Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da gefenta, a hankali ta fito ta nufi hanyar da taga Fu’ad yabi cikin sand’a..... SameenaAleeyou📚 [5/24, 9:28 PM] +234 703 453 9908: *👑✨MUHIBBAH✨👑* *007* *©️Sameena Aleeyou...✍🏽* Lokaci ne na almuru hakan yasa ko bayi ma jifa jifa kake gani, kowa yana k’ok’arin komawa mahutarsa ne.... Hakan yasa sam babu wanda ya lura da Muhibbah da tuni ta takewa Yarima Fu’ad baya..... Sashe ne madaidaici ya shigo mai kyaun gaske, gini a jere masu kama da juna wanda ko ba’a fad’i maka domin yaran Sarkin akai, nan Muhibbah Ta hango Fu’ad ya shige d’aya daga cikin dogayen ginin... Tana nan tsaye taji motsin mutum na dosowa cikin sashen... Gabanta ya yanke ya fad’i tai saurin matsewa jikin gini k’irjinta bai daina bugu ba, jin tafiyar take Tamkar mab’oyar da take aka nufa.... Jim kad’an sai hango mutum tai ya shige parlorn da taga Fu’ad d’in ya shige... Ta fito daga mab’oyarta cikin sand’a kana ta nufi saitin window d’in parlorn ta lab’e jiki tana lek’e... Sosai ta hango Fu’ad na kuka tamkar k’aramin yaronda ya kasa jin lallashi... Yana tsugune gaban drawer dake jikin center table da akima parlorn ado dashi sai faman bincika drawer d’in yake yana kuka sosai, duk wasu tarkacen dake cikin drawer d’in jifa Fu’ad keyi dashi, gaba d’aya ya hargitsa wajen ya wargaza... Can ya ciro wasu magunguna cikin sachet yana k’ok’arin b’are ledar maganin... K’wayoyin sun kusan guda goma jikinsa na matuk’ar rawa musamman hannayensa da ya rik’e k’wayoyin dasu... Take ya d’aga kansa sama had’ida lumshe idanunsa masu zuban ruwa ya toshe hancinsa da hannu guda yana k’ok’arin watsa drugs d’in a bakinsa saiji yai an bigesu sun zube k’asa.... Ba Fu’ad dake k’ok’arin bud’e lumsassun idanunsa a hankali ba harta Muhibbah saida ta d’ago idanunta tana duban wanene ya hana Fu’ad aika ma cikinsa da k’wak’walwarsa wannan gubar.... Jamal ne tsaye ya hard’e rai sosai tamkar bai tab’a dariya ba, lokaci guda ya durk’usa suna fuskantar juna shida Fu’ad d’in.... Fu’ad ya matsa can jikin k’afar kujera yana tak’urewa waje guda yake fad’in “No...No no Jamal, I don’t want to live... I’m tired of living like this Jamal.. na gaji.....Na gaji Jamal....!” Ya k’arashe yana mai bin drugs d’in yana tattarosu tamkar dai mai tab’in hankali... Cikin zafin nama Jamal ya kamo fuskar Fu’ad yana fad’in “Look up Fu’ad, kalle ni nan....!” Ya k’arashe yana mai kuma matse fuskar Fu’ad da tuni har ya koma ja sabida tsananin damk’a da yasha.... Dole Fu’ad yai shiru sai duban Jamal da yake da idanunsa masu zuban ruwa, lokaci guda Jamal Keci gaba da fad’in “Now you’d do exactly as I say...!” Girgiza kai Fu’ad yake da k’yar yana mai furta “No no Jamal... No...!!” Ganin bazai shiru ba ya sanya Jamal zaro wata sirinji na allura cikin aljihun wandonsa, lokaci guda yai injecting Fu’ad da allurar.... Kankace mai Fu’ad ya fad’o jikin Jamal tamkar sumamme.... Sauk’e nannauyan ajiyan zuciya Jamal yai kana ya rungume d’an uwan nasa sosai kaman mai tsoron kada a raba tsakaninsu.... Cikin rawar