ran Amarya Muhibbah zata tare yayinda juma’a ake bukin nad’in sarki Mahmood..
Fadah ta kacame gaba d’aya, matan masu mulki daga ta ko ina Zuwa suke, kama daga matan Su Talba Galadima Matawalle da dai sauran Hakimai, harta matar Baba Wambai tazo, Majidad’i kansa ya samu Mahmood ya risina gaba garesa ya basa hak’uri dan ya yarda idan Rana ta fito tafin hannu bata kareta, Zakaran da Allah ya nufa da cara ko Ana muzuru ko ana shaho toh fah sai yayi... Hassada taki ne ga mai rabo inji masu iya magana... Nan ya sanar da Mahmood d’in duk abubuwan da suka k’ulla masa shida Yazeed.. Ya kuma nemi gafara.. Mahmood yace bai tab’a rik’esa cikin zuciyarsa ba Allah yasa ya amfana da darasin rayuwa da ya d’auka bisa abubuwan da suka aikata.. Shi kuwa Ja’afar tsaresa da idanu yai yana fad’i a hankali daidai kunnen Majidad’in “Fadah bata marhaban da munafukai balle azzalumai, dan haka ka tabbata tuban gaske kayi ba tuban d’an muzuru ba dan idan na fahimci tuban d’an muzuru kayi.. Zaka amshi sakamako irin wanda ya dace dakai..!” Majidad’i ya d’an d’ago yana duban Ja’afar dake tsume da fuska yana dubansa shima.. Ubandoma ya dubguri k’eyar Majidad’i yace “Yarima yana magana amsa masa ake..! Hattara Majidad’i..!”
Majidad’i ya jinjina kai a hankali yace “In sha Allah Masarauta zata sameni da cika alk’awari.. Tuban k’warai nayi Yarima Ja’afar..!”
Ja’afar ya jinjina kai a hankali ba tareda ya furta komai ba...
Manyan masu sarautun gargajiya sai sanyawa ‘ya’yan Sarkin Albarka suke.. Tun ana sauran sati Tambura da algaita suke guguwa a masarautar... Ga duk wanda yasan Masarautar shekaru k’alilan baya ya kuma ganta yanzu yasan abubuwa da dama Sun sauya.. Wani ni’iman kwanciyar hankali da annashuwa ne zalla cikin d’inbin Masarautar...
A can b’angaren mata ma kowa ya hallara idan ka d’auke matan Waziri wanda abin kunyar da mijin su ya jaza masu ya hanasu shiga cikin mutane...
Yau ta kama laraba Washe gari ake saka ran gudanar da bukin aurensu itada Rankaidad’e... Tana zaune ana shafe tafin k’afafunta da lalle kaman yanda yake a al’ada, Umaima da Zahra suka shigo murmushi saman fuskokinsu... Zahra ta Ware idanu tana duban yanda ‘yaruwar tata ta k’ara shek’i da kyau a ‘yan kwanaki biyun da tayi a killace, tace “Kai Tia Wai Dama haka kikeda fitanennen kyau ne.. Black is gold, Kinga fuskarki kuwa.. Gaskiya Paa dole ya k’ara sadaki..!”
Umaima ta kai mata bugun wasa tana fad’in “Ja’irar yarinyar matar Baban naki ne abokiyar wasanki..”
Zahra ta d’anyi k’ara kad’an tana furta “Ouchh Aunty Umaima daga wasa.. Kuma ma ai Paa Yaya na ne ta wane b’angaren.. Ni daga yanzu ma Yaya Rankaidad’e Paapa angon Tia zanke kiransa..!” Harta da dattab’an matan dake zaune wajen saida suka nurmusa Umaima na kuma janyo kunnen Zahra guda.. Ita kaw Muhibbah shiru ta b’ace wajen tana jin wani bak’on al’amari tattareda ita, Wai bukin aurensu ake da Rankaidad’e... A tare Umaima da Zahra suka k’arasa gabanta suka duk’a, tausayinta sai ya kamasu... Umaima ta sanya hannu a robar lallen ta d’an lakata ta shafa mata a hanci tana mai furta “Be happy sister.. Coz you deserve all the happiness in the world..!” Muhibbah ta murmusa kad’an tana duban ‘yar uwar tata cikeda shauk’i... Zahra ma ta lakata lallen kad’an a yatsarta ta shafa mata a goshi tana furta “ Sé feliz hermana...!” (Ki kasance cikin Farin ciki ‘yar uwata.)
