bainar jama’a mutanen da yake jin nauyinsu yake kuma da kima a idanunsu...”
Zahra ta dubeta cikin rashin fahimta tace “But I know Paa, bazai bani amsa direct ba... Ni nasan ko Shid’in wane irin mutum ne...!”
Muhibbah Ta murmusa kad’an sai kuma tace “Kema ba direct zaki tambayesa ba... You accuse him of something very big... Abinda kike tunanin shi yake b’oye miki... Like mutuwar mahaifiyarki... Ina mai tabbatar miki muddin baida saka hannu ciki zakiji komai dan bazai juri jin kunyan idanun duniya ba... Take zai fayyace miki duk wani Abinda ya jima yana b’oye miki...!” Ta k’arashe cikin jaddada kalamanta...
Murmushi Zahra Ta saki kana tace “Kai amma na gode Tia... Perfecto, wannan shine kawai hanyar da Paa zai sanar dani abinda yake b’oye min.. Thank you thank you Tia... Gracias..!” Ta k’arashe tana mai rungumarta...
Murmushi Muhibbah keyi tana shafa kan yarinyar lokaci guda tana hango fuskar Mahmood yanda zai falling gaban d’inbin jama’an Masarautar nan... Zai sha kunya zai fad’i k’asa warwas kuma abinda zaifi masa ciwo shine d’iyarsa itace downfall d’insa... He’d definitely get what’s coming for him.... Finally zata gama da Mahmood da martabansa cikin Masarautar...! Ta k’arashe hawaye mai ciwo na gangaro mata, lokaci guda tinanin k’uncin rayuwa da uk’uban da ta shiga ansanadiyan yaran Sarkin na zuwa mata daki daki... Ta lumshe idanunta tana k’ok’arin saita kanta dan kar Zahra ta fahimci wani abu... A tare sukai bacci nan d’akin Muhibban tana mai kuma calming Zahra harda bedtime stories tai mata Zahra na dariya take fad’in Ta tuna mata lokutan baya haka Maa d’inta da Paa sukan sakata tsakiyan gado suyita bata tatsuniyoyi da labarai masu dad’i har bacci yayi gaba da ita kafin su tafi nasu d’akin.. Wasu lokutan ma haka gaba d’aya bacci yakan d’aukesu gaba d’aya.... Muhibbah saidai tai murmushi tana jin Zahra na labarin wasu kyawawan d’abi’u na mahaifinta.. Ba tareda tasan cewa cikin zuciyar Muhibbar babu komai sai tsanar Mahaifin nata da k’yamatarsa.... A haka bacci b’arawo ya sacesu...
**
Washe gari Fada ta cika fam da masu sarautun gargajiya, yaran Sarkin kaf suna nan idan ka d’auke Mahmood wanda tun safe yai ficewarsa daga Masarautar... Yazeed sai famkam famkam yake za’a tabbatar dashi matsayin sarki mai jiran Gado sannan Juma’a mai zuwa a nad’asa... Sautin algaita da tambura sai tashi suke cikin masarauta... Yazeed yasha gayu cikin kayan sarauta tamkar wani d’awisu haka yake taka k’asa Hadiminsa na biye dashi yana masa kirari da yabo irina gidan sarauta....
Babban Zauren taro ya cika fam da masu sarauta... Yazeed ya k’araso gaban Fu’ad dake binsa da muguwar kallo tun shigowarsa, murmushin nan nasa ya saki da gefen baki, yayi tsayuwa irinta masu ji a Mulki gaban Fu’ad, hannayensa hard’e yake dubansa kana yai gyaran murya kad’an yace “Aren’t you gonna congratulate me little brother... Ko har yanzu kana shakkun ni ne nan zan zama Sarki...?!”
Fu’ad ya d’an murmusa had’ida shafe fuskarsa da tafukan hannunsa biyu wanda yin hakan d’abi’arsa ce, ya k’arewa Yazeed kallo daga sama zuwa k’asa ya d’an kauda kai gefe yana kuma sakin murmushi yace “Ai banga Sarkin ba balle nai maka murna... B’ata lokacinka kawai kake don na tabbata kai d’in har abada bazaka tab’a zama Sarki ba muddin za’a bi cancanta da kuma dacewa...!” Ya k’arashe cikin kakkausar murya...
