Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
min gardama, let me remind you Idan kin mance..!!” Fincika tai daga rik’on da yai mata tana mai ci gaba da sakin huci take fad’in “Kash..!! Wannan ba Zuhrar da ka sani bane wacce take matuk’ar tsoronka da shakkanka... Idan baka sani ba ka sani, kan mage ya riga ya waye... Zaman d’an wani lokaci nake a gidanka... Da zaran wa’adin dana d’ibar wa kaina da ‘ya’yana zaka nememu a Masarautar nan ka rasa... Bana shayin duk abinda zaka min Yazeed... Ka rigada ka gama dab’awa zuciyata wuk’a mai bak’in guba wanda zai wahala ya warke... So duk abinda zaka min yanzu bana shakku... Go ahead Your Royal Highness... Kai duk abinda zakayi...!!” Ta k’ararashe cikin huci... Shima hucin kurum yake saki yana dubanta da tsananin mamaki, ko a mafarki ne akace masa Zuhra zata dawo haka zai fark’a yace k’arya ne sai gashi a zahiri yana sa’insa da Zuhra wacce a baya babu irin cin kashin da bai mata ba... Ya had’iyi miyau mai d’aci na bak’in ciki... Yana mai nunata da yatsa saidai ya kasa furta koda kalma sai idanunsa dake kuma kad’awa... Cikin huci yasa kai ya fice jin yaransu na haurowa saman benen a guje... Yana ficewa ta lalumi saman gado ta zauna tana mai dafe kanta dake tsananin sara mata, lumshe idanunta tai had’ida kishingid’a cikin gadon Dan gaba d’aya bata gane kanta kwana biyun... ** Turaki ya shigo da sallama yanda ya sami abokin nasa na zaman jiran k’arasowarsa, yanda yaga fuskar Turakin ya tabbatar masa da zarginsa kan yarinyar ka iya zama gaskiya.... “Barkada hutawa your Highness..!” Turaki ya fad’i yana mai zama daga can gefe, lokaci guda ya mik’awa Mahmood d’in wasu takardu... Mahmood yasa hannu ya amsa yana mai ware takardun... Saida ya karance tsaf kana ya d’ago yana duban Turaki da mamaki saman fuskarsa.. “Does this means she’s a fraud...?!” Turaki ya nusa kad’an yace “Lets not judge her right away Rankaidad’e... Maybe tanada dalilinta na yin k’aryar...!” Girgiza kai Mahmood yai yace “What could be her motive Turaki..? Kan mai zatazo Masarautar nan tayi k’aryar ita d’aliba ce a jami’ar garin nan alhali ba haka bane, sannan har tayi k’aryar batada masauk’i...Ko mai irin fuskarta basu tab’a gani cikin makarantar ba... Turaki yarinyar nan mak’aryaciya ce kuma tanada babban dalilinta na zuwa Masarautar nan... Kar ka mance tun farkon zuwanta Masarautar nan nakeda alaman tambaya akanta, what if da biyu ta shiga jikin Zahra...? Wayasani ma ko itace taita feeding Zahra da k’arerayi har Zahra ta koma yanda take a yanzu..?!” Turaki ya katsesa da fad’in “Ka gafarceni Your Highness, ni a tunanina kaida kanka kace zamanta da Zahra alkhairi ne Dan ita ta shawo kan Zahra lokacin da Yazeed ya tasamma gurb’ata zuciyarta da k’arerayi...” Mahmood ya kuma katsesa da fad’in “And what makes you so sure itada Yazeed basu san juna ba....?? Maybe she’s helping him in some ways.....! Waht if itada Yazeed are lovers,maybe d’aya ce daga cikin ‘yan matansa da yake cin amanar matarsa dasu.... wayasani ma ko ya d’aukota ya aje cikin Masarautar