matar Yazeed suka nufa....
**
Sanda Zahra ta k’araso sashen mahaifin nata, samansa ta haura don sanar dashi ta dawo ya sauk’o suyi breakfast saidai wayan da taji yana yi ne ya sanyata tsayuwa ba tareda Ta iya ci gaba da tafiya ba...
Mahmood da sam baisan da isowar d’iyar tasa ba yaci gaba da fad’in “Must we talk about that Turaki... Sau nawa zance maka sanin gaskiyar babu wani amfanin da zaiwa Zahra... I cannot break my daughter’s heart, rashin mahaifiyarta da tai is enough... Zahra went through a lot already... Rasuwar Aliya, d’aukota daga Spain mu dawo Nigeria, rabata da rayuwar data saba, makarantar ta abokanta da sauransu don’t you think is enough for her... Bai kamata na kuma bijiro mata da wani tashin hankali ba... The only abinda na sani shine bazan tab’a bari tasan gaskiya ba muddin gaskiyan zai jefata cikin tashin hankali... I already lost my wife, I can’t lose my daughter Turaki...!”
Dukda k’arancin shekarunta hakan bai hanata k’ok’arin saita natsuwarta ba... Taji jiri na neman kada ita... Mai Paa d’inta yake b’oye mata... Meye ne wannan abin da baiso ta sani...? Meye a k’unshe da rayuwarta da yake b’oye mata...? Ta yarda da Paa d’inta tsawon rayuwarta, bata tab’a kawo akwai abinda zai b’oye mata mai girma har haka ba.... Ita zata iya cewa ma tafi shak’uwa dashi sama da mahaifiyarta... Toh meye ne ake mata rufa rufa akai... Toh kodai Paa d’inta nada masaniya ne akan mutuwar mahaifiyarta tinda gashi taji yana cewa ya rasa matarsa bazai kuma rasa d’iyarsa ba... Idan bata mance ba zuwansu Nigeria ne aka tsinci gawar Maama a d’aki... Toh ko Paa yasan wani abu ne gameda mutuwar mahaifiyarta shine yake b’oye mata...?! Take taji wasu k’walla suna kuma zuwa idanunta.. No Paa d’inta bazai tab’a yin wani abu mai kama da wannan ba, bama zata bari zuciyarta ta raya mata hakan ba.... Tayi nisa cikin tinani ta jiyo muryarsa yana fad’in “I guess my princess’s starving already... Forgive your Paa ya barki kinata jiranshi... Do you want me to serve you...?” Ya k’arashe yana mai k’arasowa jikin dining table d’in....
K’ak’aro murmushi tai kana tace “No it’s alright Paa... Just sit down I’ll serve you...!” Ta k’arashe tana mai mik’ewa tsaye cikin tsananin sanyin jiki... Yarima Mahmood yai mata K’uri yana duban yanda yanayinta ya sauya gaba d’aya...
Ta k’araso tana k’ok’arin had’a masa shayi, har lokacin idanunsa akanta.. Hannunta ya d’an rik’e alamun dakatarwa kana yace “Are you sure you’re alright sweetheart..? Wait ina friend d’in taki... Why isn’t she here...?”
K’ak’aro murmushi ta kumayi na k’arfin hali kana tace “I’m fine Paa... Tace ba yau ba maybe some other time...!”
Ya jinjina kansa a hankali yana mai ci gaba da karantar yanayin d’iyar tasa... Har Ta gama had’a masa shayin ta koma mazauninta ta zauna Yarima Mahmood bai daina karantarta ba, yasan dole akwai abinda Ke damunta... Sai yai k’ok’arin danganta hakan da rashin amsar tayinta da Muhibbah batai ba....
Yana son d’iyarsa sosai, a Duniyarsa baison ganin b’acin ranta haka yaita k’ok’arin cheering d’inta, ita kaw Zahra har yanzu wayan dataji mahaifin nata nayi take tinani....
***
Tafe suke hanyar da zai sadaka da b’angaren Yazeed wata kuyanga Ta k’araso cikeda risinawa ta gaidasu kana ta dubi Umaima taceda ita Yarima Fu’ad ke son magana da ita...
Umaima ta d’anyi still tana dubanta kana tace “Ina Yarima Fu’ad d’in yake...?”
Kuyangar Ta kuma sadda kanta kana tace “Yana bayan lambun dake b’angaren sashen Giwa, yana jiranki a cen Rankishi dad’e..!”
