isa haka...”
Sai wannan lokacin Mahmood ya murmusa kad’an yace “Ashe dai kaid’in gawro kake...!” Yai maganar yana k’ok’arin had’o kalaman wanda daji kasan bai saba ba...
Turaki ya murmusa kad’an yana mai mik’ewa tsaye danyiwa abokin nasa rakiya, lokaci guda yake furta “Na shigo layinku Rankaidad’e for the time being muji yanda kukeji tunda kak’i kaba da himma kan batun Auren nan naka...!” Yai maganar yana sosa kai...
Mahmood dai murmusawa kurum yai without saying a word... Turaki ya kasa gane cewa shid’in ba aure ne ko soyayya ne ya dawo dashi ba... Yanada babban dalilinsa, dalilin kuwa shine to find answers and get justice ga wad’anda aka zalunta cikin Masarautar....
**
Wani jahilin mari Waziri ya kuma sauk’ewa d’an Aiken nasa wanda Ke bibiyan Mahmood... “Ashe kai shashasha ne ban sani ba, ta yaya Mahmood d’in zai b’ace maka... A iska yake tafiya kokuwa....!”
D’an Aiken Waziri ya dafe k’uncinsa yana sosawa sabida zafin marin lokaci guda yake fad’in “Allah shi taimakeka wllhi nemansa nayi na rasa nadai ga kaman wani gida ya shige daga nan ko k’yallin motarsa ban kuma gani ba...”
Waziri yaci gaba da sakin fuci yana aika masa jahilin kallo... “Tashi ka b’ace min a nan kafin nai maka horonda ruhinka zai gaza d’auka...!!”
A d’ari d’an Aiken ya mik’e a guje yana mai ci gaba da sosa fuskarsa...
Waziri ya dafe kumkuminsa da duka hannayensa biyu, Ta yaya zai soma sanar da Giwa wannan batu... Inaa ko kusa bazai sanar da ita Sun sami mishkila ba gwara ya bada himma a k’ok’arin kawarda Ubandoma da suke k’ok’arin yi... Buge babbar garensa yai ya shige cikin sauri tamkar wani zai kifa k’asa...
**
Yazeed yai K’uri yana duban Majidad’i dake tsaye gabansa yanaci gaba da sakin fuci “You mean my brother was here...?!” Ya tambaya yana duban Majidad’in...
“Maimaita maka kake so na sakeyi... Wllhi idan mahaifina ya mutu alhakin mutuwansa nakan Mahmood ne... Shine ya kashe Wambai...!” Ya k’arashe cikin tsananin fuci...
Yazeed ya jinjina kai cikeda jin dad’i yace “Zuwa yai to finish what he started... To kill Wambai... Kar ka damu kaji da mahaifinka ni zanji da wancan munafukin Hadimin Mahmood d’in ya k’arashe yana mai d’an bubbuga kafad’ar Majidad’i... Suna tsaka da zancen ne kaman daga sama suka sinkayo kururuwan Innani tana fad’in ta shiga uku ta mutu ta lalace Sun kashe mata miji..!
Yazeed da Majidad’i suka dubi juna a tare... Babu shiri suka fad’a cikin d’akin Majidad’i kaman zai kifa k’asa yake ambato mahaifinsa....
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un..! Dukkanin mai rai mamaci ne, yanda akazo haka wata rana dole a tafi duk daren dad’ewa, koda anaso koda ba’aso idan wa’adi yayi dole bawa ya komaga mahaliccinsa.. Allah ka bamu k’arshe mai kyau Ameen..!
Koke koke sukaci gaba dayi cikin asibitin, yayinda Yazeed ya zame jikinsa ya fice daga cikin asibitin...
**
A can Fada kuwa tun bayan dawowan Mahmood gida ya aika ai masa kiran Fu’ad...
Yana zaune parlornsa yana duba mail d’insa da ya jima baibi takansa ba sabida abubuwa dake kan faruwa a Masarautar Fu’ad yai sallama ya shigo...