Murmushi take tana dubansu lokaci guda itama ta lakaci lallen tana k’ok’arin shafa masu suka mik’e suna zagaye kampacecen d’akin suna cewa su ba amare bane bazata shafa masu lalle ba.. Aiko nan taita binsu tana fad’in saita shafa masu suma.. Haka saida suka sa Muhibbah taita ‘yar dariya kafin suka k’yaleta.. Zahra da Umaima suka dubi juna suna ‘yar murmushi...
Muhibbah ta dubesu tana Ware idanu “I know you two are up to something again..!”
Suka murmusa a tare kana Umaima tace “Manyan bak’i muke tafe miki dasu..”
Ta d’anyi Jim tace “Manyan bak’i..”
Zahra ta jinjina kai tace “K’warai kuwa.. Wait..!” Ta isa tana mai yin iso ma bak’in..
Ga mamakin Muhibbah ba kowa bane face Meenatu aminiyarta ai ko Meenatu tana shigowa ta tafi ta rungume Muhibbah cikin murnan tsalle, lokaci guda take k’ok’arin saita kanta had’ida furta “Wayyo Rankidad’e tuba nake.. I just couldn’t hold myself..!” Muhibbah ta dungureta kad’an tana mai fad’in “Zaki sani ne... Kai k’awata naji dad’i da zuwanki zaki halarci bikina ashe..!” Meenatu tace “Of course I wouldn’t miss your wedding for any thing in the world k’awata...!” Muhibbah ta kuma rungumeta cikeda Farin ciki, nan kuma annurin fuskarta ya d’an ragu tana fad’in “Mommy fah, batazo ba..? She’s not coming koh..?!” Bata kai aya ba ta sinkayo sallaman Mommy k’awayenta guda biyu kuma aminanta na biyeda ita, Aunty Gudidi da Aunty Salma..! Su Gudidi sai rarraba idanu ake yawa mage ta fad’a talge.. Sai kwantar dakai take tana ganin abin kaman a mafarki Wai Muhibbah itace sarauniyar wannan Masarautar gaba d’aya...
SameenaAleeyou 📚
[10/6, 2:34 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*85*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Suka rungume juna itada Mommy, Ta d’ago tana duban Mommy tace “Mommy ashe dai zaki zo..?”
Murmusawa kad’an Mommy tai tace “Kin tab’a ji anyi biki babu uwar Amarya.. Kuma da irin wannan karramawa da Mai Martaba yayi min ai dole na amsa gayyatarsa koda kuwa Uwar Amarya bata zuwa Bikin d’iyarta... Sannan ni da kaina zan sakaki a lalle Hibbah am..”
Kunya ya d’an kamata sai kuma tace “Mommy Rankaidad’e ne ya tura maku katin gayyata..?”
Mommy ta murmusa tana kuma duban fuskarta tace “Komai ma ya tura Muhibbah, duk wasu abinda kika sani na al’ada na aure ya tura an raba kaf unguwa dangi na kusa dana nesa, inaga idan akwai wad’anda basu shaida ba bazai shige Yawale da iyalansa ba dan ni da kaina na hana a tura masa ko dan abinda yayi miki..”