Jinjina kai Umaima tai kana tace “Ki sanar dashi Ina zuwa...”
Kuyangar ta jinjina kai cikeda ladabi irinta babban gida had’ida amsawa kana tasa kai ta shige...
Umaima ta dubi Muhibbah kafin tai magana Muhibbah tace “Just go your Highness, ni zan k’arasa sashen Gimbiya Zuhra idan yaso sai ki sameni a cen...!”
Umaima ta jinjina kai murmushi saman fuskarta dan tasan kiran da Fu’ad Ke mata bazai shige akan Muhibbar ba kana tace “Da fatan dai bazaki b’ata a hanya ba...!”
Murmusawa Muhibbah tai kana tace “Tinda ban b’ata cikin duhun dare ba ai ina tinanin banzan b’ace cikin hasken rana ba ranki shi dad’e..!” Suka kuma murmusawa a tare kana Umaima tace “Haka fah... Kinyi gaskiya, I’ll see you later...”
Muhibbah Ta jinjina mata kai kana Ta nufi sashen Yarima Yazeed...
Tana isowa sashen ta tadda Kuyangi daga waje sai risinawa suke suna gaidata, ita kaw taita jinjina masu kai alamun amsawa, a haka Ta nufi cikin gidan...
Shiru ta tadda parlorn saidai tana shiga tai arba da k’atoton hoton Yazeed wanda akai masa daga sama har k’asa yai tsayuwa irinta masu mulki, yana sanye da kaya irinta mulki da sarauta, komai na jikinsa na sarauta ne har zuwa takalmin kufta dake k’afafunsa...
Kansa nad’e cikin Farin rawani mai kunne biyu, idanunsa rufe da bak’ar tabarau wanda ya dad’a fito da hasken fusakarsa, yana sanye da alkyabba fara k’al haka nan hannunsa na dama rik’eda doguwar sanda irinta masu mulki... Kaman ka kirasa ya amsa....Sosai zuciyarta ke tafarfasa tana duban wannan hoto na Yazeed... Ji take kaman ta janyo hoton k’asa tai rugu rugu dashi wala’alla zataji sauk’in zoginda zuciyarta ke mata... Da k’yar Tai k’ok’arin saita kanta kana ta nufi cikin parlorn...
Ganin babu kowa cikin parlorn ya sanyata d’an waige waige... Nan ta hangi hanyar upstairs... Take taji zuciyarta na raya mata ta haura saman... Ta kuma d’an waigawa kana ta nufi hanyar da zai sadaka da upstairs....
A hankali takejin kaman sautin kuka na tashi... Ta kuma kasa kunnuwanta had’ida mak’alewa jikin k’ofar kad’an...
Tana iya sauraro muryar Zuhra cikin kuka tana fad’in “Wlhi Raheema na ga sark’ar buduwar tasa da idanuna kuma a nan cikin drawer na ajiye shine da nai masa yamin wulak’ancin da ko kare bazai ci ba...”
Raheema da k’irjinta Ke tsananin bugu tace “Toh yanzu ina sark’ar...?”
Zuhra ta kuma goge hawayen dake idanunta kana tace “Ya d’auka yana wajenshi.. Na d’aga sark’an ne da niyyan na nuna miki evidence cewa ba sharri nakewa Yazeed ba, wllhi yana cutar dani...!”
Raheema data sauk’e ajiyan zuciya a hankali jin Yazeed ya d’aga sark’ar, kamo hannun Raheema tai kana tace “K’awata you don’t need to show anything for me to believe you K’awata,nasan zaman hak’uri kike da wannan azzalumin mijin naki.. But Zuhra dole haka zaki ci gaba da hak’uri don kare martabarki da na yaranki... Nasan maybe wataran zai kaiki bango da wannan d’abi’u nasa har kiyi tinanin komawa masarautarku, Toh ki sani yin hakan na nufin tonon asirinki ne Zuhra... Kici gaba da hak’uri akan wanda kikeyi... Kuma Ki d’auke idanunki kan abubuwan da mijinki keyi balle ya saka miki wani ciwon kinji koh....!”
Zuhra ta jinjina kai tana mai godiya wa Raheema da kyawawan shawarin da take bata...
A hankali Muhibbah ta nufo downstairs bayan Ta gama jin komai....Daidai tsakiyar stirs ta hangesa tsaye ya kafeta da mayun idanunsa....