Idanunsa naga computer dake bisa teburi gabansa ya amsa sallaman Fu’ad d’in had’ida masa izinin zama ....
Fu’ad ya furta kalaman godiya kana ya isa ya zauna a d’arare dan harga Allah mugun nauyin Yayan nasa yake tamkar wani mahaifinsa...
Shiru ya d’an ratsa tsakani Mahmood naci gaba da abinda yake bisa computer... Sai bayan kaman ahud’ewar wasu dak’ik’ai Mahmood ya kashe computer d’in had’ida zame farar tabarau dake mak’ale fuskarsa wanda ko ba’ace Kai tsaye zaka iya cewa na k’ara k’arfin gani ne... Hakan ya baiwa Fu’ad daman zamowa kad’an daga cikin kujera ya gaida Mahmood d’in...
Babu yabo babu fallasa ya amsa masa kana ya soma masa tambaya gameda sabon karatunda bai jimada farawa ba “Ya karatun naka... Kanadai yi koh...?” Yai maganar yana mai daidaita zamansa cikin kujera
Fu’ad ya jinjina masa kai alamun tattabatarwa kana ya k’arada “Alhamdulillah Yaya jiya na kammala registration..”
Jinjina masa kai yai kaman bazaice komai ba sai kuma yace “Yayi kyau...!” Shiru ya d’an ratsa tsakani kafin Mahmood d’in yai gyaran murya kad’an yace “Fu’ad I want you to concentrate on your studies for now... Banda maganan mata da abokai barkatai, ba komai zasu haifar maka ba face distraction....Priorities your studies first... Ka fahimta..?” Ya k’arashe yana mai tsare Fu’ad d’in da idanu...
A hankali Fu’ad Ke jinjina masa kai “Na fahimta Yaya... And in sha Allah this time around I’d not disappoint you, zanyi iyaka k’ok’arina naga nayi graduating da yardar Allah... But Yaya wani hanzari ba gudu ba...!”
Mahmood ya d’ago yana dubansa.. Kafin Fu’ad ya sami zarafin magana Sarkin Gida ya shigo a firgice had’ida zubewa k’Asa yana furta “Tuba nake Allah shi taimaki ‘ya’yan Sarki.. A gafarceni na shigo babu izini Babban Al’amari Ke tafe dani...!”
Yarima Mahmood yace “Fad’i damuwarka Sarkin gida meke tafe dakai...?”
Sarkin gida ya kuma risinawa yana mai yarfe gumin goshinsa yake fad’in “Allah shi taimakeka Wambai ne...!”
Baikai aya ba Mahmood ya mik’e tsaye zunbur yana furta “Ya jikin Wambai...?”
“Allah shi taimakeka Wambai dai Allah yayi masa cikawa....!!” Ya k’arashe yana mai karanto addu’o’i ga Wambai d’in...
Hannayensa hard’e Ta baya ya lumshe gajiyayyun idanunsa yana mai furta Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un cikin zuciyarsa...
Fu’ad ma ambaton Allah ya somayi yana mai jinjina lamarin...
Take Yarima Mahmood ya d’au wayar salulansa saman center table ya nufi k’ofa babu shiri lokaci guda yake ceda Fu’ad “Call your brothers Yazeed and Jamal, and please ka shiga ka sanar da Maami calmly...” Fu’ad ya jinjina kai yana mai furta “Okay Yaya... Right away...!” Mahmood ya kuma duban Sarkin Fada yace maza a sanar da ahalin Fada shi ya wuce gidan Baba Wambai.... Sarkin Fada ya amsa yana mai masa addu’an sauk’a lafiya had’ida karanto addu’o’in neman rahama ya Wambai...
Yana tafe ya kirawo Turaki ya sanar dashi, babu b’ata lokaci Turakin yace su had’u can gidan Wambai d’in....
