ko muce Sarki Mahmood mai jiran nad’i....
Haka kurum taji tabi bayan Ubandoma taga mai yake shiryawa...
SameenaAleeyou 📚
SameenaAleeyou 📚
SameenaAleeyou📚[8/23, 10:35 AM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*51*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Jikin tsakankanin gini ta mak’ale tana duban Ubandoma da ya shige wani d’aki... Mamaki ya cikata dan koda wasa batai zaton akwai d’akuna a wannan waje ba a ciki Masarautar... Ikon Allah watau shidai wannan masarauta wani irin gine gine yakeda masu rikitarwa wanda idan bakasan kansa ba tabbas zaka auka ramin da bazaka iya ficewa ba har a mance dakai... Ta kuma lallab’awa ta isa jikin k’ofar d’akin da taga ya shige tana lek’e a hankali... Duhuwan dake cikin d’akin ya hanata ganin abinda Ke aukuwa cikin d’akin amma kam jikinta ya bata wani abin yake k’ullawa a wannan waje mai surk’ullen gaske...
Tana jin alamun zai fito tai saurin komawa mab’oyarta Ta b’oye... Ubandoma ya fito yana ‘yan waige waigensa kana yasa kai ya shige cikin sauri.... Abin mamakin data gani wannan karon sai yafi d’aure mata kai... Gashi dai gini ne Babu alamun k’ofa amma sai gashi ginin ya bud’e Ubandoma ya fice... Tinanin Taswira mai wahalan fasaltuwan nan ya fad’o mata... Tabbas yayi kamanceceniya da ire iren wannan gini.. Amma ko dan Ta kuma fahimtar Taswiran nan zata isa jikin ginin taga ko Allah zaisa ta iya bud’e wannan k’ofa da baida wani alamu...
Yana shigewa da wasu ‘yan dak’ik’ai Muhibbah ta fito ta nufi jikin ginin tana shafawa a hankali.... Sosai ta k’urawa ginin idanu nan ta hangi wani dogon layi jikin ginin yasha kwalliya da fenti irinta gidan sarautar wanda sam bazakai zaton ba ado ne kawai na gine ginen gidajen sarauta ba... Dukda gabanta dake tsananin fad’uwa hakan bai hanata saka ‘yar tsarta tsakankanin wannan ginin ba... Ga tsananin mamakinta saiji tayi kaman ginin na motsi... Ta kuma yin basmalah ta tura yatsarta taji tabbas motsi yake.... Allah mai iko Wato ashe k’ofa ce aka yita cikin gini wanda sam ga wanda bai sani na bazai fahimci hakan ba... K’irjinta yaci gaba da fad’uwa tana tunanin mai zata gani bayan wannan gini idan ta bud’e... Lumshe idanunta tai tana k’arfafawa kanta gwiwa da fad’in zata iya da yardar Allah... Ta kuma ambato sunan Allah kana ta d’an bugi ginin da hannunta.. Ga tsananin mamakinta sai gani tai ginin ya soma bud’ewa d’aki mai tsananin duhuwa ya bayyana... Mamaki ya kuma cikata, tabbas d’aki ne a wannan waje.... Toh miye a ciki..? Bata kaiga samo amsa ba ta hango mutum daga can k’uryar d’akin tana ci gaba da karjan gini alamun bataji shigowarta ba....
Dukda bayanta kawai take iya hanga bataga fuskarta ba dashike Ta bada baya ne ma k’ofar, hakan bai hana Muhibbah ci gaba da takowa cikin d’akin k’irjinta naci gaba da bugawa ba, addu’o’i kuwa duk wanda yazo saman harshenta shi takeyi....
A hankali take takawa har ta isa taga abinda matar take.... Cak Izzatu Ta dakata da abinda take dan taji kaman mutum ne a bayanta... Aiko take ta juyo da zummar capko mutumin dake bayanta, Muhibbah ta rintse ido tana jiran mai auka ya auku tinda ta gane matar mahaukaciyar nan ce da Ta kirawo sunanta.... Bata auka mata ba saima tsayawa da tai tana binta da kallo...
Muhibbah ta bud’e idanunta a hankali tana duban matar da tai mata K’uri, cikin d’an tsoro tsoro take takowaga matar wacce tuni Ta soma sakar mata murmushi... Muhibbah taji k’warin gwiwa na zuwa mata.... Murmushi itama ta sakar mata kana tace “Mai kikeyi a nan... Wa ya canza miki d’aki...?!”