SameenaAleeyou 📚
[6/19, 9:22 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*020*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Kallo yake binta dashi daga sama har k’asa, wannan karon sai yafi samun daman k’are mata kallo fiyeda wancan lokacin da yai arba da ita a cikin duhun dare...
Ala dole tai k’ok’arin saita kanta dikda tsananin zogi da zuciyarta Ke mata musamman ganin irin duban da Yarima Yazeed yake mata.... Bazata bari ya zargi wani abu daga gareta ba... Dan haka lokaci guda tai k’ok’arin d’aura murmushi saman fuskarta “Barkada safiya Your Highness...!” Ta fad’i daga nan yanda take tsaye kyakkyawan murmushi saman fuskarta...
Bai amsata ba saima duba na k’urilla da yake mata... Ganin haka ya sanya Muhibbah soma takowa cikin salo na yaudara da d’aukan hankali.... Saida ta k’araso dab kusa da Yazeed kana ta d’an risinar da kanta tana mai furta “Idan Yarima yamin izini zan sauk’a k’asa....!”
Ga tsananin mamakinta karkacewa taga Yazeed yayi yana k’ok’arin bata hanya...
Ta k’araso zata rab’a ta gefensa ta shige dikda tsananin bugu da k’irjinta keyi...
Dab saitin kunnenta dake b’angarensa Ta sinkayo muryarsa yana fad’in “Looks like destiny wants us together...!” Yai maganan yana mai aika mata wani irin duba shu’umin murmushinsa saman fuskarsa....
Batakaiga Koda motsa ‘yar yatsarta ba Ta kuma jiyo muryarsa yana fad’in “Be careful what you’re getting yourself into... You might get trapped in the middle..!”
Tai saurin d’agowa tana dubansa, shid’inma ita yake duba babu ko alamun gizau a tattaredashi, lokaci guda ya sakar mata wannan murmushin nasa maras kyaun gani... Muhibbah tai saurin kauda fuskanta gefe tana mai ci gaba da tafiya har ta sauk’a k’asa... Sauk’anta Keda wuya Umaima suka shigo tareda yaran Yazeed da dawowarsu kenan daga islamiya....
Noor ta taho da gudu ta rungume Muhibbah tana k’ok’arin biya karatun da Ta koya a islamiya... Shikaw Sultan sakai yai ya shige abinsa ba tareda yabi takansu ba dan dama hakan nan yaron yake ga k’asaita ga miskilanci... Kana ganinsa Kaga jinin sarauta....
Muhibbah ta saci duban upstairs yanda ta bar Yazeed tsaye saidai sam bata hange koda k’yallinsa ba da alama ya shige wane wajen... Ta sauk’e ajiyan zuciya a hankali dikda yawo da kalaman Yazeed Keyi a kwanyarta... What if Yazeed ya ganeta ne..? What if ya fahimceta ne... Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un! Idan hakan ta kasance ya kenan zatai ita da bata fara komai cikin abinda ya kawota ba... Muryar Umaima ne ya dawo da ita daga duniyar tinaninda ta tafi yanda take sanarda kuyangar dake rik’eda Noor zasu haura sama data sanarwa Gimbiya Zuhra shigowarsu... Kuyangar ta jinjina mata kai cikeda risinawa kana Ta nufi benen rik’eda Noor...
D’an duban Muhibbah Umaima tai Dan Ta lura kaman wani abu na damunta... “Hibbah lafia...? Akwai wani abu ne..?”
K’ok’arin saita kanta Muhibbah tai had’ida girgiza kai kana tace “No babu komai, mai kika gani..?”
Umaima ta d’an murmusa kad’an kana tace “Well, ni inada wani batu da nakeso muyi dake..”
Muhibbah ta d’an zaro idanu waje kana tace “You seems serious... Hope all is well..!”
Umaima ta kuma murmusawa kana tace “K’alau saima alkhairi...!”
Muhibbah Ta d’an kuma yin fari da idanunta kana tace “Now you’re making me nervous... Rankishi dad’e wai meke faruwa ne..?!”
Kashe mata idanu guda Umaima tai kana tace “Idan mun fice a nan zan sanar dake komai in details... Relax K’awata na fad’a maki babu komai sai alkhairi...” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta...
Murmushin yak’e Muhibbar ma tai daidai sanda Zuhura da Raheema suka nufo parlorn...
