Yarima Yazeed... Toh amma wani hanzari ba gudu ba... Shin kana tunanin Masarauta zata amince ta dawo da Al’adar da aka jima da banning d’inta, Al’adar da aka jima da kasheta a wannan masarauta tamu...?!”
Gajeren murmushi Yazeed yai “Kadai muyi k’ok’arin kawar da Mahmood a tsakani duk abinda zaizo daga baya mai sauk’i ne.... Partners..?!” Ya k’arashe yana mai mik’a masa hannu alamun musabaha....
Majidad’i ya mik’o masa hannu sukai masabaha yana mai jinjina kai yake furta “Partners..!!”
Daga nan sallama sukai da Yazeed yanda Yazeed d’in ya kirawo abokinsa Zayyad yazo ya d’aukesa dan tuni Majidad’i yayi tafiyarsa bazasuso a gansu tare ba...
Zayyad na k’arasowa da mamaki yake duban Yazeed sanda ya bud’e marfin mota ya shige “Rankaidad’e Wai mai ya faru ne... What really happened... Why are you here all alone... Ina motarka, Ina Hadiminka...?!”
Ko tambaya guda Yazeed bai amsa ba sai ci gaba da sakin murmushi da yake lokaci guda yake furta “I’ll soon get rid of one of my major problems...!” Ya k’arashe yana sakin murmushin nan nasa....
Zayyad da tuni ya soma driving murmusawa yai kad’an yana furta “WOW! This calls for celebration Your Highness... Fad’a min ina zamuje muyi celebrating...?!”
D’an dubansa da wutsiyar idanu Yazeed yai ba tareda yace komai ba... Zayyad yaci gaba da fad’in “I guess ka sami kan yarinyar nan ne dataci maka mutunci ko kuma ka samo hanyar da zakai ka fitar da Mahmood daga masarauta...!”
Dubansa da wutsiyar idanu kana yace “Abokina na yarda ka sanni sosai yanzu kam... Idan na zama sarki komai mai yuwa ne sannan ne zan rama abinda tai min don bataci banza ba... No one messes with Prince Yazeed AbdulJabbar..!” Ya k’arashe yana sakin murmushi sanda yake tuna kalan wulak’ancin da zaiwa Muhibbah muddin ya zamto Sarki... Sai ta gwammaci dama batazo duniya ba da irin wulak’ancin da ya tanadar mata...
Zayyad na tambayarsa destination ko answer sa bai ba sai sakin murmushin mugunta da yake ci gaba da yi a hankali.... Sanin Yazeed d’in bazai amsasa ba ya sanyashi yin shiru da bakinsa ya nufi shisha spot d’insu da suka saba zuwa...
**
Waziri ya gama had’a kan ‘yandabansa cikin dare ya basu umarnin su shiga Gidan Wambai su nemo k’undin nan yanda ya shiga ya fita, idan ta kama su tone k’asan gidan ne su tone su ciro masa k’undin nan duk yanda za’ai....
Ya kwance bakin rawaninsa ya nunawa shugaban exactly kalan jakar fata da k’undin ke ciki Wanda zasu d’auko masa....
Shugaban ‘yandaban ya amsa ya juyata ya k’are mata kallo kana ya risina yace “An gama mai girma Waziri... Idan cikin tandu take sai an d’auko maka ita...!!”
Waziri yace “Yauwa haka nake sonji... Kuyi dik yanda zakuyi ku d’auko min wannan jaka sannan Koda wasa kar ku bari a kamaku, kuma kada ku bar wata alama da zata nuna cewa Waziri ne ya turoku...!”
Suka jinjina kai suna masu furta an gama Mai Girma Waziri..!
Ubandoma dake lab’e bayansu murmushi yai dan yasan tinda wad’annan ‘yandaba ba ma’abota sarauta bane bazasu fahimci yanda Wambai zai aje wannan k’undi cikin sauk’i ba, dan haka zai k’yalesu su gama dube dubensu har su fice sannan ya shiga ya d’auko k’undin cikin tsanaki yakaiwa Giwa da sharad’in mallaka masa ‘yanci...! Ya saki murmushi yana mai gyara zaman layarsa da zai danna dan ya b’ace da zaran yaji alamun za’a kamasa...