Yazeed ya kai k’ololuwar b’acin rai... Sai faman sakin huci yake yana tururi yake duban Fu’ad ji yake tamkar ya kai masa naushi sai faman dunk’ule hannunsa yake... Bazai iya jure kalaman Fu’ad ba... Ya yunk’ura zai kai mai naushi Jamal dake gefe yai saurin rik’esa a hankali yake furta “Don’t make a scene here please Yazeed..!”
Fu’ad na murmushi yake fad’in “Barshi... Please do it... Go ahead, do it Yazeed... Ka nuna musu asalin kaid’in ba wanda kake faking ba... Just do it...!” Ya k’arashe cikin huci....
Jamal ya janye Fu’ad yana fad’in “Ya isa haka Fu’ad, karku bamu kunya dan Allah... Martaban gidanmu zaku tab’a...!” Fu’ad ya d’an dubi Jamal had’ida fincike hannunsa ya koma gefe ya zauna yana sakin huci dan dukansu biyu da Yazeed d’in har Jamal d’in haushi suke basa idan ya tuna tilasta masa da sukai ya aikata laifin da har yau yake danasanin aikatawa tsawon rayuwarsa.. Laifin da ya zama silan rugujewar rayuwarsa da Farin cikinsa....
Yazeed kaw k’arasawa yai yana ci gaba da taku cikin babban Zauren masu muk’amin cikin Fada na kawo masa caffa (Gaisuwa irinta masu mulki) kai kace an riga an nad’asa... Shi kad’ai sai wani cika yake yana ayyana hukunci mai tsauri da zai yanke wa Mahmood da zaran an nad’Asa Sarki.... Tabbas Mahmood zai zama abin kwatance cikin Masarautar, sai ya d’and’ani kud’ansa Ta yanda sunan Sarki Yazeed kawai yaji an ambata zai daburce hankalinsa ya gushe... Ya murmusa kad’an yanajin badon Shid’in yanzu sarki bane da tuni ya fashe da dariya tsaban tsananin munin horon da ya tanadarwa Mahmood d’in.... Yana tsaka da tinanin ne yaji cak sautin algaita da tambura sun tsaya kaman daga sama ya hango Majidad’i ya shigo cikin Zauren kai kace jeho sa akai... Doguwar takobinsa rik’e a hannunsa sai faman huci yake tamkar wani zaki....
A d’ari Yazeed ya mik’e tsaye yana ware idanu tabbas wannan mahaukacin ne rik’eda takobi....
Majidad’i na dariya yake fad’in “Wow wow wow..! King Yazeed AbdulJabbar ai ban zanci har munyi wasan Takobin har kaci har an nad’aka ba.... Ka mance ne na tuna maka...? Agreement d’in namu ba haka bane Dark Prince... Bayan mun kai Mahmood k’asa Wasa za’ai d’aya ya fille kan d’aya wanda yai nasara shine zai zama Sarki..!!” Ya k’arashe cikin tsananin karaji yana mai zaro Takobin daga cikin gidanta...
Gaba d’aya illahirin jama’an dake wajen suka mik’e tsaye suna kallon kayan Al’ajabi wannan ya dubi wannan wancan ya dubi wancan....
Ana tsaka da wannan yanayi kururuwa da hayaniya had’ida ihu ya gauraye cikin Fada ana fad’in bayyanar Mahaukaciya... Dogarai sai faman guje guje suke ana kokawan Kamata amma sun kasa....
Giwa Alkyabba a hannu ta nufo k’asa dan ita kanta kururuwan da hayaniyar har tsakan kanta takeji ga hannunta dake tsananin mata k’aik’ayi wanda bata tab’a jin irinsa ba.... Tafiya kurum Giwa take ba tareda sanin yanda take jefa k’afafunta ba... Bayi sai k’amewa suke suna bata hanya ... lokaci guda take doka kiran Jakadiya a hargitse...
