ta ,
Mama ki tafi a hankali kin ga ba wani ƙwarin jiki kika samu sosai ba ,
Bata kula ba
Ta taka da ɗan gudun ta , da sassarfa shima ya ƙaraso ya chafe ta sama ya cillata ,
Yana juyi da ita kafin ya sauke ta zuwa ƙirjin sa yana dariya ,
Bonjour papa , ina kwana papa .
tace daidai lokacin da take kai hannu tana ƙoƙarin cire hular kan sa ,
Taya ta cire hular yayi ya ɗora mata bisa kan ta da aka mata manyan kitson kalba suka zubo har kan kafaɗun ta ,
Bonjour mon cher ," yaya kin ka tashi ?
Lafiya papa
tace da shi daidai lokacin da take ƙoƙarin sauƙa daga ƙirjin sa ,
Ya sauƙe ta yana riƙe da hannun ta suka ƙarasa cikin falon , ya samu mazauni kan ɗaya daga cikin kujerun wajen yana gaisawa da hajja wacce ta miƙe zaune daga kishingiɗar da tayi ,
Kamar yadda ta saba , yanayin ta babu walwala idan har yana waje ta gaida shi , tana riƙo hannun mama wacce take ƙoƙarin ajiye mata hular baban ta a kai ,
Bata iya hana ta ba sai da ta ɗaura mata hular akan hular da take rufe akan ta wacce take mahaɗin doguwar rigar jikin ta ruwan madara me ɗan nawi saboda tashi da aka yi da ɗan sanyi garin sakamakon ruwan sama da aka kwana yi daren jiya .
Shafa fuskar ta mama tayi , kamar yadda yake al'adar su ita da mamar ta .
Maama kin yi chau dayawa ,
Papa ka ga maama na tayi chau , donne-nous des photos ,
ta ƙarasa zancen tana hayewa kan kujerar da falmata take ta zagaya ta bayan ta gami da sarƙafa hannuwan ta biyu ta wuyan falmatan ta cusa fuskar ta gefen wuyan ta .,
Biyamuradi wanda ya fara yiwa hajja bayani game da shirye-shiryen da yake na tafiyar su US , ya juyo da duban sa kan su idanun sa suka sauƙa kan fuskar falmata wacce haƙoranta ke buɗe tana murmushin da yake bayyana farin cikin ta da ganin walwalar mama ya assasa mata ,
Kamar maganaɗisu ya riƙe shi , ya kasa janye idanun sa daga kan ƴar fuskar ta da komen ta yake ɗan madaidaici idan aka cire manyan idanun ta ,
Ba tare da ya iya ɗauke ido daga kallon ta ba ya zaro wayar sa daga aljihu , ya juyo baki ɗayan sa ya saita cemara ya haska musu hotuna wajen kala shidda ,
Da gudu mama ta sake sauƙowa ta dawo wajen baban ta , tana cewa zata ga hoto ?
Ta ɗare cinyar sa ,
Batare da ya sake mata wayar ba ya nuna mata hotunan , da sauri ta sanya hannu tana sake tura huton gaba , fuskar wata ƴar baby me kyau kamar ta ya cika fuskar wayar , ƴar yarinya ce da bata wuce shekaru biyu ba tana tsaye a hoton ,
A hankali mama ta ɗago kan ta tana duban fuskar sa
Papa bebe waye ?
Zare wayar yayi daga hannun ta ba tare da ya bata amsa ba, daidai lokacin da hajja ta ke cewa ,
Wannan yarinyar da surutu kike kamar aku , duk kin bi kin tsare shi da surutu kin hana shi ya yi magana , bayan kuma yayi shirin tafiya aiki , ni zo nan ki zauna na miki tafiyar tsutsa a ƙafar ki .
Sauƙa tayi daga jikin sa , maimakon ta tafi wajen hajja , sai ta nufi mamar ta , tana zuwa ta zauna a gefen ta gami da kwantar da kai a jikin ta tayi shiru ,
Boyayyar ajiyar zuciya Biyamuradi yayi , cikin ran sa yana hamdala da hajja ta katse masa tambayoyin mama , domin Alƙawari ya ɗaukarwa kan sa ba zai taɓa yiwa ƴaƴan sa ƙarya ba , akan duk wata tambaya da suka masa , sai dai ko ya sakaya amsar idan kaifin hankalin su bai kai su fahimce ta ba , amma a yanzu bai shirya amsa ba ga tambayar da mama tayi ma sa .