Bata bata amsa ba sai nuna mata ramin da take tono datai jikin gini wanda tuni yayi zurfi.... Muhibbah ta dubi ramin da mamaki Ta kuma duban matar... Jinjina mata kai matar tai k’walla tab idanunta... Lokaci guda take kuma janyo hannun Muhibbah ta zaunarta jikin ramin tana mata alamu da hannu kan ta tayata suci gaba da tonon ginin....
Ita dai Muhibbah duk bata kawo komai ba, duk a nata zaton cikin haukar wannan matar take ceda ita su karje gini... Ta k’ak’aro murmushi ta sakar mata kana Ta mik’e ta shiga janyo hannunta tana fad’in “Zo mu tafi... Zan fitar dake daga Masarautar nan, bazan bari su kuma zaluntarki ba... Zo muje..!” Ta k’arashe tana mai kuma janyo hannun mahaukaciyar wacce tak’i koda motsa k’afarta ne...
Muhibbah ta juyo ta dubeta da mamaki kana tace “Bakiso ki kub’uta daga hannun wad’annan azzaluman ne...?”
Matar ta girgiza mata kai alamun a’a kana ta kuma mata nuni da ginin da take karja.... Muhibbah ta dubi ginin ta d’an murmusa kad’an dan tasan duk cikin gushewar hankali ne kana ta matso kusanta tace “Kar ki damu ni nasan k’ofar da zamubi mu fice ba sai kin karje gini ba... Idan kika tsaya yin wannan har zasu cimma Ki su kuma kamaki... Zo muje kafin ya dawo...!” Ta k’arashe tana mai kuma janyo matar wanda wannan karon sosai ta b’ata fuska tana duban Muhibbar... Lokaci guda ta finciki hannunta daga rik’onda Muhibbar tai mata ta koma jikin ginin taci gaba da karjewa ba tareda Ta kuma bin takan Muhibbah ba...
Muhibbah ta bita da idanu cikeda mamakin yanda ta koma ta duk’a gaban garun tana ci gaba da k’walk’walewa... Sauk’e ajiyan zuciya tai a hankali wata zuciya na cewa bazaki Iya da matar nan ba Ke kad’ai, Ki fice Ki karya Giwa kafin ki dawo ki ceci matar nan idan ba haka ba kema in suka kamaki haka zasu maisheki, kinga baki taimaki matar nan ba gashi kema an kamaki.... Da wannan tunanin Muhibbah tasa kai zata shige ta k’yale Mahaukaciya Izzatu...
Har takai k’ofa sai kuma ta tsaya cak tana tunanin anya lafiya mahaukaciyar nan Ke karjan gini haka kurum... Anya bazata duba abinda mahaukaciyar nan keyi ba...? Take taji tana son ganin abinda mahaukaciyar keta k’ok’arin nuna mata tai zaton cikin haukarta ne... Dawowa da baya Muhibbah tai ba tareda taceda mahaukaciyar komai ba ta duk’a a hankali tana duban abinda take... A hankali Muhibbah ta saka idanunta tana duban cikin ramin wani irin yanayi da bazatace gashi ba yana fuzgarta, zuciyarta na bugawa cikin nastuwa... Tai k’ok’arin janye hannayen Izzatu daga jikin ginin kana ta saka k’wayar idanunta tana lek’awa.... Duhu ne iyaka ganinka amma taji wani irin yanayi kam... Toh nan d’in kuma inane... Wata zuciyar tace k’ila mahaukaciyar tayi zaton ta nan d’in zata sami hanya...! Hakan yasa Muhibbah waigowa da niyyan k’ok’arin shawo kan mahaukaciyar nan Ta amince Ta bita su fice... A yunk’urin da zatai da zummar waigowa kunnenta guda ya tsaya daf jikin ramin da Izzatu ta karje yayi zururu... Kaman wanda iska ya koro sautin haka ta jiyo sauk’an numfashin mutum cikin kunnenta... Zuciyarta ta kuma tsinkewa.. Tabbas akwai bil’adam bayan wannan gini... D’agowa tai Ta dubi Izzatu da tai mata K’uri kana tace “Akwai mutum a bayan ginin nan..!”
