agida kijirani_ "
Fateemah najin hakan tafara masa kuka dayake daman acike take da damuwa so kamar jira take yayi maganar kawai tafara masa kuka tana fa'din "wallahi ita bazata zauna ba.
Yayi -yayi ta sanar dashi matsalan amma ta'ki, sai kawai taci gaba da kukanta, haka Mahmud ya6ata tsawon lokaci yana bata baki da lallami akan ta ha'kura ta zauna agida amma ta'ki.
Daga 'karshe kawai ya ha'kura yasata agaba yace toh suje a lokacin ma har 8:01am tayi.
Haka suka kulle 'kofan suka nufi inda motarsa take.
Har yayiwa motar key sai ya tuna ashe ya baro jakansa aciki wanda ke 'dauke da dukkan muhimman abubuwansa na wajen aikin.
Fita yayi yakoma ya 'dauko jakar wanda ya barta anan kan cough inda ya zauna dan rarrashin Fateemah.
Gurin motar ya koma ya bu'de baya ya ajiye jakar duk da idanu kawai take binsa.
Be shiga motar ba taga yasake komawa cikin gidan can bayan mintina biyar sai gashi yafito da 'dan saurinsa yashiga yace " _kin wani ha'da min Tea me sa fitsari sai da na koma na yi kafin naji dama dama_ .
Kauda kai kawai tayi dan batasan me zata ce dashi ba damuwar ta ma ka'dai ya isheta.
Horn ya dannawa Gate man 'dinsu dake daga can baya yana duba flowers 'din gidan.
Da gudu yazo yafara 'ko'karin bu'de gidan, kafin ya 'karasa tura gate 'din ne sai Mahmud yasake ce mata " _inajin kamar nayi mantuwa aciki wallahi, kuma fah bakomai bane tsaban yanda kika_ _rikitani ne da rigimarki yasa nake ganin haka_ ."
Shiru tayi masa yanzun ma shima kuwa sai ya shareta yaja motar yayi gaba dai-dai inda gateman 'din yake ya tsaya kamar yanda suka saba kullum suka gaisa sai de yau Mahmud yaciro ku'di ya dan'ka masa ko jiran godiya be yiba yaja motar suka fita.
Sai da suka hau kan titi kafin ya 'dan kalleta yace
" _inajin nextweek fah zan koma katsinan nan, se ki shirya tafita bakince_ _zaki_ _rakani ba_ ?
" _Umm_ "
Tace a'kasan ma'koshi.
" _toh sai ki fara shiri domin da mota zamu_ "
'Dan sake fuska tayi ka'dan tace " _zamu har Abuja ko_ _Yayah_ "
" _Insha Allahu, ko ni banje ba ke zaki je_ "
ya bata amsa atakaice.
_Toh fah readers sai ku mammatso kusa domin jin yanda ha'duwar Mahmud, Munnira da kuma_ _Teemah_ _zai_ _kasance_ ........za'a kafta🤞🏻
~Taku akullum Salmerhmd.I heart u all masoyana.~ 🥰
_Comment, follow, Share and Vote@_ ~Serlmerh-md~
*Salmerh ce* 😍
[10/2, 6:03 PM] Ummiyo: 💕 *CAPTAIN ABBAS* 💕
By
*Salmerh MD*
Luv story😍
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
Dedicated 2my lovely fans da ke ~whattsapp~
~facebook~ &
~Wattpad~
Inayinku sosai nima,
Allahu ya bar 'kauna.
💫 *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
💫
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir rahmanir raheem*
_True friends are not the ones who are there when it’s convenient. True friends are there when it’s not._
🅿 *65*
Sa'kon gaggawa ne ya iso musu cewar kayan da za'a kawo musu a Lagos za'a sau'ke su so sai aka wakilta Abbas akan zuwa kar6o kayan, dama da farko maiduguri za'a taho da kayan direct sai kuma aka samu wani matsala inda dole sai de a sau'ke a Lagos sai suje su 'dauko.
