da abinda take sakamakon sinkayo muryarsa da tai yana fad’in “Idan kin gama karantawa Jakadiya tana jiranki a k’ofa..!” Daga haka bai kuma cewa komai ba ya fice cikin taku irinta masu mulki hannayensa hard’e Ta baya..
Muhibbah ta lumshe idanunta, wasu hawayen suka gangaro mata, Wato ma Jakadiya ce zatai mata rakiya zuwa k’ofar Fadah.. Aiko ya bari dai tayi sallama da ‘yaruwarta Umaima da kuma Ummi...
Lokaci guda tasa d’aya hannunta tana share hawayenta take furta “Enough Muhibbah, ya isa haka... Ina amfanin zama da mutumin da bai k’aunarki.. Tinda ya zab’i ku rabu, fine, sai ku rabu d’in.. He’s not worth a single drop of your tears..!” Lokaci guda ta shiga warware takardan a hankali..
Cak Ta tsaya tana kuma nanata abinda ta gani saman takardan, a hankali Ta furta...
“DNA test result..!”
Idanunta suka sauk’a k’asa, sunanta take gani ga kuma sunan Zahra... Zuciyarta tai wani irin tsinkewa... A fili take furta “70% matched..!” Kenan itada Zahra are related... Kusanci mai tsanani wanda zasu iya kasancewa sun had’a both iyaye.. Kenan Zahra ‘yaruwarta ce da suka fito ciki guda, mahaifiyarta da mahaifinta aune suka haifi Zahra... Take taji duniyar na juya mata.. Ta dafe kujera a hankali ta zauna tana kuma juya takardan.. Nan wata takardan Ta fad’o tai saurin d’auka Ta warware da zummar karantawa..
Daidai lokacin Ummi, Mommy da Umaima suka shigo...
SameenaAleeyou 📚
[10/5, 6:23 AM] +234 703 881 5154: *MUHIBBAH*
*84*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Takarda ce mai k’unshe da bayanan komai gameda Zahra... Hawaye basu daina zubowa daga idanunta ba take ci gaba da juya takardan, ta d’ago idanunta masu zuban ruwa tana dubansu d’aya bayan d’aya, sud’inma ita suke duba hawaye saman fuskokinsu... Umaima ta d’an dafe hannunta guda tace “Go ahead Sis, read it... Read..!” Ta k’arashe murmushi da hawaye saman fuskarta...
A hankali Muhibbah ta jinjina mata kai kana Ta soma karantawa
_”Yammacin wata Rana ce mai d’aukeda bak’ar hadari wanda ya sanya tsaban duhun hadarin da k’yar mutum Ke iya ganin gabansa.. A wannan yammaci d’iyata Zahra ta shigo rayuwata... Kan hanyarmu muke na dawowa daga garinsu matar abokina Turaki, nayima Turaki rakiya a lokacin yana zuwa neman auren Hidaya.. I was the one driving the car sanda wata mata from no where ta bayyana gabanmu, ban kula da ita ba kasancewar akwai duhun hadari sosai.. Ga sauri da muke dan mu samu mu iso Masarauta kafin wannan ruwan ya sauk’a...”_ Muhibbah ta d’anyi fasali kafin taci gaba da karantawa
_”Sam ban kula da wannan matar ba wacce take rungume da jaririya sabuwar haihuwa, kafin na ankare na buge wannan matar da mota.. Cikin tsananin tashin hankali muka fito muka nufi wannan matar dake kwance gefe tamkar bata numfashi, sam bamu kula da jaririyar da take d’aukeda ita wacce tuni ta fettu gefe, muka nufo kan matar muna k’ok’arin bata agaji na gaggawa tareda tabbacin cewa tana numfashi... Cikin sauri muka d’auki wannan matar muka nufi Mota da ita dan muyi rushing d’inta zuwa asibiti dukda cewa wajen daji ne babu asibiti kusa... Sam bamu kula da jaririyar ba a zatonmu k’unshin tsummokaranta ne marassa amfani.. Bamu takan k’ullin kayan ba dan rayuwarta yafi mahimmanci, sam bamu San cewa ba k’ullin kaya bane d’iyarta ce lullub’e cikin zanin... Nan da nan muka nufi asibitin cikin garin Yalwan Shandam da ita dukda cewa a lokacin garin yana hautsine sabida rikicin ta’addanci da