Izzatu Ta jinjina mata kai a hankali alamun tabbatarwa... Cikin sauri Muhibbah ta mik’e tana duban Izzatu take furta “Wannan gini bazamu iya turasa ba, koda zamuyi kwanaki muna tono... Amma da izinin Allah zamu kub’utar da mutumin nan dake rufe a wannan fursuna mai tsananin duhuwa...”
Ta kamo hannayen Izzatu duka biyu tace “Kin tuna Taswiran da kika bani..?”
Izzatu ta jinjina mata kai alamun eh.. Muhibbah taci gabada fad’in “Zanen dake cikin Taswiran yayi yanayi da ire iren wad’annan gine gine na sarauta, yau d’in na tabbatar da haka... Idan muka fice a nan zamu zaga ta baya ko Allah zaisa mu sami k’ofar da zata cimmamu da d’akin da aka rufesa... Muje bamuda sauran lokaci...!” Ta k’arashe tana mai janyo hannun Izzatu suka fice cikin sauri....
Saidai koda suka fito babu wata alamu da zasu iya gane akwai hanya da zai sadasu da wata d’aki a wajen... Muhibbah tai K’uri tana kallon dogayen gine ginen... Waigowa tai Ta dubi Izzatu da itama gine ginen take duba... Fuzar da fuci kad’an Muhibbah tai kana ta nufi wata hanyar dake nan b’angaren hagu da ginin... Nan ma shiru babu alamun hanya...
Magana Izzatu take mata saidai maganar bata fita baka fahimtar komai sai gwalamniya... Muhibbah tai mata K’uri cikeda tausayawa, lokaci guda ta matsoga Izzatu ta kuma dafe hannayenta tace “Banjin zamu samu hanyar da zamu kub’utar da mutumin dake wancan d’akin amma mu koma cikin wancan d’akin muga idan zamu iya karje ginin cikin gaggawa...!”
Ta fad’i hakan ne Dan baiwa mahaukaciyar da a yanzu take tantaman haukarta k’warin gwiwa.... Muhibbah ta kamo hannunta suka saka kai zasu koma cikin d’akin... Kaman daga sama suka sinkayo murya yana furta “Ina kuke tunanin zakuje..!!!”
Cak suka tsaya yayinda Izzatu ta finciki hannunta ta soma jada baya tana nok’ewa had’ida yin wasu abubuwa na marassa hankali.... Muhibbah kaw rintse idanunta tai a hankali Dan ta tabbata yau kam shikenan an kamata....
Mutumin yaci gaba da takowa yanda suke har lokacin idanun Muhibbah a rintse suke, ya bud’e murya yace “Juyo Ki kuma nuna kanki..!”
************* Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
Bata juyo ba sai addu’o’i da take jerowa cikin zuciyarta.... The more tana add’ua the more tana jin k’warin gwiwa na zuwa mata tsoro na yaye mata... Ji tayi zata iya fuskantar koma wanene idan ta kama su kara ne ma sai su kara d’in...
Fuska a matuk’ar murtuk’e Ta waigo cikin dakewa...
Ubandoma yai mata K’uri yana son gane ina ya santa... Ya saki murmushi yana nunata da yatsa yace “Kece.!! Haba ai biri yayi kama da mutum, Jakadiya tayi gaskiya da tace bata yarda dake ba... Ashe ked’in kin jima kina k’ulla abubuwa cikin Masarautar nan.. Akwai babban dalili da ya shigo dake... Zaki gane kurenki yarinya... Zaki d’and’ani kud’arki, zaki gane cewa ba’a diran mik’iya ma Masarauta irin wannan... Kin tapka babban kuskure yarinya.. Kin hak’i kabarinki da kanki... Yanzu ba tareda b’ata lokaci ba zan d’aukeki ga Giwar Amale... Na tabbata zan samu babban rabo...!!” Ya k’arashe yana mai fashewa da dariya...
Yayinda Muhibbah tai masa K’uri tana duban yanda yake dariya... ita kaw Izzatu gefe ta koma ta mak’ale jikin gini tana girgiza kai... Ubandoma na k’ok’arin takowa yanda Muhibbah take Izzatu ta k’arso a guje ta rungume Muhibbah tana hawaye take Girgiza wa Ubandoma kai alamun a’a...
