Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dai ba ruwana ai baka jin tausayina shine har kake cewa next year in sake haihuwa kama san wahalar dana sha kuwa kafin na haifi Annur?" Yace " ina tausayin ki mana kinfi son sai na fa'da da baki ne?" Sai tace " ai cewa kayi wai in 'kara haifan baby" "Ehh mana zaki haifa min Doctor mana daga ita shikenan sauran kuma ganin damar kine?" Teemah kam kafa'da ta no'ke tace " Ni dai ah ah baga Annur nan ba?" Abbas amsa ya bata da fa'din " shi ai zai gaje ni ne, burina uku ne kacal a duniya a yanzu nasamu biyu, kinga na farko na sameki wannan ya wuce, sauran kuma shine inga na samu yara na sun kuma cika min burina na zama doctor da kuma airforce ko bana raye ki cika min wannan Burin kinji.....insha Allahu Annur 'dina Major Mahmud Muhammad Al-hassan ne kinga insha Allahu in da raina Burina na biyu zai cika da yardar Allah is just d matter of time, kinga saura na ukun sai ki sake haifamin wata babyn wanda ko su biyu ka'dai Allah ya bani bazan yi takaici ba zan gode masa dan sune cikar BURINAH, idan ma suka fi hakan duk ina so bazan 'kiba sai dai fatan Allah ya bamu masu albarka" Teemah a ranta ta amsa da Ameen a zahiri kuwa kawai sai tayi shiru. Yace " kinyi shiru baki ce komai ba me yafaru?" A hankali tace " ba komai" Murmushi yayi tare da fa'din " matsoraciya an gaya miki ana surrender ne addu'ah akeyi sai kiga Allah ya kawo da sau'ki ko har kin daina son yaran ?" Teemah cewa tayi "Ah ah baga Annur ba ai shima ya isa " Sai yace " ni bai ishe ni ba to" "Allah ya kawo masu albarka to" ta fa'da da 'kosawa. Abbas kuwa cikin farin ciki ya ce " yauwa 'yan mata na abinda ya kamata ki fa'da tun 'dazu kenan ai" Da haka bacci ya 'dauke su kanta akan dantsen hannun sa tayi pillow dashi. ***** *Wai ina labarin Munnira ne?* Munnira na can yanzu rayuwa tai mata ba da'di domin bata samun ku'di kamar baya, hatta kasuwancin da mahaifiyar ta ke yi ma sai da ya ja baya saboda 'karancin ku'di, ita kam Munnira hakan bai wani dame ta sosai ba, babban abinda ya dame ta a yanzun shine neman gafarar mahalicci bisa ga abubuwan data aikata a baya, tun daga yawace-yawacen bin maza, zuwa wurin boka rashin cika ibadar ta ga kuma hakkin bayin Allahn data 'dauka wanda duk da da kunnan taji Mahmud yace ya yafe ta amma sai ta kasa sakin ranta gani take yi kamar alhakin bazai ta6a barin ta ba. Bata da abin yi a yanzun daya wuci ibada da istighfari tare da ro'kon ubangiji neman samun kyakkyawar 'karshe, bata damu da komai na duniya ba a yanzun, tuntuni ma ta yanke cewar zata koma sokkoto gidan kakannin ta gaba 'daya da zama ko dan ta samu islamiya mai kyau ma ta shiga ta nemi ilimin addinta. Allah cikin ikon sa kuma kafin tafiyar sai Allah ya ha'da ta da wani bahaushen ba kano, babban mutun ne domin matan sa har guda biyu da yara kusan bakwai, kasuwanci ya kawo shi garin ikko da nufin ubangiji kuma sai ya ha'da su inda ba'a wani 'dau lokaci ba aka saka ranar auren su wanda a kayi kafin bikin su Hannah aka kaita kano cikin matan sa, da da'di ba da'di haka dai