ake a garin a wancan lokacin... Mun samu da k’yar muka samu Likitan da yayi attending wannan matar.. Hankalina sosai ya tashi a wancan lokacin dan ban tab’a buge koda k’aramar dabba bane tinda na soma tuk’i sai gashi na buge mutum sukutum kuma Ta shiga cikin mawuyacin hali na kota ta mutu ko tayi rai dukda cewa a zahiri babu ko k’warzani alamun ciwo jikinta..Muka jira aka dubata ta ta d’an farfad’o kad’an, Likitan yace damu mu shiga mu ganta Ta farfad’o but her heart was very weak, Da alama batada k’oshin lafiya, komai ka iya faruwa.. Likita ya k’arada fad’in kaman akwai abinda take son fad’i.. Aiko muna shiga muka samu tana magana kaman sumbatu tana fad’in yaranta yaranta, Sansanin Yalwan Shandam, akwai jinjirarta a goyo bayanta.. ina jinjirarta..? Daga wad’annan kalaman bamu kuma sinkayo muryarta ba.. Na dubi Turaki cikin tsananin tashin hankali nace matar nan akwai jaririya a tareda ita dole mu koma wajen da muka bugeta.. Turaki yace anya kuwa Rankaidad’e kodai sumbatun zafin ciwo kawai take.. Na girgiza kai naceda Turaki hankalina bazai kwanta ba sai na koma wannan wajen na tabbatar da kalaman matar nan...Haka na fice a cikin sauri Turaki na k’ok’arin dakatar dani kasancewar garin ba’a kwance lafiya yake ba ga dare ya soma shiga.. Naceda Turaki koda zan had’uda ajalina Zanje na duba na tabbata bamu bar wata rai a wannan wajen ba wacce bazata iya yiwa kanta komai ba.. Haka na fice na nufi wannan wajen... Nayita dubawa banga k’ullin kayan ba.. Ga yayyafi da tuni aka soma ga kukan hadari, har na hak’ura zan tafi na sinkayo kukan jaririya... Nai saurin juyawa ina duban yanda nake sinkayo kukan.. Can k’asan wata bishiya na hango k’ullin kayan.. A hankali na duk’a na shiga warwarewa.. It was a baby girl.. A beautiful baby girl wacce kallo guda nai mata naji wane irin shauk’i had’ida tausayi.. Hannayena suna rawa nasa na d’auko jaririyar wacce taketa kuka sabida yunwa da jigata, Na soma jijjigata a hannuna amma batayi shiru ba, nai saurin shigewa da ita mota tsoron kar ruwa ya jik’ata ya k’ara mata fever, nan da nan muka bari wajen dukda cewa ana iya tareni a tuhumeni a ina na samu jaririya musamman sabida halin rashin tsaro da ake fama dashi.. Haka tana hannuna Ina jijjigata Ina driving har Allah ya taimakeni tayi bacci... Kasancewar motata lambar emirate council ne shiyasa van sami wani matsala da Jami’an tsaro ba... Haka na nufo asibtin rungume da jaririyar saidai a lokacinda na iso na tadda Turaki yayi jigum yana jiran k’arasowata.. Na k’arasa da fari’ata rungume da yarinyar ina fad’ida Turaki gashi na samo jaririyar ina mahaifiyarta take...? Jiki a sanyaye Turaki yake girgiza kai, na tsaya ina dubansa cikin tsananin sanyin jiki.. Lokaci guda na fad’a d’akin da matar take rungume da jaririyar a hannuna.. Saidai ga dukkan alamu lokaci yayi Allah ya amshi ran matar nan kafin na kawo mata jaririyarta... Na k’arasa cikin sanyin jiki na ajiye mata jaririyar a gefenta ina furta ga d’iyarki na kawo miki.. Ki tashi ki ganta... Ina maganan hawaye suna gangaro mun.. Likita ya shigo ya dafani yace Rankaidad’e Allah yayi mata cikawa, Ina ‘yanuwanta suke..? Daga ni har Turaki babu wanda yasan inda dangin wannan matar suke amma saidai munji ta ambaci Sansanin Yelwan Shandam.. Muka fito nida Turaki muna tunanin abinyi ga jaririya rungume hannuna.. Turaki yace Rankaidad’e yanzu meye abinyi..? Nace dashi sassafe idan Allah yasa muna