Hakan ce kuwa ta kasance tuni ‘yandaban Waziri sun isa gidan Wambai Ubandoma na biye dasu ba tareda saninsu ba....
Gidan babu kowa sai ma’aikata, ba tareda b’ata lokaci ba suka kame ma’aikatan gaba d’aya suka d’auresu suka kullesu a nan D’akin Maigadi... Tuni suka shiga suka soma bincikensu... Sun kwashe kusan awanni biyu suna wannan bincike babu k’undi babu alamunsa... Haka suka wargaza gidan gaba d’aya sukai d’add’aya da komai amma babu k’undi babu alamun k’undi...
K’arshe haka suka hak’ura suka fice, ogansu ya kirawo Waziri yana mai sanar dashi Rashin sa’an da sukai...
Suna ficewa shi kuwa Ubandoma ya shigo ya soma nasa binciken musamman da yaji basu dace ba...
Waziri ya sanar da shugaban ‘yandaban nasa da suyi maza su fice daga gidan kafin azo a kamasu, daga nan Fada ya nufa wajen Giwa dan dole taji wannan batu cewa dik yanda akai Bak’on Buzu ya rigasu isa wajen Wambai, ya tabbata wannan mutumi bak’on Buzun shine ya amshe k’undin nan daga wajen Wambai.. Ya zama dole su zak’ulo waye Bak’on Buzu kafin Mahmood ya rigasu sanin ko wanene Bak’on Buzu....!!
Majidad’i yasha mamaki sanda ya shigo gidan Mahaifinsa ya tadda mai gadi da ma’aikata rufe nan d’akin Maigadin sunsha d’auri... Take tunanin Bak’on Buzu ya fad’o masa... Babu shiri ko takan mai gadin da ma’aikatan baibi ba ya fad’a cikin gidan a guje, yasan duk wanda ya shigo gidan ba b’arawon gaske bane akwai abinda ake nema ne wajen mahaifinsa kuma ta haka ne kawai zai capke wanda keda alhakin ciwon mahaifinsa....!
Ya zaro takobinsa ya nufi cikin gidan cikin sand’a...
Ubandoma dake faman bincike kaman b’era sai k’wak’ule k’wak’ulen rami yake sam bai aune da shigowar mutum ba sai jin sauk’ar takobi yayi a wuyarsa ana furta “Mik’e ka nuna fuskarka..!!!”
Muryar Majidad’i ya daki dodon kunnuwansa...
Take jikin Ubandoma ya d’auki rawa, karkarwa kurum jikinsa keyi ga gumi dake keto masa... Ya kasa tashi ya kasa d’ago fuskarsa da tuni ya jik’e da gumi...
Majidad’i ya capko wuyarsa da k’arfin gaske yana k’ok’arin d’agosa.. Daidai wannan lokaci Ubandoma ke kokawan danna layarsa saidai ga tsananin mamakinsa ko gizau layar tak’i dannuwa....
Majidad’i ya kwashe da muguwar dariya sanda layar ta fad’i k’asa... K’afa yasa ya shura layar yana fad’in “Kana tunanin laya tana tasiri a wannan gidan ne... Ai bari kaji ba Fada bane kawai takeda shiri ko wane gida nada nasa shirin... K’aramin munafuki tashi ka nuna kanka kuma ka fad’i waye Ubangidanka..!!” Ya k’arashe maganar yana mai fincike rawanin Ubandoma... Take fuskar Ubandoma ya bayyana gumi sai tsartsafo masa yake...
Baki sake Majidad’i Ke dubansa “Kai..!!! Kaine kenan... Kaine Bak’on Buzu...!!!”
Cikin rawar murya Ubandoma Ke fad’in “Allah shi taimakeka wllhi bani bane... Wllhi banida masaniya sahub b’arawo na taka kamin rai dan Allah..!”