rayuwar tayi ta gungurawa. Kishiyar Anty ma ta haihu inda Allah ya nufi Abbah da samun kyautar 'yan biyu mace da namiji tsaban murna Abbah har sai da yayi hawaye haka duk wanda yaji ma farin ciki sosai yake tayashi. Ranar suna yara suka ci sunan Mahmud da Khadija (takwaran Mummy. inda Abbah ya hana acanza wa namijin suna yace a 'kirashi da Mahmud 'dinsa macen ce dai ne ake 'kiran ta da Nanah. *Naso na kammala a page 'daya amma hakan bai samu dan haka ayi min ha'kuri plz.....insha Allahu next page zamu kammala labarin da iznin ubangiji wata 'kila ma zuwa gobe kuji ni.* _Comment_ _Vote_ _Share_ *Salmerh ce* ๐Ÿ˜ [10/13, 12:50 PM] ๐ŸŒธSalmerh๐ŸŒธ: ๐Ÿ’• *CAPTAIN ABBAS* ๐Ÿ’• By *Salmerh MD* Luv story๐Ÿ˜ *Wattpad @* *Serlmerh-md* ๐Ÿ’ซ *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS* ๐Ÿ’ซ We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all..... *DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO* _Wannan shafin naku ne masoyan_ *_cApTaIn_ _AbbAs* _wanda na sani da wa'danda bansani ba, a duk inda kuke *SALMERH*_ _na jinjina muku_ .๐Ÿ˜ ~*LAST PAGE*~๐Ÿ’ฏ *Bismillahir* *Rahmanir Raheem* _U ll never find luv if what u ar seeking is perfection.....cuz d best qualities we have ar d ones we never see.....d worst qualities we have ar d ones we always see_ . ๐Ÿ…ฟ *94* Sati 'daya da komawar su suka nufi Dubai inda suka yiwa Mummy diran mikiya, bazata kawai ta gansu da mamaki dan batayi zaton haka ba. Yanayin yanda ta saki baki da ganin sun yasa suka kwashe da dariya Teemah har da ri'ke ciki taje ta rungume ta gudu tana fa'din " mu 'din ne de Mummy ba mafarki kike yi ba". Murmushi Mummy tayi tace " kun shammace ni ne ai shiyasa" Daddy kam daya gansu kar6an lil Mahmud yayi a hannun Mummy yana fa'din " Masha Allah yaro har yayi wayo yace da Mummy ta bashi abokinsa su gaisa yasan cewa yana da babban aboki. Kusa da Abbas yaje ya zauna da babyn a hannun sa ya kamo kunnan Abbas yana ja tare da fa'din wai dan yayi familyn kansa shine ya manta da shi ko a wayar ma bai fiya 'kiran sa ba sai sa'in da yaga dama....." yana yin yanda Abbas ke neman agajine ya saka Teemah murmushi Daddy kuwa ya'ki sakin shi sai ji sukayi yace " Daddy Annur fa na kallo kuma zai min dariya". Sakin kunnan nashi Daddy yayi suka 'dan dara gaba 'daya, sai Daddy ya 'daga Annur sama yana 'dan jujjuya shi yana murmushi, shima Annur idanun sa na kan Daddyn kamar wanda yana gane kamar sa ne, Daddy albarka ya ta sanyawa yaron tare da yiwa mai sunan sa addu'ah kana yace daga yau ya samu aboki tunda Abbas ya 'kisa. Su Teemah kam na ganin Mummy ai sai shagwa6a ta dawo sabuwa fil, kacokam 'dawainiyar Annur ta tattara ta barwa Mummy, ita kam sai dai zuwa yawo da Abbas suje can suje nan har mantawa take yi da tana da yaro ma a gida, kwanaki ka'dan ne kawai suka fita dashi da yake ma bashi da rigima sosai indai a 'koshe yake baya kuka shiyasa ma take barin sa hankalin ta a kwance. Satin su biyu a Dubai sai suka dawo inda suka sau'ka a Lagos gidan Anty ya barsu shi kam ya tafi hotel, duk da Abbah ya nuna rashin