wannan mafi muni daga cikin su ba watau ,"luwaɗi," baya kuma son ta sani domin yana matuƙar son ta bai haɗa ta da kowacce mace ba cikin rayuwar sa ita take biya masa bukatar sa uwa uba ita ce silar arzikin sa tare da bazar ta yake taka rawa ," neman yara maza da basu kai ga balaga ba da yake yi a duk daren lahadi wayewar litinin wani sirri ne cikin rayuwar sa ,"
Dan haka a wannan karon cikin hakin da gajiyar kokawar da yake yi ya haifar masa , gami da tsabar mugunta ya ɗaga falmata a karo na takwas ya maka ta da kan katifar gami da sanya hannun sa ya danne mata baki , ya fara ƙokarin zare mata bujen ta da ɗaya hannun ,"
Bai ankara ba yaji ta gantsara masa wani fitinannen cizo a ɗan yatsan sa babba , wanda hakan ya sa shi sakin wani ihun azaba jin tana yunkurin gutsire mishi ɗan yatsa ,"
Da ɗaya hannun sa yayi amfani wajen kai mata maruka da duka ta ko'ina amma falmata ko gizau taƙi sakin ɗan yatsan da zuwa yanzu take jin gishiri-gishiri a bakin ta da ta tabbatar jinin sa ne ," ƙara nutsa haƙoran ta tayi da ya sanya shi ba shiri ya daina dukan ta ya koma roko cikin kuka akan ta sakar masa yatsa ,"
Bata sakar masa da yatsan ba sai da ta tabbatar ta jikkata shi ta inda ko ta sake shi jinyar raunin da tayi masa zai fara sannan ta sakar masa yatsan ta miƙe da sauri tana tofar da jinin da ya zuba mata cikin baki,"
Tana sakin sa ya tashi da gudu ya buɗe kofar banɗaki da yake cikin ɗakin ,'
Tana jin tashin muryar sa tare da ihu lokacin da ya buɗe fanfo yana wanke yatsan ,"
Bin bango ta fara yi da lalube tana neman hanyar fita duk kayan jikin ta sun yamutse , tsumman da take ɗaure kirjin ta da shi ya zazzago wanda hakan ya bawa kirjin ta damar tasowa ,
Sai dai duk yadda ta kai ga lalubawa ta gaza gano kofar bare ta buɗe ta sai kewayawa take yi cikin hawayen tausayin kai da take yi ," makanta mutuwar tsaye ,"
Ido jawur ya fito ya tsaya ta bayan ta yana kallon ta cikin ran sa yana aiyana irin azabar da zai ganawa yaron nan a daren yau ,"
Cigaba yayi da naɗe hannun sa da Bandage yana kallon yadda take ta laluben bango , chak ya tsaya da abun da yake lokacin da idanun sa suka fara bayyana masa ainahin surar ta ta ƴa mace ,'
Sosai ya ƙura mata ido yana kare mata kallo daga sama har ƙasa domin tabbatarwa ,"
Wata chafka yayi mata tare da haɗa ta da bango yana mai ɗaura hannayen sa akan kirjin ta ,
Zabura tayi ta angaje shi baya,
Dan ubanki daman ke mace ce ??
Shine aka kawo min ke a matsayin namiji ??
Kika bani wahala irin wannan har da yi min rauni ? ashe ma ungulu da kan zabo ce ? Me zanyi da macen titi ? Kuma ma ƙwaila ?