nan ne just to ruin me, and they used my own daughter to bring me down....! And after she learns yana cin amanarta da Raheema shine ta fallasa Raheema kuma kar ka mance mun tab’a kub’utarta hannun Yazeed,maybe Yazeed gaskiya yake fad’i ba raping d’inta yaso yi ba... Maybe dama sunsan juna tuntuni... Is her way of getting back at him shiyasa ta tona asirinsu shida Raheema...!! I was such a stupid for believing in her..!!” Ya k’arashe yana sakin huci mai wane irin zafi yanaji zuciyarsa kaman tana rarrabewa gunduwa gunduwa, lokaci guda yasa hannu ya daki jikin gini zuciyarsa na kuma masa d’aci... Turaki yai shiru Dan bayan tabbatarwa da sukai Muhibbah ba d’aliba bace a makarantar kaman yanda tace Mahmood yanada duka damar da zai zargeta da komai, wacce har tai k’arya irin haka baida lasisin da zai kareta dukda cewa shi sam zuciyarta bata aminta da cewa Muhibbah mutumiyar banza bace musamman da ya fahimci abokinsa ya aukawa soyayyarta wanda bai tab’a ganinsa cikin irin wannan soyayyar ba koda kuwa zaita denying... Turaki ya d’an shafi fuskarsa da duka hannayensa biyu yana mai tsare abokin nasa da idanu wanda sosai yake iya hango tsagwaron b’acin rai kwance saman fuskarsa... Shi zai iya cewa ma bai tab’a ganin hakan daga garesa ba... Ya d’an nusa kad’an yace “What are you suggesting your Highness..?!” Wane irin duba kurum Mahmood yai masa ba tareda ya kuma cewa komai ba yai hayewarsa sama... Turaki yabi bayansa da kallo tausayinsa na kuma lullub’esa Dan yayi imani sosai ya kamu da san yarinyar sai gashi tayi breaking zuciyarsa tun ba’aje ko ina ba.... Bai ida tunanin ba ya hango Mahmood ya sauk’o cikin shiri irinta Buzaye... Turaki ya mik’e babu shiri yana dubansa baki sake.... “Bak’on Buzu kuma Rankaidad’e..?!” Turaki ya fad’i yana duban Mahmood d’in dake k’arasowa cikin parlorn.... Lokaci guda yaci gaba da furta “Ai na zaci an rufe shafin Bak’on Buzu tuntuni Rankaidad’e...?!” Har lokacin bai tankasa ba saima k’arasawa jikin babban mirror na alfarma dake gefe daga nan cikin parlorn yana gyara nad’in buzayensa.... Lokaci guda ya soma furta “Jikina yana bani Baba Wambai bazaice na nemeta itada zata linking d’ina to all the answers I’ve been looking for a banza ba, watak’ila itada Yazeed sun jima suna shirya abubuwa akaina... Idan ban samu amsoshin a wajen Yazeed na ita zan iya samu a wajenta...!” Turaki ya jinjina kai yace “Toh yanzu ina muka nufa Rankaidad’e..?!” Ba tareda ya dubesa ba yace “Bauchi..!!” Saida gaban Turaki ya fad’i, ya d’ago taintsiyar hannunsa yana duba time... “Rankaidad’e da dai mun bar tafiyar zuwa gobe, Idan muka tafi yau zamuyi dare sosai a hanyar dawowarmu...!” Mahmood ya katsesa da fad’in “Are you coming or not..?!” “A’a yanda kace hakan za’ai Your Highness..!” Turaki ya fad’i yana mai take masa baya... Babu wanda yaga ficewarsu ko hadimin Mahmood d’in baisan Sun fice ba hasalima da motar Turaki sukai amfani suka fice. ** A b’angaren Jakadiya kuwa neman duniya anyi ba’a sameta ba cikin Masarautar, hankalin Giwa yakai k’oluluwa wajen