Cigaba da yiwa hajja bayani yayi , inda yake sanar da ita , yana son ranar litinin ya zo su je ayiwa falmata da mama passport , zai fara nema musu visa
Idan Allah ya yadda daga sun samu visa shi da su zasu tafi US , da ba zai wuce tsawon nan da wata ɗaya da ƴan kwanaki ba nan gaba ,
Ba shi da masaniya akan tsawon lokacin da zasu iya yi a chan ,saboda harka ce ta neman lafiya , bai san yadda lamura zasu kasance ba , amma dai visa ta tsawon watanni shidda zai samar musu .
Ya ɗora da neman hajja ta masa bayanin duk wasu abubuwan da zata iya buƙata bayan kayan abinci da sauran abubuwan buƙata na rayuwar yau da kullum wanda zai iya kai ta watanni shidda ko fiye da haka ,
Da farko addu'o'in samun nasara akan abunda zasu nema tare da addu'ar nemawa mama samun waraka tayi ta jerowa , tana jin yadda tausayin su duk ukun ke kama ta ,
Babban soja , ni ba sai an min tanadin kome ba , saboda ka ga nima wajen shekaru biyu ake nema rabona da ƴan uwa da dangi , dan haka idan har tafiyar ta tashi , bayan kun tafi a washegari nima zan ɗau hanya zuwa nigeria nima naje na sada zuminci na ga ƴan uwa da dangi , shekaru sun fara jaa , mutuwar nan ta yanzu kar ta gifta tsakani ba'a nemi gafarar ƴan uwa ba , idan ya so bayan dawowar ku ko kuwa ma kafin ku dawo sai a sanar min nayi dawowa ta , ai ka ga nima na ribaci lokaci ko kuwa ?
Babu shakka hakane hajja , to babu kome idan har tafiya ta kama lokaci yayi sai ki tafi zouwa gida kafin dawowar mu , Allah ya saka da Alheri , ki min duk wasu bayanai na abubuwan da kike buƙata da zaki yiwa mutanen gida tsaraba don Allah .!
Toh madallah Babban soja , amma dayake nima a wajen nawa akwai ƴan kuɗaɗe irin waɗanda kake min kyautar su ai ba ma sai na maka lissafin kayan tsaraba ba , idan tafiya ta zo ni da kaina zani nayo ƴar tsaraba ta ,
A ah hajja , don Allah kar ki ce hakka , irin Alherin da kika mouna a rayuwa ba zamou iya biyan ki ba sai dai Allah shi saka da Alheri , ƙwarai ƙwarai ina miki godiya , ki min lissafi abun da kike buƙata duk zan sa a kawo kome ranar da zaki tafi sai direban da ya kai ki wancen karon ya sake kai ki nagode !
Ni ce da godiya Babban soja ni ce da godiya , Allah dai ya ƙara buɗi , ya ba wa mama lafiya ,
Ameen ameen hajja ya amsa yana miƙewa ,
Sashin da suke ya mayar da duban sa , mama har tayi bacci fuskar nan a chakuɗe alamun fushi take ,
Bai yi mamaki ba saboda sanin ta da yayi da saurin bacci ,
A hankali ya taka zuwa gaban falmata wacce tayi shiru , tana ɗan shafar kan mama da yake bisa cinyar ta ,
Fatima ni zan tafi bakin aiki zouwa le lundi zan dawo mu tai à muku passeport , ki kula da mama kar tayi wassa dayawa idan ta ji sauƙi sosai sai ta cigaba da zouwa école .
Toh Allah ya kiyaye hanya ,!
Ta amsa masa ,
Ɗan jim yayi a tsaye yana ƙure mata kallo da buɗaɗɗun idanun sa , hular ta shi ta karɓi yar zagayayyar fuskar ta me ɗan haske kaɗan , ji yake kamar ya bar mata hular a kan ta yayi ta kallon ta a haka ,
Jin yayi shiru kuma ta san da tsayuwar sa a wajen ya sa ta ɗan dago kan ta , tana sake haɗe fuska ,
Gyaran murya yayi ganin yadda tayi kicin-kicin kamar zata fashe masa da kuka .