Baikai aya ba Majidad’i ya kwahesa da wata irin jahilar mari wanda ya sanya Ubandoma zubewa k’asa yana mai ci gaba da rantsuwa yana fad’in bashi bane Bak’on Buzu baida masaniya kan Bak’on Buzu....
Damk’o wuyarsa Majidad’i yai yana fad’in “Ka shiga hannu kuma kenan ai... Sai ka sanar dani Ubanda kakema aiki...!!”
Ubandoma yaci gaba da magiya yana fad’in ai masa rai baisan komai ba...
**
A cen Fada kuwa hankulan Giwa da Waziri ne yakai k’ololuwa wajen tashi... Giwa bataga Ta zama ba, tabbas akwai wanda Taguwarsa tafi tasu Gudu cikin Masarautar ya zama dole a yau d’in ta gana da Tal’udu duk yanda za’ai... Wannan mummunan labari da Waziri ya kawo mata ba k’aramin barazana bane a gareta...
Waziri na tafiya Giwa da Jakadiya sukai shirin zuwa ganin Tal’udu...
Giwa tai zaune saman jar dardumanta mai d’aukeda tambarin masarauta na tsafi... Jim kad’an guguwa ya kaure mai cikeda jan hayak’i, nan take Tal’udu ya bayyana cikin shigarsa maras kyaun gani....
Yana fitowa Giwa ta kifa kanta alamun gaisuwa, tinda taga jan guguwa tasan yau ba kanta, tashin hankali ne take fuskanta...
“Turai kinyi kuskure..!” Tal’udu ya fad’i cikin tsananin huci...
Giwa Ta shiga girgiza kai tana fad’in “Babu laifina ko guda Uban tsafi... Na tabbata wani ne da yasan da batun K’undin nan ya rigamu isaga Wambai... Amma yanzu so nake ka duba min mai fitilar tsafi ta hasko maka gameda wannan K’undi... Shin ina k’undin yake a halin yanzu...?”
Cikin tsananin b’acin rai ya buga jan sandar dake hannunsa, lokaci guda yake furta “Har abada K’undin nan bazai tab’a dawowa hannunki ba Turai... Kin riga da kin tapka kuskure... Kuma iyaka abinda fitilar tsafi Ta hasko mana shine K’undin zaiyi nisan tafiya har ya isaga wannan yarinya SAUDATU... Ita kad’aice zata iya bud’e wannan k’undi domin idan baki mance ba K’ADDARAR MASARAUTAR nan yana ratayene a wuyarta... Da ace yaranki sunyi nasaran kasheta tun a wancan lokacin k’ila da K’addarar Ta iya sauyawa... Barinta a raye yafi muni fiyeda rashin tarewa da banyi da ita ba.... Turai kina cikin had’ari muddin baki nemo Saudatu yanda Ta shiga Ta fice ba...!!” Ya k’arashe yana mai kuma dukan k’asa da sandar hannunsa...
Tashin hankali wanda ba’a saka masa rana.... A ina Saudatu take... A wane duniya Ta b’uya da har Tal’udu ya kasa gano yanda take rayuwa... Tabbas ya zama dole duk nisan duniyar data tafi ta nemo ta... Har abada bazata bari wulak’antacciya irin wannan yarinyar tayi sanadin mulkinta da duk wani Farin ciki nata ba...
Ta d’ago idanunta da sukai jazir tana duban Tal’udu
“A ina zan samo Saudatu Uban tsafi...?!”
Gashin girarsa guda d’aya ya tsinko ya aza saman tafin hannunsa yaceda Giwa matso nan ki gani... Babu musu ta matsa kusa tana Ware idanunta sosai... Ga tsananin mamakinta tsillin gashin taga ya kama da wuta yanaci sosai baka iya ganin komai sai bak’in hayak’i...
Tal’udu yaci gaba da fad’in “Yanda wannan wuta Ke ruruwa baki iya ganin alamun tsillin gashin nan Toh haka Saudatu zata k’ona rayuwarki ba tareda kin iya ganin koda alamunta ba....!!”