cikin masu rai zamu tafi Sansanin Yelwan Shandam mu bincika ahalin matar nan, Turaki ya dubeni yace yarinyar fah..? Sai sannan na tuna da jaririyar dake rungume cikin hannuna..! Nai mata k’uri Ina dubanta ba tareda na iya furta koda kalma ba.. Bamusan a ina sansanin yake ba hakan yasa muka soma tambaya cikin daren.. Nan ake sanar damu ai ‘yan tadda Sun tashi wannan Sansanin Sun k’oneta babu wanda yasan yanda Refugees d’in suka koma... Wani sabon tashin hankali, kenan bazamu samu sauran ahalin matar nan ba, Turaki ya kuma dubana rik’eda yarinyar yace Rankaidad’e yaya zamuyi da yarinyar nan..? Na kuma dubanta k’walla Tab idanuna, lokaci guda naceda Turaki I won’t give her away.. She’s mine Turaki, Zan zama mahaifinta..! Batada kowa bayan ni.. She lost the only family she had left, which’s her mom.. na zamto sanadiyan rasata da tayi, zan zama gatanta in sha Allah... Zan bata duk wani kula da mahaifi yake baiwa d’iyarsa.. Har abada bazata tab’a sanin cewa bani na haifeta ba..! Turaki ya dubeni sosai yace Rankaidad’e are you sure about this.. This is a serious decision your Highness..! Naceda Turaki k’warai ni ne mahaifinta, kuma matata Aliya itace mahaifiyarta...Zamu binne hakan dani dakai yanzu a nan wajen.. Kamin alk’awari babu wanda zaiji wannan batu..? Turaki yai shiru yana nazarin girman alk’awarin da zai d’auka..! Na kuma dafa kafad’arsa nace ka min alk’awari brother..? A hankali Turaki ya jinjina kai yace nayi maka alk’awari amma ta yaya zaka b’oye hakan daga mutane..? Nace dashi yazo a daidai tinda dama shirye shiryen barin k’asar muke nida matata Aliya a lokacin sabida tak’urawa matata da Giwa tayi a cewarta Baiwa ce bata kamaceni ba.. Nace dashi zamu tafi da ita K’asar Spain zamu raineta a can, a lokacin da zamu dawo zamu Zo da ita matsayin d’iyarmu da muka haifa can k’asar Spain.. A wannan daren na kawowa matata Aliya d’iyata wacce na sanya mata suna Fatima Zahra... Yanda Aliya taimin alk’awarin cewa zata rufa wanann sirrin itama, Zahra ta zamto d’iyarta.. D’iyarmu nida ita... Washe gari muka koma wannan garin muka had’a jama’a akaiwa Mahaifiyar Zahra sutura da sallah kaman yanda yake a addini muka kaita makwancinta na gaskiya.. Na kuma d’aukan alk’awari saman k’abarinta cewa zan rik’e d’iyarta bisa gaskiya da amana...! Wannan shine Labarin d’iyata Zahra.. Zahra k’anwarki ce Muhibbah..! Zahra itace jaririyar k’anwarki wacce kuka rabu da ita da mahaifiyarku a Sansanin Yalwan Shandam..!”_
Tana ida karantawa ta saki takardan ya fad’i k’asa tana mai shessh’ek’ar kuka.. Zahra wacce itama tana durk’ushe wajen tinda Muhibbah ta soma karantawa tana fitar da wane irin kuka mai ban tausayi.. Da rarrafe Muhibbah ta K’araso yanda Zahra ke duk’a lokaci guda ta janyota cikin jikinta suka rungume juna cikin wane irin shauk’i, su duka biyun kuka suke mai tab’a zuciyar mai sauraro.. Illahirin mutane dake wajen hawaye suke da jin irin wannan al’amari... Cikin kuka Zahra Ke fad’in “My sister..! You’re my sister..!!” Tsananin kuka ya hanata ci gaba da magana..
K’ank’ameta Muhibbah ta kumayi tana mai kuma kwantar da kanta cikin k’irjinta take furta “Yes Zahra.. I’m your sister.. Your big sister... Allah ya kuma had’amu bayan mun rabu na tsawon shekaru..!”
Zahra ma cikin muryar kuka take ci gaba da furta “Since the I first saw you... I felt something very special about you, like we’re connected somehow..!” Muryarta ya carke sai kuka...