Dan uban ki yau zaki yabawa aya zaƙin ta , sai na wassafa ki ta yadda gaba baza ki sake yadda ayi haɗin baki da ke ba , ƴar yarinya da ke amma har kin san ta kan bariki , kin san yadda ake maguɗi ,
Bugun kofar falon da aka Fara yi da karfi shi ya sa shi dakatawa da maganar da yake yi ,tare da yin kasaƙe domin sauraro , ai kuwa ya tsinkayo muryar matar sa tana danna masa kira tare da cigaba da bugun kofar , wani irin zillo yayi cikin taraddadin riskar falmata da zata yi cikin ɗakin sa ,'
Diri-diri yayi yana neman abun yi ba tare da ya lura da falmata wacce ta fara kokarin kintsa kanta ta cikin shigar ta na maza ba,
Bugun yana tsananta tare da ƙarin fargabar sa juyowa yayi da nufin chafkar falmata ya tura ta cikin wardrobe Ya kulle domin ya san muddin matar sa tayi ido hudu da budurwa a ɗaƙin sa da daren nan kome zai faɗa mata baza ta yadda ba , bai kuma san wanne irin mataki zata ɗauka akan sa ba , da ya san ba mai sauki bane domin ya san kalar kishin ta na masifa dan haka ya gama yanke shawarar ko ta halin ƙaƙa sai ya rufawa kan sa asiri ko da kuwa zai kashe falmata ne,
Sai dai ga mamakin sa shirye ya ga falmatan tsaf yaro namiji kamar dai yadda ɗan liti ya kawo masa ita , wanda ya tabbatar a kallo ɗaya baza'a taba gane falmata ƴar budurwa bace ,
Wani ɗan sanyin daɗi ya ji cikin ransa ,
Dan haka ya matso kusa da falmatan
Dan uban ki ga mata ta ta zo tana buga min kofa , idan kika yadda kika yi wani abun da ya sa ta gane ke mace ce sai na kashe ki kin ji ko baki ji ba ??
Cikin sauri falmata take gyaɗa kan ta tana gwalalo ido jin kalmar kisa daga bakin sa wanda azabar da ya gana mata a cikin mintuna da suke ƙasa da talatin ya sa ta tabbatar tsaf zai iya sheƙe ta har lahira ,"
Ungo nan ya watso mata kayan sa masu datti da ya ciro su daga loƙo ,
ki riƙe su a matsayin garƙuwar ki da zata fidda ki gidan nan lafiya
Da gudu ya fita ya buɗewa matar sa da take tsaye daga bakin kofa tana ƙuta , tare da mamakin meye yake yi haka a ciki da bai jin bugun kofa kuma ta kira wayar sa bai ɗauka ba , ita ba kome ya kawo ta ba illah ihun da ta tsinkayo daga sashin nasa ," ta ɗaga hannu da nufin sake buga kofar ,karaf ya buɗo kofar
Yanayin fuskar sa kawai ta duba ta san ba lafiya ba , lafiya kuwa baban sadiq?
ta tambaye shi ,
Subahananlahi ta furta hakan tana mai riko hannun sa da ta gani naɗe da bandage kafin ta ja shi ciki tana tambayar sa cikin tashin hankali akan meye ya same shi , ' shi kuwa sai faman yamutsa fuska yake cikin alamun nuna jin zafin ciwon ,"
Kwantar da hankalin ki my dear ɗan ciwo na ji da wuƙa ,ya furta hakan yana me satar kallon kofar ɗakin sa cikin ransa yana zagin falmata akan me ta tsaya yi masa kuma cikin ɗaki ?
Fitowar falmata rungume da kayan da ta naɗe su da kƴar cikin daya daga cikin rigunan nasa , shi ya maida hankalin matar sa kan falmata ,'
Bin falmatar tayi da kallo lokacin da ta ga ta doshi jikin bango gadan-gadan tana shirin cin karo ,"
Kai yaro kai kuma daga ina da daren nan ?
Chak falmata ta tsaya lokacin da ta ji kafar ta ta zunguri garu ,
Juyawa tayi ga mijin ta wanda yayi kicin-kicin da fuska ,
Baban sadiq kana ganin yaron da nake gani koh dai gamo nayi ?
Cikin bagararwa yace wane irin gamo kuma bilkisu ? Yaro ne ya shigo karɓan kayan wanki ,?
Kayan wanki kuma ? A daren nan ?
Kuma naga kai kake kai kayan ka laundry da kan ka yaushe kuma ka koma bawa masu wanki , ? Tukun ma yaron baya gani ne naga yana bulunbutuwa ?
Bagarar da sauran tambayoyin ta yayi ya bata amsar tambayar ta ta karshe almajiri ne kuma makaho ," nuna masa hanyar fita daga falon , ya saki ƴar wata ƙarar da ke bayyana azabar da hannun sa yake yi ,da hakan ya tilasta bilkisu ta bar sauran tambayoyin ta tare da watsar da wasi-wasin da ya fara zuwar mata na ganin yaro a turakar maigidan nata har uwar ɗaki da dare ,'
Ta kama hannun falmata wacce tun da a garin neman hanya ta bige ɗan yatsan ta da kafar kujera ta raƙube ta tsaya daga wajen tana sauraran duk maganganun su ,cikin ranta ta gudurta muddin ta ga matar nan zata zalunce ta , zata fyaɗe mata biri har wutsiya ta faɗa mata gaskiyar zancen , idan ya so shi mijin nata ya kashe ta a gaban matar ta sa kamar yadda ya ce ,"
Ga hanya nan ka miƙe nan kar kayi kwana ,'
Ɗan turus tayi cikin kokonton
Kai yaro !