Daga can Sarkin Mota ya hangoshi ya taso a guje ya nufosa yana masa fadanci yake fad’in “Allah shi baka yawan rai Ka baiwa Sarkin mota izini ya tuk’a ka rik’e sitayari(Steering) ba naka bane... Kokuma d’aya daga cikin drebobin gidan ya tuk’a Allah shi taimakeka... Balle ma kaid’in Sarkin Mota shi yafi cancanta ya jaka... Godiya nake Allah shi taimakeka...!” Ya k’arashe yana mai bud’ewa Mahmood d’in owners corner...
Shidai kawai shigewa motar yai ba tareda ya tsaya sauraren Sarkin Mota ba... Bafaje guda d’aya ya shige gaban mota...Kankace mai Sarkin mota ya jata sun fice cikin Fada....
A can k’ofar gidan Wambai suka tadda su Waziri Hakimi Galadima Jarmai da dai sauransu.... Sanda Mahmood ya iso suka soma gaisawa suna masa ta’aziya had’ida sanar dashi Wambai na cikin ana masa sutura...
Fitowar Majidad’i tareda Yazeed kenan sukai tozali da Mahmood.. Ganinsu su biyu a tare sosai ya baiwa Mahmood mamaki, ya akai har Yazeed ya sani ya rigasa k’arasowa kuma Sarkin Fada mashi ya soma sanarwa... Toh Wai ma ya akai yaga Yazeed da Majidad’i a tare... Wata zuciya tace rasuwa akai so ba komai bane dan ka gansu tare... Mutuwa na sa a aje duk wani gaba da k’iyayya a gefe... Majidad’i sai aika masa muguwar kallo yake yayinda Yazeed ya k’arasoga su Galadima yana sanar dadu an gama shirya Wambai...
Mahmood kaw k’arasawa wajen Majidad’i yai ya masa gaisuwa dukda cewa ba wani amsa sa yai ba...
Isowar Turaki dasu Fu’ad su Jamal dadai wasu tsiraru daga cikin tawagar Fada suka d’unguma zuwa cikin gidan gaba d’aya sukaima iyalan Wambai gaisuwa...
**
Kasancewar hankulan mutanen gidan ya karkata zuwa rashin da akai ga d’aukacin Masarautar hakan sai ya baiwa Muhibbah dama domin ta binciko zanen da takeda tabbacin Jamal ya d’aika daga wajen Umaima..
Sashen Jamal a kulle yake gashi wannan shine damarta na k’arshe dan batasan sanda zata sake samun dama irin wannan ba... Mayafin kanta Ta cire Ta had’a da d’ankwalinta tai majajjawa ta jefa sama nan ta samu kuwa ya kama... Tuni Ta soma k’ok’arin haurawa sama da igiyar data k’ulla dikda cewa k’iris ya rage bata zulo k’asa ba... Cikin sa’a da ikon Allah ta samu ta dafe jikin gini ta k’arasa haurawa da k’yar tana mai tsananin haki... Ta koma gefe tana maida numfashi tana duba hannayenta yanda Ta kukkuje... Cikin sauri Tai azaman tashi had’ida kakkab’e jikinta Ta bud’e sliding door da zai sadaka da cikin d’akin Jamal daga nan sararin shak’atawa dake a saman nasa... Cikin sand’a take gudanar da al’amran nata...
D’akin Ta soma k’arewa kallo kafin ta soma binciken drawers tana duba ta yanda zata sami wannan zanen...
Drawers da dama ta bincika bata samu ba saidai tana janyo wani drawer dake a k’Asa gabanta ya yanke ya fad’i, hannunta na tsananin rawa take janyo abinda Ta gani cikin drawer d’in... Farin k’yalle Ta gani da shatin jini jiki... Jikinta bai ida mutuwa ba saida taga Fararen k’yallayen har guda goma sha biyar ne ko wanne da shatin jini a jiki.... Sosai jikinta Ke tsananin rawa tana mai ci gaba da k’arema k’yallayen kallo.. Gabanta ya kuma tsinkewa ya fad’i sanda taga ko wani k’yalle d’auke yake da suna daga k’asansa... SAUDATU shine sunan data hanga jikin k’yalle na k’arshe wanda shima d’auke yake da shatin busasshen jini....