Masarauta babu lafiya...
*Toh fah yau akeyinta ga Izzatu ta bayyana....Ga kuma Yazeed da Majidadi ko yaya wasan zata kaya.....???
SameenaAleeyou📚
[8/13, 7:34 PM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*44*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
A daidai mashigar sashen nata suka had’uda Jakadiya jikinta sai karmami yake, illahirin jikinta rawa yake... Cikin tsananin tashin hankali Giwa taceda Jakadiya “Jakadiya mai nakeji... Shin da gaske Izzatuce ta bayyana...?!”
Jakadiya tai saurin jinjina kai tana mai zubewa saman gwiwoyinta “Allah shi taimakeki gaskiya ne Izzatu...Izzatu itace Ta bayyana cikin Fada...!”
Giwa ta zaro idanu waje tana dafe da k’irji take fad’in “Jakadiya hakan ba mai yuwa bane... Sanin kanki ne bayyanar matar nan tashin hankali ne tsantsa da musiba cikinta... Bayyanar Izzatu yana nufin za’ai babban rashi cikin Masarauta... Jakadiya ina Ubandoma... Shi kad’ai yake iyawa da Izzatu ta k’arashe cikin wane irin yanayi mai gauraye da d’imauta....
Jakadiya Ta had’iyi miyau da k’yar tace “Allah shi taimakeki kin mance cewa Ubandoma yana tsare hannun Masarauta... Bamuda hurumin tunk’aransa a halinda ake ciki...!”
“Jakadiyaa!!” Giwa ta darara mata wani irin gigitaccen tsawa wanda ya sanyata mik’ewa tsaye zumbur ba tareda tasan tayi hakan ba...
Giwa taci gaba da fad’in “Mune Masarauta, mune Fada Jakadiya babu Uban da ya isa ya hanani aiwatar da dik abinda naga dama cikin Masarautar nan, ba’a haifa ba kuma baza’a haifesa ba... Badon mahimmanci da rayuwar Izzatu kedashi a gareni ba da yau d’in Ta bak’unci lahira kowa ya huta...!! Jakadiya inaso Ki nemomin Ubandoma yanda ya shiga ya fita..!!”
Cikeda risinawa Jakadiya tace “An gama rankishidad’e..!!” Daga haka sa kai tai Ta famtsama cikin Masarauta tana tinanin Ta yanda zata soma neman Ubandoma gashi babu Waziri babu dalilinsa, duk tulin kiran da Giwa Ke masa sam bai d’aga ko guda d’aya ba... K’irjin Giwa yaci gaba da bugawa ba tareda tasan dalili ba... Hankalinta bazai kwanta ba muddin bataga Izzatu a hannunta ba... Ya zama tilas Ta canza ma Izzatu ma’ajiya idan ba haka ba tabbas duk wasu abubuwan da ta jima tana ginawa tsaf zasu rushe, sadaukarwar data jima tanayi zai tashi a aikin banza ita kuwa sam bazata tab’a barin hakan ya kasance ba...! Ta k’arashe tinanin nata tana mai fitowa daga sashen nata...
Ganin Masarautar a cike mak’il yasata tina cewa ashe akwai taron cikin Masarautar sam sabgogin gabanta sun sa ta mance hakan... K’irjinta ya kuma bugawa tamkar an sauk’e mata guduma... Lallai kuwa Izzatu bata zab’i rana mai kyau ba... Bazai yuwu yau d’in tayi shawagi cikin Masarauta ba hakan barazana ne Babba gareta... Babu shiri ta koma sashenta yanda ta umarci Hadimanta guda biyu su fiddo mata sutura na mulki da k’asaita dole ta nufi babban Zauren taro zama a fadarta bai ganta ba yau d’in....
Muhibbah da fitowarta kenan daga b’angaren su Umaima tayi rakiyawa Zahra ta barota tareda Umaiman bayan taceda Umaiman ta kula da ita dan har lokacin Zahra bata wani dawo dai dai ba nan ta hangi wilk’awan Giwa tamkar giftawan walk’iya... Koda ganin irin tafiyar da Giwa take kasan babu lafiya... Tai d’an jim tana mamakin meke faruwa dan su sam basuji duk hayaniyar da ake cikin Masarautar ba...