Ko ka'dan Abbas be kwana da niyyan tafiya ba amma da asubar fari aka sanar dashi lokacin ma yana zaune dafe da kansa bayan farkawar da yayi daga bacci da mafarkin Fateemah sosai mafarkin ya tsaya masa aransa, wai tana ta kuka saboda tarasa hanyar zuwa ko'ina ne oho, duk inda tabi de sai taga gurin yah mata duhu gashi wai tana ganinsu agabanta sun kewaye ta, a wurin akwai Mahmud, yaga Hannah, Antyn Mahmud yaga Daddy ma da kuma wasu mutane kimanin biyar da be sansu ba, amma inda akwai hanyan 6angaren Mahmud ne, Antyn Mahmud, wata da be santa ba da kuma shi kanshi, so take ta wuce amma tarasa ta ina zatabi, cikin wa'yancan ukun duk inta bi 6angarensu duhu ke mamaye gabanta, dalilin haka sai ta sake sakin kuka tana yarfe hannu, shi ka'dai ne kawai 6angarensa be yi mata duhu ba, amma ko data biyoshi 'din sai hanyan yayi mata nisa sosai yanda zai yi mata wahalar cimmasa shi kansa ma nisan yayi mata tana hangoshi yayinda har hannunsa yake mi'ka mata dan ta kama amma bata iya kamawa, hakan sai yasa taci gaba da kuka tana fa'din " _Yah Abbas_ !
_Ya...... Abbas_ !!
Yana san taimaka mata shima amma sai ya kasa, Mahmud kuwa daganin tana bin inda Abbas 'din yake tana 'kiran sunan shi sai shi kuma ya juya bayansa yana murmushi, taku 'daya biyu zuwa uku yayi sai ya 6ace 6at suka daina hangoshi sai haske ya mamaye gurin gaba 'daya tare da wani lumshi me 'kayatarwa.
Dai dai 6acewar Mahmud 'dinne Abbas ya farka daga baccin yatashi ya zauna dafe da kansa yana sake bitan mafarkin dayayin tare da juya al'amarin acikin ransa, yarasa ma'anar mafarkin gaba 'daya, abu 'daya ya iya fahimta shine Fateemah na bu'katar taimako arayuwarta sai de be san dalilin da ze kawo hakan ba.
Yana cikin tunanin mafarkin ne sai ya samu sa'kon tafiya zuwa Lagos, wanda yazo masa a bazata a kuma dai dai lokacin da ze fi bu'katan hakan, haka ya tashi yayi komai cikin hanzari ya gama shirinsa tsaf.
Su shida suka tafi , jirgin 'karfe 6:30am na safiyar ranar juma'ah suka bar Maiduguri zuwa Lagos.
Sai dai kuma cikin rashin sa'a sai da suka isa Lagos suka sake tarar da sa'kon cewa sai zuwa yamma zasu iso dan haka sai suka nemi gurin da zasu huta kafin yamma amma sam basuji da'din hakan ba.
Da wannan damar Abbas yayi amfani ya nufi office 'din Mahmud wanda a'kage yake yaji ya Fateemah take agurin Mahmud 'din, dan shi gani yake kamar rashin son auren da Mahmud yace baya yi ne yasa shi ya kasa kula da ita, be san gidansa ba office 'dinsa yasani dan haka sai ya nufo office 'din, yana da tabbacin adai dai wannan lokacin Mahmud na office.
*****
Fateemah da Mahmud kuwa basu suka isa office 'din ba sai 9:13am
dayake ansamu ha'duwar holdup sosai ahanyar shiyasa ma suka 'dan 6ata lokaci kafin su isa.
Da isarsu office 'din ko zaman 20minutes be yi da ita ba, bayan isowarsun Mahmud ya amsa 'kira through landline 'din dake kan table 'dinsa, yana gama wayar kuwa ya mi'ke tare da sanar da Teemahn cewa yana zuwa bazai da'de ba zai dawo.
Tashi tayi da sauri tace zata rakashi itama, saboda sosai yau 'din take jin babu da'di aranta, fa'duwar gabanta kara yawaita yakeyi acikin kowani da'ki'ka.
Mahmud kuwa yadakar da ita da fa'din " _ah'ah please wait 4me mana Fateemah u ar safe here karki damu_ , yace mata files 'din da ze kai 'din masu matu'kar muhimmanci ne dole akwai wasu 'karin bayanin daya kamata shi zaiyi kafin aturasu zuwa China shiyasa zashi.
Duk tunanin Mahmud tsoron da takeji ne yasa har a office din ma takasa sakewa.
Haka ta tsaya 'ki'kam batare da tayi masa magana ba domin haka kawai yau 'din take jin wani sabon yanayi game da Yayah Mahmud 'din har bataso yayi nesa da ita.