Fatima donne moi mon chapeau! ( miƙe min hula ta )
Ya furta hakan yana sake rage amon muryar sa ,
Falmata wacce tsayuwar sa akan ta da idanun sa da take ji suna mata yawo a jiki tamkar suna mintsinin ta ya sa ta diririce ta gaza fahimtar me yake cewa , ba wai dan bata jin yaren da yake yi ba ,
Mama bacci take .
ta ce da shi tana fatan ya bar kan ta
A hankali ya sunkuyo har tana iya jiyo hucin humfashin sa a fuskar ta ya kai hannun sa guda ya zare hular sa dake kan ta , ya mayar kan sa .
Na tafi
Yace da ita yana juyawa ya bar wajen .
Wani irin yanayi ta ji a jikin ta uwa wacce aka zubawa ruwan sanyi , har ga Allah ta mance da hular sa da take kafe a kan ta ,
Runtse idanun ta tayi da ƙarfi tana jin yadda zuciyar ta ke bugu .
Hajja wacce duk abunda ya faru akan idanun ta tana iya hango su daga inda take .
auho ! aikin banza ihu bayan hari , da kike wani runtse ido kina wani kawar da kai ya ƙadangariyar gobara , ai wallahi ni dai na daina saki a hanya kan sha'anin auren ki , tsakani na da ke ido ,!
Ace wai tsawon shekaru fiye da biyar kin kasa zama cikakkiyar matar gida , ke kenan ɗaurewa miji fuska kina muzurai , zauna nan yarinya za'a yi bake lokacin da Babban soja ya gaji da halin ki ya sillo auren sa babu ni a masu yi miki dannar ƙirji , ko muƙamuƙi ba zan danna miki ba .
Cikin rashin kulawa da zantukan hajja wanda falmata ta riga ta saba da jin makamantan su , tace
Hajja ta me kika ce ?
Abunda wancan yace , shi nace
Ta amsa mata tana shirin miƙewa daga inda take tana cigaba da mita ,
Ƙatuwar mace kamar ki ace wai har yau tana da miji amma bata san amfanin sa ba sai rainon ƴa ,?
Ai ni ina kamar ki nayi aure na na biyu ma ,
Ki ka ce me hajja ta ban ji da kyau ba ??
Na ce gidan ku !
Ta amsa mata tana ƙarasa barin wajen
Murmushi falmata tayi domin ta san ta ƙular da hajja ,
Cikin ran ta tana juya maganganun hajja ,
Ban da abun hajja shi mutumin da kullum.take kumfar baki akan a kula da shi ɗin , shi ya taɓa nuna wata alama ne na kasancewar ta matar sa ? Tsawon shekarun auren su a tun bata san me takamaimai kalmar auratayya ke nufi ba ,
har ta zo ta san me ake nufi da aure ta hanyar malamar da take koyar da ita wacce a farkon fara ɗaukar darasi a wajen ta take yawan yi mata bayani akan auratayya a addinance da yadda mace zata kula da kan ta da mijin ta ta fuskar auratayya ba tare da kunyar kome ba cikin rashin sanin ta hajja ce ta yiwa malamar bayanin ƙarancin ilmi da wayon falmata ta kuma roƙi da ta dunga mata darasi na musamman akan auratayya ,
A hankali yau da gobe ta fahimci manene aure , matsayin miji a gun matar sa da matsayin mata a wajen mijin ta ,
Ta shiga ruɗani na sosai da har kawo yau bata fita daga cikin sa ba , " yaushe yakaka da Baban mama suka yi aure ?? Ita ba ta san lokacin ba kawai jin yakaka tayi da cikin mama .
Akwai tsoro me tafe da son bada kariya tare da kyautata zato ga ƴar uwar ta yakaka , haɗi da son tsaftace mama shi yasa a duk lokacin da tunanin hanyar da aka bi aka samar da mama ya taso mata , take yaƙar tunanin da ƙarfi da yaji , bata son wani abu da zai aibata yakaka ya raɓi tunanin ta ,
Kewa tare da ƙaunar ƴar uwar ta bai ragu ba ko kaɗan a cikin ran ta sai ma zurfafa da yake sake yi yayi mata ƙaton miƙi a cikin rai .
Rashin son suyi zaman auratayya irin na sauran ma'aurata da Biyamuradi ya nuna tsawon shekarun bai taɓa damun ta ba ,
Hasalima ta fi son hakan .
Zaman mama take , tana rayuwa ne a ƙarƙashin sa kaɗai domin mama , za kuma ta cigaba da tsayawa ɗauke da auren sa a kan ta har abada muddin tana tare da mama .