Muhibbah ta kuma rungumarta tana furta “Likewise Zahra... I felt the same, mu d’in ‘yan uwa ne..!” Ta kasa ci gaba da nagana itama sai kuka... Umaima ta k’araso ta duk’a gefensu tana kuka itama, lokaci guda ta dafa hannayenta saman kafad’unsu.. Suka d’ago suna duban juna su duka ukun... Lokaci guda suka rungume juna gaba d’aya su ukun suna wane irin kuka mai tab’a zuciyar mai sauraro.. Gimbiya Turai ta taso ta had’esu gaba d’aya ta rungume tana matsan hawaye itama.. Lokaci guda take furta “Alhamdulillah..! Alhamdulillah..!! Allah na gode maka daka had’e kan ahalinmu waje guda.. Bayan duk k’ok’arin da wasu sukayi suga Sun tarwatsa kan wannan ahali sai gashi ka had’emu waje guda cikin labaru da k’addarori na rayuwa daban daban.. Wa zaiyi tunanin wad’annan ‘yanmata guda uku tsatso guda ne.. Sai gashi cikin hikimarka da buwayarka ka had’esu waje guda.. Allah na gode maka daka had’e kan ahalin Alfah waje guda..!” Kuka yaci k’arfinta ga tsananin rawa da muryarta yake...
Mommy dake gefe sai matsan k’walla take tana duban wannan al’amari mai cikeda al’ajabi ga kuma tab’a zuciya.. Allahu Akbar Allah mai iko... Ashe wannan masarauta k’unshe yake da ahalin Muhibbah shiyasa taji duk yanda zatayi sai tazo wannan Masarautar.. Ashe dai Allah ne ya dawo da ita cikin ahalinta.. Kai wanann kayan Farin ciki da yawa yake.. Ubangiji ya cika abin godiya...!
Wannan rana ta kasance wani sabon rana ne na Farin ciki ga wannan ahali, Muhibbah ta had’e kan ‘yanuwanta ta shige tsakiya ta rungumesu tamkar mai tsoron kar wani abu ya kuma gifta tsakaninsu.. Mafarkinta da mahaifinsu ta tina, ashe dai ahalinsa gaba d’aya suna a cikin wannan masarauta, yau da za’a tashi mahaifinsu ya gansu gaba d’aya su duka uku tare Tabbas da ya cika da Farin ciki... Allah ya had’e masa kan ahalinsa waje guda, duk yanda Izzatu taso Ta k’arar da zuri’ararsa a doron k’asa Allah bai nufi hakan ba.. Shiyasa Bawa baya iyayiwa d’an uwansa Bawa abinda Allah bai k’addara masa ba.. Duk abinda ya sameka ka k’addara daga Allah ne, shi ya k’addari yuwar hakan.. Wani bai isa ya maka abinda Allah bai k’addaro maka ba... Suka kasa sakin juna sai wani sabon shauk’i da k’aunar juna suke.. Sai nan nan da juna suke musamman ‘yar autarsu Zahra wacce ita d’in shalele ce a wajensu...
Zahra sai tambayar Muhibbah take ya kamannin mamansu da wa take kama, ya na babansu da waye yake kama cikinsu.. Umaima tace gaskiya zataso sanin kamannin Abbansu tinda tin tana k’arama Giwa ta rabasu bata sanshi ba.. Muhibbah ta murmusa tana dubansu gaba d’aya ukun wane irin Farin ciki maras misaltuwa yana ratsa duk wani k’ofa na zuciyarta, hannayensu ta rik’o cikin nata, ta dubi Umaima dake b’angarenta na dama tace “Well, Ke kin d’an d’auko kamannin Abbah kad’an dan kin d’auki hasken fatarsa dukda bansan ya kamannin mahaifiyarki yake ba...” Ta juyo b’angaren hagu ta dubi Zahra, ta kuma murmusawa tace “Kema kin d’an d’auko hasken fatarsa tinda kinfini haske ni Umma na biyo.. Saidai kin d’an d’auko manyan idanunmu nida Umma..!” Gaba d’aya suka murmusa cikeda jin dad’i Muhibbah ta rungumesu tana shak’an Ni’iman canjin rayuwa wanda bata samu ba a baya... Umaima tace “Giwa itace tayi sanadiyar rabuwarmu gaba d’aya..!”
Zahra ta k’ara da “Zanso na sake ganin fusakar azzulaman matar nan naji dalilinta na wanann bak’in zalunci da tayima ahalinmu..!”
Umaima tace “Ko kad’an banji tausayinta ba, She got what she deserved after all..!”