Take ta rintse idanunta had’ida toshe bakinta da duka hannayenta biyu jin wane irin kuka mai k’arfin gaske na zuwa mata.... Ta koma gefe guda ta tak’ure sosai tana kuka mai tsuma zuciya.... Abubuwan da suka faru da ita shekarun baya sukaita dawo mata... Da k’yar ta iya saita kanta tai saurin tattare k’yallayen ta maidasu yanda ta samu... Har ta saduda bazata sami hoton zanen ba dan gara tai ta fice kafin a taddata cikin d’akin komai ya rushe mata... Kaman ance ta d’aga bakin katifa nan taji ta kamo alamun abu... Tana janyowa kuwa taga frame d’in ne... Sauk’e deep breath tai kana tai saurin ciro wayarta ta soma d’aukan hoton zanen... Sauri sauri take k’ok’arin maidawa...
Tana shirin ficewa ne taji alamun ana haurowa saman babu shiri Ta koma da baya k’irjinta naci gaba da bugu... Ta rintse idanunta tana karanto addu’a cikin zuciyarta...
Muryar Giwa ta sinkayo cikin fad’a fad’a tanaima Jamal d’in magana shi kuma yak’i tsayawa ya saurareta sai haurowa sama yake...
D’aki ya shigo rai a matuk’ar b’ace kafin ya maida k’ofan Giwa ma ta bangaji k’ofan ta shigo tana furta “Ka saurareni nace Jamal.... Kana jina koma wacece budurwar taka ka aje maganar soyayya ba yanzu ba na fad’a maka sai babu adadi akwai shiri na musamman da nake maka...!”
Cikin tsananin k’unan rai yake dubanta kana ya girgiza cikeda rashin yarda da kalaman dake fitowa daga bakinta “Har yaushe kenan Maami... Har yaushe zanyita zama a haka... Maami girma nake ba k’ank’ancewa nake ba... I want to start my own family, na rok’i arzikinki Ki k’yaleni haka nan... Ya isa haka please..!” Ya k’arashe cikin tsananin rawar murya yana mai had’e hannayensa biyu waje guda alamun rok’o...
Giwa ta k’araso ta rik’o hannayensa cikin rawar murya itama take furta “Zakai naka family d’in d’ah nah believe me... Kawai so nake ka k’ara hak’uri kaji...!!”
Ya d’ago rinannun idanunsa yana dubanta, lokaci guda yake sakin murmushin da za’a iya kira da na takaici “Oh really..! Na k’ara hak’uri... Wai mai kike tsoro Maami... Na fad’a miki ko nayi aure bazan daina miki biyayya ba ki k’yaleni nayi aurena kafin na sanar da Ya Mahmood cewa kin hanani aure...!”
Saurin toshe bakinsa tai tana mai furta “Kul ahir d’inka, na haneka... Idan ka sanar da Mahmood shikenan asirinmu ya tonu kasan shi bazai fahimci komai ba... Toh naji kanaso kai aure wacece matar daka samu... D’iyar wace masarauta ce..? Ko kuwa d’iyar wani mai mulki ne...?”
Jamal ya saki murmushi a hankali yana mai dubanta kan ya isa saman gado ya zauna “Maami kinfi kowa kusanci da ita...”
Giwa ta gyara tsayuwarta tana mai dubansa “Ban fahimceka ba.. Wacece ita..?”
Murmushin bai bar saman fuskarsa ba yake furta “Your niece Umaima...!”
K’iris ya rage Giwa batakai k’asa ba... Tashin hankali ana wata ga wata... Umaima dai... Umaima Jamal Ke so...Take annurin fuskar Giwa ya d’auke cak... Ta shiga nunasa da yatsa tana mai furtawa da k’yar “Koda wasa kada ka kawo min wannan rainin hankalin a gidan nan... Bazaka auri Umaima ba.... Na gama magana...!” Tana ida fad’in haka ta fice fuu tamkar zata tashi sama...