murya Jamal Ke furta “I’m sorry brother, I’m so sorry... I really don’t have a choice.... Ka yafe min Fu’ad....!” Ya k’arashe yana mai kuma k’ank’ame Fu’ad da har lokacin tamkar bai numfashi.... Lokaci guda Jamal ya mik’e ya aza Fu’ad a kafad’arsa kana ya nufi upstairs dashi, d’akinsa ya shigar dashi ya kwanyarsa saman gado, ya gyara masa kwanciyarsa sosai ya lullub’esa kana ya sauk’o k’asa ya tattare drugs d’in dake zube wajen... Saida ya tabbata ya tattare kaf drugs d’in kana ya saita kansa ya fice daga b’angaren Fu’ad.... Muhibbah dake lab’e bayan window a hankali Ta koma Ta jingina jikin bango tana maida numfashi a hankali... Meke faruwa...?” Fu’ad is living a miserable life... Meke faruwa dashi...?” Take taji b’angare na zuciyarta tana ayyana mata cewa ya cancanci fin haka, ya cancanci ya shiga k’uncin rayuwa fiyeda wanda yake ciki yanzu....Ta k’arashe tinanin tana mai sauk’e ajiyan zuciya a hankali... Lokaci guda ta saita kanta kana ta fito daga b’angaren nasa.... Tana isowa sashen da aka sauk’eta kenan ta tadda Umaima tafe wasu kuyangi guda biyu na biye da ita d’aukeda manya manyan trays an rufe da k’yalle.... Muhibbah ta d’an sha jinin jikinta amma sai ta sami k’warin gwiwar dakewa kad’an... Umaima dake bintada kallon mamaki ta bud’e murya tace “Hibba ina kika fito da magrib d’in nan...? Hope all is well...?” Muhibbah ta murmusa kad’an kana tace “Gida na mulki da sarauta yanada gizo da kuma cika idanu, amma saidai dikda wannan gizo da cika idanu nasa idan wanda bai tab’a zama cikinta ba ya halarceta tabbas zaija yana matuk’ar k’aunar ya zaga cikin gidan ya baiwa idanunsa abinci.... Tsananin son naga yanda yanayin Fadar take ya sanyani fitowa, amma saidai koda na fito na lura dare ya sako Kai babu abinda zan iya gani... Sannan naji tsoron nai gamo da abubuwa na babban gida wanda da yawan mutane suka aminta cewa a cikin Masarauta ko wacce iri ne akwai d’inbin abubuwa da idanunmu bazasu iya gani ba... Allah yasa banyi wani laifi ba ranki shi dad’e...!” Ta k’arashe kyakkyawan murmushi saman kyakkyawan fuskarta... Cikeda jin dad’in baiwan kalamai da Muhibbah kedashi saman harshenta Umaima ta girgiza mata kai kana tace “Bakiyi laifin komai ba sai guda d’aya...” Muhibbah ta d’an d’ago tana dubanta tana jiran taji laifin nata, nan ta tina cewa Alkyabban Umaima ne jikinta, ta d’ago da zummar bata hak’uri saidai tuni Umaima ta katseta da fad’in “Laifinki shine kink’i ki daina kirana Ranki shi dad’e... Sunana Umaima, Ki kirani da Umaima kawai....” Murmusawa kad’an Muhibbah tai tana mai sauk’e ajiyan zuciya a hankali kana tace “Tuba nike bazan sake ba... Umaima....!” Umaima ta jinjina kai kana tace “Shigar sarauta ta amsheki, kiso kiga yanda Alkyabba tai kyau sosai a jikinki....” Tai maganar fuska fal fari’a.... Cikeda jin nauyi Muhibba tace “I’m sorry na saka babu izini.....” Umaima ta kuma murmusawa kana tace “Babu matsala dik lokacin da kike so zaki saka, hasalima hardai kina rayuwa cikin gidan nan zaki koyi saka kayan sarauta... Mu k’arasa ciki gobe idan