiga nan ta tasamma ,   A zaune ta tarar da falmatan daga ƙasa a bakin ƙofar ɗakin ta takure , Kallon ta tayi ta ji tausayin ta ya tsirga mata , hakkun ta fara hango ƙalubale a rayuwar auren yarinyar da ko fahimtar kalmar auren ma ba ta kai ga yi ba ,   mutuniyar kina zaune anan ne ?? da sauri falmata ta ɗago kan ta ,   Hajja ya tafi ??  Mama tana hannun ki ?    Eh ya tafi ga kuma mama a baya na , taso nan muyi wata magana kin ji ƙawalliye roman jaɓa ! ****** Abuja Nigeria Yakaka ta dage da neman ilmi tun ana koya mata haruffa ,A ,B,C,D , da kuma ا ب ،ت ،ث، sannu sannu ta haddace su tare da iya rubutun su , aka fara haɗa mata jimla , tana koyan rubutun su tare da sanin ma'anar su , ba ƙaramin daɗin koyar da yakaka malama maryam take ji ba saboda wankakkiyar ƙwaƙwalwa me saurin ɗauke abu da yakaka take da ita , A hankali ta fara lura da ƙarancin wayon da yake ga yakaka tare da gidadanci , sai tayi ƙoƙari tana gyara mata duk lokacin da ta ga tayi wani abunda bai kamata ba , tare da yawaita yi mata ƴan nasihu akan duk wasu manya da ƙananun zunubai . Gefe guda lubna na ƙara zage damtse ita a dole sai yakaka ta iya English da arabic ta iya magana da yarukan kamar yadda ta iya , dan haka sai ta tsiri yiwa yakaka magana da English ko Arabic ta daina yawan yi mata magana da hausa koyaushe , ga bangaren yakaka ita ma ƙwarai ƙwarai take jin daɗin haɗuwar ta da malama maryam da ƴaƴan ta , domin sun ja ta a jiki suna kuma gwada mata ƙauna hatta mahaifin su da ba sosai ma suke haɗuwa ba , amma duk lokacin da suka haɗu yana amsa gaisuwar ta faram-faram babu nuna tsangwama , Dan haka gidan su nan ne wajen yinin ta idan babu makaranta , ranakun makarantar ma daga ta baro makarantar gida zata tayi sallah ta ci abinci ta sauya uniform ɗin ta , ta dawo gidan ta kama musu ƴan aikace aikace kafin malama maryam tayi sallah ta ɗan huta , zaman ta da samy baby sai ya ƙaranta , Ranar wata litinin an tashi da hazo sosai tare da sanyi mai tsanani tun safe , zuwa yamma sai hazon ya ƙaru sararin samaniya yayi jawur iska me ƙura tare da tsananin sanyi yana kaɗa jikin al'umma , kusan kowa sauri-sauri yake ya gama abunda yake a titi ya koma gida Bayan tashin su yakaka a makaranta tare suka dawo da malama maryam ita ta wuce gida da zummar yin sallar la'asar ta ci abinci ta sauya kaya ta koma gidan malama maryam wacce ta sake jaddada mata kan lalle fa ta zo su yi darasi kar ganin yanayin garin ya sa ta ƙi zuwa , cikin ladabi ta amsa da    To zan zo Anty ! Da sallama ta tura ƙofar falon samy baby tare da danna kan ta kai tsaye , abunda ta gani ya sa jakar hannun ta saɓulewa zuwa ƙasa ,    Ɗaya daga cikin ƙawayen samy baby ne tare da saurayin ta suke yin masha'ar su nan kan kujerar falon babu kunyar ubangiji ko shakkar za'a iya shigowa agan su haka , Da sauri yakaka ta kawar da ganin ta daga kan su , tare da sunkuyawa ta ɗau jakar ta da sauri ta wuce ɗaki ba tare da ta sake kallon su ba tana jin yadda jikin ta baki ɗaya ya ɗau rawa da tasowar sabon yanayin da take ji cikin illahirin wata jijiyar jikin ta ," A kasalance ta gama kome hatta cin abincin ta da samy baby take ajiye mata shi a ɗakin ta, ta shiryo ta fito falon da fatan son sake ganin su , saboda ganin su na ɗazu da ya tayar mata da wani yanayi cikin jikin ta tare da bijiro mata da guguwar begen yarima da ta ɗan kwanta sakamakon mayar da hankalin ta da tayi kan karatu , sai dai ganin da ta yiwa waɗanan fasiƙan ya sa ta fara tuno da wasu