Giwa ta had’iyi miyau cikeda fargaba da kuma tashin hankali... Take ta kuma d’agowa tana duban Tal’udu.... Da tuni ya soma sakin murmushi... Lokaci guda yaci gaba da furta “Saidai akwai mutum d’aya wacce tasan yanda Saudatu take... Shiyasa na fad’a miki har abada bazaki iya kasheta ba domin itace kad’ai zata iya sanar dake yanda SAUDATU take... Ko ni ban sani ba amma ita d’in ta sani...!!”
Giwa da tai masa K’uri tun bai kai aya ba Ta furta “IZZATU..!!”
Tal’udu ya kuma murmusawa yace “K’warai kuwa Izzatu ce kad’ai tasan Duniyar da Saudatu Ke rayuwa a halin yanzu... Izzatu ce kad’ai makaminki na k’arahe akan wannan yarinya Saudatu... Wannan na d’aya daga cikin dalilin da yasa na hanaki kashe Izzatu, domin ita kad’aice fitilar tsafi ke hasko min a duk lokacin da na soma bincike kan Saudatu, hakan na nuni da cewa itace zatai maki jagoranci har ki isaga Saudatu...Lokacin da Izzatu zatai maki amfani yazo Turai..!!!” Yana ida fad’in haka guguwa ya kaure b’at ya b’ace daga cikin d’akin...
Tashin hankali wanda baa saka masa rana, waige waige Giwa ta soma tana kiran sunan Tal’udu lokaci guda take furta “Ta yaya matar da bata cikin hankalinta zata sanar dani wani gameda Saudatu..? Ta ya zan sami wasu amsoshi daga wajen matar da babu hankali a tattareda ita...? Ta yaya matar da babu harshe cikin bakinta zata iyayin magana..?!! Tal’uduuu...?!!” Ta k’arashe tana mai k’walla masa kira amma saidai babu Tal’udu babu alamunsa....
Giwa ta sauk’e nannuyan ajiyan zuciya kana ta mik’e ta nufo waje... Tai k’uri ma wannan d’akin da kullum yake nan a bud’e... D’akin da ya kamata ace Saudatu ke rayuwa ciki tareda Tal’udu... Tana ficewa daga cikin gidan Tal’udu ta tadda Jakadiya na jiranta...
Jakadiya tace da ita “Allah shi taimakeki ina muka nufa....?!”
Giwa ta kuma gyara bak’ar Alkyabbarta Ta rufe fuskarta sosai kana taceda Jakadiya “Wajen Izzatu muka nufa... Kiyi min kiran Ubandoma...!!”
Daga haka sa kai tai Ta wuce cikin sauri Jakadiya na fad’in “An gama Allah shi baki yawan rai...!!”
Take Jakadiya ta soma neman layin Ubandoma...
Muhibbah dake zaune haraban masauk’inta tana duba wani k’aramin littafi na addu’o’i lokaci guda tana karanta sak’onnin soyayya da Fu’ad ke Aiko mata tana sakin tsuka a hankali nan ta hangi alamun giftawan mutane cikin wane irin sauri tamkar zasu tashi sama... Ai take taji koma su wanene tana son ganin yanda suka nufa... Babu shiri ta mik’e ta gyara rufin kanta sannan ta fito cikin sand’a tabi hanyar da taga sunbi....
SameenaAleeyou 📚
[7/14, 7:36 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*033*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Cikin tsananin rud’ani da tashin hankali Giwa Ke duban Jakadiya “Jakadiya ban fahimceki ba.... Mai kike cewa...?!”
Jakadiya Ta kuma risinawa “Allah shi baki yawan rai kaman yanda kikaji na fad’i ba Ubandoma bane ya amsa kiran kuma ga dukkan alamu Uabdoma yana cikin had’arin gaske, dan wannan murya da naji cikin wayar salulan ba k’aramin tada min hankali yai ba Allah shi taimakeki...!” Ta k’arashe tana mai kuma sadda Kai...
Giwa ta fuzar da fuci kana tace “Shige ki bud’e mamu k’ofar...!”
Babu musu Jakadiya ta isa ta bud’e k’ofar da yake mai nauyin gaske, da k’yar take iya jan k’ofar... Koda gani wannan dadd’en gini ne mai matuk’ar k’argo da aminci...