Muhibbah ta kuma rungumosu tana fad’in “Kar mu tuna bak’in ciki, tuna wannan baiwa da rahama da Allah ya lullub’emu dashi.. Mu gode masa sai muyi Farin ciki...!”
Gaba d’aya suka murmusa Zahra na fad’in “Y la parte más asombrosa de todo es que ahora estamos todos juntos, como siempre deberíamos estar..!” (Sannan abu mafi birgewa muna tare yanzu gaba d’aya, kaman yanda ya kamata mu kasance tun daga farko..)
Hancinta Muhibbah ta d’an jawo tace “Mudai a daina mana Spanish a nan dan bamuji.. Right Umaima..?” Ta k’arashe tana mai d’agawa Umaima gira guda sama..
Umaima ta d’an kashe idanu guda tace “Ahh yaren masoyi ni na isa nace a dena yi..!”
“Au kema haka zakice..?” Muhibbah ta fad’i tana duban Umaiman sanda suka shagala da dariya daga Zahran har Umaimar.. Suna a haka Jakadiya ta nemi izinin shigowa.. Ta risina ta gaidasu kana ta k’arada “Rankidad’e.. Mai Martaba Sarkin mu na gobe mai jiran nad’i yace a sanar Gimbiya yana son ganinta..!” Ta k’arashe kanta a k’asa..
Gaban Muhibbah ya fad’i jin Mahmood yana kiranta... D’an duban Sisters d’inta tayi tace “Gaskiya nidai yau d’in gaba d’aya taku ce banson matsawa daga kusa daku..!”
Umaima Ta d’an rausayar da idanu tace “Mu mun isa mu hana Rankaidad’e ganin Queen d’insa, a’a Sistu gaskiya dai ki amsa kiran Mai Martaba.. Right Zahra..!” Ta k’arashe tana d’agawa Zahra gira guda..
Muhibbah ta tab’e baki kad’an tace “Then he wait, I’m not done catching up with my sisters..!”
Umaima tace “A’a Sistu ai ba’asan sarki da jira ba mu dai zamu jira..”
Zahra ta d’anyi gyaran murya cikin sigan zolaya tace “Kaman dai ba yanzu aka gama kuka akan Paa d’ina ba..!” Muhibbah ta janyo pillow ta jifa mata tana fad’in zaki sani ne yarinyar nan.. Zahra ta zille tana dariya ta fad’a jikin Umaima tana fad’in “Aidai gaskiya na fad’i ko Aunty Umaima, Paa d’ina is one in a million.. Kuma ma mu wajen Ummi zamuje ta bamu labarin Masarautarsu Abbah..!” Ta k’arashe tana mai janyo hannun Umaima.. Umaima na jinjina kai take furta “K’warai muje muji labarin Masarautarsu Abbah..!” Daga haka suka fice rungume da juna cikeda jin dad’i.. Muhibbah tabi bayansu da kallo zuciyarta na mata wane irin sanyi.. Tunawa da tai Jakadiya na waiting room tana jiranta su tafi wajen Rankaidad’e hakan ya sanyata mik’ewa Ta soma kintsawa a nitse zuciyarta na wane irin fuzga mai gauraye da annashuwa...
Koda suka iso sashen Mahmood ita kad’ai ta shige ba tareda rakiyar Jakadiya ba.. Cikin natsuwa take takunta a hankali har ta nufi saman benensa..
Bataji alamunsa ba hakan yasa ta nufi b’angaren paint works d’insa.. Haka ta dinga takawa tana ganin baiwar da Allah yaima Sarkin nata.. Kyakyawan murmushi saman fuskarta, tai tsaye jikin wani k’aton frame tana kallo.. Kaman daga sama taji hannayen mutum saman cikinta ya rungumota ta baya daga nan yanda take a tsaye...
Zuciyarta ya tsinke ta d’an zabura kad’an Mahmood ya kuma matseta a hankali yake furta “Ina zaki gudu kije..!” Yai maganar cikin salo na d’aukan hankali...
A d’an shagwab’e tace dashi “Ba kaine ka tsoratar dani ba..!”
Ya juyo da ita suna fuskantar juna dukda cewa ita nata idanun k’asa suke duba, lokaci guda yaci gaba da fad’in “Kin cika tsoro, na kula komai tsoro yake baki.. Bansan yaya akayi kika iya lek’en asiri cikin Masarautar nan da wannan tsoron naki ba..”
Murmushi mai sanyi tayi wannan karon har lokacin kanta a k’asa...