tashi... Wai meke faruwa da ita ne..? Daga wannan sai wancan.... Yau kwana biyu kenan babu Jakadiya babu dalilinta kuma babu wanda yasan yanda take... Gashi Giwa ta hana a yad’a Labarin b’acewar Jakadiyar Dan bata so ya isa ga Mahmood balle har aje ga tono ina Ubandoma ya shige tinda shima ba’a gansa ba... Gashi Tal’udu ya mata iyaka da sashensa balle Takai masa kokenta na abubuwan dake faruwa da ita... Tashin hankali daga wannan sai wancan... Ita duk tsoron ta kar dai Ubandoma ne ya zago ya sace Jakadiya tinda tayi imani yana tareda Ja’afar da kuma Izzatu mutanen da suke barazana ga rayuwarta... Tayi imani randa duk suka bayyana cikin Fada Toh fah kashinta ya bushe... Taci gaba da zaga cikin d’akin nata yanda Jamal ya shigo ya taddata... Daga can gefe ya zauna yana k’are mata kallo dan da alama bataji shigowar tasa ba... Ya d’anyi gyaran murya kad’an yana mai daidaita zamansa had’ida aje sandarsa Ta crutches... “Maami Wai meke damunki ne..?!” Ya tambaya cikeda kulawa... Giwa Ta juyo tana dubansa da mamakin yaushe ya shigo ko k’aran sandarsa bataji ba.... “Gwarzona na yaushe ka shigo..?!” Ta tambaya cikeda kulawa... “Maami tun d’azu fah na shigo, inata miki magana amma kinyi nisa duniyar tunani... Maami meke damunki duk kika fice a hayyacinki haka... Tell me is there something I can do to help..?!” K’ak’aro murmushi Giwa tai Ta k’araso kusan d’an nata Ta zauna, hannunsa ta dafa kad’an tace “Meyasa abubuwa suke faruwa yanda bana so Jamal... Meyasa komai yake nema ya sukuruce min...? Nayi zaton inada k’arfin zuciya da k’arfin hali, Maiyasa nakeji kaman na zamto mai rauni.... Jamal babu Ubandoma, yaci amanata ya gudu da mahaukaciyar nan da kuma Jafaru... Yanzu kuma an wayi gari Jakadiya ta b’ace itama... Jamal idan na rasa Jakadiya tamkar rayuwata na rasa..!!” Ta k’arashe cikin tsananin rawar murya... Jamal yai shiru yana duban mahaifiyar tasa sai kuma yace “Maami har haka Jakadiya Keda mahimmanci wajenki..?!” Giwa ta nusa tace “Bazaka gane bane Jamaluddeen, Jakadiya tasan sirrika na da yawa wanda b’acewarta tashin hankali ne a gareni...!” Jamal ya tsareta da idanu sai kuma ya d’an gyara zama yace “Maami akwai wasu sirrikan da kike b’oyewa ne wanda Jakadiya ta sani ni ban sani ba...?!” Tambayar da ya haifarwa Giwa da fad’uwan gaba tinda tasan yaran nata basu san cewa ta salwantar da shigabanta bane ta maye gurbinta, yaranta basu san cewa ita d’in baiwa bace k’ask’antacciya maras ‘yanci... Shiyasa duk yanda zatayi dole tayi komai Dan ganin itada ahalinta sun tabbata cikin wannan masarauta tunda basuda yanda yafi masu nan...! Ta girgiza masa kai a hankali alamun a’a tace “Iyakacin abinda ka sani sune Jakadiya ta sani amma duk randa ya isa kunnen Yayanku Mahmood zai tsaneni a matsayina na mahaifiyarsa dole duk yanda zamuyi mu aje Jakadiya a k’ark’ashin ikon mu Jamal..!” Yai shiru had’ida tsurama waje guda idanu tamkar mai tunanin wani abu... Giwa ta tsaresa da idanu tana karantarsa, Ta d’an muskuta kad’an tace “Jamal... Anya kuwa babu abinda kake b’oye min..? Kodai kasan