Da fitarsa kuwa Fateemah ta 'daga hannu ta dafe goshinta, bata san dalili ba amma akowani sa'a takan tsinci kanta cikin tsananin fargaba, wanda tun da safiyar yau data' farka daga bacci ta tsinci kanta cikin wannan yanayin.
Bazata ce ga ainahin matsalarta ko damuwarta ba ayanzun ita de kawai tana ji har cikin zuciyarta ba ta da nutsuwa a hargitse take jin kanta gaba 'daya, dan haka kawai sai ta ringa maimaita _inna lillahi wa inna ilaihi raji'un, lahaula wala quwwata illah_ _billah_ acikin zuciyarta wanda yin hakan ne yake 'dan sama mata sukuni idan taji fargaban ya yawaita.
Da rigimarta sai ta wuce kan kujerar da ya ke zama a office 'din ta wani hakimce tana juyi ahankali tare da lumshe idanunta yayinda ta ringa faman sarrafa tunaninta ko zata gano babban damuwarta alokacin.
Mahmud be da'de da barin office 'din ba Teemah taji anturo 'kofar ahankali batare da annemi izinin mamallakin office 'din ba.
Dubanta takai wurin 'kofar sai ta ga wata matashiyar budurwa ce tsaye da fuskar mamaki wacce zata girme mata ahaife.
Sanye take da wata riga doguwa yellow rigar roba ce sosai kuma bawata me fa'di ba, hakan yasa rigar tabi duk jikinta ya kwanta, tare da bayyana duk wata halitta dake jikinta, kanta kuwa da wani jan mayafi ta zagaye shi, ba laifi kam ayanayin zubi da tsarinta tayi kyau sosai sai de atsarin musulunci sam bata da maki ko guda 'daya.
Kallon kallo suka tsaya yi da Teemah kowa da abinda yake sa'kawa acikin ransa, tunanin Teemah ko itama 'daya daga cikin ma'aikayar su Mahmud ne, tace wata'kila haka suka saba shigowa gurin Mahmud 'din batare da neman izini ba, sam Teemah bata san Munnira ba tunanin ta ta6a ganin ta wani guri ma sam be zo kanta ba, saboda ko lokacin dinnern auren sun akwai mutane da dama so bazata iya tunawa da kowa da ta gani awurin ba.
Yayinda Munnira aranta take jinjina kyaun da ta ga Teemahn ta 'karayi, duk da yake ta ganta alokacin hidiman bikinta kuma kwalliyar biki daban yake dana kullum amma duk da haka bata ga aibin Teemah ba koka 'dan sai ma wani fresh data 'karayi tayi kyau bayaga haka bata ga wani abu daban ba, take kuwa tsantsan kishin datake ji azuciyarta game da Teemah ya motsa, amma duk da haka sai da ta 'dan yi dariyar mugunta wanda ta 'dan cije ta maida shi murmushi yanda Teemah bazata fahimci manufarta ba.
Ahankali take takowa izuwa gaban Teemahn yayinda takalmin dake sanye a 'kafafunta yasamu daman bada sauti 'kwas.....'kwas me 'dan 'kara ka'dan saboda yanayinsa.
Teemah sam batada niyyan kulata ko yi mata magana ba duk da taga cewa ta tunkaro ne, ita tun ganinta nafarko ma yarinyar bata birge ta ba koka'dan ganin cewa girmanta be sa tasan muhimmancin yiwa mutun sallama ba sai de ta tsaya kallonta.
Komawa tayi ta jinginu da kyau da jikin kujerar ta kwantar da kanta tare da 'dora 'kafa 'daya kan 'daya harda lumshe idanu tana juyi da kujerar ahankali tamkar itace mamallakiyar office 'din, sai tayi kamar irin ba matsalarta ba ce zuwan Munniran.
Idanunta alumshen ta tsinkayo muryar Munniran akusa da ita tana fa'din
" _Amarya me da'din_ _tuwo!!!_
muryarta cike da murmushi tayi maganar.
Ahankali ta bu'de idanunta ta sau'ke su akan Munniran daga idanun kuwa bata motsa koda 'yan yatsun ta ba.
Kallon a ina kika sanni tayiwa Munniran tare da 'dan zaro idanu ka'dan ta juya su.