Ko gizau Muhibbah batai ba saima ci gaba da duban Ubandoma da take da idanunta wanda babu alamun tsoro ko sarewa cikinsu... Cikin dakakkiyar murya Ta soma furta “Shin wace riba da ka samu daga wajen Uwargijiyarka idan ka bari aka cutar da rayukan da basuda alhakin kowa..? Shin wace riba zaka samu a wannan ta duniya wacce ita d’in ba matabbatace face GIDAN ARO... Shin wace riba ka samu a iyaka shekarun da kai kana ha’intar mutane da basuda hakki... Ka dubi tsawon shekarun da kai a baya, ka d’auki tsawon rayuwarka kana bauta ne ma wacce bata ganin darajarka balle kimarka saima d’inbin wulak’anci da tozarci da kake fuskanta daga gareta... Shin mai zai ragu jikinka idan ka zab’i ka aiwatar da abinda ya dace... Na tabbata tsawon rayuwarka ka yisu ne a matsayin bawa maras ‘yanci wanda sai abinda aka umarcesa...!”
Katseta yayi da fad’in “Ke yarinya hattara, kar Ki bada shaida akan abinda bakida masaniya... Wannan abu da kikaga nakeyi nima ba son raina bane... Kaman yanda kika ce tsawon rayuwana na shafesa ne wajen bauta tabbas haka ne.. Kuma wannan abu da nake yanzu inada tabbacin shi zai bani ‘yanci da na jima ina nema sabida duniyar nan yanzu babu abinda za’a baiwa Giwa Ta shiga nishad’i tamkar wannan matar..!” Ya k’arashe yana nuni da Izzatu, lokaci guda yaci gaba da fad’in “Wannan mahaukaciya da kike gani itace tikitin samun ‘yanci na da zuri’ata..!”
Muhibbah ta murmusa kad’an tace “Kanada tabbacin zata cika maka burinka..? Kokuwa a iyaka tsawon lokacinda ka kwashe kana mata bauta Ta tab’a cika maka alk’awari...?!”
Ubandoma yai shiru yana juya kalamanta cikin sanyin jiki...!
Ganin yanayinsa ya kuma baiwa Muhibbah k’warin gwiwar ci gaba da magana...
“Babu cika alk’awari a duniyar da babu komai cikinta face zalunci... Shi azzalumi a koda yaushe hanyar da zai rud’eka ya cutar dakai ya kuma yaudareka yake nema.. Babu Aminci a duniyar da yarda da rik’on amana yai k’aranci cikinta..!” Ta kuma sassauta murya tana duban Dattijo Ubandoma tace “Baba lokaci bai k’ure maka ba, you can still do the right thing... Zaka iya zab’an tafarki mai kyau... Alk’awarin Allah gaskiya ne Baba... Shid’in yana tareda masu gaskiya ne..! Kai abinda ya dace ka juya bayawa azzalumai.. Kaji tausayin wannan Baiwar Allah da halinda Ta tsinci kanta ciki wanda idan son ranta ne bazataso ta ganta a yanayin da take ba..!” Ta k’arashe cikin rawar murya irinta mai kuka....
Allah sarki saiga Hawaye suna gangarowa daga idanun Ubandoma... Ya k’arasa jikin dakali dake wajen ya zauna yana mai ci gaba da matsan k’walla... Lokaci guda yana tuna abubuwan da Giwa ta umarcesa yayi marassa kyau, ya tuna babu alk’awarin da ta tab’a cika masa, ya tuna kalan wulak’acin da tai masa wanda bazasu lissafu ba ciki harda marin da Jakadiya tai masa, wanda tayi hakan ne bisa umarnin Giwa...
Muhibbah ta dubesa ta kuma duban Izzatu hawaye na gangaro masu gaba d’aya... Lokaci guda Ubandoma yaci gaba da fad’in “Kaico na! Kaicon son zuciya irin nawa..! Tinda nake ban tab’a jin kalaman da suka sanyar min da gwiwa suka sakani nadama ba irinta yau... Hak’ik’a na tafiyar da rayuwata ga bautawa zalunci da juyawa gaskiya baya... Ban tab’a danasanin abubuwan da nayi irinta yau ba.. Yarinya kinyi gaskiya da Kikace azzalumi bazai tab’a cika alk’awarinsa ba, hanyar da zai amfana dakai kurum yake nema... Babu lokacinda zan miki bayanin abubuwan da nayi marassa kyau bisag umarnin Gimbiya Turai amma da na baki labarin komai a yanzu basai anjima ba... Ina fata wad’anda na zalunta ta dalilinta zasu yafeni... Musamman Mahmood... Shid’in mutumin kirki ne... Kuma ina tsoron kasancewarsa cikin Masarautar nan da azzalumai sukai yawa dan rayuwarsa na cikin had’ari..!”