wani abu gameda b’acewar Jakadiya..?!” Jamal yai shiru ba tareda ya amsata ba... Giwa Ta mik’e tana fad’in “Jamal ina Jakadiya..? Mai kai mata..?!” D’agowa yayi yana dubanta sai kuma ya kauda fuskarsa zuwa d’aya b’angaren “Maami Jakadiya macuciya ce cin amanarki take a bayan idanunki shisa nake hukunta ta..!” Giwa ta shiga tafe hannaye tana salati babu shiri tace dashi maza ya kaita taga Jakadiya.... ** BAUCHI Mommy tai jigum tana sauraren Baffah Yawale yanda yaci gaba da fad’in “Haba ni nasan za’a rina, wannan yarinya da kika d’auko kika aje gidanki tsintacciyar mage ce, a tunaninki irin na mata taimako kikayi gashi nan da idanunki kin gani, Allah ya bud’i bakinta da kanta Ta sanar dake k’arya ta miki a baya... Allah kad’ai yasan yawan sauran abinda take b’oye miki.... Ki gode ma Allah da ya fargar dake kafin ki kaiga aikata babban kuskure na aura ma d’anki wannan yarinya maras asali balle tushe...!” Kaman daga sama suka sinkayo muryar Ansar yana fad’in “Dukda rashin asalinta naji na gani na amince Ina sonta a haka... Ni ne nan zanyi zaman aure da ita ba d’aya daga cikinku ba, so ni nakeda alhakin zab’awa kaina macen da ta dace Tai zama matata kuma uwar yaran da zan haifa gaba.!” “Ansaar.!!!!” Mommy ta daka matsa tsawa tana mai mik’ewa tsaye... Ansar bai daina huci ba yake furta “Mommy Ki k’yaleni na fad’I gaskiya, wannan mutumin yazo yana poisoning zuciyarki da kalamansa na son zuciya..!” Momy ta katsesa da fad’in “Nace kamin shiru... K’anin mahaifin Naka kake wa magana haka...? Ansar I didn’t raise you to become like this... Rashin kunya ba halinka bane kada ka fara kan wannan mak’aryaciyar yarinyar..!!” Ansar na tsananin huci yake girgiza kai yana duban mahaifiyarsa, lokaci guda yake furta “Mommy shin zaki bari son zuciya ya rufe miki ido..? Mommy Muhibbah bata miki komai ba, Mommy don’t judge her akan abinda bakida masaniya akai... Mommy ki bari nai miki bayani na tabbata zaki fahimci komai..!” “Shut up.!! Kamin shiru nace... Bana buk’atan naji komai, kuma bana so na fahimci komai... The only abinda na sani shine bazaka auri yarinyar nan ba period.!!” Ta k’arashe cikin tsananin huci.. Shima Ansar d’in huci yake idanunsa na kuma kad’awa, lokaci guda yake furta “Fine..! Haka kikace Mommy..? Kin mance same mutanen da suka k’yamaci aurenki da Daddy sabida ke tibabbiya ce same mutanen suke tunzuraki ki aikata abinda zakizo kina danasani daga baya... Mommy why can’t you open your eyes and see the truth...! Toh wllhi kinji na rantse miki.... ina mai tabbatar maku idan har baku d’aura aurena da Muhibbah ba wllhi bazan zauna da yarinyar da kukeso ba, zaku aura mata wofi ne Dan wllhi tafiyata zanyi ku nemi ni ku rasa..!!” Marin da Mommy Ta wankesa dashi ne ya sanyashi dakatawa da magana, ya d’ago dafe da k’uncinsa yana dubanta, Baffah Yawale ya mik’e ya tsaya a tsakiya yana duban Mommy yake fad’in “Kiyi hak’uri Murja... Har yanzu dai Yakubu(Ansar) yaro ne... Baisan menene daidai da abinda ba daidai ba... Kiyi hak’uri abi abun a sannu....!” Mommy na hawaye take