Raheema na hangosu ta rausayar da idanu had’ida fuzar da huci a hankali, Ta tsani wannan shegiyar Muhibbar, Ta tsani ganinta.. She can’t stand the sight of her... Dafa k’awarta tai a hankali tana mai furtawa cikin sigan rad’a “You take care K’awata... Da dare zan shigo mu k’arasa zancenmu... Ki kwantar da hankalin ki kinji... And think about dik abubuwan da na fad’a miki....!”
Jinjina mata kai Zuhra tai a hankali kana Raheema ta d’agawa Umaima hannu alamun gaisuwa ko takan Muhibbah batabi ba tai ficewarta....
Zuhra ta k’araso garesu da fari’arta tanai masu sannu da zuwa, sai nan nan dasu take gwanin ban tausai, dubanta kurum Muhibbah keyi amma tausayinta ne fal k’asan zuciyarta, shin ya zataji idan taji aminiyarta wacce ta aminta da ita take kawo mata kokenta da dik wani sirri nata da ita mijinta yake cin amanarta... Kai wannan duniya da amana tai k’aranci shin ina zamu kai girman hakki...
Sun jima sosai b’angaren Gimbiya Zuhra Muhibbah na karantarta tsaf, har sai bayan sallan azahar kana suka nufo b’angare Giwa....
Har wannan lokaci Muhibbah dai bata wani saki jikinta ba, sosai kalaman Yazeed ya d’aga mata hankali... Ta yaya ma zata kwantar da hankalinta bayan kalaman da taji suna fita daga bakin Yazeed... Bazata bari Yazeed ya rusa mata dik wani shirinta ba, dole tasan yanda zatai Ta tabbata hankalinsa baikaiga yanda take tinani ba....
Basu samu ganin Giwa ba Jakadiya ta sanar dasu Giwa na sama tana ganawa da yaranta, hakan yasa suka yada zango nan b’angarensu Umaima...
Hango Fu’ad daga k’asan bene da Umaima tai ya sanyata fasa shigewa parlorn dole ta nufo k’asa tana fad’iwa Muhibbah ta jeta tana nan tafe....
Muhibbah ta jinjina kai kana tasa kai kaman zata nufi b’angaren benen da zai sadaka da sashen su Umaima....
K’uri taiwa b’angaren Giwa dan tinda taji ance Giwa na ganawa da yaranta taji tana son jin kan mai suke tattaunawa... Ta d’an waiga gefe da gefe bataga kowa ba, hakan ya bata daman kutsa kai ta nufi sashen matakalan Giwa....
Cikin sand’a take tafiyar nata har saida ta k’araso jikin k’ofar dataji maganganunsu kwanakin baya... Ta tura a hankali kana ta d’an kutsa kanta ta shige cikin sauri ta mak’ale jikin k’ofa... Shigarta keda wuya kuwa ta soma jiyo muryar Yazeed yana fad’i cikin gadara da isa... “Mamee babu wanda ya isa ya hanani neman sarautar nan... I’m sorry to say not even you... Wllhi wllhi na rantse da mahaliccina ko Abbah ne ya taso daga kabarinsa saidai muyi takara dashi muga waye zai kada wani...”
“Yazeeeed!!!” Mahmood ya daka masa tsawa cikin karaji...
Shima Yazeed d’in cikin tsananin karaji yake ci gaba da fad’in “What..!!! Zaka hanani ne... C’mon Yaya, among the two of us kafi kowa sanin ni nafi cancanta da wannan
Mulki , a ijiye maganan cewa ka jima baka k’asar nan, a dawo maganan kamala da cancanta, I’m a family man bacin haka ni inada Magaji kaikuwa fah...? Bakadashi, d’iyarka d’aya ce tol kuma mace kaga bazata gaji Karagar Masarautar nan ba... Aje ma mace zata iya mulki shin taka d’iyar zatai mulki ne..? Ko ka mance cewa....!”
Bai kai aya ba Mahmood dake tsananin huci ya d’ago yatsarsa dake rawa sabida b’acin rai yana mai furta “Kar ka bari na sake maka kashedi Yazeed... Leave my daughter out of this...!!!”
Sai sannan Giwa ta katsesu da fad’in “Ya isa...! Ya isa haka nace..!! Shin wai ku bazaku tab’a zama inuwa guda ba... Haba Haba shin sai kunga bayana... Wannan wace irin masifa ne... Kai Yazeed na riga na gama magana idan bazakaga girman Yayanka ka bar masa wannan Karagar mulki ba ni dana haifeka Ina tsammanin zakaga girma na... Wllhi bazaka tab’a samun albarkana da goyon bayana ba idan dai akan mulkin nan ne..!!!” Ta k’arashe cikin tsananin karaji hawaye na k’ok’arin kawowa idanunta...