Chak falmata ta tsaya wacce har ta fara taku cikin sauri tare da hamdalar kubutar da ita da Allah yayi daga hannun wannan azzalumin mutumin da bata kai ga sanin sunan sa ba ,"
Waye ya kawo ka ? Ina nufin tare da wa kuka shigo gidan ?
Unn'umm'un tare tare da alhajin muka shigo shi ya kawo ni ," cikin inda-inda kalaman suke fitowa daga bakin falmata ,'
Shikenan tafi,"
Babu ko waiwaye falmata ta miƙa hanya , bata yi wata tafiya mai nisa ba ta fara tsinkayo tashin muryar ɗan liti da yake hira da wani , yana ta faman sheƙa dariya cikin salon maganar sa ," wata irin tsanar sa ta taso ta maƙure ta ," macuci azzalumi ta ambata a ranta ,'
Hangon ta da ɗan liti yayi ya sa shi miƙewa daga inda yake zaune akan bencin mai gadi suna hirar su ta duniya domin zamu ce ta tadda muje mu ,( yaƙin ruwa ya ci sakaina ,) shi ma maigadin tsohon ɗan iska ne wanda duniya ta gama kare masa ba tare da ya farga ba , duk wasu tsiyatakun da ubangidan sa yake yi ya sani , ya kuma san ɗan liti kawalin ubangidan sa ne , dan kuwa duk lokacin da ɗan litin ya shiga da yaron da ya kawo , nan yake zama a wurin sa yayi jiran fitowar yaron ,'
A ah kaga ɗan kachallarin Alhaji har ka fito ? Iyeeh har da kaya haka alhajin ya baka ,?? Inji dai baka yi masa gardama ba ?? Ka saki jiki ka ci tsokokin nama ka kora da ruwan tatattun ƴaƴan itatuwa yadda ya kamata ? Toh albishirin ka ɗan kachallari ? Kafin ka ce goro kawo kayan na riƙe maka ya furta hakan yana mai karɓe kayan hannun falmata ,"
Sati mai zuwa iwar haka kana nan na sake kawo ka ka dangwali arziki kayi buroshi da zuƙa-zuƙan cinyoyin kaza ɗan kachallari fiye da yadda kayi a yau,'
Ni bazan sake zuwa ba , bazan sake bin ka ba , ka maida ni gida ,' falmata ta furta hakan tana me rushewa da kuka
Wata ƴar iskar dariya ɗan liti ya kwashe da ita da ya sa falmata ƙaro sautin kukan ta wanda yake tabbatarwa da ɗan liti aikin gama ya gama a tunanin sa ,'
Tsawon dare falmata bata yi wani baccin kirki ba daga ta fara baccin zata ji ƙarar marukan da mutumin nan ya dunga yi mata , cikin ranta tana sake tsorata da mutane gaba ɗaya , abun da ta fahimta a ɗan ƙarancin shekarun ta shine mutane basu da kirki mafi yawan su azzalumai ne tana mace bata huta ba ta zama namiji ma bata tsira ba , sai dai cikin ran ta tayi niyyar boyewa yakaka abun da ya faru da ita domin ta huttashe ta shiga damuwa a dalilin ta , tasan daga lokacin da yakaka ta ji abun da ya faru baza ta sake samun nutsuwa ba har sai ta samo hanyar da take ganin ta bada kariya a gare ta , kwatankwacin wacce ta baro su daga sansanin su , a gare ta samun kwanciyar hankali tare da walwalar da take tsinkayowa daga muryar yakaka yafi mata kome , baza ta so tayi wani abu da zai Wargaza mata farinciki ba , hakan ya sa da a halin yanzun yakaka ta takura ta faɗa mata abun da ya sa ta kuka , taƙi bayyana mata haƙiƙanin gaskiya ta danganta kukan ta da tuno da mahaifan su da tayi ,
Kwanaki biyun da suka biyo baya sun yi su ne cikin takura , ita yakaka al'adar da take yi ita ta hana ta sakewa a matsayin ta na sabon shiga , dan haka duk a takure take jin kan ta gani take kamar kowa ya san halin da take ciki duk kuwa da cewa dai-dai gwargawdo samy baby ta wayar mata da kai tare da saya mata sabbin pad da pants,kuma zuwa yau da take kwanaki biyar da fara yi , ya fara jaa baya, ita kuwa falmata fargabar da take danƙare cikin ran ta akan irin matakin da ɗan liti zai ɗauka akan ta ne a lokacin da mutumin da ya kai ta wajen sa ya tabbatar masa da cewa ita mace ce ,
