Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tana dafe ƙirji a take taji zuciyar ta ta hautsina da daman tunda tafara girkin warin Albasa ke ɗaga mata hankali. Ba shiri ta bar baro kitchen ta wuce ɗaki tana mayar da numfashi "anya Sofi kan ta ɗaya ? "Samira da gaske kike ? da gaske kike da gaske ? Kamar an safure ta ta miƙe tayi hanyar fita daga ɗakin da gudu Samy baby ta bita ta riƙo ta . Kufcewa tayi tana watsa mata wani mugun kallo kafin cikin muryar da ta buɗu kamar ba ta ta ba tace "ki bar ni naje na kashe ta na farka mata ciki na zo miki da ɗan tayin cikin na ta wallahi sai na kashe ta. Kallon baki da hankali Samy baby ta jefa mata kafin ta ce . "Dallah Sofi ki nutsu ya kike abu kamar wacce ba tayi karatu ba ? Kina abu kamar wata jahila kina tunanin yanzu idan kika je kika kashe 'yar mutane ke ma za ki rayu da Hamzan ne ba tare da an miki ɗaurin rai da rai ba ko kuwa ke ma a kashe ki. "Na yarda a kashe ni idan na kashe ta akan dai mu rayu ni da ita alhalin ta raba ni da farin-ciki na ina ji ina gani bakin-ciki zai kashe ni na mutu na bar mata duniyar su rayu ita da Mijina . "Na yarda za ta mutu amma ba ta irin wannan hanyar da kike son bi ba ko da kashe ta kike son yi ki bari sai an kauda-bara ta yadda za ki kashe ba tare da an samu mai iya ɗaga ido ya dube ki ba ko kuwa ma kawai a mata abunda zai kashe ta ba tare da an zarge ki ba . "Ta yaya faɗa min hanyar ? Sofi ta furta hakan jikin ta har wani mazari yake , a kaikaice Samy baby ta dube ta cikin ran ta kuwa dariya take kwasa "Yau Sofi uwar bin Bokaye har wata nahiyar ita ke tambayar ta yaya za'a yi ? Lalle notikan cikin kan Sofi sun kwance baki ɗaya . Gyara zama tayi tana jin Allah ne ya kawo mata hanyar warwarewar tata matsalar da kome ya kwaɓe mata bariki tana ƙoƙarin kwashe kayan ta daga kanta ta juya mata baya ta bar ta a cikin rana dan kuwa ko Alhaji Gali a halin yanzu fiye da watanni uku kenan ta daina ganin ƙeyar sa alhalin lokacin biyan kuɗin gidan haya yayi haka tana ji tana gani bayan ƙara mata sati biyu da masu gidan suka yi suka zo a ƙarshe suka kore ta sai gidan ɗaya daga cikin abokan shaiɗanan ta ta koma da ko kaɗan ba jin daɗin zaman gidan take ba saboda ba shi da wani hali sosai irin mazan nan ne da Zina ta aure su wanda ko basu da sisi sai sun yi ta. Fahimtar hakan da tayi yasa ta fara ƙulla wacce za ta fissheta idan zaman Abujan ya gagara ne tana iya komawa ko Damaturi ne ta karkaɗe kwalin ta ta shiga neman aikin da za tayi ta riƙe kan ta dan kuwa ko a mafarki ta san bata doshi Maiduguri gidan Ubanta ba bata ma da matsugunni a gidan sannan ita a karan kanta bata jin za ta iya rayuwa ƙarƙashin iyayen ta. Sai dai me ? Kuɗaɗen da suke account  ɗin ta ba zasu ishe ta yin irin rayuwar jin daɗin da take tsarawa kan ta ba ko da ta koma Damaturu domin so take ta shiga gari sosai ta wataya a ƙarshe ta samu wani ɗan Matashin kyakkyawan Saurayi haka ta chaka masa su yi aure . Dan haka ido rufe take neman kuɗi tunda kuwa yanzu dama ta samu da zata iya samun su daga Sofi to me za ta jira ? Muryar Sofi ta katse mata tunani ta da take cewa " Ni kin hana ni naje na aiwatar da manufata ke kuma kin yi zaune shiru baki kawo wata hanyar ba ki faɗa min ya zan yi ?. "Sofi ki buɗe bakin Aljihu kiyi ɓarin kuɗin na san dai kin Fahimceni ni kuma na miki alƙawarin ko nan da