Muhibbah dake gefe a lab’e tai K’uri tana dubansu har suka shige cikin d’akin... A hankali ta sad’ad’o ta k’araso had’ida rakub’ewa tsakankanin tapkeken k’ofar da yake mai kunnuwa biyu, tana iya hango Giwa da Jakadiya Ta tsakankanin ramin k’ofar yanda sukai tsaye gaban mahaukaciyar matar nan dake d’aure da manyan sark’ok’i....
Matar tana ganin Giwa sai ta soma k’ok’arin fincika tana san sance d’aurinda aka mata... Ita kad’ai sai fincika take tamkar zatayo kansu...
Dama Ubandoma ke bugunta idan tai yunk’urin kaiwa Giwa damk’a gashi yau babu Ubandoma... Jakadiya ce Tai ta maza ta janyo k’atoton dutsin dake gefe ta aza saman k’afafun mahaukaciyar wanda ya sanyata sakin k’aran azaba... sai kuma ta koma tai lak’was tana fidda numfashi a hankali sabida tsananin azaban nauyin dutsen da takeji saman k’afafunta...
Giwa Ta sami zarafin k’arasowa cikeda k’asaita... Lokaci guda Ta umarci Jakadiya data baza mata mayafinta Ta zauna bisa...
Jakadiya ta d’an dubeta da mamaki kana tace “Allah shi baki yawan rai zama a wannan k’ask’antaccen waje mai cikeda k’azanta da k’ask’asanci bai kamaceki ba...!”
Batakai aya ba Giwa Ta katseta cikin tsananin daka tsawa “Jakadiya har yaushe kika fara sa’insa dani... Umarni nake baki ba shawarinki nake nema ba...!!”
Babu shiri Jakadiya ta risina “Tuba nake ya Shugabata... Allah ya huci zuciyar Sarauniya tilo d’aya a Masarautar nan...!!” Ta k’arshe tana mai yaye mayafin kanta kana Ta baza ma Giwa a nan gaban mahaukaciya Izzatu... Giwa Ta tako Ta zauna irin zaman da masu mulki keyi kana tai k’urima Izzatu...
Daga yanda Muhibbah ke tsaye bata iya sauraron abinda suke fad’i dan d’akin nada matuk’ar zurfin gaske abinka da gini irin na gidan sarauta da ya kwashe shekaru aru aru, gashi dai tana iya hangensu da duk wani motsin da suke amma bata iya sauraren abubuwan da suke fad’i duk kalan kasa kunnuwan da tai kaw... Ga kukan hadari dake k’aruwa wanda ya dad’a taimakawa wajen hanata auraron abinda suke fad’i...
Giwa takai hannunta guda cikin tsananin b’acin rai ta damk’o wuyar Izzatu, kana iya ganin yanda jiniyoyin hannunta sukai rud’u rud’u sabida tsananin b’acin rai “Izzatu kinyi kad’an kiga baya mulki na... Ke k’ask’antacciya ki bud’e baki ki sanar dani wace duniya kika b’oye Saudatu..?!!”
Giwa Ta k’arashe tana mai kuma matse wuyan Izzatu da tuni Ta soma k’ak’arin amai sabida tsananin rik’onda Giwa tai mata..!!
Jakadiya gaba d’aya Ta razana ganin Giwa na shirin aika Izzatu lahira gashi Tal’udu ya sanar da ita cewa idan har tana k’aunar zaman lafiyarta toh bazata kashe Izzatu ba...!
Tuni Jakadiya ta zube tana dannan zuciyar Giwa kafin da k’yar Giwa ta sararawa Izzatu...
Giwa Ta kuma jefa mata tambayar Ina Saudatu...? Saidai abinka da mai tab’in hankali dariya Izzatu ta kuma fashe masu dashi tana mai furta wani magana da yafi kama da gwalamniya kasancewar babu harshe cikin bakinta...