Allah ya kaimu zan zagaya dake da kyau cikin Masarautar nan....” Muhibbah ta d’an ware manyan idanunta kana tace “Da gaske...?” Jinjina mata kai Umaima tai kana tace “K’warai kuwa zan zaga dake kiga ko ina... Allah yasa dai bakida makaranta goben....?” Sai yanzu Muhibbah ta tina ashe Wai makaranta ne ya kawota garin... K’ak’aro murmushi tai kana tace “Satin nan akai resuming so babu wani karatu mai tsauri da za’ai...” Umaima ta jinjina kai kana tace “Hakan na nufi kin amince kenan...” Muhibbah Ta jinjina mata kai murmushi bai bar saman fuskarta ba... Lokaci guda suka sa kai suka k’arasa cikin madaidaicin parlorn kana bayin suka take masu baya... *** Dare ya ratsa, k’afafuwa sun d’auke a cikin fada, bakajin komai sai kukan k’anan halittu wanda wasu idanu na basu iya hangosu cikin duhun dare... Dikda cewa Masarautar gauraye take da hasken fitilu da ya k’ara mata kyau.... Jakadiya ce ke gaba da ita, bak’ar Alkyabbace mai nauyin gaske tai mayafi dashi, baka iya hango komai sai alamun bak’in abu... A haka suka isa k’ofar, hannu tasa cikin wata k’aramar aljihu dake jikin bak’ar alkyabbar nan ta zaro wata ‘yar k’aramar mabud’i... Gini ne a zahiri domin kaw sam bazakai zaton wannan waje akwai k’ofa ba balle kai zaton har akwai mabud’i da zai bud’e ta har biladama ya ratsa Ta cikinta...Take ta soma fad’in wasu abubuwa tamkar yare lokaci guda ginin ke sauya launi alamun k’ofa na bayyana... Kafin ta k’arashe karanto surkullen nan k’ofa Ta bayyana... Mik’awa Jakadiya ‘yar makullin tai kana Jakadiya ta amsa ta bud’e... Abinda zai baka mamaki shine wannan waje da sam bazakai zaton akwai k’ofa wajen ba saigashi ya bud’e, sannan ba wannan kawai ba mataye ne cike a wajen, ‘yan mata daga kimanin shekaru goma sha hud’u zuwa ashirin da d’oriya, babu alamun namiji a wannan waje sai mata.... Da alama wata Al’umma Ke rayuwa cikin wajen...Suna shigewa matayen nan dake sanye cikin shiga iri guda suka risina gaba d’ayansu... Jakadiya da Giwa basu zarce ko ina ba sai wani k’aramin d’aki dake daga cen center.... Daga k’ofa Jakadiya ta tsaya dan bata shige cikin d’akin ba, yayinda Giwa ita kad’ai ta shige cikin wannan d’aki mai cikeda duhuwa... Wani jan darduma mai d’aukeda Tambarin Masarautar Giwa ta d’ale ta zauna... Zamanta babu jimawa saiga wani Dattijo ya bayyana gabanta, bak’ik’irin dashi gashi yai masa duguzun a jikinsa, idanunsa jajazir haka nan sumarsa gabaki d’aya fari ne sol... Murmushi maras kyaun gani saman fuskarsa yake dubanta.... Risinar da kanta tayi alamun gaisuwa kana tsohon ya yaryafa mata wani ruwa dake a hannunsa,bai daina mummunar murmushin nan ba yake fad’in “Nasan zakizo nan sabida ta bayyana kuma babu wani abu da ya faru a Fada face cecekuce tsakanin Yaranki...!” Jinjina masa kai Giwa tai kana tace “Tal’udu...! Mun duba gabas da yamma kudu da Arewa babu wani abu bak’o da ya faru, sannan babu wani rai da aka rasa, Tal’udu kar kace min Cikin Yarana guda babu wanda zai gaji Karagar mulkin Masarautar nan...!” Ta k’arashe tana mai tsaresa da kyawawan idanunta