birnin Sin ne zan je miki wurin Boka ba sai kin ma tafi da kan ki ba bare har a iya zargin ki . Da wata irin Murya Sofi ta ce " ki koma min karnataka Samira gurin Bokan da ya min aiki akan zuciyar Doctor zan baki adireshin sa da kome sannan zan bayar da kuɗin da zai ishe ki har kije ki dawo da kuma kuɗin aikin sa , bana so na motsa ma daga tsakanin su domin ko kallo bana so ya sake shiga tsakanin su .... Samy Baby wacce tafi zaƙuwa da zancen kuɗin jin tarkon ta yayi kamuwa tace "amma fa kin san kuɗaɗen dayawa Friend.. "Ko miliyan ishirin ne zan sayar da gwalagwalai na na baki kuɗin bana so a ɗau lokaci nasan kin san manyan mutane a ƙasan nan dan haka samun visa ba zai miki wahala ba idan son samu ne cikin satin nan ki tafi kai ni idan zai yiwu ma cikin kwanaki biyu masu zuwa saboda bana so bana kuma fatan yarinyar nan da ita da abunda ke cikin ta su sake yin sati ɗaya a duniya . Nisawa tayi tana gatsa gefen bakin ta da haƙori tace " Sannan so nake na kashe ta da hannun na Samira da hannu na nake son kashe ta shine kaɗai abunda zan iya mata da zai sa zuciyata ta wanku daga baƙin-cikin da ta samu a ta sanadin ta dan haka daga kin isa can an yi aikin kawai ki ƙirani ki sanar min ina mai tabbatar miki da sai dai ki dawo ki tarar ana zaman makokin mutuwar ta . Shiru Samy Baby tayi tana kallon Sofi cikin ran ta tana girmama rashin Imani irin na Sofi yau ta zama rana ta farko da ta fara jin shakkun samuwar cikakken hankali ga Sofi to kodai tana da rauhanai ne ????? Ko kuwa Mai rabon shan duka ne da baya jin Bari Assalam Alaikum masu karatu. Albishirin ku ? Na san kun ce goro goriya goro . Yau Maman 'yan biyu tagwayen shafuka ta muku. Ina nufin kar ku motsa shafin nan tare yake da ɗan uwan sa da yakasance kuma murfi na baki ɗayan littafin Mafari insha Allah . A sha karatu lafiya . [4/15, 8:17 PM] +234 706 503 6187: MAFARI            ( HARGITSIN RAYUWA) UMM'MUAZ KARSHE (A) A daren ranar Doctor Hamza bai dawo daga aiki ya tarar da Sofi a gida ba saboda tunda rana suka fice ita da Samy ko Yakaka bata san fitar su ba . Hakan ba ƙaramin ɓatawa Doctor Hamza rai ya yi ba saboda ai tsagoron raini ne matar auren ka ta fita unguwa ta kai har dare ba tare da ta nemi iznin ka ba . Sai dai halin rashin lafiyan da ya zo ya tarar da Yakaka a ciki ya ɗauke masa hankali daga kula haukar Sofi . Nan take ya shiga bata duk wata kulawar da ta dace domin samun tabbacin abinda yake zato . Maƙurar farin-cikin da zai iya cewa bai taɓa jin yanayin sa ba ya tabbata a zuciya da kewayen jinin jikin sa baki ɗaya lokacin da gwajin fitsarin da ya yiwa Yakaka ya bayyana masa da tabbatuwar zaton sa Yakaka tana ɗauke da gudan jinin sa a Mahaifar ta nan da wasu watanni zai zama uba bayan shekaru bakwai da ya kwashe da yin auren sa na farko wanda hakan ya sadar da shi cikar shekarun sa arba'in cif ba tare da ya samu ɗan kan sa ba . Sai fa yanzu da Allah yayi tsiron halittar gudan jinin sa a tare da Yakaka shi kuwa da wacce irin kalma zai miƙawa Ubangiji godiyar sa ? Ganin sa ya mayar kan Yakaka wacce take bacci hankalin ta kwance da ba domin larurar saurin bacci na mata masu ƙaramin ciki ba a ɗan zaman su da yanzu-yanzu tayi fitsari ta ba shi yayi awu bai ci ace kafin ya gama gwajin har tayi bacci ba . Fuskar ta ya tsirawa idanu yana jin wani ƙaunar ta mai ƙarfi tana sake fisgar