Muhibbah ta d’anyi shiru tana mai sadda idanunta k’asa sanda Mommy ta ambaci sunan Yawale.. Lokaci guda Mommyn taci gaba da fad’in “Yanda yaso ya tozartaki Sai Allah bai nufi hakan ba.. Ashe ma Sarki ya aurar dake ba tareda ya sani ba.. Yanzu kaf unguwa labarin irin kayan bajinta na gani a fad’i da aka aika daga Masarauta ake ni kaina darajata da kimata ya k’aru a idanun mutane sabida ke Muhibbah.. Ga karramawa da aka min Sarki ya d’aga tawaga tun daga Masarauta suka tafi har can Masarautar Bauchi suka kuma yin wani zugan kana suka nufo gidana.. Shin mai yafi wannan dad’i Muhibbah.. Karkiso kiga d’aukakan da Allah yamin duk a dalilinki.. Allah dai ya baku zaman lafiya da zuri’a d’ayyiba..! Hak’ik’a kinyi dacen miji mai k’aunarki da ganin k’imanki d’iyata... Wanda har zai girmama Uwar rik’onki irin haka bama mahaifiyar data haifeki ba irin wannan miji abin alfahari ne,abin a rik’esa hannu bibbiyu ne Kinji koh.. Domin kuwa duk wanda zai daraja iyayenki shine mijin aure... Ki rik’i aurenki da kyau kinji d’iyata..!” Ta k’arashe cikin rawar murya yayinda Muhibbar ma hawaye ke ziraro mata... Kalaman Mommy duk Sai ya sanya jikinta yin sanyi...
Suka kuma rungume juna suna hawaye Mommy na fad’in zatayi kewarta sosai
Muryar Gudidi suka sinkaya tana duk’e wajen take furta “Rankidad’e nidai gafararki nazo nema.. amin aikin gafara.. Ki yafeni Gimbiya Muhibbah, wllhi duk abinda na miki sharrin shaid’an ne da kuma sharrin zuciya.. Hassada muguwar ciwo ce.. Hassada itace tamin jagoranci na aikata abinda na aikata... Nayi miki hassadan auren d’an k’awata wanda a baya naso ya auri d’iyata bai aureta ba har tayi aure.. Naji hassadan ya auri tsintacciyar mage irinki wacce batada asali balle tushe ashe ba haka abin yake ba.. Sai gashi hassadan da na miki na taya Yawale wajen ganin mun durk’usar da rayuwarki ashe d’aga darajarki mukayi ba tareda mun sani ba.. Na yarda da hausan nan da ake cewa Hassada ga mai rabo taki ne.. D’an hakin daka raina wataran shi zai tsone maka idanu.. zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzuru ko ana shaho sai yayai... Idan rana ta fito tafin hannu bata tab’a kareta..! Tabbas mun miki hassada ya kaikiga alkhairi.. Munso nisantaki da Duniyar ahalinda kika girma taredasu suka maye gurbin ahalinda kika rasa daga farko ashe mun mik’aki ma ahalinki na jini ne bamu sani ba... Munso ki k’ask’anta da muka aura miki wannan mutumin ashe darajarki muka d’aga ba tareda mun sani ba.. Gimbiya ki yafe ni kimin rai ki yafe ni... Murja taso hanani zuwa amma na dage sai nazo na nemi afuwarki..! Ki yafeni Gimbiya Muhibbah..!” Ta k’arashe tana k’ok’arin kamo k’afar Muhibbah wacce tuni ta duk’a ta kamo hannayen Aunty Gudidi, tana girgiza kai take fad’in “A’a Aunty ni ban tab’a rik’eki cikin zuciyata ba.. Ked’in tamkar uwace a gareni domin kuwa ked’in k’awar Mommy ce.. Allah ya yafemu gaba d’aya...”