Giwa ta sauk’e nannuyan ajiyan zuciya, lallai akwai aiki ja a gabanta idan har za’ace mahaukaciya kuma bebiya ce zata sanar da ita duniyarda Saudatu ke rayuwa... Wannan wane irin al’amari ne...? Bata tab’a zaton Izzatu zata zamto mata k’adangaren bakin tulu ba... Ta yaya za’a ce sa’arta na tareda Izzatu... Ta sauk’e fuci a hankali sanda Jakadiya ke furta “Allah shi baki yawan rai inaga mu k’yaleta haka nan na yau kuma har sai zuwa wani lokaci... Inaga da kad’an da kad’an idan muna bijiro mata da zancen har Allah zaisa mu dace ta bud’i baki ta sanar damu...!”
Ta k’arashe tana mai kuma k’ank’an da kai gaban Giwa...
Badon Giwa taso ba Ta mik’e tana mai ci gaba da duban Izzatu dake sakin murmushi cikin yanayin fuskarta da ya cika da datti da kuma daud’a....
Duban Jakadiya Giwa tai ta mata alama da cewa su fice... Babu musu Jakadiya tabi umarnin uwar gijiyarta...
Sam Muhibbah bata ankara dasu Giwa da tuni sun nufo k’ofa gadan gadan ba, hankalinta da tinaninta yayi nisa wajen tunanin shin wacece wannan mahaukaciyar, maiyasa Giwa ta ajeta a wannan sunk’urumin d’akin sannan mai take zuwa yi wajen wannan mahaukaciya... Ya kamata tasan wacece wannan mahaukaciyar....
Kaman daga sama taji alamun tab’a k’ofa babu shiri tai saurin komawa da baya k’irjinta naci gaba da bugu...
Giwa ce ta d’anja ta tsaya sanda taji tamkar akwai alamun mutum a wajen... Jakadiya ta d’ago tana dubanta, lokaci guda Giwa ke furta “Jakadiya, kin tabatta mu biyu ne a wajen nan bamuda wani d’an rakiya...?”
Jakadiya Ta waiga gefe da gefe kana tace “Rankishi dad’e mu biyu ne rak saiko Izzatu dake cikin d’aki...!”
Giwa Ta d’anyi Jim tana mai kuma karantar wajen.... Lokaci guda ta kaikaito sosai tana mai k’arewa d’akin Izzatu kallo... Babu shiri Muhibbah ta zame daga jikin k’ofar ta shige cikin d’akin dan tabbas idan Giwa ta matso sosai zata iya ganinta jikin k’ofar...
Giwa ta dubi Jakadiya tace “Jakadiya ban yarda babu kowa a nan ba mu koma da baya...!”
Babu musu Jakadiya tabi umarnin uwar gijiyarta...
Duk addu’an da yazo zuciyar Muhibba yinta kurum take.... Ta sadakar shikenan Giwa da Jakadiya Sun kamata, kaman daga sama taji an janyota Ta baya... Zuciyarta ta kuma tsinkewa sanda taga mahaukaciyar nan ne Ta rik’eta sosai ta b’oyeta k’asan gadon katakon da aka d’aureta bisa....
Tana jin sanda su Giwa suka dawo da baya suna masu k’arewa d’akin kallo na wasu dak’ik’ai... Giwa taceda Jakadiya ta bincika ko ina har k’asan gadon Izzatu...
Zuciyar Muhibbah ta kuma tsinkewa shikenan Sun kamata an gama... Tai saurin rintse idanunta had’ida toshe bakinta da duka hannayenta biyu...
Jakadiya na k’ok’arin duk’awa Izzatu tai tsalle Ta mak’uro Jakadiya tanai mata wani irin duka wanda da kaga mai yinta kasan babu hankali a tattaredashi...
Giwa ta Wato ido waje don basusan Izzatu likamau tayi ba ashe dai ba d’aure take ba... Bugun Jakadiya take tamkar wacce aka aikota bataji bata gani...Jakadiya na sakin k’aran azaba...
Giwa kanta saida ta firgita da irin bugunda Izzatu keyiwa Jakadiya tasan ko shakka babu idan ta gama da Jakadiya kanta zata hauro tunda ba hankali bane jikinta...