sa har yana jin kamar babu wani sarari da yayi saura a zuciyar sa da ƙaunar ta bata riga ta cika ba . A hankali ya ɗaga hannu yana shafar kumatun ta da suka sake yin suɓulɓul suna ƙyalli na musamman . Zazzaɓin da ya dawo ya tarar da shi ya rufe ta sosai a yanzu ya sauƙa saboda ya bata maganin sauƙe zafin jiki ta sha . "Wafaa . Ya ƙira sunan ta a hankali yana ɗan hura mata iska a fuskar ta ' Buɗe idanun ta da suka yi nawi tayi tana kallon sa a raunace . "Wafaa yaya kike jin jikin yanzu ? Za ki iya tashi muyi sallah ? "Habibi nayi sallar isha ina jin bacci sosai ni. "Na san kin yi wannan Sallar miƙa godiyar mu ga Ubangiji za muyi da yayi mana kyautar sa mafi girma . Hannun sa ya kai ya ɗora akan cikin ta kafin cikin taushin murya yana kallon idanun ta ya cigaba da cewa "Allah ya arzuta mu da samun rabo , Wafaa we are going to have a baby, zan zama Baba Wafaa za ki Haifa min Baby . "Da gaske ? tace da shi tana ƙoƙarin miƙewa zaune ya taimaka mata ta zauna.' Yana murmushi ya amsa mata "Da gaske Wafaa na baki Baby i am gonna be a Daddy. Wani irin yanayi ta ji mai sanyi tundaga ƙasan ran ta da ya chakuɗu da kunyar ta ta halitta dan haka ta tafi da sauri ta shige jikin sa tana ɓoye fuskar ta a ƙirjin sa . Dariyar da bata da sauti yayi yana riƙe da ita ya miƙe kafin ya sake cewa " Alhamdulillah for blessing us in the most special way as a Mum and Dad. Ya ɗago ta a hankali ya sumbanci goshin ta sannan ya sake cewa "muyi Sallah Wafaa domin mu nunawa Ubangiji godiyar mu. Gyaɗa kai tayi ba tare da ta amsa ba . Tsananin farin-cikin da yake ciki a daren ya mantar da shi takaicin Sofi dan ko da ta dawo tana wani kame-kamen ta lokacin da ta shigo falon ta tarar da shi yana aikin sa a laptop Yakaka kuma tana bacci a jikin sa . Wajen ƙarfe goma saura na dare za ta fara masa ƙwarƙwasa ya ɗora hannun sa akan laɓɓan sa yace "shittt please Sofi kar kiyi hayaniya ki tayar da ita a bacci tana buƙatar hutu Sosai bana son abinda zai dame ta . Wani sakototo Sofi tayi baki sake tana kallon sa . "yau ga sabon salo kuma , kullum abun daɗa lalacewa yake , ta aiyana hakan daga cikin ran ta . kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ta juya baya tana kwance akan kujera tayi matashin kai da cinyar sa fuskar ta na fuskantar jikin sa' Hayaƙi-hayaƙi ta ji yana safko mata yana sanya ta gani dusu-dusu . "Bata da lafiya ne ? Ta furta hakan a shaƙe tana tattaro duk wata sauran juriya da ta rage mata . Murmushi Doctor Hamza yayi da har take Iya hango ƙyallin haƙoran sa da muryar sa mai cike da nutsuwar da bata ɓoye halin farin-cikin da yake ciki ba yace "Sofi we are pregnant insha Allah in nine months we will welcome a new bundle of joy into our family. Kamar wacce aka dokawa guduma a ka haka Sofi ta ji, kunnuwan ta suka rabu da ji na ɗan wani lokaci duk kuwa da cewa a ɗazu Samira ta faɗa mata batun cikin Yakaka amma bata ji dukan zancen irin yanzu ba dan kuwa a ɗazu tana da ƙarfin jikin iya yin zabure-zabure a yanzu kuwa da  zancen ya tabbata cewa dai Doctor Hamzan tane ya yiwa Yakaka ciki ji tayi duk wata jijiyar jikin ta tayi tsayuwa daga barin yin aiki na wucin gadi . A yau taurin zuciyar ta gaza yin tasiri yayi domin kuwa ruwan hawaye ne ya ɓalle mata kamar an buɗa famfo . Sai shiƙar kukan ta Doctor Hamza ya ji wanda ya mayar da kan sa ga aikin sa . Tsam yayi