****
Daga niamey kai tsaye maraɗi ya wuce , bayan isar shi faɗa ya kai gaisuwa , kai tsaye ɓangaren sa ya nufa ba tare da ya shiga cikin gidan su wajen hajiya umma ba , yasan yanzu tana tare da jama'a masu neman taimako da ƴan barandar ta , sai zuwa yammaci zai shiga wajen ta zuwa lokacin ƙafa ta ragu a sashin nata ..
Tattaki yayi zuwa sashin sa da yake bigire guda na gidan , bayun da suke kai kawo a fada su na ta kai gaisuwa bayan waɗanda ke take masa baya tun daga ƙofar fada .
A bakin sashin sa suka jaa tunga saboda a tsarin sa bayi maza basa shiga ɓangaren gidan sa da matan sa ke ciki .
Yana sanya ƙafar sa a cikin gidan ya ji wani yanayi marar daɗi na lullubar sa , hakan kuwa yana da nasaba da rashin daɗin zama a gidan da yake ji har kullum ya kuma rasa dalili .
Taku ya fara yi da nufin isa sashin gimbiyar ta shi maimouna .
Sai dai ƴan hannuwan da ya ji sun riƙe masa ƙafafun sa su suka sanya shi ya maida ganin sa ƙasa ,!
Yumna
Ya furta yana ƴar dariya tare da kai hannu ya ɗauki ƴar yarinyar da take ta yi masa dariya , ya ɗaga ta sama ya cilla ta tana ɓangala masa dariya .
Rungume ta yayi a jikin sa lokacin da yake maida duban sa kan mamar ta wacce take ƙarasowa wajen fuskar ta ɗauke da murmushi , a shirye take tsaf , ba wata shahararriyar kwalliyar fuska tayi ba illa jikin ta da yake kiruf a rufe da babban mayafi tun daga wuyan ta da ya sha ado da tufafi irin na alfarma ,wanda ya amshi zubi da tsarin jikin ta na samɓaleliyar mace me zubin matan fulanin usul .
Janye idanun ta tayi daga cikin nasa kamar koyaushe da bata iya jurar ganin cikin idanun sa duk kuwa da tsawon shekarun da suka shafe a matsayin ma'aurata ,
Barka da zouwa Baban Yumna , da fatan ka isso lafiya ?
Lafiya mun same ku lafiya ? Yaya Yumna ?
Ga ta tana lafiya ,
Ɗan shiru suka yi kafin ya katse shirun da tambayar ta
Ina kuke da noufin zouwa da hantsi hakka ??
A ɗan ruɗe tace , zamu shiga fada gaishe da hajiya umma ,
Baza ku fita yanzou ba umma na tare da jama'a da wannan lokacin bani son idanun jama'a bisa ga kan ɗiya ta , ko dai ki bar ta ki tahi ke ɗai , ko kuwa ki bari da sanyin la'asar kun tahi tare .
Ko kusa baza ta so ƴar ta ta gifta ta kurkusa da shigifar gimbiya moumuna ba bare har ta taka ƙafafun ta cikin wani al'amari da ya gifta a tsakanin su me girma , wanda ya tarwatsa takaitatcen zaman daɗin da suka fara gudanarwa a tsakanin su , daga nan aka yi walƙiya kowa ya shaida kowa , yayin da daga lokacin ta fara bin irin takun gimbiya moumuna da nazari , nan ta fahimci dayawa daga cikin boƴaƴƴun fuskokin ta masu cike da abubuwan al'ajabi tare da sarƙaƙiya da baki yayi kaɗan wajen furta su ga wani har sai idan wannnan mutumin ya ga kome a idanun sa .
Hakan ya sa ta rufe kome ta haɗiye a cikin ta , ta kuma killace kan ta da ɗiyar ta daga gimbiya moumuna da ƴan barandar ta doumin ita ɗin ai gubba ce ga rayukan alhalin masarautar maraɗi !
Da sauri ta miƙa hannu tana ƙoƙarin amsar ƴar ta daga gare shi
Mun hakure zouwa yammaci kamar yadda ka faɗi mouna Biyamuradi .