Cikin tsananin kuka Gudidi ta rungumo Muhibbah tana fad’in ta cika mai kyakkyawan zuciya.. Mommy da Aunty Salma suka share hawayen da ya gangaro masu suma.. Daga bisani Muhibbah ta samu ta gaisa da Aunty Salma itama ta nemi yafiyarta dukda cewa duk abinda sukayi ba yin kanta bane Gudidi ce ta tilasta mata.. Daga nan kuwa suka k’ume a d’aki itada k’awarta Meenatu tana labarta mata yanda abubuwa suka kasance bayan aurenta da Bak’on Buzu... Gashi yanzu tinda labari ya karad’e unguwa Sarki take aure kowa har son sake ganinta yake, harta ita kanta Meenatun a halin yanzu wani matsayi ta samu wajen K’awaye dashike itace aminiyarta.. Rayuwa kenan, duniya rawar ‘yanmata na gaba Sai ya koma baya, na baya ya dawo gaba... Yau ga Muhibbah da har cikin k’awaye ana k’yamatar sabida rashin cikakken asalinta sai gashi yanzu har ana tsere tseren rab’an makusanta ta bama ita kanta ba.. Shiyasa sam raina d’an adam baida alfanu bakasan mai Allah ya aje wajenba shi da ya halicci kayansa.. Allah kasa mu dace duniya da lahira.. Ameen!
**
A can Bauchi kuwa tun bayan ficewarsu Mommy Ansar ya shirya tsaf ya nufi gidan surkinsa Yawale bayan gudanar da sallar la’asar, Sosai yaci gayu cikin shiga Ta kamala, jampa harda hula shida ba gwanin saka manyan kaya ba... Baffah Yawale ya fito yana Washe baki yake furta “A’a Yakubu dama kaine tafe..?”
“Eh Baffah ni ne.. Mun sameku lafiya..?” Ya k’arashe yana duk’awa cikeda girmamawa yau d’in yake gaida Yawale..
Yawale yaci gaba da goga karan asuwakin dake bakinsa ya fuzar da tuk’an kana yace “shine baka shiga daga ciki ba ka tsaya daga nan saikace wani bak’o..”
Ansar ya murmusa yace “A’a Baffah ai nan d’inma yayi.. Ai akan hanya ma nake..!”
Baffah yace “Au toh toh..! Inji dai ba ja’irar yarinyar nan Hameedah ce tai maka wani abin ba..?” Yai maganar cikin fad’a..
Girgiza kai Ansar yai yace “A’a Baffah Hameedah batai min komai ba... Tafiyar dama takace..!”
Yawale ya kuma Washe baki ganin yanda sirkin nasa yaci gayu gashi yace tafiyar tasa ce, toh kodai wani babban kyauta zai masa..? K’ila ma gida ya sai masa... Zai masa irin nasu na yaran zamani yayi masa surprise.. Yaci gaba da Washe baki yana furta “Toh toh toh Allah sarki.. Wato dai tafiyar tawa ce..?”
Ansar ya jinjina kai a hankali yana mai bud’ewa Yawale marfin Mota yake furta “Muje Baffah babu lokaci..”
Yawale ya shiga tofar da tuk’an aswakin da yake goge hak’waransa dasu yana furta “Toh Toh ai kuwa dai Babu lokaci.. Ku likitoci lokacinku ai a k’ayyade yake.. Toh Wai nace ko zan shiga naima Innar taku sallama..?”
Ansar ya girgiza kai yace “za’a Baffah ai ba sai ka mata sallama ba, muje kawai...!” Ya k’arashe yana mai kuma hangame masa marfin motar..
Yawale ya rik’e mota ya shige yana furta “Kai kaji Mota mai taushi kaman a saman auduga nake..!” Yai maganar yana d’an tsalle daga zaune saman kujerar... Sanyin AC ya dake sa yace “Allahu Akbar! Kai kaji Ni’ima kaman a turai.. Yo irin Ni’ima ai bazakso a isa yanda za’aje ba Yakubu.. Kai Yakubu kana hutawa fah..”
Ansar da idanunsa kega kwalta yace “Is the reward of my hard working Baffah..”
Yawale yace “Na’am mai kace Yakubu..?”
“A’a bance komai ba Baffah.. Nace tafiya mai d’an tsawo zamuyi..!”
Yawale ya kuma wage baki yace “Ai babu komai ni dama yau d’in babu yanda zanje... Yau ina mahaifinka yana raye yaga yanda Ka zama.. Allah sarki d’anuwna ba rabon yaga gurmanka ba..”