jin da'din sa akan hakan amma Abbas bai ce da shi komai ba dan shi haka kawai yake jin nauyin Abbah fiye da yanda yake jin na Daddy ma, har gani yake tamkar Abbah shine Father in-law 'din nasa ma, Anty ce de har yanzun ya kasa sabawa da ita da ma halayyar ta, kallon ta yake yi a komai yana ganin tamkar gaskiyar ta ka'dan ce a kullum. Sun ziyarci gidan Umar ma inda iyalan sa suka yi matu'kar farin ciki da hakan tarba mai kyau suka samu daga wurin Maman Amal inda suka rin'ka yabon kyan Baby Annur da yaran ta, har ji suke tamkar Fateemahn kar ta tafi. Abakin Anty suke jin labarin irin muguwar cutar infection 'din da ya ci 'karfin Anty chiddy ya ri'ke harda 'kafafun ta hatta tafiya ma bata iyawa a yanzun, mijin ta ma wai ya koreta daga gidan sa saboda asirin da ta tayi masa duk sun samu matsala hankalin sa ya dawo jikin sa kamar kowa, basu ma san inda take ba a halin yanzun. Teemah kam yanzu ko sunan matar ma bata 'kaunar tunawa gode wa Allah kawai take yi da bai bawa Anty Chiddy nasara akan ta ba ta cimma burin ta, tasan ba dan ikon Allah ba da yanzu itama ta zama wani abu daban " Alhamdulillah" kawai take ta nanatawa tare da tuno rayuwar ta na baya, sai hawaye ya gangaro mata, fakan idanun su Anty tayi ta goge shi Abbas ne ka'dai ya lura da ita amma bai hana ta ba kawai ya 'kura mata idanu.(Allah ubangiji kayi katanga da sharrin shai'dan kasa mufi 'karfin zu'katan mu AMEEEN). Har gidan amaryar Abbah suka je inda taga 'yan biyun Abbah gwanin sha'awa sosai suka birgeta, ga Nanah name sake d'in Mummyn ta itama kyakkyawa da ita. Photo ta ringa 'daukan su a wayar ta gwanin birgewa, sosai twins 'din suka shiga ranta sai taji tana sin su amma da ta tuna wahalar da ake sha kafin a haihu sai kawai ta basar ji take badan haka ba da babu abinda zai hana ta ta ringa ro'kon ubangiji ya bata itama. Amma wahalar da ta sha kafin ta haifi Annur yasa take jin shika'dai ma ya isheta rayuwa. Kwanan su uku a Lagos suka koma gida bayan Abbah yayi musu kyauta ta musamman wanda da 'kyar Teemah ta kar6a da yake ku'dine cash ya bata sai taji nauyin kar6a har sai da Anty ta sa baki kafin ta kar6a, suna isa gida kuwa ta ha'da Abbas da su. Bayan komawar su ne Teemah ta bawa Hannah labarin abinda ya sami Anty chiddy, Hannah ita kam " Allah shi 'kara" tace cuz ta tsani matar dama sosai tun asali. Daga baya sai suka hau hirar Dubai inda Hannah ke jin haushin rashin zuwan da bata yi ba da yake tun bayan bikin Teemah da Mummy zata koma Hannah ta so binta amma makaranta ya hana ta amma still burin hakan na nan acikin ranta. Hannah bata koma ba sai da yamma bayan sun gama hirar ta su kafin Hannah ta koma gida cike da tsarabobi. A kullum Teemah nazarin kalar rayuwar yanzu take yi musamman lokacin da sukayi waya da Anty ta sanar da ita cewa ashe Anty Chiddy Momcyn ta ma koran ta tayi saboda dama tana kawo ku'di ne shiyasa ta ke jan ta ajiki yanzu kuwa da baubu ku'din sai cuta sai taga cewa ai tatsanta kawai zatayi daga cikin 'dan abinda take dashi tunda ita yanzun bata da wani amfani, dan haka sai ta korata