Jamal yaci gaba da sakin fuci yana mai jifa da pillow... Lokaci guda ya mik’e ya nufi bathroom... Muhibbah dake mak’ale bayan cottons Ta fito a hankali tana goge gumin dake goshinta... Cikin sand’a tabi Ta hanyar data shigo.... Shakka babu ta bangaji tubalin flower Wanda hakan ya janyo hankalin Jamal... Babu shiri ya fito yana lek’en meke faruwa... A hankali yake bin alamun k’fafu har ya iso yanda ya jiyo sautin... Baiga kowa ba amma yaji alamun fad’uwan abu.... Yai saurin saurin isa jikin gini yana lek’a k’asa.... Ya k’urama waje guda idanu yanda ya tsinci k’aramin k’yalle kaman an fincika ne ya rage saura... D’aukan k’yallen yai a yatsun hannunsa yana juyawa a hankali.... Idanunsa suka kuma sauk’a kan alamun shatin jini yanda ta kuje gwiwar hannunta... Jamal yai saurin k’arasawa had’ida k’urama wajen idanu... Hannu yakai ya d’an shafi jini yana duba... Tabbas jini ne... Kenan hakan na nufin wani na bibiyarsa a Masarautar... He needs to find out koma wanene...! Ya murmusa kad’an yana mai furtawa a fili “You chose the wrong prince.. Ko wanene kai I’d hunt you down myself...!!” Ya k’arashe yana mai gimtse fuska had’ida sakin huci...
**
Tareda yaran Sarki AbdulJabbar gaba d’aya akai komai idan ka cire Jamal wanda ya tafi amsa kiran mahaifiyarsa
Daga bisani aka kai Wambai cikin Fada yanda ake bisne sarakuna da ‘ya’yayensu nan aka bisne Wambai...
Kowa ya watse aka bar Mahmood da Majidad’i suna tsaye kan k’abarin suna addu’o’i ga Wambai...
Majidad’i ya d’ago rinannun idanunsa yana duban Mahmood... Murmushi ya saki da gefen bakinsa yana mai furta “Aikin banza kenan idan kana tunanin add’u’anka zai isaga mutumin da kai ajalinsa... Da zaka matsa daga kan mahaifina da ya fiye min komai domin tsayuwarka a nan ba amfanansa da komai yake ba... Kuma bari kaji na sanar dakai Billahillazeem sai na d’au fansar mutuwar mahaifina... Kuma sai na amshe mulki ya koma gidanmu koda hakan zai zamto abinda zan aikata na k’arshe kenan a rayuwata..!!” Daga haka sa kai yai ya shige cikin tsananin huci tamkar zai kifa k’asa...
SameenaAleeyou 📚
[7/30, 7:10 AM] +234 703 453 9908: *MUHIBBAH*
*38*
*©️Sameena Aleeyou...✍🏽*
Da idanu Mahmood ya rakasa har ya b’acewa ganinsa kana ya maidoda dubansaga k’abarin Baba Wambai, abubuwa ne jibge cikin zuciyarsa da zaiso amo dasu amma saidai babu halin yin hakan... Ya kuma lumshe idanunsa a hankali kana yasa kai ya nufi k’abarin mahaifinsa wanda ratan dake tsakaninsa dana Wambai kad’an ne... Ya jima yana tsaye wajen yana karantowa mahaifinsa addu’a kana ya nufi na matarsa itama addu’an yai mata had’ida sauran mutattun dake kwance wajen cikin harda kakanninsa...
Daga nan fitowa yai ya nufi sashen Giwa yanda ya tadda ta fito tana shirin tafiya Gidan Wambai Jakadiya na biyeda ita da kumburarren fuska sai muk’arabbanta na cikin Fada dake take masu baya, Mahmood na k’arasowa suka zube suna kwasan gaisuwa, Jakadiya sai faman b’oye kumbararren fuskarta take cikin mayafi...