Sai dai a yau da ake kwana biyar da faruwar lamarin ta ɗan samu nutsuwar zuciya ganin har yau bata ji ko ganin wani sauyin da yake nuna mutumin nan ya gayawa ɗan liti wani zance ba, dan haka ta sake suka yi hirar su ita da yakaka da yagana waɗanda suke ɗan zagayowa su taya ta wanke-wanke , walwalar ta ta sauya zuwa taraddadi ne lokacin da ta ji muryar ɗan liti yana dannanawa madam saly kira ,
ahayye nanayee madam saly fito, fito , fito ki ji sabon bayani abun mamaki ciyawa da cin doki ,wai kamar mu a garin nan za'a nunawa barikanci , za'a yi mana ungulu da kan zabo ,? Chafɗijam , inji masu iya magana suka ce bar ganin ƙanƙantar allura karfe ce , yekuwa jama'a ku hallaro ku ji abun al'ajabi ango ya kwana da ƙunzugu ,
Da ɗai-ɗaya hankali mutanen wurin ya fara dawowa kan sa saboda tsabar ƙwarmaton sa hatta masu cinikin madam saly da suke cikin rumfa sai da suka ji yo shi wasu ma har suka tsallako suka zo ganin dal ,"
Liti yaya ne ? Yaya ne ?ya da irin wannan kiran haka ? Ta samu ne ? Ko kuwa ta guntso ne zata fesar , ? Kunne na tarwai ina jin ka bamu mu sha ," cewar madam saly wacce take ƙarasowa wurin tare da wasu daga cikin ƴan aikin gidan ,"
To wallahi yaran nan yaks da ƙawar ta tare da munafiki koh munafukar ƙanwar ta zan ce ? Yo abun ne ya sauya , ninke mu baibai suka yi suka buga mana stamp ɗin sakarkaru na gaya miki, "
Wani banzan kallo madam saly take sakar masa kafin ta jaa ɗan guntun tsaki ,
Ban gane ba ? Daman akan waɗannan yaran kake kwalla wa jama'a kira har da yekuwa ? , kai dai Allah wadaran ka dan liti
Tsiya ta da ke wutar ciki madam saly , toh na rantse da Allah kachalla dai mace ce , macen ma luntsumemiya kuma nunanniya , shine dan iskanci da kuturun munafurci yaran nan suka ce wani wai namiji ne , aradun Allah ma ni ban yadda da su ba idan ba turo su ɗaukar rohoto aka yi ba , atoh ki dai bincika ki kuma san abun da kike ciki kar sai kin baje kafafu ki ji anyi ramm da ke anyi sama da duwaiwan ki atoh , zamanin nan na yanzu ko inuwar ka baka sakankance da ita ba dan zata iya harɗewa ta shige cikin na makiyin ka idan kuka jeru, ji min duniya mai abun mamaki wai ƴan waɗannan ƙuya-ƙuyan yaran sun iya dabo-dabo da rufa-rufa , toh dan uban uban ku yau asirin ku ya tonu ,"
Duk maganganun da yake suna sauka a kunnuwan falmata wacce take duƙe a bakin fanfo da kuma yakaka wacce ta kawo kai domin shigowa ta karbi burkutu ta kaiwa abokan ciniki , dukkanin su tsam suka yi da jin kalaman ɗan liti , wannan fa shi ake kira an yanka ta tashi , take falmata ta fara yin hawaye , yayin da yakaka ta ɗaure ta cije tare da jaan ƙwanjin kare falmata ,"sai dai ayi wacce za'a yi wai bera ya zubda garin ƙyanwa ,"
Madam saly ce ta juya ga falmata bayan da ta gama jin zantukan ɗan liti ,
Kai kachalla zo nan
Sum-sum falmata ta taso tana laluben hanya ta sashin da taji tashin muryar madam saly
Haiyaratataa ni idan ba makantar taki ma ban yadda da ita ba , ni daman kullum ina shakkar waɗannan idanun naki da suke wural uwa na mujiya da tsakiyar dare ace wai bakya gani ??? Cewar ɗan liti wanda yake jijjiga ya dogare daga gefe ,"
Kai kachallah meye gaskiyar maganar da ɗan liti yake faɗa akan ka ? Tambayar da madam saly ta jefawa falmata wacce take durƙushe a gaban ta kenan , "