Janye yumna yayi ya hana ta ɗaukar ta , a hankali ya kamo hannun tare da sarƙafe ƴan yatsun sa a cikin nata hannun yana jin yadda taushin hannun ke tado masa da yanayin da yake ta dannewa tsawon satika , " muryar sa tafe da amo marar ƙarfi yace
Mu tai ki ciyar da ni abounci na taho tare da yunwa me tsanani .
Ƙoƙarin zare hannun ta take tana satar kallon sashin gimbiya maimouna ,
Cikin sa'a idanun ta ya sauƙa akan gnala shugabar bayin sashin gimbiya moumuna ta na abunda yake goge gilashin falon gimbiyar ta ciki a zahiri , wanda tashin farko siyama ta fassara abunda take da ɗaukar rahoto
Toh Biyamuradi , amm...
Shitt
yace mata lokacin da yake jan hannun ta zouwa sashin sa kai tsaye da yumna saɓe kan kafaɗar sa ta dama tana ƙoƙarin ɗauke hular kan sa ,
Suka fara taku tare da masaniyar yau wajen ta ya kamata ya kwana a tsarin ƙwanakin girki .
Gimbiya moumuna wacce tun isar sa fada ta samou labarin zuwan sa , inda bata yi ƙasa a guiwa ba ta tashi shirin tarɓar sa ,
Ta tashi hankulan bayun ta da aikin gyara gida wasu kuma na haɗa mata ruwan wanka tare da fidda mata kayan da zata sanya a jikin ta ,
Zuwa shigowar sa gidan ta fito daga wanka ta fara shiri , yana dosar gidan saƙo ya iso mata , hakan ya sa ta miƙe daga gaban mudubi ta ƙarasa gaban babban window na ɗakin ta dake sama ta raba labulen biyu daga inda take ta hangi kome da ya wakana tsakanin sa da siyama .
Wani irin tuƙuƙi take ji yana taso mata daga cikin rai har tana jin ɗacin sa a maƙogoro .
Meyasa ne wankin hula ya kai ta ɗare har tsakiyar sa ?? Lamarin da suka yi hasashen yiwuwar sa a watanni zuwa
Shekara bayan zuwan ta masarautar maraɗi , sai ga shi shekaru har sun fara ƙoƙarin haurawa kirgen yatsu biyar ?? Wacce iriyar mummunar rashin sa'a ne gare su haka ?? Wanne sirri ne da yake boye cikin duhu da ya zamto shamaƙin da ya shiga tsakanin ta da cikar burin ta ?? Menene shi da ya wuce tasirin ƙarfin su ??
Tattare labulen tayi ta cukuikuye shi a tafin hannun ta tana jin kamar tayi girgiza ta fasa bango ta dira a sashin yarima youssouf ta kaddamar da manufar ta ..
Ranki ya daɗe kƴakya.....
Bata bari gnala ta ƙarasa kalmomin ta ba wacce ta shigo ta durƙusa daga bayan ta ,
Da hannu ta dakatar da ita ,
Ayi gaugawar shiryawa Biyamuradi abincin sa a aika da shi shiyar sa .,
Ke zaki miƙa abincin da kan ki daga nan kin kawo mi ni labari na lamarin da ya auku gaba gare ki .
Allah ya huci ran gimbiya ƴar sarkin nahiyar mu maigirma oumarnin ki shine abun bi .!
da shigar su sashin nasa da yake me matuƙar girma , da tsari tare da wadatar tsaftar da ta haifar da kyakkyawan yanayi a wajen ,
Ya zauna bisa ɗaya daga cikin kujerun falon nasa , yana sauƙe yumna kan kafafun sa ,
siyama wacce ta saɓule mayafin ta ta ajiye a gefe ta sunkuya tare da yin gurfano a gaban sa , cikin nutsuwa ta kai hannuwan ta tana kunce masa igiyar takalmin sa tare da zare masa shi a hankali ,
Ɗan kiɗan da wayar sa ta yi dake nuna alamun shigowar saƙo ya sa shi zaro wayar daga aljihun sa ,
Lokacin da take ƙoƙarin karɓe hular sa dake hannun yumna ta ƙi bada hular ,
Ki bar mata hular mana , kin ka sani ko ɗiya tayi gadon baban ta ?
Da murmushi bisa fuskar ta ta wuce sama domin ajiye masa takalman sa , ta zo ta fara yi masa shirin girki .