Mahmood ya kuma duban Jakadiya dake ci gaba da k’ok’arin janyo mayafi tana kare fuskarta... Sunanta ya ambato wanda ya sanya gabanta fad’uwa... Cikin ‘yar daburcewa Jakadiya Ke k’ok’arin amsawa tana mai kuma risinawa “Allah shi taimaki Yarima mai jiran Gado...!”
Mahmood ya gyara tsayuwarsa kad’an “Jakadiya mai ya sameki... A ina kika samu rauni...?”
Jakadiya ta d’an saci duban Giwa dake jifarta da muguwar kallo... K’ok’arin saita kanta tai had’ida furta “Allah shi baka yawan rai k’aramin had’ari na samu amma da sauk’i...!”
Yai shiru tamkar mai nazari sai kuma yace “Likita ya dubaki....?”
Wannan karon Giwa ce ta basa amsa da fad’in “Karka damu Sadauki lafiya lou take wannan raunin ba komai bane, na riga masa likita ya dubata...”
Jakadiya ta had’iyi k’uncinta jin abinda Giwa ta gama fad’iwa Mahmood, lallai ta yarda Giwa tayi nisa a makirci tinda har ita da take ta hannun damarta bata k’yale ba...
Jinjina kansa kad’an Mahmood yai had’ida mata fatan samun sauk’i Giwa na fad’i masa zasu wuce gidan Wambai gaisuwa...
Jinjina kai yai cikeda girmamawa yace a sauk’a lafiya... Tawagar Giwa suka sa kai ana ci gaba da wasa Giwa duk wani taka k’afarta da zatai a k’asa..
**
Video call yau d’in yaji ya kirata sabida kewarta da yai sosai, yana zaune Office d’insa saman kujerarsa na duba marassa lafiya yai mata K’uri ta fuskar wayar nasa yanda take ci gaba da goge gwiwar hannunta data karje with cotton wool... Lokaci guda take ci gaba da fad’in “I couldn’t believe what I saw either, I mean... Mai ya kawo sunana rubuce jikin k’yalle, and what worries me the most shine k’yallen da sunana Ke rubuce bisa anyi crossing... Mai ahalin AbdulJabbar suka aiwatar da sunana...”
Katseta Ansar yai da fad’in “Wait what’s that... Are you injured...?”
D’an fuzar da fuci tai a hankali tana mai gyara zamanta take kuma duban hannun nata kana tace “Oh! Just a small scratch but I’m okay... Kar ka damu likita...”
Fuzar da huci yai a hankali yana mai kauda kai gefe cikeda damuwa “Hibbah bamu yi haka ba... You promised me you won’t put yourself in harm ways.. You promised me you’d take good care of yourself... Toh mai nake gani yanzu...!” Ya k’arashe cikin d’an tsawatarwa...
Fuzar da huci tai a hankali kana tace “I’m sorry..Okay, it won’t happen again...I’d be more careful next time...Yayi maka..!” Ta k’arashe cikin raunin murya...
Shafa fuskarsa yai da duka hannayensa biyu kana yace “Do I have a choice..!”
Dariya yaso bata ta d’anyi kad’an yayinda Ansar ke fad’in “Aw Wato ma dariya na baki...!”
Muhibbah tace “Gani nayi Likitana ya fini damuwa da lafiyata...!”
“Of course you’re right... Na fiki damuwa da lafiyarki... My next patient zai shigo Hibbah.. Do you want me to attend to them...?!” Yai tambayar cikin kashe murya...
Murmusawa tai kad’an tace “Likita bakada dama... We talk later.. Take care.. Bye..!”
Katseta yai da fad’in “I love you...!”
Murmushi kurum tai cikin tsananin sanyin jiki wanda ita kanta bata San dalilin jin hakan ba kana Ta katse kiran ta koma cikin kujera ta zauna sosai tana mai lumshe idnunta.. Abubuwa ne da dama cunk’ushe cikin zuciyarta...