nunawa Ansar k’ofa “Get out... Get out before I lost it all on you... Fita nace..!!!” Ta k’arashe hawaye na gangaro mata.... Ansar ya aikawa Baffah Yawale wani duba kana yasa kai ya fice kaman zai kifa da k’asa... Ansar na ficewa Baffah Yawale ya taro ruwa a dispense ya kawowa Mommy... Babu musu Ta amsa ta kurb’a... Bafah Yawale ya koma mazauninsa ya zauna, saida dak’ik’ai suka d’an shura kana yai gyaran murya yace “Murja ni inaga bata nan zamu b’ullowa yaron nan ba, idan har yana ganin yarinyar bazai tab’a cireta a zuciyarsa ya mance da ita ba... Idan bata gidan nan shine zai manceta gaba d’aya... Amma muddin yana ganinta Toh fah bazai mance ba....!” Mommy ta dubesa jiki a sanyaye tace “Yawale mai kake nufi...? Kasan dai bazan iya koran Muhibbah ba, dikda abinda taimin I still love her like my own daughter... Bazan iya korinta ba..!” Baffah Yawale ya murmusa yace “Murja kenan.. Ai nima ba abinda nake nufi ba kenan, ba korinta zakiyi ba... Aurarta zakiyi ga wani daban, kinga idan kika aurarta Ansar yasan ta haramta garesa shikenan dole ya cireta daga zuciyarsa gaba d’aya ya rungumi k’addara ya zauna da matarda Allah ya had’asa zaman aure da ita Wato ‘yar uwarsa k’anwarsa Hameeda... Kinga shikenan hankalinki kema ya kwanta..!” Mommy tai shiru kaman mai nazari sai kuma tace “Toh amma waye mijin da za’a aura mata..? Ina zan samo mata miji da zai dace da ita wanda bazai mata gori daga baya ba..?!” Baffah Yawale ya murmusa yace “Murja kenan... Ai samun miji ga kyakkyawar yarinya kaman Muhibbah bazai wahala ba... Ni zan tafi da hotonta wajen manyan mutane masu mutunci a haka zamu sama mata miji... Amma ita yarinyar karki sanar da ita an fasa aurenta da Yakubu shima Yakubun ki barsa akan za’a aura masa Muhibbah saidai yaji daga baya ba shi aka aura mata ba... Ina mai tabbatar miki rana guda za’a d’aura aurenta da Yakubu amma ba dashi ba da waninsa...Kinga dole yayi hak’uri ya rungumi k’addara... Ki share zancen Yakubu ki daina damun kanki ki bar min wuk’a da nama... Ni nasan duk yanda zanyi...!” Mommy ta jinjina kai tace “Nidai idan har bazata auri Ansar ba toh shikenan, amma Yawale ka tabbata gidan mutunci ka kai Muhibbah..!” Baffah Yawale ya Washe baki cikeda jin dad’i yace “An gama Hajjaju... Wannan ai mai sauk’i ne... Ina mai tabbatar miki yanda Yakubu ya makance da soyayyar yarinyar nan har yana sa’insa dake kika sake kika amince ya aureta Toh fah saidai Ki zuba mishi idanu Don kin haifo mata shine...!” Ya k’arashe yana mai kuma tunzura Mommy.... Mommy tace yaje yayi duk abinda ya dace... Baffah Yawale ya fice yana Washe baki... Daga nan yanda suke tsaye suka hango ficewar mutumin daga gidan... Turaki ya k’arasa ya tadda mutumi mai teburin kayan miya, yai masa sallama da musabaha suka gaisa... Idanunsa naga k’ofar gidan su Muhibbah da Baffah Yawale Ke k’ok’arin burka babur d’insa.... Mai Teburin kayan miya ya dubi Turaki yace “Bawan Allah na nawa za’a baka...?” Turaki ya d’anyi gyaran murya yace “Tambaya nake dama...!” Mai kayan lambu yace “Allah yasa na