abubuwa masu kamanceceniya da wanda ta ga suna aikatawa , da abunda ya shiga tsakanin ta da bature kam silum , ba ta tarar da su a falon ba , dan haka ta sanya ƙafafu ta bar gidan , tana tafe tana jin ƙewar bature kam silum na sake lulluɓar ta , ko yana ina yanzu ? Wataƙila ma ya manta da ita ! , ruwan hawaye ta ji suna taruwa a idanun ta ,daidai lokacin da take tura babbar ƙofar gidan su malama maryam ta shiga ,    karaf suka ci karo da lubna wacce take ƙoƙarin fitowa daga gidan hannun ta riƙe da wata leda , Yauwa ƙawata Dan Allah zo ki raka ni wancan gidan ummi ta aike ni ,    Tana mata nuni da wani babban gidan da yake chan kusa da ƙarshen layin su ,    Ba musu ta bi bayan ta , lokacin da lubnan take jan hannun ta ,    Saƙo lubna ta kaiwa matar gidan tana bata saƙon suka mata sallama suka yi fitowar su , Sun zo dai-dai tsakiyar harabar babban gidan , yakaka ta ga wani ɗan dogon saurayi ɗan gayu ya sha gaban lubna fuskar sa a marairaice idanun sa fes akan ta ,    Lubna Haba dan Allah ki saurareni , yau wajen watanni bakwai kenan ina bin ki da soyayya ta amma kina min walakanci , dan Allah ki TAIMAKA MIN ki yadda da soyayya ta wallahi ina tsananin son ki ,    Ba tare da lubna ta ɗaga ido ta dube shi ba ta kewaye shi ta wuce tana sake jan hannun yakaka , Charaf ! Ya riƙo hannun ta Lubna Dan Allah ki taimak....   Wani irin ƙara lubna ta sa kamar ya jona mata wuta , ta warce hannun ta da matuƙar ƙarfi cikin abinda bai wuci daƙiƙai ba ta cire hannun ta ta wanke shi da mari , kafin cikin muryar ta da take karkarwar kuka ta tace     Kar ka kuskura ka sake taɓa ni , ni ba ƴar iska karuwa ba ce ,    Kukan da ya zo mata ya sa ta kasa ƙarass zancen ta da gudun gaske ta juya tana barin gidan ,    Yakaka wacce take sakakai a tsaye ta bi shi da kallon tausayi a hankali ta furta kalmar     Kayi hakuri   Gƴaɗa mata kai yayi Cikin sanyin jiki ta juya ta bar shi a wajen ta nufi gida , Tana shiga cikin gidan ta tarar da lubna rungume jikin mamar ta banda kuka babu abunda take , malama maryam sai tambayar ta take me ya same ta ? Me aka mata ? Ta gaza bata amsa ,   Kallo mai bayyana haushi yakaka tayi mata lokacin da take zama a gefen malama maryam , Anty wai fa dan kawai wani mutum ya kama hannun ta yace ta taimaka masa yana son ta shine ta mare shi ta gudo gida tana wannan kukan ,    Ta ƙarasa zancen muryar ta na nuna jin haushin abunda lubna tayi ,     Waye ya kama hannun ta ? Wanne mutum ne , ke lubna ɗago ki dube ni waye ne ya riƙe miki hannu meye tsakanin ku da shi ? Ki faɗa min gaskiya ,    cikin shisshiƙar kuka lubna tace ummi , Mukhtar ne ɗan gidan Alhaji Umar , shine tun watannin baya yake tare ni yana cewa wai yana so na , shine yau ya tare ni a gidan su har ya riƙe min hannu wai na taimake shi yana so na ,     Nan take fushi mai tsanani ya bayyana a fuskar malama maryam , ta shiga yin faɗa meyasa tun ranar farko lubna bata sanar mata ba ? Ita kuma ta faɗawa baban su lubnar ya sami mahaifin yaron anyi musu tsakani ba ,     Faɗa take yiwa lubna tamkar zata doke ta , a karshe ta gargaɗe kan ko kusa ta da shi bata yadda ta sake tsayawa ba kuma zata faɗawa baban su ya sanar da mahaifin yaron su ja kunnen ɗan su , ya fitar harkar ƴar su ,   Sororo ! Yakaka tayi cikin jin mamakin malama maryam menene abun tashin hankali haka ?   