Wasu bayi dake kakkab’e babban parlorn Giwa na k’asa ta sinkayo suna fad’in tashin hankalin dake cikin Fada na bayyanar mahaukaciya... Gabanta ya yanke ya fad’i kenan mahaukaciyar nan ta kuma bayyana... Cikin d’an sassarfa Ta iso yanda bayin suke... Suna ganinta suka had’iye sauran maganganun nasu suka risina alamun girmamawa...
Muhibbah ta bisu da kallo ba tareda tacedasu komai ba tasa kai tai shigewarta... Zama bai ganta ba, dik yanda za’ai ya zama dole tasan yanda zatai taga mahaukaciyar nan k’ila wani haske ya kuma yaye mata....
Dik yawon da tai cikin Fada babu mahaukaciya Izzatu babu alamunta... Hango Giwa da tai ta nufi wata hanyar cikin shigata alfarma Hadimanta guda biyu biyeda ita hakan yasa Muhibbah tai saurin take masu baya....
Shigewarsu Giwa da kad’an Jakadiya ta iske Waziri da Ubandoma had’ida wasu dogarai majiya k’arfi dake rik’eda Ubandoman... Yanayinda Waziri ya ganta ciki ya tabbatar mata babu lafiya... Jakadiya ta dakatar dasu ta buk’aci ganin Waziri a keb’ance... Nan take sanar dashi abindake faruwa... Babu shiri Waziri ya umarci dogaran su kwance Ubandoma... Sukai yanda yace, ba tareda b’ata lokaci ba Waziri ya sanarda Ubandoma abindake faruwa... Kan kace mai sun fantsama neman Izzatu cikin Fada Ta yanda sukeda tabbacin zasu sameta....!
**
Matawalle ne ya mik’e a fusace yana fad’in “Kai Majidad’i haukar nan taka Ta ishemu kar ka kawo mana shashashanci nan...!”
Majidad’i ya d’ago Takobin sama ya nuna Matawalle dashi yace kana k’arasowa nan zan farke cikinka har lahira.... Wllhi na rantse da Ubangijin dake busan numfashi bani barin wajen nan sai na kara da wannan d’an tayin marassa kunyan... Sai na nuna masa ba’a cin amanata a kwana lafiya... Fad’a ni sayenta ma nake balle nawa... Zamu kara... Ko ni...Ko kai.... Wanda ya riga fille wuyan d’an uwansa Sarautar tasa ce..!!” Ya k’arashe yana mai duban D’angundan da suka shigo tare dashi yace “Fara aikinka..!”
Babu musu D’angundan ya soma busa irin nasu na ‘yan dauri yanayi yana wasa Majidad’i had’ida ihu irin nasu....
Daga Jamal har Fu’ad ganin abin suke tamkar mafarki... Meke faruwa ne haka... Wannan wane irin al’amari ne... Jamal yasan Majidad’i yasan ko wani kalan mahaukaci ne shid’in... Bayayiwa Majidad’i kallon cikakken mutum mai lafiya yasan sarai aka k’yalesa da d’an uwansa ko shakka babu zaiyi halin dabbobi ne ga d’an uwansa Yazeed tinda kaf abokan Majidad’i ‘yangunda ne da ‘yandauri hasalima Majidad’i yasha maganin k’arfe Takobi bata kamasa, trap shima ya had’awa Yazeed kan cewa su amince a gwada k’arfi da Takobi wanda duk yai nasaran kashe d’aya shi zai zama Sarki, yasan yasha na k’arfe dan haka a sauk’ak’e zai fille wuyan Yazeed mulki ya dawo gidansu....
Jamal yai tsalle ya raba tsakaninsu, yana mai duban Majidad’i yake fad’in “Babu wani wasan da za’ai... An jima da daina irin wannan jahilcin a Masarautar nan, addini ya wadata bazaku kawo mana abin fad’i a sauran masarautu dake kewayenmu ba...!!” Ya k’arashe cikin tsananin karaji....