ta'ki zama da ita, koda tabar gidan kuwa cikin rashin sa'a da wani dare 'yan iskan gari suka zo 'dan inda suke fakewa da wasu 'kawayen ta da basu guje ta ba anan suka yi raping 'din su inda suka yi musu kaca-kaca sa'annan suka cire mata mama duka biyu da ranta da komai azaban hakan ne ya kashe ta inda aka tshinci gawansu su biyu a wula'kance. (Rayuwar dama kenan, shuka alkhairi ne ka girbi khairi sa6anin haka kuwa kaima kasan makomarka, dama duk wani mutun a duniya sarai yasan abinda yake aikata wa, wallahi kowa yasani inma sharri kake yi kasani haka ma khairi, sai dai idan shai'dan yayi galaba akan kane shine sai kaga ka kasa fuskantar gaskiyan balle har ka bita). ALLAH UBANGIJI KA SHIRYAR DAMU BISA HANYA MADAIDAICIYA KASA 'KARSHEN MU YAYI KYAU AMEEEN. Labarin mutuwar Anty Chiddy sosai ya ta6a zuciyar Teemah sai yanzun take jin tausayinta amma kuma hakan baida amfani saboda a kurarren lokaci ne, kuma gashi bata kasance cikin musulunci ba balle tayi al'kawarin tunawa da ita cikin addu'ar ta. Abbas kam data sanar dashi shiru yayi ba furta komai akai ba sai ma ya fara 'ko'karin mantar da ita damuwar data ke ciki da salon sa. Teemah na kula da Annur 'din ta kamar yadda kowacce uwa kake yi dan a kullum ta kalle ahi jin kanta takeyi tamkar wata babba ga wani son Annur 'din dake ratsa ta kullum ta dube ahi, har bata so taji muryar shi yana kuka, idan ka ga yanda take lalla6a abinta har zakayi mamakin ta, har ayanUn ta kuwa idan Annur ya rikice da kuka ta kasa rarrashin sa itama kukan take sanyawa cuz idan yafar irin kukan baya sauraren komai ko me zata bashi ba shiru yake yi ba. Akwai ranar da Abbas ya same ta a irin halin sosai sai ta bashi dariya amma bai kulata ba sai ya 'dauki Annur daga cinyar ta yayi ya lalla6ashi har ya tsagaita kukan, kafin ya dawo da kallon sa gareta a lokacin Annur na kwance akan ruwan cikin sa yana sau'ke numfashin kukan da yayi. Suna ha'da idanu sa ita sai ya saki murmushi yace " wai dama haka kuke yini kuka idan bana nan?" Share hawayen tayi da hannun tana 'kif'kif da idanu tace " Shine ai baya jin magana kullun sai ya ringa kuka" ta fa'da cikin shagwa6a66iyar muryar ta, abin sosai ya bawa Abbas dariya sai yace da ita " har kin daina son shi dan yana kuka ko?" Da sauri ta jijjiga kanta alamar ah ah, sai ta 'kara da fa'din " ai idan yayi shiru shikenan" Murmushi yayi mata kawai ya ya kai hannun sa bayan ta sai ta taho itama ta kwantar da kanta a jikin sa Abbas sai ya cusa hannun sa cikin gashin kanta. A hankali yace da ita " idan kina kuka haka ai shima bazai daina ba, ko kina son ya raina ki yace kema kina kuka irin nashi?" Jijjiga kai taui sai yace " toh kar kina yi masa kuka idan yana shi sai ki rarra she shi kawai har yayai shiru kinji?" Yayah ai shi'din ne ba yaji idan ya fara kuka" Sai ya tareta da fa'din "...karki damu zane shi zanyi ai ince ya daina yiwa 'yan matana kuka" Murmushi yai kawai dan ta fahimci da gangan kawai yake yi mata in ba haka ba miye abin duka ajikin Annur. Kwanaki sun 'dan ja har lokacin bikin su Hannah yayi inda