Da son kwantar mata da hankali tace ,    Anty ai hannun ta fa kawai ya riƙe , kuma fa cewa yayi ta taimaka masa , wani irin kallo malama maryam tayi mata ,    Yakaka , Namiji baligi ya kama hannun mace baliga haramun ne a musulunci , muddin ba muharamman juna suke ba domin tafarki ne na samar da ZINA a tsakanin mace da namiji  , Zina kuma haramun ce a musulunci, kuma tana daga cikin manyan laifuka wanda ake kira Kaba'ir. Allah ya fada cikin Qur'ani و لا تقرب الزنى Wato kada a kusanci zina. Hikimar fadin hakan shine ba aikata zina kadai ba, aikata abunda zai janyo zinar irinsu rungumar juna , taɓe-taɓen juna da shafe-shafen jikin juna tsakanin namiji da mace dukkansu Allah yayi hani domin hanya ce ta kusanta kai ga zina , cikin sanyin murya yakaka tace Anty menene ZINA  ?? Zina ita ce Saduwa a tsakanin namiji da mace ,( ina nufin mace da namiji su kasance cikin abun rufuwa ɗaya jikin su na cikin na juna , azzakarin namiji yana cikin farjin mace ) ba tare da hukuncin aure ya shiga tsakanin su ba , duk mace da namijin da suka yi tarayya irin haka ba tare da an ɗaura musu aure kamar yadda addinin musulunci ya koyar ba to babu shakka sun aikata zina , kamar yadda na faɗa miki ita zina tana cikin manyan laifukan da Allah yayi hani da su sannan kuma ya tanadi hukunci ga duk waɗanda suka aikata ta , Hukuncin Zina a shari'ance ,  ita zina ba'a tabbatar wa da mutum ita dole sai da hujjoji, hujjoji guda biyu ne ko dai mutum ya yarda da kanshi ya aikata , ko kuma mutane huɗu su ganshi turmi da taɓarya a wannan hali ne ake tabbatar da zina, Amma ko mutune uku ne suka ce sun ganshi turmi da taɓarya sai ɗaya yace shi dai ya gansu a tube suna shafe shafe to baza a karbi shaidun su ba, za'ai musu bulalar ƙazafi tamanin tamanin , Amma idan shaidu sun kammala ko mutum ya amsa da bakin sa yayi zina Hukuncin sa a shari'ance shine bulala ɗari ga waɗanda basu taba aure ba. Kamar Yadda Allah ya faɗa" الزانية والزانى فاجلدا كل واحد منهما مأة جلدة، ولا تأخذكم بهما رأفة فى دين الله إن كنتم تؤمنون بالله واليوم الآخر. Wato mazinaci da mazinaciya ayi wa kowanne su bulala ɗari, kada tausayi ya kama masu dukan idan har sun kasance masu imani da Allah da ranar lahira. Sai wanda yayi aure akwai hadisin da yace duk mai aure ko wanda ya taɓa aure idan ya taɓa zina za'a jefe shi, amma sai idan shine da kanshi yazo yace yayi zina yana so a jefe shi, amma idan bai yadda a jefe shi ba ba za'ayi mishi dole ba za'a barshi ne. Wani irin tsoro da tashin hankali me tsanani ne ya dirar mata , cikin wata irin muryar da ke bayyana tsantsar firgicin da ruhin ta ke ciki , tace    Anty ko da mutum taimako yayi , Malama maryam cikin tsanaki tace ban fahimce ki ba yakaka wanne irin taimako ne yake zuwa ta hanyar aikata zina ?? Anty ina nufin ko shi namijin cewa yayi mace ta taimaka masa , sai ita ma ta taimaka masa , suka yi , shikenan tayi zina ?? Su dukan su sun aikata zina , saboda babu biyayya ko temakekeniya tsakanin bayin Allah wajen saɓa masa , su dukkanin su basu da hujjar kare kan su , suyi gaggawar tuba ga ubangiji domin zina babbar musiba ce , Sannan kuma yakaka ai duk namijin da zai cewa mace ta taimaka masa ta bashi kan ta suyi zina , ai wannan babban maƙiyi ne a gare ta , bata da maƙiyi sama da shi , mugu ne kuma macuci domin na farko zai ɓata tsakanin ta da ubangiji , yasa ta aikata abunda Allah zai yi fushi da ita , da zai hana ta samun ganin Alkhairi da dacewa cikin rayuwar ta duniya da lahira har sai idan ta tuba , Na biyu duk ranar da mutane suka san me suke aikatawa, mutanen kirki zasu guje ta , za'a dunga mata kallon fasiƙa, mazinaciya