Majidad’i da a yau d’in harda tozali ya shafa cikin idanunsa k’uri yaiwa Jamal kana ya tintsire da wata irin bahaguwar dariya, yana nuna Jamal da Takobin yake fad’in “Sai na fille wuyanka, na fara dakai kafin na isa kan d’anuwan naka Kaga sai ayi gawa biyu a take ku hutasar da mahaifiyarku da yin kuka biyu... Zatai kuka d’aya ma mutuwa biyu...!!” Ya k’arashe yana mai d’aga Takobin sama da niyyan sarawa Jamal... Daidai nan Giwa ta K’araso cikeda tashin hankali zuciyarta na zillo cikin k’irji... Hankalinta bai ida tashi ba saida ta hango Majidad’i na yunk’urin sauk’ewa d’anta mafi soyuwa a gareta Takobi a wuyansa... Giwa ta k’walla kiran sunan Jamaal da wane irin k’aran gaske daidai lokacinda Jamal d’in ya kauce Takobin ta samesa a kafad’a ya keta masa hannun riga had’ida kuskuran fatarsa kad’an, ji kake kyaaat....
Dukda zuciyarta dake tsananin bugu hakan bai hanata k’arasowa cikin parlorn ba tana fad’in waye ya baiwa wannan mahaukacin izinin shigowa cikin Fada...!
Kallon k’ask’anci Majidadi ya rakata dashi a daidai kokacin da aketa zubewa ana faman gaisheta....
Dariya ya kuma fashewa dashi kana yace “Madallah da isowarki Rankidad’e... Idan kin mance na tuna miki nine nan wanda ba’a sakani ba’a hanani kuma ajalin mulkin ahalin Sarki AbdulJabbar... Yayi daidai da kikazo nan ki gani da idanunki yanda basai ankai miki labari cikin Fada ba... Kiga yanda zan murk’ushe wuyan ‘ya’yanki musamman wannan babban maci amanan...!!” Ya k’arashe yana mai nuni da Yazeed da har lokacin bai daina binsa da ido yana sakin huci ba....
Dikda tsananin shakkarsa da Dogarai keji hakan bai hanasu yunk’urin dakatarda Majidad’i ba ganin yana k’ok’arin wuce gona da iri har Giwa ce zai dinga fad’i mata kalamai haka....!
Takubba biyu ya rik’e a duka hannayensa yana mai nunasu da Takobin yake fad’in dik wanda ya fasa tunk’arosa bai haifu ba... Ko step d’aya bazai k’ara ba amma duk wanda yai wauwautan k’arasowa gabansa ko shakka babu saidai uwarsa ta haifi wani amma bashi ba dan har lahira zai cire wuyan mutum... Ya k’arashe zancen nasa yana mai kuma d’ago Takubban....
Yazeed da ya kula ya maida hankalinsa ga dogarai tsalle yai ya tokari Majidad’i saida ya kaisa k’asa kana finciko Takobi guda dake hannun Majidad’in...
Majidad’i ya rakasa da kallon mamaki dan bai zaton Yazeed zai iya koda motsa Takobi hannunsa ba balle har ya k’wace.....
Lokaci guda Yazeed ya sakar masa murmushin nan nasa had’ida d’aga gira guda... Ya k’arasa gaban Majidad’i dake zube wajen yana juya Takobin dake hannunsa yasa k’afarsa guda ya take k’irjin Majidad’i lokaci guda yake nuna k’wayar idanunsa da tsinin Takobin, murmushin bai bar saman fuskarsa ba yake furta “Ina Jarumtar naka..? Kodai dama a baki ne ba’a fagen daga ba...?!” Shiru ya d’an ratsa tsakani kana Yazeed yaci gaba da fad’in “Zan iya fille kanka a nan idan naso, idan kuma naga dama muka kara naci k’arfinka sai na maidaka bawa har k’arahen rayuwarka... Ka rayu cikin yimani bauta... Na tabbata bazakaso hakan ba... Partner..!” Ya k’arashe muguwar murmushi saman fuskarsa...