Kiran sunan Mahmood da yai ya sanya wasu hawaye kuma gangarowa Muhibbah tana mai tuna mummunar zato da tai masa a baya.... Tai saurin saka hannu Ta share hawayen da suka gangaro mata tace “Baba tinda ka fahimci haka Alhamdulillah, Ina mai tabbatar maka in sha Allahu bazan bari wani ya cutar da Mahmood ba... Yanzu ka taimaka mu fitar da wani rai da yake bayan ginin nan, mu kub’utar dasu daga wannan azzaluman masarauta..!”
Ubandoma ya dubeta yace “A ina kenan...?!”
Muhibbah tai saurin masa nuni da cikin d’akin kana ta basa labarin abinda ta tadda Izzatu nayi... Yai shiru kaman nazari kana ya murmusa yace “Hak’ik’a gidan nan yanada surkulle da k’ofofi wanda wasu ma iyayenmu basu San dasu ba... Abinda yasa nima nasan da wannan waje an tab’a rufe mahaifina a ciki ne lokacin sarki Baban AbdulJabbar, mahaifina sunyi wani laifi sunci amanan masarauta aka kawosu wanann waje shiyasa nasan da wajen, ba kowa ya sani ba cikin Masarautar nan... Kuma akwai ire iren wanann da dama cikin Masarautar nan... Kinga can..!” Yai mata nuni da wani ginin... Yace inada tabbacin a nan k’ofar d’akin yake, Zo muje...!” Ya k’arashe yana mai sab’a babban gare yayi gaba...
Muhibbah tabi bayansa cikeda mamakin yanda zasu samu k’ofa a wannan waje....
Aiko suna zuwa taga Ubandoma yasa hannu ya tab’a zanen Tanbarin Masarautar da akaima ginin kwalliya da ita... Aiko nan garun ya soma gaucewa... Ga tsananin mamakinta saiga k’ofa....
Suka dubi juna itada Ubandoma, lokaci guda yace da ita su shiga... Itadai da bismillah ta shige cikin d’akin Mahaukaciya Izzatu na biye dasu... Suna shigewa kuwa Ubandoma ya zaro tocilan dake aljihunsa wanda yake haska waje idan zai kawo wa Izzatu abinci ya shiga haska cikin d’akin... Ga tsananin mamakinsu k’aton k’arfe suka hango had’e da manyan sark’ok’i an dadd’aure mutum dashi ga kwanukan abinci ga syringe na allurai a warwatse a wajen... Mamaki ya cikasu, kallo guda zakai ka fahimci mutum ke rayuwa cikin buwayar Ubangiji a wajen... Tsoro da mamakin zalunci dake cikin wannan masarauta suka kuma kama Muhibbah... Cikin sauri Ubandoma ya k’arasa ga mutumin dake fidda numfashi da k’yar alamun ya gama galabaita sabida tsananin yunwa da k’ishin ruwa.. Kai a d’auke wannan ma mutum ya rayu wannan waje saidai buwayar Ubangiji wanda babu abinda ya gagaresa, bazaka mutu ba sai ranan da yace zaka mutu, duk tsanani kuwa idan lokaci baiyi ba shi zai raya abinsa.... Ubandoma jiki na rawa dan shima ya razana sosai... Yasa hannu ya d’an mirgino da mutumin wanda babu komai jikinsa sai ‘yar bante irinta bayin zamanin da turawa Ke d’iban bayi a k’asashen bak’ak’en fata.... Cikin yankewar zuciya ya furta “JA’AFARU...!!”
Sunan Ja’afar da ya ambata ya Sanaya Muhibbah dake bin syringe d’in kallo tana karantawa abinka da wacce Ta karanci wani fanni na kula da majinyata... Tuni ta daskare zuciyarta naci gaba da tsinkewa.....