sani...!” Turaki yai nunida gidansu Muhibbah yace “Da Allah wata yarinya nake nema a can gidan sunanta Muhibbah.. Ko ka santa...?” Mai kayan lambu ya Washe baki yace “Aw Muhibbah... K’warai na santa... Ai d’iyar rik’o ce a gidan... Yaron gidan likita shine zai aureta...Idan ban b’ataji ba ma sati mai zagayowa za’ai bikinsu... Kaga wancan wanda yake k’ok’arin burka babur shine K’anin mai gidan, kuma a yanda naji basa so yaron gidan aure ita yarinyar... D’iyar wancan k’anin Baban nasa sukeso ya aura...!” Mai kayan lambu yaci gaba da zuba bayani kai kace tanbayrsa akai... Turaki ya jinjina kai yace “Na gode...!” Sukai sallama mai kayan lambu yaci gaba da ‘yar wak’e wak’ensa abinka da mutane wanda bakinsu bai iya yin shiru... Turaki na k’arasowaga Mahmood ya sanar dashi yanda duk sukaida mai kayan lambu.... Mahmood yace “What..! No Turaki dole musan abinyi... She can’t get married... Idan tayi aure komai ya lalace Turaki... Wannan yarinyar must answer to me first...Idan ta kama na janyota da kaina Ta koma cikin Masarautar nan zanyi Turaki...!!” Ya k’arashe cikeda tsanar hallaya irin nata.... Turaki yace “Alright your Highness... Bamuda time muyi sauri mubi bayan mutumin kafin ya b’ace mana...!” Cikin sauri suka nufi mota Turaki ya tada sukabi bayan Babur d’in Baffah Yawale.... SameenaAleeyou *MUHIBBAH* *60* *©️Sameena Aleeyou...✍🏽* Daga cen nesa da k’ofar gidan da Yawale ya shige sukai parking, suka k’araso k’ofar gidan Turaki ya bud’e murya yai sallama, saidai basuji an amsa masu daga ciki ba... Sun kusan minti biyu tsaye wajen babu wanda ya lek’o daga cikin gidan har kaman zasu juya saiga wani yaro ya fito rik’eda allon karantu Ta ‘yan makarantar zaure... Turaki yai saurin taresa da fad’in “Kai Yaro gidan nan kake...?!” Yaron ya jinjina kai yace Eh... Turaki yace “Shiga ciki kace ana sallama da mai gidan...” Yaron ya dubesu da mamaki sai kuma yace “Ai masu gidan sunada yawa, k’ofofi kashi kashi ne cikin gidan... Wanne zan kirawo maku...?!” Turaki ya d’an shafi kansa yace “Toh..! Bakaga wani mutumi da ya shige yanzu ba da Babur..?” Yaron yai shiru kaman mai nazari sai kuma yace “Kodai Baffah Yawale kuke nufi shine naji k’aran babur d’insa yanzu...” Turaki yaji sunan kaman wanda mai kayan lambun can na k’ofar gidansu Muhibbah ya fad’a masa, saurin jinjina kai yai yace “Yauwa shi dai... Shiga kace ana sallama dashi..!” Yaron ya jinjina ya koma cikin gidan... Jim kad’an ya fito yace dasu Wai yana zuwa.... Bayan shigewar yaron da wasu mintoci Yawale ya fito yana mamakin Ina ya samu bakin buzaye shida babu kowa nasa k’asashen hamada.. Iso yai masu cikin Zauren yanda tabarma ke shimfid’e, yai masu sannu da zuwa suka gaisa gaba d’aya, Yawale ya bud’e murya yace “Saidai kuma ban gane daga ina bane..?” Turaki ya d’an murmusa yace “Eh Toh daga k’asashen can arewacin hamada muke, dama tambaya mukazo gameda d’iyarku mai suna Muhibbah...!” Ai Tun kafin Turaki ya rufe baki Yawale ya soma fad’in “Fad’uwa tazo daidai da zama, dama mun rasa mijin da zamu aura mata, Allah yasa idan kun