Saƙon gimbiya maimouna ne mai ɗauke da tsararrun kalamai na barka da zuwa ƙarshe take sanar da shi ta bada saƙo a kawo masa ,
Fita yayi daga wajen adana saƙon yana shirin ajiye wayar hoton da ya ɗauke su ɗazu ya bayyana a fuskar wayar,
Ƴan yatsun sa ya sa ya jawo hoton ya cika wayar ya na nutsar da idanun sa kan fuskar ta me ɗan haske kaɗan da take ɗauke da wani sirri me tasirin da ya zarce a ƙira shi kyau ,
fatar ta suɓul-suɓul babu wasu ƙurarraji bare tabbuna manyan idanun ta da yankan su yake a tsaye da ƙwayar baƙi na cikin su me girma ne sosai , suna da ɗaukar hankali ta yadda ko yaya ta juya su sai mutum ya gan su , har kullum yana dogon tunani akan son sanin me ya makanta su ??
A hankali yayi ƙasa da hoton zuwa kan bakin ta da haƙoranta suke a buɗe tana dariya ,
Tsintar kan sa yayi da murmusawa, ya kai babban ɗan yatsan sa yana shafar fuskar wayar daidai zagayen ɗan bakin nata ,
lokacin da ya tuno da yadda take haɗe fuska ta tsuke bakin , duk idan ta ji motsin sa a waje , ta takura kan ta ta gaza walwala ,,
Kiyi haƙuri fatima ni ma ba zaɓi na bane irin rayuwar da muke gudanarwa a tsakanin mu a matsayin ki ta iyalina ,girman laifi na ya sa na gaza yin wani yunƙuri , ni ɗin me laifi ne a gare ki da duk ranar da gaskiya ta bayyana wataƙila baza ki yafe min ba , hakan ya sa na jinkirta miki har zouwa lokacin da kome zai bayyana agare ki , da na tabbatar ranar ta na zouwa , lokacin kike da zaɓi na zama da ni ko bari na bisa ra'ayin kan ki ,
Kiyi haƙuri Fatima zahra ina jin kunyar ki .
Ƙwanƙwasa ƙofar da aka yi ya sa shi kai duban sa ga ƙofar tare da mayar da wayar sa cikin aljihu
Daidai da ƙarasowar siyama wajen wacce kalaman sa na ƙarshe suka sauƙa cikin kunnuwan ta ,
Suka yi sanadiyyar harɗewar takun kafafun ta tare da sa zuciyar ta yin tsalle .
Wacece fatima ? Wanne matsayi ne gare ta da har Biyamuradi ke neman afouwar ta ? Shin laifin me ya aikata mata ?
Ruɗanin da ta afkawa ya hana ta tsinkayar kalaman da yake mata sai da ya ɗan ɗaga muryar sa da ƙarfi .
Siyama ki buɗe kofar nan saƙon maimounatu ne ya iso ,
Ba tare da ta amsa ba ta taka tana nufar ƙofar , cikin ran ta damuwa goma da ishirin ta san sarai saƙon ko na menene, abunda maimounatu ta saba yi mata ne a koyaushe , shine yau ma ta maimaita .
Tana buɗe ƙofar tayi arba da gnala tare da wasu bayu biyu hannuwan su riƙe da manyan farantai da aka rufe su da tumaƙasa irin na alfarma ,
Ajiye faranta suka yi tare da yin gurfano a gaban ta ,
Ranki ya daɗe barka da fitowa ! saƙo ne daga gimbiya tace a shigar da kaɓaki ga maigirma yarima .
Fuskar ta a ɗaure ta ce
Ki je sashi na yanzu yanzu ki ƙira min Rakiya ku zo tare !
Da sauri Gnala ta miƙe
Ba ke ba .
Tace da kaushin murya
Ciki sauri ta koma ta tsugunna
Ke tashi ki je ki taho da Rakiya
Tana nuni da ɗayar baiwar .
Cikin ƙasa da mintuna uku sai ga su tare da wata yarinyar mace da zata iya zuwa sa'a ga siyamar ,
Ranki ya daɗe uwargijiya ta .
Rakiya ki ɗauko waɗannan farantan ki biyo ni da su ,
Ta furta haka tana juyawa ciki Rakiya ta bita ɗauke da faranti guda , kafin ta dawo ta ɗau sauran da ɗai ɗaya ta shiga da su ,
Tana gama shigarwa ta fito gami da jan ƙofar , tana iya jiyo lokacin da uwargiyar ta ta murza ɗan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 59 Chapter of 111