SameenaAleeyou 📚
[8/24, 10:02 AM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*52*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Sunan Ja’afar dataji Ubandoma ya ambata ya sanyata mik’ewa jikinta na matuk’ar rawa ta nufo yanda yake a kwance tamkar marass numfashi... Tuni Ubandoma ya warware rawanin kansa ya suturta ma Jafar jikinsa... Muhibbah tai tsaye tana duban fuskar mutumin da Ubandoma ya ambata da Jafar, yau ahekaru goma sha hud’u da kwanaki kenan rabonta dashi... Tabbas ya canza koda kuwa bai cikin yanayin wahala da suka tsincesa ciki, girma ya k’ara canzasa saidai duba guda tai masa ta fahimci shine... Wasu irin hawaye suka gangaro mata, wannan masarauta cike yake da abubuwan mamaki... Tana nan tsaye tamkar statue ta sauraro muryan Ubandoma naci gaba da fad’in “Ja’afaru bawa ne a Masarautar nan wanda ya b’ace tsawon shekara guda yau... Ni nasan ba b’acewa yayi ba Dan a zatona Giwa ce ta gama dashi, ashe a wannan waje aka ajesa ba tareda sanin kowa... Lallai na yarda Giwa zata iya yin komai sabida Ta dawwama kan Karagar mulki... Mulkin duniya da batada tabbas wanda duk soyayyarka da ita dole ka barta..!”
Muhibbah ta duk’a a hankali hawaye naci gaba da gangaro mata... Ta dubi Ubandoma tace “Anya yanada rai...?!”
Ubandoma ya jinjina mata kai bayan ya tab’a wasu jijiyo a wuyansa “Yanada rai, zuciyarsa na bugawa... Bai mutu ba... Abinyi shine muyi gaggawan kub’utar dashi da kuma Izzatu daga cikin Masarautar nan kafin Giwa ta cimmamu Dan nasan duk yanda take yanzu hankalinta a tashe yake...!”
Muhibbah tai saurin jinjina kai tana mai mik’ewa tsaye tace “Haka ne wannan gaskiya ne... Kuma kaima idan tasan ga abinda kayi bazata k’yaleka ba.. Toh amma yanzu meye abinyi..? Ina zamu kaisu..?!”
Ubandoma yai shiru tamkar mai nazari sai kuma ya dubi Muhibbah yace “Akwai wani k’auye can gabas da Masarautar nan mai suna Galambi, k’auyen iyayen matata ne, yanzu haka na tura yarana can tun lokacin da Waziri da Yazeed suka soma min barazana da yarana kasancewar matata Ta rasu banida kowa sai yarana guda biyu... Shisa nake neman ‘yanci na bar bauta ya ko wace irin hanya domin na inganta rayuwar yarana guda biyu kada suma su taso cikin bauta.. Alk’awari na d’aukarwa mai d’akina shisa kikiga idanuna sun rufe bani gane daidai da abinda ba daidai ba burina na samu ‘yanci na cika mata burinta na fidda yaranmu daga k’angin bauta...!”
Muhibbah ta jinjina kai tace “Na fahimceka Baba... Toh yanzu ya za’ai mu kaisu garin matar taka...?!”
Ubandoma yace “Idan muka tafi gaba d’aya Ke za’a iya zarginki a Masarautar nan... Zaifi kyau ni na tafi dasu tinda nasan dole a nemeni kuma dole ayi tunanin ni ne na taimaka masu, sannan babu abunda zasu min barazana dashi a Masarautar nan tinda na tura yarana can da nisa yanda bazasu samesu ba... Ni zan tafi taredasu ayi masu duk wani jinya da ya kamata Dan iyayen matata sunada sani sosai akan abinda ya shafi cututtuka da kuma magani, Allah ya huwace masu wannan baiwar..!”
Muhibbah ta jinjina kai tace “Alhamdulillahi! Amma wani hanzari ba gudu ba Baba... Shin ya za’ai mu fice da Jafar yanda yake a kwancen nan ba tareda an ganmu ba...?!”
Ubandoma ya murmusa kad’an yace “Karki damu d’iyata wannan ai ba matsala bace, muda muka taso cikin bauta... Bari kiga yanda akeyi...!”
Ga mamakin Muhibbah dik girman jiki da tsawo da Allah ya huwace wa Jafar sai gani tai Ubandoma ya ciccib’esa ya azasa bisa kafad’arsa... Ya dubi Muhibbah yace ta fito da Izzatu su bi bayansa... Jinjina masa kai kurum tai kana ta janyo hannun Izzatu suka bi bayan Ubandoma sauri sauri gudun kada suyi artabo da wani...
Ga mamakin Muhibbah wani hanya taga sun nufa can yamma da Masarautar, itadai sai waige waige tsoron kada a gansu...