ranar wata juma'ah aka 'daura auren Hannah da Bilal bayan sallar juma'ah haka ma Leesah wacce aka kaita gidan mijin ta dake Kaduna. Hannah kama tana nan cikin gari aka bar ta a wuse 2 dan Bilal bada ita zai tafi ba saboda makarantar ta sai aka barta a Abuja kafin ta kammala gaba 'daya. Ana kammala bikin su Hannah Abbas ya tattara iyalan sa suka koma Rivers, dayake dama hutun kwanaki ya kar6a kuma ya koma shi ka'dai ya bar su su 'dan kwana biyu ma ya'ki amincewa. Hatta Ummah tasa baki amma ya'ki yadda Ummah kam sai cewa tayi " fitinanne kawai ni dai Allah yasa kar yaron nan ya biyo wannan halin naka da ba'a gane kanka sam". Duk kissa da marairaita tayi dan ya barta amma ya'ki dole badan taso ba ta tattar suka koma a taren. Zuwa yanzun Annur yayi wayo sosai har yana gane mamar sa dan watan sa shida da haihuwa yayi 6ul-6ul abinsa, yayin da yana girma kamar sa da Abbas na sake bayyana ajikinsa da fuskar sa ma gaba d'aya. Watarana da dare lokacin tana yi masa shirin bacci diaper take sanya masa yana ta irin surutan su na yaran nan da hannunsa abaki, Abbas ma na gaban mirror fitowan sa kenan daga bathroom yana tsane jikinsa da towel a hannun sa Teemah sai tace " nifa Yayah bangane wannan abin ba, yaron nan na lura ko kalar farce na bai 'dauko ba kawai ya biyo ka gaba 'daya dube shi dan Allah da wani idanu ko ina zai kaisu oho" Abbas na jin abinda ta fa'da 'din sai ya taho a hankali zuwa inda suke 'din yana murmushi yace " kina ba'kin ciki ne dan yaro na ya biyoni? so yake ya gaji babansa shiyasa amma ai wannan 'kananun surutun da yake yi kam ba nawa bane sai de in ke kike koya masa irin nakin nan..., ni kuwa bana son ya 'dauko irin surutun kin da 'kin makaranta kinnan..... in kika kuskura kika koya masa kuwa nida kene" Teemah murmushi tayi kanta na 'kasa tana cigaba da shirya Annur tace " ai ba haramun bane dan nace bazan yi makaranta ba" Juyawa yayi yana komawa gaban mirron yace " ke de fa'di gaskiya 'yan mata" Itama sai tace " gaskiyar kenan ai" Murmushi yayi mai sauti bayan ya isa gaban madubin yace " kinsan me yasa ya yi kama da ni?" Waigowa tayi tace "ah ah " tare da juya kanta ta kalle shi. Cigaba yayi da fa'din saboda jarumtar da na nuna ne gurin 'daukan cikin sa kema in kina son mai kama da ke sai kiyi 'ko'kari ki nuna taki kalar jarumtar" Bata ma san lokacin da ta banka masa harara ba tana murmushi. Sai yace " ni kike yiwa haka ko, zaki ha'du dani ne yarinya zaki gane da waye kika yi" Ya 'karashe maganar yana 'dan dariya. ***** *Bayan shekara 'daya* Abubuwa da dama sun faru ciki kuwa har da haihuwar Anty Leesah inda ta haifi baby girl 'din ta mai suna Aisha amma suna 'kiran ta da Nihal, Hannah kuwa yanzu ne ma take da cikin da bai fi 2-3month ba ga uban wahalar laulayi da take sha duk ta fita hayyacin ta gaba d'aya, har mamaki takeyi irin cikin Teemah yanda har cikin ya zama mutun ajikin ta ba tare da sun san da shi ba, ita kuwa tun baa je ko'ina ba ma ya bayyan kansa, cuz tun yana 1month ya fara wujijjiga ta da su amai ga za6an abinci kamar masifa, Teemah kanta