Ai tuni Giwa ta soma jada baya Jakadiya na fad’in ta ceceta... Inaa Giwa ko takan Jakadiya batabi ba ta fice da baya da baya tana waige waige... Da k’yar da mak’yark’yata Jakadiya ta samu ta k’waci kanta hannun Izzatu ta fito a guje babu shiri amma kam ko shakka babu Ta daku irin bugun da akewa dawa idan an ciro daga gona...
Haki kurum Jakadiya take d’ankwali a hannu haka ta nufo waje tana gumi da haki had’ida d’ingishi...
Suna ficewa Izzatu ta duk’a ta yaye mayafin k’asan gadon nata yanda Muhibbah ke b’oye ciki....
Jikin Muhibbah ya d’auki rawa ganin irin bugunda taiwa Jakadiya kardai itama ta lallasa mata nata bugun... Saidai ga tsananin mamakinta murmushi ta sakar mata kana ta mik’a mata hannu alamun tana jira ta mik’o nata hannun ta fito da ita...
Dukda rawa da jikin Muhibbah keyi hakan bai hanata jarumtar mik’awa mahaukaciyar nata hannun ba... A hankali take janyota har Ta fito da ita daga k’asan gadon... Sukaima juna K’uri su duka biyun... Sai yanzu ne Muhibbah ke iya tantance mahaukaciyar da ko shakka babu Dattijuwa ce sannan da alama ta jima a wannan yanayi sabida daud’a da jikinta yayi sosai, data k’urawa mahaukaciyar idanu sai ta fahimci farar fata ce ba bak’a bace dan ga alamun asalin kalarta Ta ramin idanunta da kuma k’ark’ashin kunnuwarta ashe bak’in datti ne ya rufe mata fata har ya zamto tamkar wani layer....
“AUDOTU” (SAUDATU) abinda mahaukaciyar kenan Ta fad’i cikin kalamanata da basa fita sosai...
Gaban Muhibbah ya yanke ya fad’i jin wannan mahaukaciya tamkar sunanta taji Ta ambata...
Muhibbah ta d’ago firgitattun idanunta tana duban mahaukaciyar wacce tuni ta kuma sakar mata murmushi....
Hannun Muhibbah taci gaba da janyowa har suka isa jikin shirgin kayanta, itada dai Muhibbah bata dawo daidai ba har wannan lokaci saima bugu da k’irjinta Ke ci gaba da yi... Tana gani mahaukaciyar ta soma bincike kayayyakinta... Can k’asan kayan ta ciro wani zane mai yanayi da zanen dake lank’aye parlon su Umaima... Gaban Muhibbah ya kuma yankewa ya fad’i... Mai wannan zane yake nufi....?
Batakaiga samo amsa ba taji sauk’ar takardan a hannunta mahaukaciyar ta mallaka mata ta dunk’ula mata sosai cikin hannunta tana mai ci gaba da sakin murmushi... Lokaci guda kuma Ta koma mazauninta Ta zauna, Ta rarumo ledar bredin da jiya Jakadiya da Ubandoma suka kawo mata Ta barka ledar ta hau mamuk’ar bredin kaman mai tsoron kar wani ya k’wace...
Muhibbah ta tsaya daga yanda take tai mata K’uri don ba kowa ta tina mata ba face Mahaifiyarta... Haka mahaifiyarta Ke tsananin k’aunar bread shine abincin da yafi soyuwa a gareta a lokacinda take raye.... Ta lumshe idanunta a hankali sanda take jin wasu hawaye daga can k’asan idanunta suna yunk’urin fitowa...
Jin kaman alamun tafiyan mutane ya sanyata saurin saita kanta kana ta nufi k’ofa sauri sauri wannan zanen na damk’e cikin hannunta ta fice daga cikin d’akin tana mai kuma waigowa tana duban mahaukaciyar nan itama mahaukaciyar idanunta k’yam akan Muhibbar har Ta fice...