aureta kuyi nesa da ita da garin nan... Ku tafi can k’asarku da ita yanda bazata kuma dawo mana ba, bazamu kuma cin karo da mai irin fuskarta ba..!” Turaki da Mahmood suka dubi juna da mamaki, Baffah Yawale yaci gaba da fad’in “Kar Kuji komai ba’a mata miji ba, dama uwar goyon nata tace duk wanda ma samu na aura mata, ko kuturu ko makaho kai ko wane irin mutum ne... Toh Alhamdulillah tinda ta samu mutumin da zai ketara da ita wata Nahiyar ai abin ai godiya ne... Dama mu kasancewarta kusa damu ne bamu fata... Wata sati ake bukin d’aura mata aure... Bayin Allah sadaki kawai zaku kawo ni ko yanzu zan kirawo shaidu a d’aura auren...!” Turaki yai murmushi wanda yafi kamada yak’e yace “Oh haka ne Baba..! Toh ai inaga zamu koma dai muyi shawari da magabata...” Turaki bai rufe baki ba suka sinkayo muryar Mahmood daga cikin nad’insa ta buzaye yana fad’in “Babu shawari Baba... Mune nan magabatan wanda mukazo nemawa auren... D’an uwana k’anina zan nemawa aurenta... Yanzu basai anjima ba zan damk’a maka sadaki...!” Ya k’arashe yana mai zira hannu cikin aljihun babban rigarsa Ta buzaye, ya ciro wata ‘yar jaka ta fata ya mik’awa Baffah Yawale... Yawale hannu na rawa ya amshi ‘yar jakar Ta fata, ya shiga warwareta yana ganin abin mamaki.. Silallala ne zallan zinari wanda darajarsu zai iya kaiwa dubu d’arurruka.... Yawale ya kuma murtsuka idanu yana ganin wannan ikon Allah, a ina mutane irin wad’annan suka sami wannan dukiya shidai bai gansu da wata babbar Mota ba hasalima bai gansu da abin hawa ba, daga su sai suturan jikinsu ya gansu... Kaman Mahmood yasan tunanin da yake ya soma fad’in “Kar kaji mamaki Baba sabida mu haka al’adarmu take, mace Tanada matuk’ar daraja, duk mutum yakaiga talauci sai ya nemo silalla na zinari kafin a basa mata, iyayenmu sukan bar mana gadon Rak’uman da muke kiwo Dan muyi kud’in aure dasu....” Yawale ya jinjina kai har lokacin jikinsa rawa yake yana juya coins na zallan gold a hannunsa... Lokaci guda yace “Ai..Toh... Toh ai shikenan, kasan kowa da al’adarsu... Babu komai sati mai zuwa kuzo ku amshi auren d’an uwanku...!” Mahmood ya jinjina masa kai ba tareda yace komai ba saima k’ok’arin mik’ewa da yake da zimmar tafiya... Yawale ya tsare fararen k’afafunsa da kallo wanda da gani kasan hutu da jin dad’i ya zauna a wajen babu wani alamun tafiya cikin hamada a k’afafun balle har ace makiyayi ne mai kiwon Rak’uma cikin Hamada...Anya wannan ba manyan mutane bane suke son b’adda kama... Wad’annan basuyi kamanceceniya da gajiyayyu ba... Shifa baya fata yarinyar nan ta samu wajen maik’o yafi so ta tagayyara, kardai ya kaita yanda zata huta... Toh amma ai shi dama so yake ta fice daga rayuwarsu dan idan har tana tareda Murja da kuma Ansar sam bazata tab’a bari ya cimma burinsa akan dukiyar D’an uwansa da ya mutu ya barwa Ansar da Murja gado, kuma dukiyar Murja ma harinta yake tinda batada magaji bayan Ansar d’in... Idan kuma Ansar ya mutu baida Magajiya face d’iyarsa Hameedah wacce zata zamto matarsa , komai ya dawo hannunsa a sauk’ak’e.... Sallaman