Murmushi Munniran tayi itama ta zuba wa Teemahn idanu,
Idon su cikin na juna Munnira ta'kara fa'din
" _soyayyan be 'kare agida ba kenan shine kuka kawo sauran a office ko mrs Mahmud_ ?
_Sai de kuma naga ai angon naki ba me amfani bane........ko de akwai wani sirrin ne bayan wannan?_
Teemah bata kulata ba saima mamakinta daya 'karu tambaya ta fara yiwa kanta shin wacece wannan haka sam Teemah ta tsani shishshigi.
Munnira tagama fahimtar Teemahn da abinda ke cikin ranta dan tasan dama Teemah da wuya tagane ta dan haka sai ta gyara zama tare da yin murmushi tace
" _kina mamakine amaryar mijina?Ki kwantar da hankalinki 'yan_ _mata kinsan fah Mahmud shine rayuwata kinga kuwa dole insan_ _abubuwa da dama game da rayuwarsa, saboda in 'karfafa soyayyata wanda nake tunanin shi_ _kansa ma 'kila be san da su ba, amma inke kina so ki sani zan iya sanar dake bawani_ _abu_ ! "
Ganin da tayi Teemahn bata tanka ta ba har yanzun illah idanu data ke binta dashi yasa tayi murmushi, murmushintan da aduk sanda tayi shi tana jin izzah ne aranta irin kamar tagama dasu 'dinnan.
Kamar an matsi bakinta ta furta.
" _kin san wani abu amarya_ ?
Bata jin cewar Teemahn ba taci gaba.
" _ni 'din nan da kike gani babbar_ _masoyiyar mijinki ne tun ranar farko dana ganshi naji wani mahaukacin_ ' _kaunarsa yakamani amma cikin rashin sa'a sai Mahmud_ _yayi watsi dani da_ _bu'ka'ata ta duk da kuwa yasan ina matsanancin son shi hakan be sa yayi min duban_ _masoyiya ba koda kuwa sau 'daya ne tak, nayi 'ko'karin ganin na fahimtar dashi 'dimbin_ ' _kaunar danake masa amma sam yakasa bani dama, ana cikin haka_ _sai maganar aurenku ya 6ullo daga bakin mahaifin sa, Anty ne tasanar da_ _Mamina komai, nayi 'ko'karin ganin na hana auren yiyuwa amma hakan ma befaru_ _ba, saboda ance auren Mahmud dake zanannen 'kaddara ce da dole sai ya faru,_ _Malamin mami na ne ya fa'di ne yafa'di haka, badan naso ba na ha'kura har aka 'daura_ _auren ki da Mahmud............ Fateemah kina ganin zan iya ha'kura naga_ _rayuwar farin ciki_ _na wanzuwa atsakaninku ne dukda tarin ba'kin cikin da Mahmud ya 'kunsa min_ ?
Kai ta jijjiga tace
" _sam bazan iya ba, bazan iya juran ganin wannan ranar_ _ba............._
_"Inajin kamar inasonki ne shiyasa nake gaya miki wannan...."_
Dai dai nan Teemah ta hango Mahmud tsaye abakin 'kofar office 'din ganinsa kawai tayi bata san tun yaushe yake wurin ba, dayake Munnira data shigo
ganin Fateemah yasa bata tura 'kofar da kyau ba hakan ne kuwa yabawa Mahmud damar gani da jin kalamanta da kyau ba batare da wani tangar'da ba.
Teemah ce ke saitin 'kofa dan haka ita ka'dai ce ta hango shi sai yayi mata ido akan ta 'dauke kanta akansa ta daina kallonsa hakan kuwa tayi sai ta meda hankalinta da idanunta wajen Munniran dan kalaman data gama furtawa yanzun yasa ta ji tausayinta sosai harta fara jin cewa dama Yah Mahmud be mata haka ba tunda tana tsananin son shi daya daure ya aure ta, Munnira bata san da zuwan Mahmud ba, dan haka sai taci gaba da maganarta kanta tsaye, Teemah kuwa taci gaba da sauraro bata 'kara kallon 'kofar ba koda asace.