wanda suke cike dam da butulciwa mak’aginta..... Murmushi mai sauti wannan karon Tal’udu yai maras dad’in sauraro kana ya janyo wata jaka ta fata ya baje jakar a k’asa... Take jakar ta koma tamkar tray ta fata ga yashi mai tsananin taushi akanta... Da yatsunsa guda biyu yasa ya zana alama kusan guda hud’u kewaye da juna kan ya zana wani abu tamkar karagar mulkin Masarautar a tsakiya...Ya d’ago yana duban Giwa da kyau kana ya kuma Sa yatsunsa biyu ya zana wani alama daga cen gefe... Saida ya gyara zamansa sosai kana ya soma mata bayani... “Kinga wad’annan alamu hud’u dana zana yaranki ne guda hud’u.... Wannan da yake tsakiya Karagar Mulki ne... Tabbas a cikin yaranki akwai wanda zai gaji mahaifinsa, sannan sarautar Masarautar nan bazata fice daga cikin jinin ahalin Sarki AbdulJabbar ba.... Toh amma....!” Shiru yai yana dubanta... Giwa ta katsesa da fad’in “Amma mai Tal’udu..? Sannan shi wancan alaman da ka zana na menene.....?” Murmusawa yai kad’an kana yace “Wancan alama ta k’arshe dana zana fitilar tsafi bata hasko min komai ba, tsantsan duhuwa ne mai gauraye da bak’in k’ura a wajen wanda yake nunida cewa dik d’anki da ya d’ale wannan Karagar Mulki toh fah mulkinsa bazai k’argo ba sannan duk wasu sirrika da kika bisne a Masarautar nan zasu bayyana... Zaki rasa mulkin Masarautar nan dake da ahalinki zaku zamto tamkar ba’a tab’a yinku ba... Abubuwa da dama zasu canza....!” Katsesa Giwa tai da fad’in “K’arya ne wllhi.. Babu wani mahaluk’in da ya isa ya rabani da wannan gadon mulkin... Nida zuri’ata zamu ci gaba da mulkar Masarautar nan... Kawai ka sanar dani mai ka gani gameda bayyanar mahaukaciyar nan....!!” Kai tsaye ya soma fad’in “Naga guguwa mai k’arfin gaske gauraye da bak’in k’ura a cikin gungun mayaka... Naga TAKWABI mai kaifin gaske sannan naga mashi da kibiya mai tsananin tsinin... Kinyi kuskure da kika bar wannan k’ofa d’aya tak a bud’e...!!!” Giwa ta katsesa da fad’in “Wannan k’ofa kana nufin Ja’afar ne...?” Murmusawa yai kad’an kana yace “Ba Jafaru bane amma ita wannan k’ofar da kika barta da gib’i ka iya zamtowa sanadin ‘Yanta Jafaru....!!!” Daga haka dariya ya kwashe dashi mai mummunar sauti... Kan kace mai ya b’ace b’at kaman bashi a wajen..... Giwa ta mik’e da k’yar gumi na karyo mata... K’ofofi guda goma shabiyar ne rus a jere a gefen d’akin Tal’udu, ko wata k’ofa a k’ulle take sai guda d’aya da take hangota a bud’e wanda duk randa ta shigo wannan gida haka nan take a bud’e.... A hankali ta furta “Muje Jakadiya...” Babu musu Jakadiya tace “An gama Allah shi baki yawan rai....!” ‘Yan matan suka sadda kawunansu k’asa har saida su Giwa suka fice daga wannan gida da yafi kama da sansani.... Koda Giwa ta komo sashenta haka abubuwan saukaita mata yawo, batai mamakin ganin Jamal zaune hard’eda k’afofi alamun yana jiran dawowarta ba.... Domin kaw bazai tab’a bacci ba ba tareda ya nemi albarka mahaifiyarsa ba koda kuwa zai jira dawowarta har asubahi ne... Yanayin da yaga mahaifiyar tasa ciki na tashin hankali ya sanyashi k’arasawa gareta ya