Matarsace rik’eda ruwa a faranti ya dawo da Yawale daga duniyar tunanin da ya tafi, da alama baima San bak’in nasa sun fice ba har sun tafi.... Matarsa ta tambayesa Ina bak’in...? Yace Ai har sun tafi Ta koma da ruwan... Ya k’arashe yana mai b’oye silallan zinarin cikin aljihunsa.... Bai isa kowa yaga wannan dukiya ba, ko Murjah bazata gani ba... Kasuwa zai tafi ya saida guda d’aya tak ya kaiwa Murja a matsayin kud’in auren Muhibbah... Sauran kuma ya dafe Allah ya kashe ya basa, shikenan ya samu kud’ad’en da zai kayan d’aki wa Hameedah a sauk’ak’e... ** Har suka shige Mota Turaki bai daina mamakin abinda Mahmood yai ba, shi tsananin mamaki ma ya hanasa furta koda kalma.... Da alama shi kuwa Mahmood d’in ko a jikinsa... Turaki ya nusa kad’an yace “Your Highness, ka tabbata da abinda kayi..? Shin waima cikin k’annenka waye ka nema masa auren Muhibbah, Yazeed ne ko Jamal ne kokuwa Fu’ad ne..?!” Ba tareda ya dubesa ba yace “Maiyasa ka faye gaggawa Turaki..?!” Turaki ya girgiza kai yace “Your Highness zarginta kawai kake baka tabbatar ba, bakada k’wakk’waran shaida da zai tabbatar maka da hakan...!” Idanunsa da suka kad’a sukai jazir naga kwalta yake furta “Bayan k’aryar da tayi mana, Iyayenta ma neman kai sukeda ita... Ai kai shaida ne tinda gabanka akayi komai... Wannan kawai ya isa na kuma aminta da cewa ita d’in ba mutumiyar K’warai bace..!” Turaki ya girgiza kai yace “Mugaye sunyi yawa a duniyar nan, wasu idan har basu suka haifi yaro ba toh basu damu da duk halin k’uncin da zasu jefasa ciki ba, your Highness ya kamata kayi tunani akan hukuncin da kake k’ok’arin zartarwa... Nasan kana son yarinyar nan, kar kayi abinda daga baya zaizo ya dameka ...!” Katsesa yai da fad’in “Bana sonta ban tab’a sonta ba kuma bazan sota ba..!!” Turaki ya murmusa kad’an yace “Idan da baka sonta bazaka tab’a damuwa da al’amranta ba... Your Highness case d’in Muhibbah da Raheema ya banbanta, Raheema ka kamata dumu dumu ita kuwa Muhibbah zarginta kake wanda ni nayi imani can k’asan zuciyarka baka yarda zatayi duka wad’annan abubuwan ba... Nasan baka yarda ba Mahmood..!” Turaki ya k’arshe cikin sanyin murya.. Window kurum Mahmood yake duba Dan baiso ya yarda da kalaman Turaki... Shi hukuncin da ya yanke shine daidai... Idan har yana so Muhibbah Ta dawo cikin masarauta toh hanyar kenan ya aura mata wani cikin Masarautar kafin iyayenta su aurarta ga wani tinda idan tayi aure babu hali ta dawo cikin Masarautar, dole duk yanda zai ya nemama wani cikin Masarautar aurenta...! Ya k’arashe tinanin yana mai dunk’ule hannunsa sabida tsananin b’acin rai... Muryar Turaki ya sinkayo yana fad’in “Toh idan ka aura mata d’aya cikin ‘yan uwanka ita kuma Raheemar fah... Wa zaka aura mata..?!” Ba tareda ya dubesa ba yace “Idan Allah ya kaimu lokacin zakaji ko wanene mijin nata...!” Turaki yai shiru yana duban abokin nasa ba tareda ya kuma cewa komai ba saima maida hankalinsa ga tuk’i da yayi.... ** MASARUTA Giwa da mamaki take duban yanda halitta Jakadiya ya jirkid’e lokaci guda... Ko

Chapter 39 of 65