Bai janye idanunsa daga dubanta ya kamo hannayenta ya sakale yatsun cikin nasa lokaci guda yake furta “Gashi kuma na saka Ki kuka, yanzu kuma na baki tsoro.. Duk ni kad’ai..?!”Ya k’arashe murya a hankali
Ta kwantar da kanta cikin k’irjinsa cikeda kunyan abinda tayi...
Ta d’an mak’e kafad’a tana nan kwance cikin k’irjin nasa, tamkar wacce zata kuma wani kukan tace “Nifa ba kuka nayi ba Rankaidad’e..!”
Ya murmusa kad’an yana mai kuma shigar da ita cikin jikinsa “Oh na mance ashe sakamakon jarabawar ne bai miki ba.. Kodai a sake wani jarabawar ne..?”
Ta d’ago a d’an zabure tana dubansa wannan karon sai kuma taji kunyar kanta da kanta Ta kuma bama kanta dariya.. Rufe fuskarta da tafukan hannayenta tai tana mai murmusawa a hankali..
Lokaci guda Mahmood wanda shima sihirtaccen murmushi ne saman fuskarsa ya kuma janyota cikin jikinsa yana mai furtawa a hankali “Karki damu ni da ke auren zobe mukayi.. Mutuwa ce kawai zata rabamu kinji koh..!” Ya k’arashe yana mai aika mata wasu salonsa masu sanyawa taji duniyar tamkar su biyu ne kad’ai suka rage a ciki... Hannunta ya kamo yana mai furta “Come let’s talk..!” Ya k’arashe yana mai masu masauk’i saman Yalwataccen Darduma ta alfarma mai d’aukeda manyan cushions irinta gidajen masu sarauta.. An k’awata saman darduman da kayan marmari sai wanda zuciya ta zab’a...
Zaune suke suna fuskantar juna, idanunsa akanta yayinda ita kuma Muhibbah ta sadda nata idanun k’asa...
Dak’ik’ai sukad’an gifta kafin yai gyaran murya ya soma fad’in “I believe by now keda Zahra kunsan cewa kud’in ‘yanuwan juna ne.. Harma da Umaima..!”
Ta jinjina masa kai a hankali ba tareda Ta amsa ba.. Lokaci guda yaci gaba da furta “Abubuwa da dama Sun faru ko nace suna kan faruwa..! Ban tab’a tsammanin rana irin wannan zatazo ba, ranan da zan sanar da Zahra cewa bani na haifeta ba.. But as they say No secret remains hidden forever... Duk daren dad’ewa dole wata rana zata sani..!” Ya d’anyi fasali kana yaci gaba da fad’in “I don’t know, bansan ta yaya zan soma sanar da matata da kuma yarinyar da na raineta like my own cewa I was the one who ran over their Mom, ni ne nayi sanadiyan rasa mahaifiyarku da kukayi Hibbah.. Bansan yaya zaku d’auki al’amarin ba, it was hard for me to confess, but I had no choice ya zama dole na sanar daku koda bazaku Iya yafe min ba.. Muhibbah ni Mahmood ni na buge mahaifiyarku da Mota wanda yayi sanadiyar barinta duniya.. Zafin wannan abin yasa naji Eh gwara na swwak’a miki dan kar abin ya maku yawa nima kuma bazan iya rayuwa da hakan cikin zuciya na ba.. But then I realize I couldn’t... I can’t let you go... Because I love you...!” Cak ta d’ago idanunta masu zuban ruwa tana dubansa jin abinda yake fad’i, lokaci guda Mahmood da idanunsa tar suke kanta yaci gaba da fad’in “So much...!” Ya d’an had’iyi throat d’insa yanda kana iya hango motsawar wuyan nasa ta waje kana yaci gaba da fad’in “I’ve always loved you since the day I first saw you, when you were little...!” Ya d’anyi fasali yana daidaita numfashinsa, idanunsa wanda babu komai cikinsu face tsantsan gaskiya suna dubanta yaci gaba da furta “Bayan na sake had’uwa dake a cikin Masarautar nan a karo na biyu as a full grown woman, I can admit I feel something... Something very special... Te amo demasiado Muhibbah..!” (Ina matuk’ar k’aunarki Muhibbah)
Tinda ya soma magana take duban cikin k’wayan idanunsa hawaye na gangaro mata... A hankali ta lumshe idanunta hawaye naci gaba da gangaro mata... Hannayensa taji saman nata ya rik’o nata hannayen.. Cikin rawar murya yake furta “Will you still accept me, after learning that I was the one who ran your mom over..! Hibbah will still accept me.. Talk to me please Hibbah...!!” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya yana mai kuma matse yatsun hannunta cikin nasa..