Gaba d’aya ya cika masa kunne lokaci guda ya murd’a radio yana fad’in “Baffah kaji radio kasan ba’a rabaku da ita..”
Daga haka bai kuma bitakan Yawale ba saima maida hankalinsa ga yuk’i da yayi.. Yawale Sai maganarsa yake shi kad’ai k’arshe dai har bacci ya soma d’aukansa basu isa yanda zasuje ba..
**
Kaman sauk’an aradu haka Raheemah dake asibiti wajen Yazeed ta tsinci zancen, sai huci take tana zagaya d’akin, tanata k’ok’arin neman layin Ansar amma bai shiga.. Ta buga tsuka tana fad’i a fili dole ta tafi Masarauta taje ta tsayar da wannan auren koda za’a mutu ne...
Muryar Yazeed Ta sinkayo cikin tsananin jinya yana fad’in “Please call me Mahmood and his wife... Dan Allah ki kira mun su...!”
Raheemah ta dubesa da mamaki tace “Mai zaka masu... Ina ruwanka dasu.. Ko bakaji cewa bukin aurensu had’eda nad’in sarautar Mahmood ake ba..?”
“Ki kira min su Raheemah..!” Ya kuma fad’in cikin rawar murya..
Raheemah ta girgiza kai cikin rashin yarda da abinda takeji “Yazeed mai zakaida mutanenda sune sanadin kasancewarka a asibitin nan.. Mai zaka ce masu..?”
Idanunsa na duban sama hawaye na ziraro masa yake furta “Just call them, Ina matuk’ar son Nayi magana dasu..Please ki kira min su, kimin wannan alfarmar..”
Raheemah ta sauk’e ajiyan zuciya a hankali had’ida jinjina kai.. “Fine zanyi yanda kace idan haka zai saka Farin ciki...”
Yazeed dake hawaye ya furta “Na gode..!”
Raheemah ta kuma dubansa cikin tsananin sanyin jiki Wai yau Yazeed ne ke godiya.. Ikon Allah kenan..
Tinda ta baro asibitin haka ta nufo Masarauta jikinta a matuk’ar sanyaye, saidai tinda ta iso Masarautar jikinta ya kuma yin sanyi ganin d’imbin Al’umman dake cikin Masarautar, ga algaita nata tashi ga Dogarai sai wasa Sarki da amaryar suke wacce itama amaryar sarkin d’iyar sarauta ce gaba da baya.. Gwiwoyin Raheemah suka kuma yin sanyi, sanda ta isa sashen Gimbiya Zeenat ta tadda ita kanta Gimbiya Zeenat d’in bata k’asa bata sama.. Sai kai komo Kuyangi suke a sashenta ana had’a kyautttuka na bajinta, na sarki daban na matarsa daban na mahaifiyarsa daban.. Baki sake Raheemah Ke dubanta yanda take bada umarnin inda za’a kai kyauttukan wanda aka rurrufesu saman manya manyan parantai masu ruwan zinari an rufesu da manyan k’yalle masu d’aukan idanu kaman yanda sukeyi a al’ada lokutan auratayyansu...
“Aunty kema murna kike da auren..?!” Raheemah ta tambaya jiki a sanyaye..
Gimbiya Zeenat ta dubeta galala tace “Bak’in ciki kike so nayi.. Mutanen da suka mana halacci, yau da sunso bayan irin k’ulle k’ullen da mukai cikin Masarautar nan da sun koremu daga cikin Masarautar nan...Amma basuyi ba suka amshe mu hannu bibbiyu... Yau ko Masarautarmu kinaji kina ganin wulak’ancin da suka mana a lokaci aurenki sai gashi su Sun amshe mu Sun mance duk abubuwan da mukai a baya.. Ke nayi bak’in ciki na mai bayan wanda Allah ya riga ya d’agasa kai baka isa ka karyasa ba.. Ya kamata ki d’auki darasi cikin abubuwan da suka faru a Masarautar nan... Yau Ina Giwa da ahalinta..? Babu su kaman an shafesu a doron k’asa wasu ma sun fara mancewa dasu tun basu bar duniyar ba.. Toh ita rayuwa haka take, abinda ka shuka shi zaka girba.. Kiyi wa’azi ma kanki Raheemah, kiyima kanki karatun ta nastu tin kinada ikon yin hakan... Idan kuma rikici zakici gaba da janyo min cikin Masarautar nan toh gaskiya banida zab’in da ya shige na sallameki daga cikin Masarautar nan.. Ko ki tafi kibi mijinki can b’angaren Bayi kokuma ki koma can Masarautar mu wanda nasan bayan abubuwan da suka faru da k’yar idan zasu amsheki...”