Madam karya yake min ni ban san kome akan abun da yake cewa ba ,"
Wata irin zaburowa ɗan liti yayi ya dako tsalle ya bangaje ƴan matan da suke tsaye daga gaban shi ,ya dire a gaban falmata ,"
Dan ubanki Alhaji basko zai miki karya ne ,? Toh idan kin ce karya ne ɗaga rigar ki aga kirjin ki , nace ɗaga rigar ki mu ga kirjin ki ƴar iska jaririyar ƴar bariki ,'
Toh kai kachalla ai sai ka cire rigar mu ga kirjin naka domin cire zargi cewar madam saly," sunkuyar da kai falmata tayi tana matsar ƙwalla
Koh kafin su farga ɗan liti yayi charaf ya kaiwa gaban rigar falmata chafka , baiyi wani jinkiri ba ya sa karfin tuwo ya balla baturan da suke jere gaban rigar , yana cewa
Dan uwar ki rigar uban waye ya saya miki ba ni ba ?? Yau sai mun ga karshen karya ,"
Da gudu yakaka ta karaso wurin ganin ana neman tozarta ƙanwar ta ayi mata tsirara cikin taron maza da mata ,"
Ƙoƙarin raba hannun ɗan liti da jikin rigar falmatan ta fara , tana cewa
Ɗan liti ka sake mata riga meye hakan ? Wai ina ruwan ka da harkar mu ,"
Wata dariya ɗan liti ya sake , kin ji koh madam saly nace kin ji koh ? Da bakin ta take ambaton ta a jinsin mata , shegu munafukai , yau me raba ni da ku sai Allah tun da kuka jawo min asara , yana gama faɗin hakan ya ingije yakaka tayi faɗuwar ƴan bori , kafin ta taso , ya sanya dukkanin karfin sa ya jijjiga falmata gami da keta mata riga , ya sanya hannayen sa duk biyu ya cisge tsunman da take ɗaure kirjin da shi ,ya murɗa hannayen ta tare da lanƙwasa su baya ya banƙaro kirjin ta gaba wanda hakan ya bayyana haliltar kirjin ta tsai a tsaye ,"
Wani irin guntun salatin da ba'a ƙarasa shi ba tare da shewa da ihu sune suka cika wajen daga bakunan mata da mazan da ke wajen , cewa suke wallahi chika ce , laaah ,
A toh idan har yanzu ba'a yadda ba sai na ɗaga muku ƙasan shi ma ku gani dan gaba kar a karkace a kuma sharo wata ƙaryar ace mata-maza ce gara a ga ƙarƙashin ,
Nan dai wasu suka fara ihu suna cewa a ɗaga su gani a ɗaga su gani
Da gudu yakaka ta taso tare da yi wa falmata rumfa da jikin ta idanun ta kuwa tuni suka fara zubar ruwa , cewa take menene hakan ?dan Allah kuyi hakuri ku kƴale ta , ƙanwata miskiniya ce makauniya ce , ni ce da laifi , ni nace ta koma shigar maza , kowanne hukunci zaku yi mata ku min a madadin ta ,' tana faɗin hakan tana warware ɗankwalin kan ta tare da rufawa falmatan da take risgar kuka , cikin tsokar jikin ta take jin idanun jama'ar da suke zagaye da wajen , cikin ran ta tana jin wani irin rauni da bata taɓa jin irin sa ba tabbas an cuce ta an tazorta ta matuƙa an tsaraita ta a gaban jama'a
Yagana ma matsar ƙwallar tausayin falmata take ,
Madam saly kuwa wani malalacin kallo take bin su da shi ,"
Yanzu daman dan uwar ki yaks ƙarya kuke min ? Toh kuwa yau yau ɗin nan zaku bar min gida ƴan iska maƙaryata , da sauri yakaka ta matso gaban saly ta shiga rokon ta akan ta taimaka kar ta kore su domin basu da kowa ,"
Da ƙyar da jibin goshi larki da hema suka sanya baki wurin taya yakaka bawa madam saly hakuri saboda tausayin yaran da ya tsirga musu , bayan sun ƙora ɗan liti wanda ya zama ziga-zigi yana sake tunzura madam saly ta kori su yakaka , ya dage akan cewa turo su C.I.D aka yi wanda hakan ke ruda madam saly , sanin cewa ita ba mutum bace mai gaskiya , sanna a cewar ta kewaye take da makiya ƴan hassadar ta .