tarota... “Mamy...Mamy na meke faruwa....? Ina kika fito cikin daren nan...?” Idanu ta zuba masa tana dubansa, lokaci guda ta shafi gefen fuskarsa kana tace “Babu komai masoyina... Ya ka baro d’an uwanka Fu’ad...?” Fuzar da fuci Jamal yai a hankali kana yace “Karki damu Mamy zan kula da Fu’ad...” Ta jinjina masa kai a hankali ba tareda ta kuma cewa komai ba, Jamal ya d’an dubeta cikeda kulawa kana yace “Maami akwai wani abu ne..?” K’uri tai masa kana ta muskuta kad’an tace “Jamal ka tabbata gaskiya ka fad’in gameda batun Ja’afar...?” Wannan karon da gefen bakinsa ya murmusa kana ya tako zuwa gabanta a hankali... Durk’usawa yai nan gabanta kana yace “Ban tab’a miki k’arya ba Maami na dik abinda na sanar dake da gaske hakance Ta faru....!” Ya k’arashe murmushi kwance saman fuskarsa... Sauk’e nannauyan ajiyan zuciya Giwa tai kana ta shafi gefen fuskarsa tace “Kaje ka kwanta D’ah na Allah shi maka Albarka...!” Ta k’arashe tana shafa sumarsa cikeda so da k’auna... Jamal ya amsada “Ameen Maami na kana ya kuma mata sallama ya fice... Giwa taci gaba da tinanin abububuwan da suka faru cikin Masarautar.. *** Ko kallo bata ishesa ba saima cire zobban hannayensa da agogo da yakeyi, ya zuba su saman bedside kana ya kwab’e rigar mulkin dake jikinsa kyakkyawar suffarsa Ta bayyana, Rahima tai saurin rintse idanunta tana tina yanda alak’arsu da Yazeed ya samo asali... Gimbiya Raheema k’anwacega Gimbiya Zeenatu amaryar Sarki AbdulJabbar mai rasuwa... Su d’in ‘Ya’yaye ne ga Sarkin Akwanga wanda ke k’ark’ashin mulkin Sarki AbdulJabbar gaba d’aya dashike garin a k’ark’ashin k’asarsa take,...A lokacin da Rahima tazo Masarautar Jos bikin ‘yaruwarta Zeenat a nan tai gamo da mutumin da zuciyarta Ke muradin mallaka, wannan mutumi kuwa ba kowa bane face Yarima Mahmood AbdulJabbar, saidai kash abinda yai mata cikas shine Yarima Mahmood baida lokacin wata Mace face na iyalinsa Aliya.... Hasalima Auren mahaifin nasa ya kawosa k’asar bayan matsa masa lamba da mahaifin nasa yai da cewa lallai lallai sai ya halarci d’aurin aurensa da zai sake... A lokacin daga shi sai matarsa Aliya suka zosu Nigeria d’aurin auren Mai Martaba basu taho da Zahra ba a cewarsu tana makaranta, sannan bayan sunyi Abinda ya kawosu da kad’an suka kuma tattarawa suka koma Spain dikda cewa Giwa bataso d’an nata ya kuma tafiya ba amma babu yanda zatayi wannan tsinanniyar matar tasa d’iyar matsiyata tasan dan ita yake gudun gidansu dan yasan muddin yana Nigeria idan batasa ya rabu da wannan matsiyaciyar ba toh kuwa ko shakka babu aure zasu sake masa a Fada ‘yar asali ‘yar babban gida kaman yanda yake d’an manyan mutane.... Rahima bata sami hakan ba taci kuka har ta gode Allah dan Shi Yarima Mahmood baima San akwai wata halitta mai suna Raheema dake k’aunarsa ba... Tun bayan auren Maimartaba Sarki AbdulJabbar da ‘yaruwarta Zeenat tai sai tai zamanta a wannan masarauta da burin wata rana Mahmood zai dawo gida ya aureta dan bata cire rai ba, a wannan zaman da tai a masarautar suka k’ulla abota da Zuhra matar Yarima Yazeed