Baki sake Raheemah ke dubanta hawaye na gangaro mata “Aunty ni zaki kora cikin Masarautar nan..?”
“K’warai kuwa idan dai fitina zaki jazamin... I won’t hesitate to throw you away.. Dan haka gwara tun wuri Ki zaba, ko ki natsu ki zama mutumiyar kirki ko ki kama gabanki..!”
Tana ida fad’in haka tasa kai Ta nufi d’aki yanda k’awayenta Ke jiranta, sune su keta tayata shirya kyaututtukan...
Raheemah ta zauna dirshan tana matsan k’walla, yau itace Aunty Zeenat take cewa zata koreta daga Masarauta kaman wata shara.. Lallai ta yarda rayuwa ta sauya... Da k’yar ta Iya mik’ewa ta fice ta nufi Sashen Gimbiya Turai...
Tana isa ta tadda Hadimai masu kai komo a sahen Ta shiga tambayarsu ina zataga Muhibbah..
Hadima guda d’aya Ta dubeta sama da k’asa kana tace “Mai kikace..? Gimbiya Muhibbah ce kike zare Sunana ta babu wani girmamawa..?!”
Raheemah dake sakin huci tace “A wajenku ne take Gimbiya.. Nida Muhibbah ‘yar lek’en asiri na santa kuma dashi zan kirata..!” Bata kai aya ba Hadima guda ta matso zata d’auketa da mari, wacce take gefe ta dakatar da ita... Hadimar tace da kin barni na wanketa da mari dan batada wani maraba damu matar Bawa ne a cikin Masarautar nan, matar Yazeed ce..!”
Dukda hawaye da suka ciko idanun Raheemah sabida wulk’anci da wad’annan Hadiman suke mata, bai hanata hura hanci tana nunasu da yatsa tana fad’in “Zaku sani.. Duk sai kun yaba wa aya zak’inta zakusan kun shiga hurumin da ba naku ba k’ask’antattun bayi kawai..!”
Hadiman basu daina bata amsa da fad’in batada wani maraba dasu d’in ba..
Umaima da Zahra ne suka taho zasu shige sunci uban gayu irinta yaran masu mulki wanda kallo guda zaka masu kaso sake kallonsu nan suka tadda Raheemah na rikici da wad’annan Hadiman...
Umaima ta katsesu da tambayan ba’asin abinda Ke faruwa..
Hadima guda d’aya tace “Rankidad’e Wai wannan matar Bawan ne tazo nan zatai rashin kunyawa Gimbiya kuma Giwar Masarautar nan matar Amale ...Shine muke son koya mata tarbiyan Bauta tunda itama cikinmu zata shigo yanzu, ai Bawa take aure..”
Harga Allah yanda Hadimar Ke magana taso baiwa Umaima dariya.. Amma tai k’ok’arin saita kanta sanda ta sinkayo muryar Raheema tana fad’in har abada bazata tab’a zama jinin Bauta ba... Umaima tai alamawa Hadiman cewa su tafi su basu waje su barsu da Raheemah.. Babu musu suka risina sukai yanda Umaima tace...
Umaima ta dubi Raheemah tace “Kiyi hak’uri da abinda Hadiman nan sukai miki, Kinsan...”