Ficewa yayi bayan ya tabbatarwa yakaka duk inda kuɗi suke ta nemo ta biya sa kayayyakin da ya sissiyawa falmata domin shi bai yin asara koh ta sisin kobo , kuma kar falmata ta sake taka ko da kofar ɗakin sa ne , idan har kuwa ya gan ta a gaban ɗakin sa babu abun da zai hana ya kirɓe ta ,'
Toh yanzu da ku ka nace kar a kore su akan ku zasu dunga kwana su biyun ? Kun san dai ku ukun ma a matse kuke tamkar kifin gongoni , cear madam saly
Da sauri yakaka wacce har lokacin rungume take da falmata da take ta faman sauke ajiyar zuci akan kukan da ta sha , tace
Ni zan dunga kwana a kan benci cikin rumfa idan ya so falmata ta kwanta tare da su a ɗakin idan kin yadda ,
Sai da madam saly ta wurga mata harara domin har yanzu tana ɗan jin haushin su
Ƙya ce haka mana dan kun samu na ƙyale ku algungumai , ni dai ku kiyaye ni kar ku bari na sake kama ku da wani laifi domin gaba ko kun fi kuturu naci sai kun bar gidan nan , tun da kin zaɓi kwanan kan benci a cikin shagon toh ke kika sani sautun mahaukaciya , duk abun da ya biyo baya ki kuka da kan ki , kar ki ce ban faɗa miki ba ,
Ba tare da fargabar kome ba yakaka ta amince da zantukan madam saly cikin ran ta tana sa mata albarka ,
Wanene Alhaji basko ?? Aina kika san shi ? meye haɗin ki da shi ? Kuma ta yaya yasan cewa ke mace ce ??
Su ne tambayoyin da yakaka ta jerowa falmata lokacin da take taya ta shiryawa cikin ɗaya daga cikin kayan da take warewa take ajiyewa falmatan su ,
Ba tare da jinkirin kome ba falmata ta fayyace mata kome ,
Hawaye ne yake sauka bisa kumatun ta , meyasa mutanen duniya suke son zukatan su ?meyasa taimako domin Allah yayi ƙaranci meyasa zalunci ya yawaita , meyasa fasikanci ya zama mahaɗin rayuwar mafi yawan mutane ,??? Meyasa meyasa ? Ji tayi tsanar dukkanin mutanen da suke kewaye da duniyar ta ya kama ta idan aka ɗauke ƙanwar ta ,'
Nan gaba kar ki sake yadda da kowa falmata , idan na ce kowa ina nufin kowa ,! Kin ji ko ?
Ba tare da falmata ta hakiƙance da inda kalaman yakaka suka dosa ba ta amsa mata da toh ,"
Daga ranar yakaka ta koma kwanan cikin rumfar da suke sana'ar su ciki , yayin da idan kafafu sun yanke a wurin kamar sha biyun dare sun riga sun gama sana'ar su, zuwa lokacin duk ƴan iskan sun watse wasu sun shige ɗakunan su tare da abokan iskancin su sai ta haɗa teburan da suke gaban kujerun , guda huɗu ta shimfiɗa zanin ta akai tayi matashi da hannunwan ta tare da rufuwa da wani zanin , sai tayi baccin ta ba tare da tsoron duhu da shirun da wajen yayi ba ko kuma tsoron ƴan iskan da ka iya kawo mata farmaƙi , wurin kwanan ta na cikin ɗakin kuwa ta barwa falmata ,
A haka kwanaki suka fara miƙawa har yau da ake kwana na uku da faruwar lamarin falmata ta gagara sakewa dan kuwa tuƙuru ƴan matan gidan suke tsokanar ta , har suna cisge mata ɗan kwali , suna faɗin ta koma shigar maza ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Chapter 104
Chapter 105
Chapter 106
Chapter 107
Chapter 108
Chapter 109
Chapter 110
Chapter 111
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 111