domin zasuzo tsara da Zuhra, tasu tazo d’aya sosai hakan yasa daga abokai har suka koma tamkar aminai, so tari Yazeed yakan tsinci hirar matarsa Zuhra da Rahima yanda Rahima Ke sanar da ita irin k’aunar da takewa d’an uwansa Mahmood... Shak’uwar Raheema da Zuhra dai tai nisa sosai tamkar wasu ‘yanuwan juna, ko Akwanga Rahima ta tafi Zuhra taita damunta da waya kenan tana tambayarta yaushe zata dawo tsaban shak’uwa da aminci dake tsakaninsu musamman dashike Zuhra mutum ce mai Saurin yarda da d’anadam ga sanyin hali da kyakkyawar zuciya.... Wata ranan jumma’a Rahima Ta shigo b’angaren Zuhra da niyyan surprising d’inta dan ranan ta dawo daga tasu Masarautar.... Bata tadda Zuhra da yaran a k’asa ba sannan babu motsin mutane cikin sashen, sai tai zaton Ta sallami kuyangin ne dan wataran idan zatai baccin rana takan sallamesu idan da mai yin wani abu nasa na k’ashin kansa ma ya samu yajesa yai, sannan watak’ila yaran na makaranta basu dawo ba, hakan yasa kai tsaye ta haye d’akin Zuhra ta bankad’e k’ofar da k’arfin gaske tana mai furta “Surprise...!!!” Birki tai da kalaman nata ganin abinda idanunta suka gano mata... Yana tsaye gaban gado jikinsa babu riga sai k’aramar towel dake rik’e hannunsa wanda da alama jik’akk’en sumarsa dake d’igan ruwa yake gogewa.... Rahima tai saurin rintse idanunta jiki na rawa take furta “I’m so...I’m sorry...I’m sorry please..!!” K’afarta har na hard’ewa take k’ok’arin juyawa saidai tuni taji an fizgota an dawo da ita cikin d’akin ta fad’o saman k’irjin mutum... Ta bud’e idanunta masu cikeda tsoro tana dubansa, saidai ga tsananin mamakinta shu’umin murmushin nan ne nasa saman fuskarsa... Lokaci guda kuma sai gani tai ya mugun had’e rai yana mai k’arewa fuskarta kallo idanunta zuwa bakinta... Jikin Rahima bai daina rawa ba mak’ale jikin Yazeed... Lokaci guda kuma sai gani tai ya d’an murmusa kad’an kana yace “Malama idan zaki saki jikinki ki saki jikinki, ce miki akai bansan ke d’in ‘yar hannu bace... Sai wani k’ifi k’ifi da idanu kike min, sarai target d’inki kenan tinda kinsa every Fridays Zuhra na tafiya sashen Giwa da yara suyi mata yini shine kika kasa rik’e kwad’ayinki kika lab’ab’o kika hauro har sama kika kawo kanki yanzu zaki wani matse fuska tamkar tsoron gaske kike, ko ce miki akai bana lura da irin kallon maitan da kike bina dashi ne...” Ya kuma murmusawa da gefen bakinsa kana yace “You don’t play such games with Prince Yazeed sweetheart.... Abinda kikazo nema zaki samu, batai aune ba sai jin fuskokinsu tai sun had’e waje guda.... Rahima ta raina kanta ta kuma raina duk wasu mazaje da tai huld’a dasu a baya, ta yarda Yazeed k’arshe ne yanda yake a zahiri haka yake a shimfid’a, idan kuwa har bazata sami Mahmood ba tinda batada tabbacin zai dawo Masarautar dan haka ta zab’i taita maida kwad’ayinta da d’an uwansa Yazeed wanda takeji tamkar da Mahmood d’in take tare.... Saidai bayan komai ya lafa tsakaninsu ko takanta bai kuma bi ba saima ficewa da yai kaman babu abinda ya faru tsakaninsu, haka dai Rahima ta mik’e ta kintsawa