Lokaci guda ya kuma d’agowa yana bin illahirin mutanen dake wajen da ido ciki harda mahaifiyarsa da tsananin tashin hankali ya nuna saman fuskarta... Fuskar nan nasa a matuk’ar d’aure ya bud’e murya yana fad’in “Inaso kowa ya bud’e idanunsa da kyau yaga yanda zan gama da wannan d’anta’addan kuma sannan hakan ya zamto izna da ishara ga duk wani mai yunk’urin ta’addanci irin nasa... Masarautar nan bazata lamunci ta’addanci ba..!!” Ya k’arashe cikin tsananin karaji
Majidad’i dake kwance k’asa gaban Yazeed da ya take masa k’irji da k’afa guda murmusawa shima yai ba tareda ko gizau ba yace “Tsari mai kyau Your Highness, dad’ina dakai akwai kwanya da kaifin basira... Kai da kanka kake kawo shawarin abinda za’ayi kuma shawarin Naka yayi daidai da tunanin duk wani mai san mulki... Naji dad’in shawarinka a karo na biyu... Mu kara a fafata wanda dik yaci galba kan d’an uwansa sai ya k’arashi rayuwarsa cikin Bauta... Zanso jinin AbdulJabbar ya zamto Bawa mafi k’ask’anci a gareni...Amma saidai kashh banjin zan yafewa duk wani wanda yaci amanata har na bashi daman sake rayuwa... Abu guda nake ma duk wanda yaci amanata shine KISA... Dama guda kake dashi yanzu da nake kwance gabanka ka gama dani tin ina kwance k’asa k’ark’ashin k’afanka dan nayi imani ni kuma idan har ka bari na tashi sai na kasheka...!!”
Yazeed da baisan dawan garin ba dan sam baisan Majidad’i yasha maganin k’arfe ba cikin tsananin huci yake kuma danna k’afarsa saman k’irjin Majidad’i ya shiga k’ok’arin darza masa Takobin da iyaka k’arfinsa, sai faman haki yake yana kuma darza Takobin amma saidai abin mamaki ko kad’an tak’i ratsa fatar Majidad’i balle ta shiga cikin jikinsa... Majidad’i yai masa K’uri saima sakin murmushi da ya soma lokaci guda murmushin nasa na rikid’ewa dariya had’ida shewa...
Jikin Yazeed yai bala’in sanyi... Ya darza ya darza Takobi ta kasa shigewa... Idanunsa suka firfito waje...
Cikin tsananin tashin hankali Giwa Ke girgiza kai tana k’ok’arin fincika daga rik’onda Jamal yai mata take fad’in “Jamal ka k’yaleni na ceci d’an uwanka mahaukacin nan kashesa zai...!”
Illahirin jama’an dake wajen wannan ya dubi wannan wancan ya dubi wancan... Harta Muhibbah dake lab’e daga gefe abin itama tsoro da mamaki ya bata... Ta kuma duban Majidad’i tana mamakin wanene wannan da tsana mai k’arfi yai k’amari tsakaninsa da ahalin sarki AbdulJabbar... Kuma ga dukkan alamu baida tsoro ko gizau a tattaredashi.... Tinaninta ya katse sana Majidadi ya tsagaita da dariyarsa yana duban Yazeed da tuni ya gaji da darza Takobi sai faman haki yake gumi na gangaro masa... Murmusawa yai kana yace “Ka d’auka zanzo wajen nan ne unprepared your Highness.... Ka tapka babban kuskure daka zaci you can outsmart someone like me.... Yanzu ni kuma zan baka abinda kake nema... Zan kashe na cire wuyanka ayi min roman k’wak’walwanka sannan nayi sark’a da k’wayan idanunka na ratayeta a wuyana...!!” Ya k’arashe yana mai daka tsalle daga kwance sai gashi ya mik’e tsaye Yazeed ya zube k’asa... Lokaci guda ya soma nufo Yazeed yana sakin muguwar murmushi Yazeed d’in na faman jada baya daga zaune zuciyarsa naci gaba da tsinkewa yaga mutuwa muraran....