yana jin ɗan guntun tausayin ta na kawo masa , daga can ƙasan ran sa sai ya ji kamar fa bai kyauta ba yadda ya sanar mata da batun cikin Yakaka dole za ta iya jin babu daɗi tunda ita Allah bai bata ba musamman da yakasance Sofi tana da bala'in kishi. A hankali ya ɗago kan sa yana kallon ta sai dai kafin yayi wani yunƙuri ta miƙe kamar ana tunkuɗa ta ta bar wajen . Girgiza kai yayi yana mai mayar da kan sa ga aikin sa da yake so ya kammala kafin gobe saboda a gobe da yamma yake so ya bar garin zuwa Kano . Washegari D octor Hamza da kansa ya shiga kitchen domin samarwa Yakaka da abunda za ta ci saboda kusan kwana tayi da zazzaɓi asubar farko kuma ta fara Amai . Dan haka ya kama ta zuwa falo ya kunna mata tv yace tayi kallo kafin ya gama haɗa mata abun karyawa. Ba dan ta so ba ta haƙura ta bar shi ya shiga kitchen sai dan ko kaɗan bata jin ƙarfin jikin ta wata irin kasala ce take bin gaɓɓan jikin ta jikin ta babu ƙarfi gefe guda kuma bata son warin Albasa da tasan muddin ta shiga kitchen to kuwa sai ta shaƙa . Lokacin da ya gama ya kawo mata bata wani ci dankalin da ya kawo mata tare da ƙwai na kirki ba tace ta ƙoshi . Yana tsakiya da rarrashin ta kan ta daure ta sake ci kaɗan Sofi ta sauƙo bata dubi inda suke ba ta zauna akan kujera ta ɗau remote. Lokacin da ya dubi fuskar ta sai da zuciyar sa ta doka da karfi ganin yadda fuskar tata ta kumbura suntum idanun ta kuwa har kamar kwanciyar jini. Da sauri ya baro Yakaka ya juyo gare ta "Subhananlah Sofi me ya same ki haka ? cikin dare ɓarayi sun shigo gidannan ne ? Ba tare da ta dube shi ba tace "Da aljanu muka yi dambe ko ka manta? Yadda tayi maganar a cushe ya so ba shi dariya amma sai ya gintse fahimta da yayi so take ta zo da rainin na ta da tayi alƙawarin ta daina ' "Oh i see . Yace yana barin kusa da ita ya koma ga Yakaka wacce ita ma ta tsorata da ganin yadda Fuskar Sofi ta kumbura tayi jawur kamar wacce ta shiga filin dambe da wanda ya fi ƙarfin ta . Bayan ya shirya ya fito gargaɗi ya yiwa Sofi kan kada ta yarda ta fita ko'ina ta zauna ta kula masa da Wafaa . Kafin azahar zai dawo su yi Sallama saboda bayan Azahar zai tafi . Bai yi zaton samun amsa mai daɗi daga gurin ta ba amma ga mamakin sa sai ya ji ta amsa har tana masa fatan alheri hakan sai ya faranta masa tare da ƙara masa kuzari ya bar gidan cike da nishaɗi farin-ciki goma da ashirin . Sai dai yana fita Sofi ma ta fice kai tsaye inda suka yi za su haɗu sa Samy baby domin ta bata cikon kuɗin da za'a yi harkokin aiki kama daga kuɗin jirgi da Samy Baby ta bata tabbacin ta samu wanda zai mata hanya muddin ta saki kuɗi cikin kwanaki uku ma za ta ɗaga India, da yake kan Sofi ya kunce ilmin zamanin ta tare da wayewar ta sai suka gaza yi mata amfani saboda taƙi basu dama shaiɗan da muƙarraban sa kaɗai ta sau wa ragamar rayuwar ta cikin tsakanin jiya da yau ko ibada ta daina yi kwata-kwata da daman dai ba sosai take tsayar da Sallah ba amma daga jiya zuwa yau ko Sallah ɗaya bata yi ba,  cikar mummunan burin ta kawai take mafarki a bacci ko a farke ita dai burin ta ta ga bayan Yakaka "kaicho Sofi . Haka ta ɗau kuɗi zunzurutu naira Miliyan biyar da dubu dari shida ta bawa aminiyar ta Samy Baby bayan naira Miliyan huɗu da rabi da su kenan kuɗin da ke account ɗin ta da tun a jiya tayi transfer su zuwa account na Samira. Wannan farin kudin kuwa kudin duk wasu gwala-gwalan ta ne tare da wani daya na Momy kori da ta amsa Aro bata mayar mata ba duk ta hada su ta sayar ta dankawa Samira kudin.  "Samira dan Allah ki tabbatar kome ya tafi yadda ya dace kin ga Doctor tafiya zai yi to so nake kafin ya Dawo kome ya kammala sai dai ya dawo ya tarar da gawa kawai . "Kar ki damu ƙawata to meye amfanin ƙawancen mu idan ban miki ba ? Ke ce fa Sofiya ? kar ki damu jibi-jibin nan zan bar ƙasar nan ke dai ki kwantar da hankalin ki bana son yadda duk kika bi kika tada hankalin ki kin ga yadda kika koma kuwa? Kamar wata bazaurar Jaɓa . Ɗauke kai Sofi tayi tana jin zagin walaƙancin da Sofi tayi mata a fakaice . Cikin wayencewa Sami baby ta miƙa hannu ta ɗau wayar Sofi da take ajiye a tsakanin su ba tare da Sofin ta hana ta ba tayi wasu 'yan taɓe-taɓen ta a wayar ta ajiye mata daga nan Sallama suka yi saboda Sofi ta ce bata so Doctor Hamza ya dawo bata gida . Haka kowaccen su ta nufi motar ta Sofi ita ce ta fara barin harabar wajen kafin Samy Baby ma ta tada tata motar ta jaa ta cike da nishaɗi ta kama hanya ' Kome ya tafi mata dai-dai yadda ta tsara yanzu abunda ya rage mata kawai shine ta tattara duk wasu abubuwan da ta mallaka a garin Abuja ta cika motar ta ta bar garin zuwa garin Damaturu inda ta zaɓa domin gina sabuwar rayuwar ta . Ita da Sofi kuma daga ta ƙarasa rufta ta a rami kamar yadda ta shirya a jibi kafin ta bar jahar Abuja sun rabu kenan haihatan ah to aina Sofi ta san za ta kama ta ? Sannan ma cikin shirin ta na ƙarshe da zata yi ta san za ta ingiza Sofi ta aikata abunda zai sa ta iya ƙarasa rayuwar ta a gidan Yari da ba zata samu damar neman ta ba ma dan haka ita ta sha kenan ta kuma rufe shafin Sofiya a rayuwar ta "kayya Samira . Lokacin da Doctor Hamza ya dawo gida ya tarar da Sofi a kitchen tana girki ba ƙaramin daɗi ya ji ba dan haka ya saki jiki da ita ya tsaya a kitchen ɗin suka yi 'yar hira yana ta jaan ta da wasa . Ƙarfe biyu dai-dai ya musu Sallama ita da Yakaka bayan ya haɗa su ya musu 'yar nasihar kan su zauna lafiya kafin dawowar su sannan ya ɗau kuɗi masu kauri ya danƙawa Sofi ko za su buƙaci wani abu sai suyi amfani da shi duk da ya san a store da kitchen akwai kome na daga kayan abinci Dauriya Sosai Yakaka ta nuna lokacin da suka masa rakiya bata yi kuka ba sai Sofi ce ma ke zuba masa shagwaɓa wai za tayi  kewar sa shi kuma gaba ɗaya hankalin sa yana kan Yakaka Ko kaɗan ba son ransa bane yayi nisa da ita a dai-dai wannan lokacin sai dai dan ba yadda zai yi aikin sa aikin ceton rai ne dan haka bashi da zaɓi na lokacin da zai yi tafiya a bakin aiki inda za shi ma ceton rai zai tafi dan haka tilas ne tafiyar sa. Haka suka yi Sallama cike da alhini ya jaa motar sa da zai tafi da ita zuwa gidan Doctor Suleiman wanda shi ne zai kai shi airport ya koma da motar tasa gidan shi . Yakaka ita ta bada hanya Sofi ta fara wucewa cikin gidan suna shiga Sofi ta rufe ƙofar ta murɗa ɗan makulli ,  ta ƙasan ido Yakaka ta dube ta Kallon nan da take tsoro shi ta hango a idanun Sofi idan ba gizo idanun ta ke mata ba ma ta ga kamar tana mata wani guntun murmushi. Zuciyar ta ta doka da ƙarfi sum-sum ta wuce ɗakin ta ta bar Sofi a wajen . Kitchen ta shiga a gur-guje tayi girki ta zuba a kula ta bar sauran a tukunya sannan ta jidi ruwan gora da juice ɗin da take ɗan sha ta kai fridge