" _Tun kafin auren ku nake ta neman hanyar da zan hana auren ku ya'duwa tunda hana yiyuwar_ _auren ya gagareni, nasha fama sosai da 'kyar nasamu hanya_ _wacce itace ta 'dan sanyaya min zuciya har tasa na rage damuwata domin na yadda da aikin_ _danayi_ "
Ido 'daya takashe wa Teemahn tana murmushi taci gaba da fa'din,
" _ba sai na tuna miki ba nasan kinsani tunda ke ke fama da matsalar......._
Cikin izgili tace " _ya kike yine idan jarabar ki ta tashi cikin dare? ai an gaya min cewa da dare ne kawai kike da damuwa da rana kina rayuwarki ne kamar kowa_ "
Dariya ta yi ita ka'danta sannan taci gaba da fa'din
" _ranar dinnern aurenku da nasa Anty ta shirya shi nasamu nasaran_ _aiwatar da niyyata akanki... zaki iya tunawa dani kuwa_ ?
Goshi Teeemah ta ha'da tare da kawar da kanta gefe alamar ita ta manta.
" _Ai nasan bazaki iya tunawa ba, yanzun ma inajin fah kamar inasonki ne shiyasa na_ _ke fa'da miki wannan maganar dan kinsan sirri ne_ _babba awajena fiye ma sirrin dake_ _tsakaninki da Mahmud.Kuma kinsan wani_ _abin birgewa aciki mother in-law 'din ki ce take 'kara min_ ' _kwarin gwiwa akan komai wanda har hakan yasa tayi kyautar ki gaba daya wa 'kawarta_ _musamman saboda farin cikina.........._
Sau'kar mari kawai Munnira taji akan kuncinta wanda yakusan gigita ta kafin ta gama fahimtar ta inda marin yazo sai ta sake jin wani marin, sai da ya mata mari lafiyayyu guda hu'du wanda yasa har takai 'kasa ta zube tana kuka tare da dafe kuncin nata da hannayen ta duka biyu.
Kalle- kalle yafara yana neman abin duka kasancewar ba belt ajikinsa jumpa ya saka shiyasa shi neman abin, haka ya gama kalle-kallen sa be ga komai ba.
Tunawa yayi da wani toshon cable 'din daya daina amfani dashi da sauri ya tashi ya bu'de drawern yajanyo wayar ya fara nanna'de ta ransa amatu'kar 6ace kana ganinsa zaka san an ta6o shi yau 'din dan Mahmud ba haka yake ba.
Teemah ce taje dagudu ta ri'ke masa hannu dan ita tuni ma harta fara kuka saboda bata ta6a ganin tsantsan 6acin rai azahiri na Mahmud 'din ba irin yau .
" _Yayah please karka daketa kaji! dan Allah.... Yayah kayi ha'kuri._ "
ta yi maganar da muryar kuka.
Mahmud kuwa ko kulata ma be yi ba dan shi ka'dai yasan abinda yakeji azuciyarsa game da kalaman Munniran be ta6a tunanin haukarta har ya ha'da da cin zarafi da shiga hakkin wani ba.
Yana isa inda take ya sau'ke mata cable 'din abayanta, yayi niyyan yamata dukan tsiya ne na fitan hankali yanda gaba ko ganinsa tayi ahanya bazata tunkari gabansa ba ballantana hartayi tunanin cutar dashi.
Amma yana 'daga cable 'din akaro na biyu Fateema tazo dagudu ta ru'kunkume shi ta baya tana kukan itama, idan baka sani ba zakayi zaton ko dukkan su biyu yake duka.
" _Yayah........please kabari, karka daketa dan Allah Yayah kayi_ _ha'kuri.........kaifa musulmi kar kabiye sharrin zuciya_ _Yayah please kabarta ka yafe mata kaji....._
Cikin sanyin jiki ya sau'kar da hannunsa daga barin dukan nata.
Munnira kuwa gaba 'daya tabi ta rikice dana sanin zuwan ta office 'dinsa ma takeyi ayanzun, domin tunda take arayuwarta, ba'a ta6a marinta bama balle har takai ga duka da cable.
Kuka takeyi kamar ranta zai fita tana so ta fice a office 'din amma babu dama dan Mahmud sai da yarufe da lock kafin ya 'karaso ciki.