tausayin ta takeji yanzun. Domin taso rana tsokanan ta amma yanda yanayin Hannah ake sai ta ma manta da waccen batun tausayin ta duk ya cika ta. Munnira kuwa babu labarin ciki agareta dan ta ziyarci asibitoci kusan uku ma amma duk ce mata suke yi mahaifarta ta riga ta lalace ikon Allah ne ka'dai zai sa ta haihu ko da gaba ne. Munnira tayi kuka sosai da jin sakamakon ta amma daga 'karshe sai ta ha'kura ta fawwalawa Allah komai dan tasan shine ka'dai mai bayarwa da hanawa in da rabon ta samu ko min daran da'de wa wataran zata haihu. Anty ma kullum mutuwar Mahmud sabo yake dawo mata musamman idan taga yanda Abbah ke nan-nan da twins 'din sa gashi kullum cikin farin ciki zaka ganshi saboda bashi da damuwar komai, koda kuwa ranar da yake gidan ta ne Abbah dole sai yayi waya da yaransa duk da dama ba maganar suka iya sosai ba amma a hakan wai shi muryar yaran sa yake son yaji, cikin dokar kwanan su ma sai da ya ro'ki Anty akan ta yi ha'kuri koda lokutan girkin tane yana so yana zuwa dubo yaran sa dan bazai iya har kwana biyu kuma suna gari 'daya amma bai gansu ba tare da 'daukan mata al'kawarin babu cin amanar ta koka'dan da zaiyi bayaga ganin gudan jininsa. Dolen Anty ta amince batare da ta nuna masa damuwar komai ba a fili, duk da bata ba'kin ciki da yaran nasa amma ita ka'dai ta san yanda take ji idan taga Abbah na zumu'di akan 'yan biyun yaran sosai ta ke 'kara neman gafarar mahalicci akan banzatar da rayuwar nata 'dan da tayi sanadin haka ma yasa kullum sai Mahmud ya samu kyakkyawar addu'ah daga wurin ta bata ta6a shagala da hakan ba. Gashi itama Allah sai ya jarabce ta da masifar son twins 'din, ji take kamar ta 'kwato su a wurin ta, amma babu dama lura da hakan da Anty Sadiya tayi yasa ta yanke aranta cewa idan ta yaye su zata bata little Mahmud kyauta ya zama 'dan gidan ta in yaso ita sai ta ri'ke Nanah in Allah yasake bata wani kuma sai ta hada ta ri'ke su, kuma tana da ya'kinin Abbah ma bazai 'ki amincewa ba, inyaso sai suyi yarjejeniya koda a rubuce ne akan bazata ta6a goran ta mata ko kuma kar6an sa ko da kuwa menene zai faru yariga ya zama 'dan ta, ta dan itama Anty Sadiyan tausayin Anty take ji sosai. Tana yaye su kuwa ta sanar da Abbah ku'durin ta sai dai Abbah ya so ya nuna 'kin amincewar sa sai da ta ta fahimtar dashi kafin nan ya yarda, amma ba wai har ransa ba dan shi yaso yaransa su taso a tare kamar yanda aka haife su kuma a hannun mahaifiyar su saboda ya yaba da hankali tarbiya da nutsuwar ta k'warai da gaske shiyasa bashi da haufi akan tarbiyar da zata bawa yaransa. Da Anty ta sami labarin hakan kuwa har sai da tayi kuka dan farin ciki, tun da aka yaye su aka kawo mata shi sai ta sa aka nemo mata mai kula dashi tun daga kano tazo tana tayata rainon sa da kukawa dashi Anty kam sosai taji da'din wannan karamcin kawai sai take ta godewa mahalicci bisa ga chance 'din daya sake bata akaro ba biyu matsayin mahaifiya wannan karon kam tana jin rayuwar 'danta zai kasance ne kishiyar rayuwar da ta bawa Marigayi bazata sake yin haukan da tayi a wancan lokacin