A haka Muhibbah ta nufi d’aki, har lokacin bata dawo daidai ba, abubuwan da suka faru suna kuma dawo mata... Musamman da Ta tuna taji kaman matar nan Ta ambaci sunanta... Toh wacece mahaukaciyar nan...? Ya akai ta santa...? Shin wacece ita..? Ta k’arashe tunanin nata tana mai bud’e wannan taswira da mahaukaciyar ta damk’a mata... Tai k’urima zanen ginin tana mai kuma k’are masa kallo... Lallai ya zama dole tasan yanda za’ai tai comparing wannan zanen da wanda Ke lank’aye parlorn su Umaima, idan har sun zmato iri guda toh ko shakka babu akwai wani b’oyayyen sirri tattareda zanen...! Ta k’arashe tinaninta tana mai kwanciya rigingine saman gado... Ta janyo wayarta tana mai k’ok’arin neman layin Ansar... Saidai kira kusan sau uku tai bai d’aga ba... Sai sannan ta duba time taga dare ya d’anja sosai dan haka bata kuma kiran nasa ba barshi har sai zuwa safiya...
**
Kafin Washe gari iyaka buguwa Ubandoma yayi laushi a hannun Majidad’i... Idan Kaga Ubandoma dole ya baka tausayi irin yanda bugu ya sauya masa halitta... Kankace mai labari ya bazama Fada cewa an kama Ubandoma a gidan Wamabai... Wannan labari ba k’aramin d’aga hankalin Giwa da Waziri yai ba... Mai yakai Ubandoma gidan Wambai... Shin kodai munafuntarsu yake... Shin kodai shid’in ya amintada Mahmood ne...? Bacin haka ma Uban wa yake aiki Tunda dai sunsan su basu aikesa gidan Wambai ba..
Shi kuwa Mahmood mamaki abin ya dinga basa... Shin mai yakai Ubandoma gidan Wambai..? Shin kodai yasan cewa shine bak’on Buzu...? Ya zaci Ubandoma aminatccen hadiminsa ne, kenan Ubandoma na munafuntarsa ne..? Yayi daidai da bai aminta dashi ya bud’e masa wasu sirrika nasa... Tabbas zarginsa ya tabbata wannan gida ba kowa ba abin yarda bane... Kenan zata iya yuwa wasu sunyi amfani da kusancin dake tsakaninsa da Ubandoma dan yai masu aiki.... Lallai ya zama dole ya k’ara taka tsantsan kuma Ubandoma zai fad’i abinda ya kaisa gidan Baba Wambai da kuma wanda ya turasa...
Da wannan tunanin Bawa guda ya k’araso ya zube gabansa yai gaisuwa kana ya k’arada “Allah shija zamaninka an tafida Ubandoma Gidan Yarin wucen gadi dake nan cikin Masarauta Dan a tsaresa...!”
Jinjina kai Yarima Mahmood yai a hankali alamun amsawa... Lokaci guda ya haura sama domin shiryawa dan ya zama dole ya gana da Ubandoma a yau d’in....
****
A daidai k’ofar shiga masarauta Yazeed da Majidad’i suka had’u...
Yazeed ya fad’ad’a murmushinsa sanda yake k’ok’arin k’arasowa dab da Majidad’in... Bayan sun gaisa ne Yazeed yai gyaran murya cikeda k’asaita “Ashe an kama b’era... Bravo gaskiya kayi k’ok’ari Partner... I’m so proud of you..!” Ya k’arashe yana mai tafe hannu a hankali shu’umin murmushi kwance saman fuskarsa...
Murmushin Majidad’i ma yai kana yace “Idan nasa abu a gaba bana fasawa har sai naci nasara domin ni d’in mai sa’a ne a koda yaushe...!” Ya k’arashe cikeda ziga kansa...
Shu’umin murmushin bai bar saman fuskar Yazeed ba ya d’an kwanto da fuskarsa kad’an saitin kunnen Majidad’i “Kar kayi gaggawa Abokina domin tafiya ce mai tsawo a gabanka...!”
Majidad’i ya murmusa kad’an yana mai duban Yazeed yake furta “At least yanzu na nuna maka what I’m capable of....Kai kuma fah shin ka nuna wani jarumta...?!”
Murmusawa kad’an
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 65