Giwa na kuma fincika take fad’i ma Dogarai su kama wannan d’anta’addan amma ko gizau babu wanda ya matsa sabida tsananin tsoron Majidad’i dan yanda yace d’in tabbas zai kashe rai.. Ta koma gasu Galadima su Hakimi dansauransu tana fad’in haka sunaji suna gani zasu bar wannan mahaukacin ya kashe mata d’a... Suma babu wanda ya motsa saima muzurai da suke, yanda Takobin Majidad’i Ke tsananin k’yalli tabbas tsaf zai fille wuyan mutum....
Fu’ad da tuni kansa ya soma juyawa waya ya ciro ya kirawo Yayansa Mahmood amma bai d’agawa... Kansa taci gaba da sara masa... Sosai ya kame kansa dake tsananin sara masa ya fice daga cikin wajen gaba d’aya cikin wane irin sauri kaman zai kifa k’asa...
Muhibbah tana ganin ficewarsa tai saurin bin bayansa dan babu sauran abinda zata tsaya kallo ko shakka babu wannan D’angundan zai kashe Yazeed kisan wulak’anci a sauk’ake sakayyanta data ahalinta na bibiyan wannan ahali... Koda wannan tashin hankalin aka k’yale Giwa tasan ta sami nata ajalin kenan...
Gwara tabi wancan mahaukacin Fu’ad taga shi kuma mai yake shiryawa....
**
Kafin kace wani abu cikin Masarauta gaba d’aya ya yamutse, hargitse ne ta ko ina, Isowar Ubandoma da Waziri ya hana Majidad’i sarawa Yazeed Takobin wanda tuni ya sadakar Majidad’i ya fille wuyansa....
Ubandoma yace “Ku dakata zan fad’i gaskiya..!!”
Kallo ya dawo kan Ubandoma da Waziri..
Waziri ya jinjina masa kai alamun yayi magana....
Ubandoma ya soma fad’in “Yarima Mahmood baida laifi... Kawai na fad’i hakan ne dan ceton rayuwata da Yarima Yazeed yayi kuma shima Yarima Yazeed baida laifi duk abinda na fad’i ni ne nan na k’ago na fad’a babu laifin ahalin Marigayi Sarki AbdulJabbar ko d’aya..!!” Ya k’arashe yana mai duban Majidad’i..
Dariyar rainin hankali Majidad’i ya fashe dashi yace “Ni ne nan zaku rainama hankali ku maisheni dolo wanda baisan mai yakeyi ba... Kunje kun kitsa yanda zakuyi... Nayi imani ku kuka kashe min mahaifina dan ku d’in ba’a aminta daku nayi kuskure da na yarda dakai Yazeed bayan kaid’in kaci amanan d’anuwanka... Gashi nima kaci amanata... Kaid’in ba d’an halas bane dan haka yanzu zan gama dakai bayan na sanar da d’inbin al’umman dake wajen nan irin cin amanar dakaiwa d’an uwanka Mahmood kaso d’aura masa gagarunin sharri...!!”
Daidai lokacin Mahmood da Turaki suka shigo... Muryar Mahmood suka sinkayo yana fad’in “Mai kake cewa Majidad’i... Meye kuka k’ulla min kaida Yazeed..?!”
Giwa ta k’ara so ga Mahmood tana fad’in “Sadauki kada ka yarda da zancen wannan mahaukacin so yake ya raba tsakaninku.. So yake ya tarwatsa ahalinmu shid’in D’anta’adda ne... Kar ka yarda da kalma guda da zai fito daga bakinka....!”
Dariyan da Majidad’i ya fashe dashi ne ya sanyata dakatawa tana mai rakasa da wani irin duba...
Mahmood ya d’an dafata kad’an yana mai furta “Maami Kiyi hak’uri, Ina son jin abinda Majidad’i Ke son fad’i...!”