Jamal da k’irjinsa Ke tsananin bugu hango hawaye da yai kwance cikin idanun Mahaifiyarsu, a tamanin ya tafi ya duk’a gabanta yana lallashinta yana bata baki cikin tsananin damuwa da nuna tashin hankali...
Wani wulak’antaccen kallo Yazeed ya watsa mata, kana ya murmusa da gefen bakinsa... “I thought I made myself clear Maami... You can’t stop me... I won’t allow you to deny me what’s rightfully mine...!” Yana kaiwa nan yasa kai ya nufo k’ofa cikin sassarfa kaman zai kifa da k’asa...
Jin takunsa ya sanya Muhibbah saurin mak’alewa bayan k’ofa... Tana ganin Yazeed ya fice cikin tsananin huci da b’acin rai...
Yazeed na ficewa Mahmood ya k’araso gaban Giwa ya zuba gwiwoyinsa a k’asa... Lokaci guda ya d’aura hannunsa guda saman nata...
Giwa ta d’ago idanunta masu rauni a yau d’in tamkar ba ita ba tana duban Mahmood dake duk’e gabanta...
Yarima Mahmood yaci gaba da fad’in “Maami Ki yafe min, Ki yafewa d’an uwana Yazeed... Ba nufinmu bane mu sakaki cikin k’unci da bak’in ciki, na sani a koda yaushe Uwa batada burin da ya shige Ta sanya yaranta cikin Farin ciki... Na sani dik wannan fad’i tashin da kikeyi sabida mu ne... Amma Maami abu guda da nakeso Ki sani shine, shifa Mulki Allah Ke badashi ga wanda yaso ya kuma hana wanda yaso a kuma lokacinda yaga dama... So Maami idan Allah ya k’addari Yazeed shine wanda zai d’ale Karagar Masarautar nan inaso ki bashi full support d’inki ki kuma bashi albarkanki da addu’o’inki domin hakan ne zai leading d’insa to what’s right...”
Saurin d’agowa Giwa tai tana dubansa, kaman Ta shak’esa Ta huta haka takeji... Fad’i take cikin zuciyarta _”K’arya kake Mahmood, baka isa ka tsallake Karagar nan ba a yanzu... Dole ka d’ale sannan ka mutu kafin d’ah na Yazeed ya k’arb’a yai dogon zango har k’annensa da d’ansa ma suzo suyi... Mahmood kenan, ai nafi kowa son ganin Yazeed saman Karagar nan amma hakan ba mai yuwa bane a halin kana nan da rai.. Sai ka shid’a ka tafi ka tadda iyayenka a cen barzahu kafin Yazeed ya d’ale... Na riga nayi tanadima yarana Mahmood.. Ni ce nan na datse mahaifar matarka donma kar Ta haihu balle ka sami Magaji har ka saka ran wataran zai sarauta, Kaga da zaran ka mutu zuriyarka Ta k’are kenan a Masarautar nan Mahmood, saiko wannan shegiyar d’iyar taka wacce koda namiji ne shege bai gadon sarauta...!”_ Tana ida tinanin taji wani irin sanyi na sauk’a mata cikin zuciya, taji murmushi na zuwa saman fuskarta... Hannu tasa ta shafi fuskar Mahmood tana mai furtawa a fili “Mahmood d’ah na Allah dai shi maka Albarka... Ka cika d’ah mai biyayya da ko wacce uwa zatai mafarkin samu... Kalamanka gaskiya ne Mahmood, Allah shine mai bada mulki, shiyasa nake rok’onsa babu dare babu rana da ya mallaka maka wannan gadon mulki... Ni kaine zab’ina Mahmood, idan baka d’ale Karagar mulkin nan ba zanji kaman ban cika burin mahaifinku bane na ganin cewa kai ka zamto magajinsa... Kullum burin mahaifinku kenan ka gajesa Sadauki...!” Ta k’arashe cikin rau rau da murya...
Daga Mahmood har Jamal saida mahaifiyar tasu Ta basu tausayi, sam rauni ba d’abi’arta bane, idan ta shiga yanayin sai ta baka tausai...