ƴar iska , karuwa . Na uku idan ta hanyar zina da suka aikata ta samu ciki ta haihu , abun da ta haifa idan ya girma shi ma da kan sa zai tsane ta , ƙimar ta zata zube a idanun abunda ta haifa , saboda ta zamto sanadin da mutane zasu dunga ƙyamatar sa da ganin sa wani mutum da aka samar da shi ta haramtatciyar hanya , Bayan haka illolin zina suna da yawa , daga ciki akwai ɗaukar munanan cututtuka da zasu iya kai me su ga mutuwa , A ƙarshe namijin da duk zai yi zina da mace abu ne me wuya ya aure ta , ko da ya aure ta kuma bazai taɓa ganin ƙimar ta da mutuncin ta ba , sannan ƙanƙanin kuskure zai iya haifar da zargi a tsakanin su da zai lalata musu aure , Kuma duk macen da tayi zina kafin tayi aure bata da wata martaba a idanun duk wani namijin da zai zo ya aure daga baya saboda ta rasa ƙima da mutuncin ta na ƴa mace tunda tayi zina . Ki gujewa abunda duk zai kai ki ga aikata ZINA yakaka cikin ta akwai tarin masifu kin ji ko ?? Bata amsa ba illa miƙewar da tayi bata tsaya ba ta taka da gudun gaske tana barin gidan ba ta ko tsaya ta sanya takalman ta ba bare ta saurari ƙiran da malama maryam take mata , gudu take bata ko dub Inda take jefa ƙafar ta ,    Da ƙarfi ta tura ƙofar ɗakin tana shiga ta zuɓe a tsakiyar ɗakin tana sakin wani irin kuka marar sauti da yake tuƙowa daga ƙasan ruhin ta ,    Cikin wata irin murya ta fisgo kalmar ,    ALLAH NA TUBA , NA TUBA ALLAH , BAZAN SAKE BA ,ALLAH NA TUBA KA YAFE MIN ,   Kuka take tana maimaita kalmomin nan jikin ta har tsuma yake , Ashe haka ne girman laifin da ta aikata batare da ta sani ba ? Ashe ita ɗin me tarin zunubi ce ? Ashe baza ta samu wani alkhairi ba arayuwar ta tunda tayi zina , Ta jima a zaune a wajen tana kuka har duhun dare ya shigo , zuciyar ta ta tsorata iyaka , neman yadda zata yi Allah ya yafe mata take yi , sai dai bata san yadda zata yi Allah ya karbi tuban ta ba , ji take kamar zata mutu , Tashi ta sake yi tana gama hanya saboda kukan da ta ɗauki lokaci tana yi yasa kan ta sarawa tare da fara jin jiri , tana gama hanya ta fito , bata ko dubi ɗakin samy baɓy da kiɗa ke tasowa ta cikin sa alamun da ke nuna ta dawo gidan ba , ta sake fita , hanyar gidan malama maryam ta sake  ɗauka ,   tana so ta san yadda zata yi Allah ya yafe mata , tana so ta san yadda zata yi ta gyara kuskuren ta , a falo ta tarar da malama maryam tare da iyalan ta suna cin abincin su na dare ,    Babu sallama ta rakaɓe daga bakin ƙofar gami da sakin kuka me ciwo , hankali tashe malama maryam ta tsame hannun ta daga abincin da suke ci ta miƙe , ta zo ta kama yakaka ,     Tambayar ta take lafiya ?meye ya same ta ? Ko wani abu ya samu antyn ta ? Daman yanzu take so idan ta gama cin abinci lubna ta raka ta gidan nasu ta duba ta domin ɗazu ta fita bata cikin nutsuwar ta yanzu kuma ta dawo tana kuka , shin menene yake damun ta ??      Cikin muryar ta da kuka ya fara disarwa , tace nayi ZINA malama maryam , ki taimake ni ki faɗa min yadda zan yi Allah ya yafe min , ban sani ba malama maryam wallahi ban sani ba ,   Ta shi , ta shi mu shiga ɗaki ki nutsu ki min bayani yadda zan fahimce ki ,    Ta kama hannun ta zuwa ɗaki ta zaunar ta bakin gado , ina sauraran ki me kike son faɗa min yakaka ? Tiryan tiryan , yakaka ta fara bada labarin tun daga farkon haɗuwar ta da yarima har yanayin yadda abubuwa suka kasance har zuwa yadda alaƙar ta da samy baby da yadda ta yaudare ta ta zo da ita garin  abuja ta baro ɗanyar jaririyar ta

Chapter 47 of 111