ba zata ja 'dan ta ajiki ta bashi tarbiyar data dace ta kuma cika rayuwar sa da farin ciki har sai yaji cewa yafi kowa sa'an mahaifiya. Wannan abin da amaryar Abbah tayi ba 'karamin daraja ya 'kara mata a idanun Anty ba, sai take jinta tamkar 'yar uwarta ta jini domin tayi abinda ba kowa ne zai iya ba a wannan zamanin da kishi ya zame wa mata tamkar ibada a zu'katan su. ***** Teemah ma tuni ta yaye Annur 'din ta tun yana da 15months da haihuwa ganin yanda yake girma, tsayi da wayo duk lokaci guda, yana da 7 month yafara takawa, da kansa ma sai bai damu da yasha maman ba, dan wataran a yini bai fi sau biyu yake sha ba kuma ko bata bashi ba baya rikici, ganin hakan yasa Abbas yace da ita kawai ta daina bashi ma gaba 'daya ita kama ai dama gaba ta kaita dama bata son ta jima da shi abakin mama har ranta take jin tsoron kar su lalace ganin cewa Abbas nan yafi so a ilahirin jikinta shiyasa take nan nan da shi itama. Ginin makarantar ta da Abbas yace za'a yi mata ma an kammala shi tuntuni amma a Abuja aka yi, wanda makarntar ta tsaru iya tsaruwa, sosai Abbas ya kashe maku'dan ku'da'de dan ganin makarantar ta ginu bisa tsari da daraja har an luncher shi, inda ake bayar da karatu arabi da boko daga 8am to 5pm ha'de da babban masallaci aciki 6angaren mata da maza, inda suke ajiye fannin boko 'karfe 'daya bayan sun yi sallah sun 'dan huta kuma 2:30 sai su siha fannin islamiya sosai ake horara da yara kan dukkan 6angarorin biyu. Abbas ne ya sanyawa makarantar suna A-Z international School, kuma ba laifi makarantar ta samu kar6uwa sosai musamman da yake suna da fannoni da dama tun daga 6angaren Nursery, primary har secondary duk aciki. Haka kuma Abbas bai manta da su Innah ba, bai sake komawa ba kam amma a duk 'karshen wata yake transfer 'din ku'di wa Rabi'u wanda yasan zai ishe su hidimar makaranta da kuma gida, kuma Rabi'u na 'ko'karin 'kiran sa akai-akai yana ha'da su da Innah ma su gaisa da ita. Yanayin yanda yake jin ta ka'dai ma ya ishe sa sanin cewa Rabi'u bai ci amanar su ba daga abinda yake tura masa. ***** Wata ranar Alhamis da 'karfe biyu na rana 2:09pm, Abbas ne ya shigo gidan jikin sa uniform kaki ne da hular sa da wayar sa duk ri'ke a hannu. A gajiye yake gaba 'daya dan haka sai ya zube a parlour kan kujera yana 'kwala 'kiran sunan ta. Teemah iska ta hura a bakin ta ta furzar da jin muryar tashi bata so ta amsa da 'karfi har baccin da Annur ya fara yanzun ya yanke gashi daga jin tashin muryar Abbas 'din har ya bu'de idanu dayake baccin ya 'dan fara cin idanunsa sai take ya kuma mai da wa ya rufe su tasan badan baccin ba da ko ita bata isa ta riga shi isa wurin Abbas 'din ba, dan wata muguwar sha'kuwa ce a tsakanin su, itan ma shiru tayi bata amsa ba dan kar ta tashe sa tun safe be yi bacci ba sai rigimar tsiya yau 'din yake ji dashi, hatta bathroom bai barta ta shiga ba sai da ya bita sukayi wankan tare, inda da dabara ta samu da tayi masa nasa sai ta ha'da shi da abin wasa cikin bathtub daya 'dauki hankalin sa sannan ta samu ta faki idanun sa

Chapter 65 of 67