Yarima Mahmood ya jinjina kai a hankali yana mai furta “Kici gaba da mana addu’a Maami, addu’anki yafi komai... Allah yai mana zab’i na alkhairi...!”
Ta jinjina masa kai a hankali tana mai kuma saka masa albarka kana ya mik’e yana furtawa Jamal zai duba Zahra ya kula da mahaifiyarsu...
Jamal ya jinjina masa kai yana mai furta “Alright Yaya, kaje zan kulada Maami...”
Jinjina masa kai Mahmood yai kana yai sallamada mahaifiyar tasu...
Yana fitowa Muhibbah tabi bayansa da kallo, harga Allah bata San dalili ba amma cen k’asan zuciyarta sai ta sami kanta da jin tausayinsa, wani b’angare na zuciyar nata kuma na waswasi da kokonto kan batun da taji Yazeed nayi akan d’iyar Mahmood d’in... Kaman akwai wani ayan tambaya kan d’iyar tasa... Take taji tana son sanin menene Yazeed yake son fad’i kan Zahra....
Bayan Mahmood ya fice itama ta sad’ad’o ta fito daga mab’oyarta...
Yarima Mahmood na fitowa bai zarce ko Ina ba sai d’akin Zahra....Kwance ya hangota saman gado tamkar mai bacci, ya saki murmushi a hankali kana ya soma takowa cikin d’akin...
Ita kaw Zahra tanajin tafiyar mahaifin nata ta lumshe idanunta tamkar mai baccin da gaske, dan bayan maganganun da taji yanayi a waya bata tunanin zata kuma iya duban idonsa and act like babu wani abindake faruwa....
Tana jin sanda ya zauna a gefenta had’ida gyara mata mayafinda Ta rufa.... Murmushi saman fuskarsa yake dubanta, ya d’an d’auki lokaci yana dubanta kafin ya sumbaci goshinta ya mik’e ya fice daga d’akin gaba d’aya...
Yana ficewa, hawayen da Zahra ke mak’alewa suka gangaro mata, lokaci guda Ta mik’e Ta zauna sosai kana ta d’auki family picture d’insu dake aje saman bedside d’inta.... A hankali take shafa hoton, hawaye na gangaro mata lokaci guda take furta “Paa why... What’s that you’re hiding from me... What’s that that you don’t want me to find out... Does it have to do with my Maama’s death... ¿Tienes algo que ver con la muerte de mi mamá? (Shin kanada sa hannu ne a mutuwar magaifiyata.) Paa I love you, I love you so much... And I don’t want our relationship to be ruined...Pero Paa, si me entero de que tienes algo que ver con la muerte de mi Maama ... no sé si alguna vez podré perdonarte Paa (Idan na fahimci da saka hannun ka a mutuwar mahaifiyata, Bana tinanin zan tab’a yafe maka Paa..)”
Ta k’arashe tana mai rungume hoton cikin k’irjinta hawaye na kuma gangaro mata...
Muhibbah dake lab’e tana duban yarinyar a hankali ta saka hannu ta d’anyi knocking... Zahra ta shiga goge hawayenta da sauri tana mai juyowaga k’ofan...
Ganin Muhibbah ce ya sanyata sakin murmushi... Muhibbar ma murmushin take kana tace “May I...?”
Jinjina mata kai Zahra tai tana mai furta “Please come in....”
Fuskarta d’aukeda murmushi ta shigo kana ta zauna a gefen Zahra... Lokaci guda ta k’ura mata idanu tamkar mai karantarta....
Saida ta d’an muskuta kad’an kana tace “Are you alright mi Amiga...?”
Jin Ta ambaceta da Amiga ya sanyata sakin murmushi kana tace “Did you just call me your friend..?”
Jinjina mata kai Muhibbah tai kana tace “Of course I did... Ko mu ba k’awaye bane...?”
Murmusawa Zahra ta kumayi kana tace “Yeah, haka ne... You’re my only friend here... After all..!”
Muhibbah ta kuma murmusawa kana takai dubanta ga hoton da Zahra ke rik’eda... Ta d’an dubi Zahran wacce itama ita take duba
Lokaci guda Muhibbah Ke furta “You really miss your mom, right...!”
Jinjina mata kai Zahra tai tana mai kuma goge ragowar hawayen dake idanunta “So terrible... I miss my Maama... Ina kewarta sosai...!” Ta k’arashe wasu hawayen na gangaro mata...