na ɗakin ta ta sa ta dawo ta ɗau abincin tazo fitowa daga kitchen ɗin ta ga Sofi ta tare hanya har yanzu dai wannan kallon ne a idanun ta sannan bata janye murmushin mugunta da take mata ba . Muƙut Yakaka ta haɗiye yawun tsoro . "Mai ciki girki aka yi ne ? Sofi ta tambaye ta fuskar ta a yanayin da bai yi dai-dai da kalmomin da ta furta ba. "Eh nayi girki ne Anty Sofi , naki ma yana tukunya daman yanzu zan zuba miki ' "Bari na kai nawa ɗaki . Sai da Sofi ta mula sannan ta ɗan matsa da kyar Yakaka ta wuce tana shiga ɗaki ta murza ɗan makulli tana jin nutsuwa na safko mata daga nan bata sake fita daga ɗakin ba har dare komen ta a ciki take yi tsakanin banɗaki da tsakar ɗakin Sai wayar ta take yi da Falmata da kuma Lubna da su duka biyun suke cikin watan haihuwar su . Washegari Kamar yadda tayi a jiya haka yau ma tayi girkin ta ta kai ɗaki ta rufe tsawon yinin bata bari sun haɗu da Sofi ba duk kuwa da cewa ta ji motsin ta daga falo . Sau biyu ta samu damar yin waya da Doctor hamza wanda ya shaida mata cewa a gobe zai dawo idan Allah ya yarda dan haka ta ƙarasa yinin ranar cikin nishaɗi da jin daɗin dawowar sa duk da cewa tsakanin jiyan da yau laulayi sosai ya taso ta gaba gadan-gadan kawai dauriya take yi . A washegari da safe Bayan tayi wanka taso fita ta haɗa abin karyawa amma jin yadda Sofi ta ƙure muryar tv tana jin kiɗa ya bata tabbacin tana falon ita kuma cikin kwanakin nan kamar Allah ya ƙara mata tsoron Sofi ne wani irin matsanancin tsoron ta take ji ta yadda ko haɗuwa bata so su yi dan haka ta fasa fita tayi zaman ta kawai a ɗakin da daman ba jin cin abincin sosai take ba yau ta tashi da matsanancin ciwon kai ne . Can kamar hantsi haka tana ɗan taɓa bacci ta ji wayar ta ta ɗau kiɗa , da kyar ta miƙa hannu ta ɗau wayar ganin ƙiran daga masoyin ta ne yasa tayi azamar ɗagawa . Cike da ƙauna da kulawa suka gaisa kafin Doctor Hamza ya shiga rarrashin ta a ƙarshe ya shaida mata cewa dawowar sa a yau ba zata yiwu ba sai nan da kwanaki biyu watau ranar juma'a Wannan karon bata ɗaure ba sai da ta sanya masa kuka da kyar ya iya shawo kan ta tayi shiru da alƙawarin zai dunga ƙiran ta akai-akai duk dai idan ya samu dama . Ba dan sun so ba suka yi sallama saboda  jiran sa da ake yi., duk da cewa ya so yayi magana da Sofi ma domin ya sanar da ita ɗaga dawowar ta shi amma sau uku yana gwada ƙiran ta yana nuna masa cewa tana  amfani/waya da layin nata dan haka ya haƙura ya tura mata saƙo kafin ya kashe wayar sa . Sofi da take baccin asara ƙiran waya ne ya tada ta lokacin da ta ɗau wayar wasu numbers ta gani haka irin na ƙasar waje idan idanun ta sun gani dai-dai ma numbers ɗin na ƙasar india ne dan haka cike da ɗoki ta ɗaga kiran Kamar yadda ta zata ne Samira ce take ƙiran ta daga ƙasar india kamar yadda numbers ɗin suka shaida mata kafin ma ta ji daga bakin Samy Baby . Bata jira sun gaisa ba a ƙagauce ta fara tambayar "Samira kada dai har kin isa india ? Nan Samy Baby tace mata ai ma tana karnataka har kuma ta gana da Boka yanzu haka ma da take jin hayaniya a cikin jirgin ƙasa take kan hanyar ta na komawa masauƙin ta ta kasa haƙura dai dole ta ƙira ta fara mata albishir Boka yace nan da awa biyu zai kammala aikin ta . Wani irin ihun jin daɗi Sofi tayi tana jin kamar an mata bishara da gidan Aljanna. za ta sake yin magana ɗif

Chapter 108 of 111