Majidad’i ya kuma fashewa dariya kana yace “Da kyau Rankaidad’e, ni kuma yanzu zan sanar dakai abinda wannan k’Aramin maras kunyan yaso shirya maka..!” Babu b’ara lokaci Majidad’i ya fad’I duk wani shirinsu da Yazeed a bainar jama’a... Yana ida fad’i ya kuma d’aga takobin zai dab’a masa Jamal ya isa a guje da zummar taimakawa d’anuwansa Yazeed ya janyesa daga wajen dan har lokacin Yazeed zube yake wajen gaban Majidad’i ya kasa koda motsa ‘yar yatsansa sabida hanjin cikinsa da suka gama kad’awa.... Saidai akayi rashin sa’a duk’awan da Jamal zai da niyyar taimakawa d’anuwansa Yazeed Takobin mai d’aukeda guba mai muni ta sauk’a kan k’afar Jamal... Ta yanki Jamal a k’afarsa na dama... Wane irin k’ara ya saki had’ida zubewa wajen yana mai kama k’afarsa... Sara Takobin da Majidad’i zai Dogarai suka sami chance d’in rufe kansa cikin buhu sukai masa caa suka cafkesa, D’angundansa zai arce shima aka capkosa... Tuni aka fice da Jamal neman agaji na gaggawa dan tuni ya had’a gumi sabida tsananin guba da Takobin Ke d’aukedashi, da ace a ciki ko wuya yankan ya samesa tabbas da tuni ya shek’a lahira...
Babu shiri Giwa da Hadimanta harmada Jakadiya suka take masu baya, saiga Giwa na kuka sharhsar da hawaye... Cikin zuciyarta take furta Jamal d’inta bazai mutu ba dan muddin ya mutu ko shakka babu itama binsa zatai... Tabbas wannan shine ma’anar bayyanar Izzatu... Jamal d’inta ne ashe.... Wani sabon kuka ya kuma kufcewa Giwa sai had’e hanya take suka nufi asibitin cikin Masarauta, Jamal bai daina damk’e k’afarsa dake tsananin masa zogi ba yana fad’in Giwa ta yafe masa mutuwa zai...
A b’angaren Mahmood kaw tinda Majidad’i ya ida fad’in abinda d’an uwansa na jini Yazeed yai masa bai kuma sanin meke wakana wajen ba... Yanajin hayaniyar mutane daga can nesa nesa.. He couldn’t believe his own brother can do this... Turaki ne ya taimaka masa ya zaunarsa saman kujera...
Turaki cikin Washe baki yake fad’in “Allah ya wanke ka abokina... Allah ya wankeka a idon duniya.... Mahmood d’ago kaji gashi nan ana sanarwa kaine Sarki, ka zama Sarkin Masarautar nan your Highness...!”
Siririyar hawaye ne ta gangaro masa sanda yaji Tambura da algaita na tashi ga zigazigi yana wasashi yana ambato sunansa anai masa kirari irin na Saraki “D’an Toron Giwa... Gaba salamun baya salamun... Allah ya baka... Allah yaja zamanin Sarki Mahmooda d’an AbdulJabbar jikan Mahmooda...!!”
Siririyar murya ce ya katse shagalin tana fad’in “Ku dakata shid’in bai cancanta ya zama Sarki ba...!”
Da tsananin mamaki illahirin jama’an cikin Zauren suka juyo suna dubanta da tsananin mamaki....
Mahmood ya furta “Zahra!!!” A hankali... Lokaci guda Zahra taci gaba da takowa cikin tapkeken parlorn hawaye na gangaro mata... A haka ta isa gaban mahaifin nata....
**
Haka Muhibbah ta dinga bin bayan Fu’ad har suka shige sashensa yanda ya fad’a bedroom ya janyo wata drawer ya jawo k’wayoyi cikin hannunsa yana k’ok’arin afasu cikin bakinsa yake fad’in “No no no please... Please forgive me... I was forced to do it.... Please just leave alone..!!” Ya k’arashe yana mai kuma tak’urewa jikin gini daidai lokacin Muhibbah ta shigo jiki a matuk’ar sanyaye take dubansa.... Yana k’ok’arin afa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 27 Chapter of 65