Tausayin yarinyar ya kuma kama Muhibbah, lokaci guda ta matso kusanta sosai had’ida bata warmed hug... Lokaci guda take lallashinta had’ida kwantar mata da hankali...
“Ki kwantar da hankalinki Zahra, kuma kisa a ranki duk mai rai mamaci ne... Wataran muma duka babu mu, and be thankful you still have your Father who adores you very much... Ganinki haka cikin damuwa I’m sure it will break him.. So instead ki d’agawa mahaifinki hankali ki kwantar da hankalinki kici gaba da yiwa mahaifiyarki addu’a kinji koh...!” Ta k’arashe cikeda kulawa...
D’agowa Zahra tai tana dubanta kana Ta shiga jinjina mata kai alamun amincewa, lokaci guda take furta “You still have your mother, right.?”
K’uri Muhibbah tai mata, tana tina sanda mahaifinta da ‘yanuwansa sukai tarayya wajen kassara mata rayuwarta... Idanunta suka kad’a sukai ja lokaci guda....
Zahra ta d’an matsa daga jikin Muhibbah tana mai furta “Oh... I’m sorry, I’m sorry please...!”
Girgiza mata kai Muhibbah keyi had’ida k’ak’aro murmushi ta d’aura saman fuskarta “No is okay dear... Yeah, I still have my mom... But I lost my father when I was your age....!”
Zahra ta dubeta cikeda tausayawa kana tace “Kin rasa mahaifinki ni kuma na rasa mahaifiyata...!”
Muhibbah ta jinjina mata kai tana mai k’ok’arin saita kanta, lokaci guda taci gaba da furta “It’s part of life... Samu da rashi, wasu lokutan mu rasa mutanen da muke matuk’ar so sukeda mahimmacin a rayuwarmu... But babu yanda muka iya da hukuncin Ubangiji.. Saidai mu karb’e k’addararmu a yanda yazo mana...!”
Zahra ta jinjina kai kana tace “Yeah.. You’re right..!”
Muhibbah tai mata K’uri ganin kaman tana son fad’in wani abu ne... Hannayen Zahra ta kamo kana tace “If you need someone to talk to... Don’t forget I’ll always be here kinji koh...!”
Jinjina mata kai Zahra tai murmushi saman fuskarta take furta “You’ve no idea how much your presence means to me... Thank you Tia for being here with me...!”
“Ki daina min godiya Zahra.. Haka nan Allah ya jefa k’aunarki cikin zuciyata....!”
Yarinyar ta kuma murmusawa kana tace “Nima Ina k’aunarki...!”
Suka kuma murmusawa a tare kana Muhibbah ta hangi textbook na mathematics a gefen Zahra da alama karatu zatai... Ta d’an gyara zamanta tana mai furta “Lissafi ne za’ai...” Tai maganan da sigan wasa to cheer her up..
Zahra takai dubantaga book d’in kana tace “Oh.. Exams zamu fara gashi I’m not good at mathematics shiyasa zan fara dashi... Ko zaki koya min ne.. Dama Paa ke koya min...”
Ta zaro ido kad’an “Ni da lissafi.. Lissafi ba layina bane inama kice biology ne ko chemistry maybe wannn na iya karambani...”
Zahra ta murmusa tace “Wannan ma zaki koya min... But I don’t believe baki iya lissafi ba....”
Muhibbah ta d’an dubeta kana tace “Maiyasa Paa d’inki bazai koya miki ba tinda dama shi yake koya miki...?”
Take mood d’in Zahra ya canza, Muhibbah kaw na hankalce da ita dan dama so take ta d’ago wani abu shisa ta ja zancen nasu yai tsawo...
Zahra Ta d’an girgiza kai tace “I don’t want him to be my tutor anymore..!”
Gyara zama Muhibbah Ta kumayi kana tace “But why...?”
Dubanta Zahra tai kana tace “Paa d’in dana sani a Spain yasha banban da Paa d’in da nake gani a Nigeria.....”
Sameena📚
[6/19, 9:22 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*021*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Gyara zama Muhibbah tai tana duban yarinyar sosai kana tace “I don’t get you Zahra... What exactly are you trying to say...?”
Without any hesitation Zahra ta d’ago tana dubanta had’ida furta “Paa ya canza, I’ve a feeling he’s hiding something from me... Something very serious..!” Ta k’arashe damuwa k’arara saman fuskarta...
Gyara zama Muhibbah Ta kumayi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 65