**
A can gidan Wambai kuwa yanda aketa karb’an gaisuwa Gimbiya Zeenatu ma da tata tawagar Sun halarta... Raheema sai faman aikawa Juwariyya muguwar kallo take, dik itace ta janyo Mahmood yanzu bai kulata, gashi ta kula sam maganinsu baiyi tasiri akan Mahmood d’in ba tinda gashi shiru shiru har yanzu babu wani canji tun ranan data barbad’a maganin a sashensa... Tai k’wafa tana mai kuma hararan Juwariyya...
Ga mamakin Raheema Murmushi Juwariyya Ta sakar mata kana ta tura mata sak’o ta waya
_Haba mutumiyar ko gaisuwa babu, ai ya kamata Kimin ta’aziya for old time sakes... How about idan muka keb’e Ta baya, I’ve something special for you..!_
Raheema ta karance sak’on ta kuma d’agowa tana duban Juwariyya dake ci gaba da sakar mata murmushi tana mai mik’ewa tsaye kana ta shige wata k’ofar.. Tana shigewa Raheema ma ta mik’e tana mai gyara mayafinta had’ida satan idanun mutane musamman Su Zuhra da Zahra da Umaima dake zaune daga can gefe... Ta d’an rank’wafo taceda Zuhra “Best bara na d’an amsa waya...”
Zuhra ta jinjina mata kai tana mai ci gaba da jan cazbaha dake hannunta Raheema tasa kai tabi k’ofar da taga Juwariyya tabi...
Raheema na shigewa Juwariyya ta maida k’ofar ta rufe... Raheema ta finciko wuyan Juwariyya tana fad’in “How dare you... Laifinki ne Mahmood bai kulani yanzu, you messed everything up...!”
Fincikewa Juwariyya tai tana fad’in “Ki saurareni Raheema shisa na kiraki wajen nan to make it up to you.. Amma idan bazaki saurareni ba fine kina iya tafiya...!” Ta k’arashe cikin huci...
Gyara tsayuwarta Raheema tai tana fad’in “Fine, tell me mai kike son sanar dani... Wani amfani abinda zaki sanar dani zai min...?!”
Juwariyya ta murmusa kad’an kana tace “Zai muku amfani both you and Mahmood, it might help you win him back.... Shi kuma Ya Mahmood zai masa amfani yasan yanda zai ya kare kansa da mulkinsa...!”
Raheema ta d’an gyara tsayuwarta tana fad’in “Mai kike nufi...?”
Juwariyya ta fuzar da iska kad’an kana tace “You know nafi kowa san Ya Mahmood ya d’ale Karagar nan... Banson Yaya na ya d’ale...”
Raheema ta katseta da fad’in “Ke naji naji... Just go straight to point da Allah bansan iyayi...!”
Juwariyya tace “I saw my brother and Ya Yazeed together at the hospital before my father passed away...!”
“So, sai mai dan kin gansu tare..Ta yaya hakan zai taimaka min win Mahmood back...?”
Juwariyya ta fuzar da fuci a hankali... “Dad’ina dake baki cin Riban zance Anty Raheema.. Ahalin gidan nan da ahalin Sarki AbdulJabbar basa jituwa anyi masu wannan shaidan, so zai matuk’ar wahala for those two to get along, naji sun ambaci sunan Ya Mahmood, and one thing to be certain of shine ba abin arziki suke k’ullawa ba..They might be planning something against him... Ya kamata ki sanar da ya Mahmood yasan yanda zai fuskanci wad’annan biyun kin fahimta...”
Shiru Raheema tai tamkar mai nazari sai kuma ta jinjina kanta tana mai sakin murmushi a hankali...
Juwariyya Ta murmusa tace “Na gyara abinda na b’ata I guess...”
Kafad’anta kad’an Raheema ta dafa kana tace “Baki tab’a birgeni irin na yau ba... I must say thank you...” Ta k’arashe tana mai nufan k’ofa... Saida ta fice da wasu dak’ik’ai kana Juwariyya ta fice....