Katseta Raheemah tai da fad’in “Where’s Muhibbah.. I need to speak to her right this instant..”
Umaima bata kaiga bata amsa ba Zahra Ta k’araso gabanta rik’eda kunkumi.. Tana duban Raheemar daga sama har k’Asa lokaci guda take furta “Ba ko wace shara bace take iya ganin Sarauniya kai tsaye.. Dan haka bazaki samu ganinta ba, Ki b’ace a nan kafin na saka wad’ancan Hadiman su b’atar dake da k’arfin gaske..!” Ta k’arashe tana ware manyan idanunta..
Zuciyar Raheemah taci gaba da tururi, ta yunk’ura zata cakumo Zahra take fad’in “Ke yarinyar nan wllhi yau sai na cire miki rashin kunyarki tsaf naga gatanki dan ko Ubanki bazai iya k’watanki ba...!”
Umaima tai saurin shiga tsakiya, yayinda Zahra taci gaba da fad’in “Ya riga ya miki nisa nisanda sai gani daga nesa... Saidai Ki k’are da auren Bawa..!” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta...
Umaima ta girgiza kai tace “Raheemah ki tafi kawai, bazaki samu ganin Muhibbah ba.. Just go please..”
Zahra ta kuma katseta da fad’in “Har sai kin rok’eta Sis..? Ai kawai wad’ancan Hadiman zamu sa suyi mata bugun surfe a turmi...! Zaki b’ace ne ko sai na kirasu..?” Zahra ta kuma fad’i cikin daka tsawa wanda saida ‘yar muryar tata ta firgita Raheemah.. Babu shiri ta juya da baya tana jin zuciyarta na mata wane irin d’aci...
Tana shigewa Umaima ta dubi Zahra tana girgiza kai, lokaci guda kuma suka tintsire da dariya a tare musamman da suka dubi yanda Raheemah Ke buga sauri tana waige waige tsoron kar hadiman nan su capkota...
Zahra ta tab’e baki tace “Allah dai ya ceci Paa wannan matar a naira goma aka baka ita an cuceka wllhi.. Can ta k’arata wutsiyar rak’umi yayi nesa da k’asa Paa d’ina ya d’ara ajinta.. Saidai a k’are a fannin Bayi..!”
Umaima Ta janyo hannun Zahran tana fad’in “Yarinyar nan bakida da Dama, ni ko shige muje Meenatu naga missed call din Meenatu nasan yanzu haka Sistu Ke nemata..”
“An gama Rankidad’e..!” Zahra ta fad’i harda ‘yar risinawarta... Suka kuma murmusawa a tare kana suka shige...
**
Yamma Lis suka iso bayan Yawale ya gama baccinsa, yaji Ac yasha bacci harda su miyaun bacci...
Ansar na ida parking bai tashesa ba saida ya ciro wayarsa yai making call yana fad’in gasu nan sun iso... Yana zaune gefe yana duban Yawale dake ci gaba da baccinsa harda su gwarti yanda kasan wanda ya kwana bai bacci ba... Jim kad’an wata Mota bak’a k’irar corolla ta iso tai parking gefe.. Ansar ya d’an bibbigi kujerar da Yawale yake bisa wanda har kwantar masa da kujeran Ansar yai dan yaji dad’in yin baccin... Ya bibbigi kujerar yana furta “Mun iso Baffah..”
Yawale ya mik’e zaune da k’yar yana mutsuka idanunsa wanda har lokacin da sauran bacci ciki.. Lokaci guda yake furta “Mun iso Yakubu...Oh Yakubu wannan wane irin gida zamuje da sai yanzu muka iso.. Kodai Habuja muka taho zaka yanka min tikin kujerar Makkah na sauk’e farali bana..”
Ansar bai amsasa ba sai bud’e masa marfin Mota da yayi yace “Baffah gasu nan..!”
Ai a d’ari Yawale ya kuma ware idanunsa yana sake murtsukasu ganin k’artai da yayi tsaye bisa kansa sun rurrufe fuskokinsu da bak’ak’en masks...