Zuhra d’akinta can k’asar zuciyarta tana jin sam bata kyautawa Aminiyar tata ba... Tin Daga wannan lokaci haramtacciyar alak’a ta k’ullu tsakanin Yazeed da Rahima... Tayi nisa cikin tinanin nan ta sinkayo muryarsa Cikin dakewa yana furta “ “Kinsan ba’a min yanga, so take that thing off....” Ya k’arashe yana mai kuma relaxing cikin gadon.... Jiki a matuk’ar sanyaye Rahima tasa hannu tana zame doguwar rigar dake jikinta hawaye basu daina gangaro mata ba.... Da gefen idanu yake dubanta har ta k’araso gabansa a d’arare tamkar mai tsoron taka k’asa, yau d’in ko idanunsa ta k’asa duba.... Saida ya kwashi dak’ik’ai yana k’are mata kallo daga nan yanda take tsaye kana ya bata izinin zama dan bata isa ta zauna saman gadon ba ba tareda yace tai hakan ba....Ta narka masa harara tana mai kuma ci gaba da share hawaye... A hankali ya mirgino gareta, Rahima na jin hannayensa cikin jikinta Ta fashe masa da kuka... Da tsananin mamaki Yazeed ke duban sabon salon nata... “Ke..!!” Ya daka mata uban tsawa, ta d’ago idanunta masu zuban ruwa tana dubansa, lokaci guda take furta “This is not good Yarima... Wllhi ni dama nayi zaton Yarima Mahmood bazai dawo bane nai zaton bazan tab’a samunsa ba shisa na biye maka... But wllhi na tuba daga wannan mummunar sab’on ni da aure nake son Mahmood, family nake so nidashi muyi building a sabon kingdom d’inmu...Pl....!” Sauk’an marin da taji ne babu zato ya sanyata had’iye sauran kalaman nata... Ta d’ago idanunta masu zuban ruwa tana duban Yazeed dake tsananin huci lokaci guda yake furta “Prince Yazeed AbdulJabbar can never be second option!!!... Ke kinyi kad’an kice a rashin wani kike taredani... And let me remind you this princess, idan kina tunanin jin kunyan idon duniya ne Toh ki sani a wannan duniyar babu wani abin jin kunya... Cos life itself is full of disappointment... Get out of my sight..!” Ya k’arashe yana nuna mata k’ofa... Da tsananin tsoro take dubansa kana tace “Yazeed a daren nan zan fita, ka kuwaga time...?” “I’ll be saying it twice if I said it again... Kuma kinsan bana maimaita magana....!” Jiki a matuk’ar sanyaye ta fice dan tasan kad’an da aikinsa yasa ai waje da ita.... Haka ta fice cikin daren nan k’afa dik ya d’auke, domin a nan d’aya daga cikin guest house d’in marigayi Mahaifinsa suke akasarin had’uwarsu... Tana fitowa ta shige cikin motarta k’irar Mercedes Ta nufi Fada, batabi ta babban gate d’in Fada ba dan tasan komai ka iya faruwa dan haka ta k’ofar bayi tabi ta shigo cikin Masarautar.. Motarta ma a nan sashen bayin Ta barota, Haka nan take tafe tana waige waige tamkar mai tsoron kar wani ganta... Muhibbah da ta kasa bacci dan idan ta tafi bak’on waje hakan ne Ke faruwa da ita a ranakun farko dan haka harabar masauk’inta ta fito tai zamanta tana bin taurari da suka haska sararin samaniya da kallo, lokaci guda tana tinanin Fu’ad da halinda ta gansa ciki.. Nan ta hango giftawar mutum, ta d’an mik’e kad’an tana kuma lek’awa tabbas mace ce kuma cikin shiga irinta alfarma nan ta hangeta ta shige hanyar da zai sadaka da wani sashen.... Jim kad’an sai hango hamshak’iyar jeep k’irar Ford tai ta shigo cikin Masarautar, ta nufi wani sashen gefen sashen dakeda tabbacin na Fu’ad ne.... Toh su waye wad’annan masu dawowa Fada cikin dare....? Tambayar da ya tsaya mata a rai.... SameenaAleeyou📚 [5/27, 10:42 AM] +234 703 453 9908: *👑✨MUHIBBAH✨👑* *008* *©️Sameena Aleeyou...