A hankali yaji tana janye hannayenta... Yayi tsam ya rik’e yatsun nata, lokaci guda yake furta “Bazaki tab’a yafe min ba koh...?”
Bud’e idanunta tai masu zuban ruwa Ta ware su tsaf saman kyakkyawan fuskarsa wanda ya cika da rauni a yanzu saikace ba Sarkin nata ba..
A hankali Ta soma furta “Rankaidad’e Maiyasa zaka ce haka, bayan bada ganganci ka aikata hakan ba.. Maiyasa zakace haka bayan kaid’in Allah ne ya k’addari had’uwarku da ita don ka zamto garkuwa ma jaririyarta wanda azzalumai suke neman ganin bayan ahalinmu a wancan lokacin.. Allah ya maido da Zahra cikin ahalinta ne shiyasa ya k’addari rik’onta a hannunka..! You’re like an Angel Your Highness..Ka bayyana a rayuwar Zahra kuma ka haskaka rayuwarta, ka bata dukkan kulawa da ya dace.. Rankaidad’e ka mance cewa buge Umma da kayi ko k’warzani bata samu ba, kawai kaid’in ka bayyana ne domin ka kula da Zahra..! Sannan Bawa baya shige ajalinsa, kowa ajalinsa a rubuce yake Rankaidad’e.. Kuma Idan akwai wad’anda zamuce sunyi sanadin mutuwar Umma toh ba kowa bane face Giwa da ‘ya’yanta domin kuwa tun bayan abinda ya sameni da mahaifina, zuciyar Umma yayi rauni bata kuma lafiya ba ga juna biyu da take d’aukedashi.. Koda Ta haifi Zahra cikin jinya take batayi lafiya ba.. Idan baka manta ba kaman yanda kace Likita yace her heart was weak toh haka d’in ne zuciyarta tayi matuk’ar rauni tun bayan wad’ancan iftila’i da suka auku mana.. Baka kashe Umma ba Rankaidad’e.. Lokacinta ne yayi sannan Giwa da ‘ya’yanta sune sanadi..!” Cikin tsananin rawar murya take ci gaba da fad’in “You gave my sister a life Rankaidad’e..! Thank you, thank you for taking care of my sister..? Thank you your Highness..!” Muryarta ya sark’e sabida kuka...Lokaci guda Mahmood ya janyota cikin jikinta cikin jikinsa kaman jira take nan kuma ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro... Ya matseta cikin jikinsa sosai yana lallashinta.. Haka yayita riritata yana bata baki had’ida jero mata kalaman k’auna masu sanyaya zuciya wanda har saida tayi mamakin Wai Dama ya iya fad’in kalmomi haka... Kaman dai ba Rankaidad’e d’in data sani ba...
Rayuwa ta kumayin dad’i abubuwa Sun kuma warwarewa, ahalin sun cika da Farin ciki maras misaltuwa... Tuni an soma gudanar da shirye shiryen bukin tarewar Muhibbah da Mahmood.. Shi Mahmood kam ma da anbi Ta nashi ne baza’a tsayawa wani biye wa al’ada ba zai tare da amaryarsa amma Ummi tak’i amincewa tace sai nan da sati guda bayan an ida yiwa Muhibbah duk wasu tanadi da ake na al’ada an kuma yi bukin yanda yake a al’adance.. Tuni ta killace Muhibbah yanda ko samun ganinta Mahmood baiyi, gaba d’aya ji yake wannan al’ada da sarautar ba k’aramin tak’urasa sukai ba... Mommy ma ta koma gida dan gudanar da ‘yan kintse kintse, a zaton Muhibbah mommy ta tafi kenan bazatazo Bikin ba, haka taita magiya tana cewa Mommy ta taya ayi da ita, Mommy tace bayan abubuwan da sukai musamman Yawale da Gudidi ita har kunyar Muhibbar take balle ahalinta, uwa uba kuma ga abinda Ansar yazo yayi daga baya... Da k’yar dai ta amince watak’ila ta dawo ayi da ita...
Zahra da Umaima basu sama basu k’asa, hidimar tasu ce ta ko ina... Ranan alhamis ake saka
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 60 Chapter of 65