Ubandoma ya d’an dubeta yace “Ki kwantar da hankalinki babu wanda zai ganmu, wannan k’ofa da kike gani ba kowa ya san da ita cikin Masarautar nan ba... K’oface da dakarunmu suke kwanton b’auna ga abokan gaba musamman a lokutan da suke kokonton samun nasara... Tsohuwar k’oface mai tsohon tarihi wanda a mutanen wannan zamani dake rayuwa cikin Masarautar ba kowa yasan da ita ba...!”
Muhibbah ta jinjina kai suna ci gaba da tafiya tace “Baba da alama kanada ilimi sosai gameda wannan masarauta, kasan abubuwa da yawa k’unshe cikinta...”
Ubandoma ya jinjina kai yace “Shiyasa Giwa Ta janyo ni jiki take amfani dani... Kinsan ance da d’an gari akanci gari... Mahaifina shine Hadimi mafi kusanci ga mahaifin Sarki AbdulJabbar Wato Sarki Mahmuda, Mahaifina yasan tarihin Masarautar nan sosai wanda shima wasu daga nasa Mahaifin ya gada ya sani, nima nawa mahaifin ya sanar dani wasu abubuwa gameda Masarautar har kawo lokacinda aka had’a baki dasu tsautsayi ya auka masa yaci amanar masarauta aka kawosu wannan fursunan da kikaga na San da ita... Giwa Tasan inada masaniya sosai gameda Masarautar nan shiyasa batai wasa da tarayyarmu ba... Babu wanda ya kaini sanin cikin Masarautar nan wannan dalili yasa idan Mahaukaciya Izzatu ta b’ace cikin Masarauta ta shiga wani sak’on babu mai iya zak’ulota sai ni...!”
Ubandoma yaci gaba da fad’in “Kar na shiga miki wani labari daban kinji dalilin...!”
Muhibbah ta kuma jinjina kai a daidai sanda suka shige wata k’ofa wanda itama ba lallai ka fahimci k’ofa bace idan ba kanada masaniya ba.... Haka sukaita ture gidan gizo gizo suna kutsawa alamun an jima ba’a non wannan hanyar....
Tafiya mai d’an tsawo sukai kana suka fita daga cikin Masarautar...
Ubandoma yace “Alhamdulillah mun fita daga cikin Masarauta... Shin zaki iya gane hanyar komawa..?!”
Muhibbah tai shiru tamkar mai nazari sai kuma tace “Idan ban gane ba sai na bi ta Sabon titi na shiga ta babban k’ofa wanda kowa ya San da ita...!”
Ya jinjina kai yace “Hakan yayi dan kar wani ma ya zargeki, nasan watak’ila Giwa ta soma nemanmu cikin Masarautar....!”
“Toh yanzu Baba wa zai kaiku tashar mota...?!” Ta tambaya tana dubansa...
Ubandoma yai shiru yana dubanta cikeda kulawa, wasu abubuwa suna zuwa kwanyarsa... “Amma yarinya kafin mu d’auki hanya ina son sanin wacece Ke...?!” Tambayar da yai mata kenan yana mai tsareta da idanu...
Ta d’ago idanunta masu cikeda rauni wannan karon jin irin tambayar da yai mata... Kafin ta kaikaga basa amsa ya d’ago ‘yar yatsarsa guda yana nunata... Lokaci guda yake furta “Tabbas kece... Kece SAUDATU... Yarinyar da matsafan Giwa suka bata tabbacin cewa K’addarar wannan masarauta na tafe da tata k’addarar... Tabbas kece yarinyar da Gimbiya Turai take nema... Kece silan aje Mahaukaciya Izzatu da Turai tayi... Bansan labarinki ba yarinya amma Rayuwarki na cikin had’ari Babba a wannan masarauta, mai ya dawo dake yarinya..?!”
Muhibbah ta share hawayen da suka gangaro mata kana tace “Kaman yanda kace Baba, da izinin Allah ni ce nan zan kawo k’arshen mulkin zalunci da Turai ta d’aura Masarautar nan bisa wannan kad’ai ya isa dalilin da zaisa na dawo... Karka damu Baba, Allah bazai bata nasara ba wannan karon... In sha Allahu bazata kuma cutar da wani wanda baiji ba bai gani ba...!”
Ubandoma ya jinjina kai yace “Tinda kikace Allah kin gama magana... Wanda duk yakeda Allah shi yake da babban makami da kariya a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 33 Chapter of 65