Jiki na rawa Yawale ya soma furta “Kalu Innalillahi.. Yakubu mai zan gani..? Ina ka kawoni..? Su waye wad’annan..?!”
Ansar yace “Baffah ba kud’i kake so ba shiyasa ka saida Muhibbah, Toh ai wad’annan da kake gani sunji labarinka kana saida yaranka da sunan aure shine suka taho suna nemanka, sud’in masu cinikayyan bil’adam ne.. Da suka sameni nace ‘ya’yan Naka sun k’are dan Ta k’arshen kenan ka aurar min shine suka bani kud’in kanka mukayi cinikin kanka dasu.. Yanzu haka zan kaima Innah kud’in kanka tinda da dai ace ka saida sauran yaranka mata k’anana gwara ace babu kaid’in.. Gwara a sayar dakai.. Yara kuma k’annen Hameedah zan rik’esu in sha Allahu.. Amma ka gama saida Bil’adama Baffah..” Ya k’arashe yana fad’in ku d’aukesa..
Cikin kuka had’ida tsananin tashin hankali Yawale yake fad’in “Kamin rai Yakubu.. Nifa k’anin mahaifinka ne..! Kuma ita wancan yarinyar ai ba jininmu bane, Kai kana tunanin zanyi haka ma ‘ya’yan ciki na ne..! Dan Allah ka rufa min asiri dama akanta kawai nayi haka kuma bazan sake ba..!” ya k’arashe yana kuma zillewa had’ida daka tsalle yana son k’wacewa daga hannun mutanen...
Ansar ya dakatar dasu ya dubi Yawale yace “Auho sabida ba ‘yarka bace shine ka zab’i ka cutar da ita koh.. Ka bayarda ita ga mutanen da baka San daga duniyar da suke ba ka aura ma d’iyarka saurayinta koh..? Toh ai d’ah na kowa ne Baffah.. Muhibbah d’iyarka ce tinda kaine alwalinta.. Kawai kaje Allah yajik’anka Baffah.. Allah yasa k’arshen wahalan kenan.. kar ka damu zan kula da iyalanka in sha Allahu..! Ku tafi dashi..!” Ya k’arashe yana kuma masu umarni..
Yawale yaci gaba da tsalle yana kokawan k’wace kansa yake fad’in “Kamin rai Yakubu.. Kaji k’aina Yakubu.. Wllhi na tuba.. Na tuba bazan sake ba..!” Inaa tuni gardawan mazan sun jefa Yawale cikin mota mai lullub’e da tint..
SameenaAleeyou 📚
[10/9, 1:10 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*86*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Gefe ya koma yanda Turaki Ke tsaye yana dariyar Baffah Yawale da Dogaran da suka b’adda kama suka sauya tufafi harda rufe fuskokinsu da masks... Turaki yace “Gaskiya Likita baka kyautama surkinka ba.. Ya zaka sake had’a idanu da d’iyarsa..?”
Ansar ya murmusa kad’an yace “Mai Sarauta kenan, ai ni nasan halin Baffah tinda tin ina k’aramin yaro Babana ya rasu.. Babu irin karan tsaye da Baffah baiyiwa rayuwata data mahaifiyata ba duk akan abinda Babana ya bari, ba don Allah ya rufa asiri Mahaifiyata tsaye take kan k’afafunta ba wajen neman abinda zata rufa mana asiri da yanzu Allah kad’ai yasan yanda rayuwata zata kasance sabida Yawale ya handame duk wani abinda mahaifina ya bari da ka sani...”
Turaki ya girgiza kai yace “Ai wasu dai basu san illan cin dukiyar maraya ba, kuma k’alubalen da yanzu muke fama dashi kenan.. Wani yana Allah Allah nasa ya mutu ya hau kan dukiyar yayi babakere kuma karkaji da Wai idan ya cinye dukiyar nan bazai taimakawa marayun ba, basusan cewa wuta suke ci ma cikinsu ba..”
Ansar yace
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 61 Chapter of 65