Dawo da Fateemahn yayi ta gabansa yana bubbuga bayanta alamar rarrashi yace " _yi shiru ya isa haka Fateenah, bakya ganin cutar da rayuwarmu datayi_ _ne, Fateemah wannan da kike gani babbar shai'daniya ce_ _ki bari in koya mata_ _hankali_ "
Kai Teemah ta jijjiga masa alamar " _ah ' ah_ "
Sai yace
" _okay......on one condition, zan barta amma sai ta fa'damin komai_ _data sani game da munafurcin da suka 'kulla gaba 'daya in_ _bahaka ba wallahi ba zan 'kyaleta ba_ "
Munnira kam tun kafin ya rufe bakinsa cikin sheshshka tace
" _wallahi Mahmud zan gaya maka gaba 'daya nayi al'kawari_ "
Idon su gaba 'daya suka maida shi kanta inda taci gaba da basu labari gaba 'daya.
Asirin datayiwa Teemah dashi kanshi Mahmud 'din sai da ta fa'da tace " _manufar hakan kuma shine wanzar da fitina da rashin aminta da junansu wanda_ _hakan ne zai iya yin sanadin rabuwarsu cikin sau'ki_ .Tace kuma Anty ma tasan da maganar dan ita ta'kara goya mata baya kuma itace ta ke jagorantar 'kawarta Anty Chiddy domin samun kan Fateema wanda hakan ma wani shirin ne daban a6oye.
Kasa jurewa Mahmud yayi saida ya zauna tsaban haushi da takaici.
Zaman ma sai ya gagare shi yasake mi'kewa.
Yana huci yace
" _Ai kuwa kinyi kuskure, Munnira munafurcin ki beyi tasiri ba koka'dan, domin Fateema bata_ _san ma tana da wannan_ _matsalarba balle har ta 'daga min hankali akai, har yaushe......Munnira_ _har yaushe zaki tsaya 6ata lokacinki akan yarinya_ ' _karama irin wannan, ko angaya miki ma ko na rabu da Fateema zan aureki ne?, wallahi_ _ko babu mata aduniya Munnira bazan ta6a auranki ba........._
_Kuma aurena da kike gani ni da Fateema auren zobe ne in bakisani ba ma yau ki sani, Allah_ _ne ya ha'da kuma shika'dai zai iya rabashi ba de ke ba kam Munnira_ ".
Yana kaiwa nan yayi Wulli da wayar ya ja hannunta zuwa gabansa wanda hakan ya tilasta mata tashi tsaye tare da fasa wani 'kara, zaton ta ko wani dukan ze kuma mata.
Teemah ma da sauri tace
" _Yayah please........_
Juyawa yayi ya kalli Teema sai ya sake kallon Munniran, fasa fa'dan abinda yayi niyya yayi sai kawai yaja hannunta suka nufi 'kofar fita.
Be damu da takalmanta da mayafinta dasuke jefe a'kasan office 'din ba haka yajata suka ratsa cikin Companyn har zuwa inda yayi parking, yana zuwa yaturata abaya yarufe sannan ya zagayo ya shiga driver seat.
Teemah ce cikin sauri ta tattaro sauran tarkacen Munniran ta ri'ko ahannunta da gudu tabiyo bayansa amma kafin ta iso har yaja motar da 'karfi 'kuran bayan motar kawai ta tarar.
Zuwa lokacin kuwa hankalin dayawa daga cikin ma'aikatan yadawo kansu dan ko lokacin daya bar cikin companyn ma wasu nata mamakin dalilin daya sashi hakan.
Umar ne da shigowansa kenan ya 'dan fita waje yasamo Teemahn tsaye hannunta rike da wasu kaya.
Mamakin dalilin hakan yayi sai yanemi ji daga bakinta.
Amma bata sanar dashi ba sai ma ro'konsa data fara yi akan ya taimaka yakaita gida wata'kila Mahmud can yanufa da Munnira.
Tana cikin ro'kon Umar sai ta hango Abbas na 'kokarin giftasu, gaba 'daya sai hankalinta ya koma gurinsa.
Hatta Umar sai da ya juya ya kalloshi dan yanda hankalin Fateemah ya 'dauku izuwa kallonshi dole tasa Umar ma yabi gurin da kallo.
Take ya gane shi domin sun ha'du wajen 'daurin auren Mahmud a damaturu duk da be da'de tare da su ba amma hakan be sa Umar ya manta da fuskarsa ba.
" _Yah..... Abbas_ !
Ta fa'di sunansa da tunanin shi 'din ne ko kuwa wani ne me kama dashi.