Ko ba komai yau ta sami abinda zatai amfani dashi ta karkato hankalin Mahmood zuwa gareta, amma kafin nan ya kamata ta soma shan cikin Yazeed taji mai yake shiryawa kan Yarimanta... Tai k’wafa tana jinjina bak’in zuciya irinta Yazeed wanda har zai kaisa ga halak’a d’an uwansa...
**
Yazeed ya kuma gyara zamansa yana duban Ubandoma daketa faman had’iyan abincin da Yazeed d’in ya kawo masa hannu baka hannu k’warya... Ya ida ci yana mai tand’e yatsu yake fad’in “Godiya nake rankashi dad’e shakka babu yau d’in Sun mance dani... Yunwa kaman zai karni sai gashi Allah ya kawoka, Ubangiji ya saka da Alkhairi Rankshidade...!”
Yazeed ya katsesa da fad’in “Daina godiya tun yanzu kasan ance komai yanada lada...!” Yai maganar shu’umin murmushin nan nasa saman fuskarsa...
Ubandoma ya had’iyi miyau da k’yar yana k’walalo idanu yake duban Yazeed... Yazeed ya kuma gyara rigar kufta dake sanye jikinsa cikin yanayin salonsa da yafeyi idan yana shirya wani mugun abin... “Ubandoma na tabbata ka yarda dani tinda har na baka abinci ka ci without thinking twice... Ba tareda kayi wani tunani ba sabida yunwa dake azalzalanka ka amsa kaci...!” Ya d’anyi fasali yana mai rage girman idanunsa yake furta “Baka tunanin zan iya sanadin rayuwarka yanzu a wajen nan...?!”
Gumi ne ya shiga karyowa Ubandoma, ya shiga zaro idanu waje jikinsa na rawa yake furta “Kamin rai Allah shi baka yawan rai... Wayyo na shiga uku ni jikan Tandu inada yara kada ka maidasu marayu Allah shi baka yawan rai...!” Ya k’arashe yana hawaye had’ida had’e hannayensu biyu waje guda alamun rok’o...
Murmusawa kad’an Yazeed yai da gefen bakinsa kana yace “Kar ka damu ni ba mugu har haka bane... Abu guda yanzu nakeso kamin shine ka biya ladan abinda na maka yau...!”
Ubandoma ya zaro idanu yana fad’in “Mai kenan Rankaidad’e...?”
Yazeed ya kuma murmusawa kad’an yace “Da kyau Ubandoma, kai d’in kanada saurin fahimta... Nasan ba Yayana Mahmood bane ya baka umarnin shiga gidan Wambai... Kuma ban damu nasan ko wanene ya kake ma aiki ba, iyakacin abinda na sani shine kaid’in munafukin Mahmood ne... Toh inaso kai amfani da wannan shara taka ta iya makirci da munafunci ka d’aura alhakin dik abinda kai akan Mahmood... Ka sanar da Masarautar nan cewa Mahmood shine bak’on Buzu kuma ya turaka ne domin ka kashe Wambai... Ka fahimta...?”
Da tsananin mamaki Ubandoma ke dubansa. Lokaci guda ya shiga girgiza kai yana duban Yazeed d’in yake fad’in “Ta yaya zan soma k’age irin wannan Rankaidad’e... Da dai ka nemi wani abin amma banda wannan...!”
Huci kurum Yazeed yake yana dubansa rai b’ace... Lokaci guda ya shak’o wuyan Ubandoma yana fad’in “Kai k’ask’antaccen Bawa, kai kayi kad’an Yarima Yazeed ya nemi wata alfarma wajenka... Umarni kawai zan baka kabi .... Ka fahimta...?!!!” Ya k’arashe yana mai jifada Ubandoma gefe wanda tuni ya zube yana haki had’ida sosa wuyarsa dake masa zogi, sai tarin azaba yake...
Yazeed ya d’an yarfe hannunsa kad’an had’ida gyara zaman zobensa da ya kusa ficewa kana
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 65