✍🏽* Tinda ya kwanta yake wasu irin mafarkai marassa kyau, da fari mafarkin matarsa Aliya da mahaifinsa yai, bayan yayi addu’a ya sake komawa wani mafarkin ya kuma tadashi... Wannan karon akan K’annensa guda Uku ne, abinda ya gani cikin mafarkin sosai ya tada masa hankali... Tsaye ya hangi Yazeed da Fu’ad rik’e da takubba a hannayensu ko wanne takwabin dake hannunsa na d’igar da jini wanda yake jajazir.... Sunayensu ya ambata cikeda tashin hankali ganin abindake rik’e hannayensu, cikin kid’ima ya nufi yanda suke a tsaye suna maida huci suna nunasa da takubban dake hannayensu lokaci guda suka fashe da dariya basu daina nunasa da takubban ba... Mamakin dariyarsu yake bayan abinda ya gani rik’e hannayensu, k’arasowar da zai kusansu sai hango wani d’aki yai a bud’e cikin jerin wasu d’akuna... Basu daina dariyar da suke ba har Mahmood ya nufi cikin d’akin mai tsananin duhuwa.... Saidai yana shiga d’akin ya hango mahaifiyarsu zaune saman gadon sarautar masarautarsu... K’irjinsa yaci gaba da bugawa sanda ya hango d’an uwansa da yakeda tabbacin ya fita zakka cikin sauran ‘yan uwan nasa durk’ushe kan wata yarinya sai darza mata wuk’ar yake... Ga jini na kwarara amma da alama bata mutu ba.... Cikin zafin nama ya ambato sunan Jamal da k’arfin gaske, saidai ko gizau Jamal bai ba saima ci gaba da darza mata takwabin da yake... Tsalle Mahmood yai ya finciko Jamal don ceton yarinyar amma mai..? Yana d’agosa saiji yayi an luma masa takwabi a cikin cikinsa... Mahmood ya rik’e cikinsa yanda jini ke malala a k’asa.. Ya d’ago yana duban ‘yan uwansa guda Uku rikeda takubban saidai bazaice ga wanda ya caka masa ba cikinsu, maida dubansaga mahaifiyarsu dake zaune saman Karagar mulkin yai saidai wannan karon matarsa Aliya ya gani ba mahaifiyarsu ba...Hannu yake mik’a mata alamun neman taimako amma inaa batai ko gizau ba tana nan zaune saman Karagar mulkin saima sakin dariyar da take mai firgitarwa... A hankali yake ji numfashinsa na d’aukewa jikinsa na zamewa har saida ya fad’o kan yarinyar da Jamal ya gama yankata da takwabi, su duka biyu jini na malala daga jikkunansu.... A daidai wannan lokaci ne ya farka daga baccin cikeda tsananin tashin hankali... Addu’o’in da sukazo bakinsa kawai yake iya karantawa had’ida jero hasbunallah wa ni’imal wakil... A hankali yake jin natsuwa na sauk’o masa cikin zuciyarsa... Hannu ya mik’a ya kunna side lamp kana ya dubi k’aramar agogo dake gefen bedside ya nuna k’arfe 4:30am, anata kiraye kirayen assalatu... Shafe fuskars yai da duka hannayensa biyu kana ya mik’e ya nufi bathroom ya d’auro alwala, shimfid’a abin sallah yai amma ko tsayuwar sallar saiji yai ya kasa... Ya zauna nan

Chapter 4 of 65