Cak kuwa ya tsaya duk da be gama tantance shine ake nufi da 'kiran ba ko waninsa, amma muryarta ba ze ta6a mantawa ba ko a ina yaji ta.
Hakan ne kuma yashi waigowa ahankali sai caraf idanunsu ya sar'ke cikin na juna.
Teemah kam kasa juran hakan tayi dan haka sai ta meda idanun nata 'kasa ta taho ahankali zuwa inda yake kayan Munnira rungume a 'kirjinta.
Mamaki Abbas yakeyi ganin Fateemah a harabar companing su Mahmud kuma batare dashi ba.
Tana isa inda yake sai taji idanunta na 'ko'karin tsatstsafo da ruwan hawaye ahankali tasake 'daga idanu takalleshi amma kwarjininsa ya hanata sakewa.
" wai ke faruwa ne? Ina Mahmud 'din?
Ya tambayeta cikin sauri.
Daidai nan Umar ya iso ya mi'ka masa hannu suka gaisa sai ya sanar dashi cewa yana zaton Mahmud 'din be jima da fita ba saboda wata 'yar matsala dake faruwa yace shima yanzu yake so ya sau'ke ta agida.
Tare suka koma motan dukkan su inda Teemah tashiga baya sukuma Abbas da Umar na gaba.
Rintse idanu yayi yana sake recalling mafarkinsa wato dagaske Fateema na bu'katan taimako, in bahaka ba meyasa yaganta haka tana kuka?
Amma ba ze iya bu'dan baki ya tambayeta ba.
Ganin da Umar yayi kamar abin ya sar'ke zuxiyar Abbas ne yasa shi sake tambayarta abinda ke faruwa.
Zuciyarta na tsananin bugu ga damuwa da suke son suyi wa zuciyarta yawa amma haka ta daure tayi musu bayani atai'kace dan muryarta shaking yakeyi sam bazata iya dogon magana ba ahalin yanzun.
Abbas jiyayi tamkar zuciyarsa zata fito waje tsabar haushi ba'kin ciki dan Teemah batun Anty Chiddy ka'dai ta sanar dasu bazata iya fa'da musu 'dayan maganar ba.
Jikin Abbas har rawa yake yi saboda yanda ransa ya 6aci amma ko 'kala be ce ba shi de yayi shiru Allah ne ka'dai yasan yanda yakeji azuciyarsa wato Mahmud zuwa yayi ya watsar da ita har wasu banzayen 'yan iska suka samu daman shiga rayuwarta da haukarsu.
Jiyake da zaiga mutanen awannan lokacin dashi ka'dai yasan abinda ze musu.
Da wannan tunanin suka isa gidan Mahmud amma baya nan, Abbas ne yayita gwada 'kiransa amma kusan missed call uku yamasa be 'daga ba.
Hakan kuwa ya 'kara tunzira zuciyar Abbas aciki yake jin ciwo da 'kunan abin.
Shiru Umar yayi duk da be gama fahimtar abinda yafaru duka ba amma ayanayin labarin da Fateemah ta basu ya fahimci cewa ran Mahmud yagama 6aci ayau 'din. Tunanin inda zai samu Mahmud yake a dai-dai wannan lokacin, ina yanufa da yarinyar da Fateemah tace yafita da ita.
*****
Mahmud kuwa be zame ko'ina da Munnira ba sai gidan Anty, yana shiga kuwa ya hangota tana shirin shiga mota itama ga dukkan alamu fita zata yi.
Ko gama parking beyiba ya fita tare da jawo hannun Munniran yakawo ta gaban Anty da tun shigowar motan ta tsaya saroro tana ganin ikon Allah dan ayanayin daya shigo ka'dai ma sai da mamaki ya kamata balle data ga Munnira ahannunsa wujuga wujiga ai shikenan tunaninta ya tsaya cak.
Yana isowa yatura Munniran kamar kayan wanki ta fa'di agaban Anty tana kukan fitan rai.
Azuciye yace
" _saurari yarinyar nan Anty kiji abinda take fa'da, Anty bana fatan abinda_ _naji ya kasance gaskiya domin hankalina baze iya 'dauka ba._
_Anty wai dake za'a ha'du acutar dani da rayuwata, Anty idan ma kina_ _gadaran 'danki ne ni toh ita Fateemah fa?,miye yarinyar nan ta tsare miki_ _aduniyan nan da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 35 Chapter of 67