masa 'kabarinsa, nasan beyi gaggawa ba muma kuma ba jin kiri mukayi ba.
Dayake Ummah tariga su Mummy isowa yasa Teemah tunda taga Ummahn ta tafi ta lafe ajikinta tayi shiru gaba 'daya koman ta ya tsaya mata cak hatta tunani bata iyawa sai de idanuwa da take faman rarrabawa ko rintse idanu bata son yi saboda tana rintse idanun sai taga Yayah Mahmud nayi mata murmushi lokacin dayake kwance a hospital, hakan yasa ta 'kin rintse idanu koka'dan.
Sai da Mummy tazo sannan tatafi wajen Mummyn ta rungume ta tare da sanya kuka abin tausayi tace
" _Mummy ance wai Yayah Mahmud ya rasu_ "!
" _Yi shiru toh ki daina yi masa kuka, addu'ah zakiyi masa ba kuka ba kinji_ "
tace
" _ai kema kukan kikeyi Mummy_ !
Janta Mummy tayi ta ha'da ta da jikinta sosai ta rungumeta dukkansu na kuka da rashin Mahmud 'din, ga kuma tausayin Teemahn datake ji sosai ahalin yanzun.
Sai ganin Anty sukayi tsaye akusa dasu tace " _Khadija kema kuka kike yiwa Mahmud ko_ ?
'Dagowa Mummy tayi ta kalleta idanun ta duk hawaye.
Murmushi Antyn tayi me ciwo tare zama daga gefen Mummyn sannan tace
" ba ke ya kamata kiyi kuka ba Khadija nice,
kuka dani ya dace, inajin kamar da hannayena na kashe shi, ha'ki'ka na cuci rayuwata na cuci rayuwar mutanen da basu ta6a min koda kallon tsana ba balle su cutar dani, bansani ba Khadija ashe sakayyata me girma ce, ban ta6a tunanin mugun halina ze iya sanadin 'dana na cikina ba, banta6a tunanin haka ba, sai gashi Allah ya nuna min iyakata ta yanda ban isa inja da yinsa ba koka'dan koda da wasa"
Idanuwa ta lumshe sai ga hawaye sun ziraro mata da gudunsu bata damu ba taci gaba da fa'din " yaune rana ta farko dana ta6a yin dana sanin aikata mummunan laifi arayuwata, Mahmud 'dina yarasu Khadija, Mahmud ya tafi ya barni da tarin laifukana bansani ba ko Allah ze ji'kaina ya yafeni"
Wata mata dake zaune daga gefenta ce ta fara bata baki akan tayi shiru ta daina kukan mana tace fa'de-fa'den ma bashi da amfani.
Ko kallonta Anty batayi ba kawai ta jijjiga kanta tace
" baki san yawan abubuwan dana aikata ba ne, na tabbata da kinsani nasan da kema tsanata zakiyi kamar yanda yarona yatafi da mugun tsanata azuciyarsa, juyawa tayi ta kalli matar tace kinsan abinda yakashe min Mahmud ne ? Kinsan sanadin mutuwarsa?
ko kinsan mugun ciwon da ya dasu acikin zuciyarsa kafin ya rasu?
Ni naga wannan 'kuncin acikin idanuwansa naga hawayensa dayake fitarwa me ciwo kafin yabar gidan nan, duk naga hakan rintse idanu nayi ban ko ji tausayinsa ba, ni de 'kudurina kawai ke gabana"
Mahmud yaro ne me matu'kar biyayya yana kula da dukkan hakkin iyayensa daya rataya akansa be ta6a yin abu dan ya 6ata min rai ko mahaifinsa ba duk kuwa da surutun da Allah ya bashi hakan be sa ya kasance mara kunya ba, nice nafara 'kuntatawa rayuwarsa ta hanyar dasa masa 'kaunar yin makaranta a'kasar waje wanda tun bashi da ra'ayin haka har yazo ya amince saboda yanda yaga na kafe akan hakan , nariga nasan mahaifinsa baso yakeyi ba amma na dage nace sai anyi, sanadiyyar haka har ya 'debi shekaru kusan biyu batare da yayi makarantar ba, daga 'karshe me yazo yafaru ?
"anan garin lagos yayi makarantar kuma yagama lafiya, tun anan ya kamata nasan abinda kalmar 'kaddara yake nufi amma sam ban yadda ba sai ma na 'kara jahilta kaina da tunanin sakacina ne yakawo hakan, lokacin da Mahmud yace min zai je service ajahar yobe wallahi hankalina ba 'karamin tashi yayi ba, naso na hana hakan badan komai ba sai dan muguwar 'kiyayyar da na kewa Khadeeja wanda alokacin ajahar yoben take da zama, anan kam Mahmud yace shi fa sai yaje dole na nayi ha'kuri na barshi yatafi duk da raina be so ba amma haka na ha'kura na barshi se de har yayi yagama hankalina be kwanta, nakan yawaita takura masa akan yazo gida duk da bani da wani takamman dalilin yin hakan amma zuciyata tariga da tayimin muguwar sa'kar 'kiyayya da be anfane ni da komai ba sai da nasani da bashi da amfani.
Mahaifinsa da kansa ya nema sa auren Fateema musamman dan yabawa da yayi da natsuwarta da tarbiyyarta wanda kafin hakan ni kuma nayi masa maganar auren Munnira duk da ya nuna min baya ra'ayi amma na nace akan sai ya aureta haka abaya so 'din ya amince min sai de mahaifinsa dayake yafini iko dashi, shine ya nemasa auren Fateema alokacin bazan iya misalta yanda naji ba dan haushi da takaici, nayi-nayi iya 'ko'karin dan ganin na hana auren amma hakan ya gagareni, hatta bokaye da malamai duk nabi amma ban iya dakatarwa ba, tsana kuwa 'karara nake nunawa duk wani abu daya danganci auren, sanadin haka mahaifin Mahmud yakai 'karata wajen mahaifina a kano, sosai mahaifina yaja kunnena, yayi min garga'di, yamin wa'azi amma duk abanza koka'dan ban 'dauka ba, ganin haka mahaifina har la'antata yaso yi amma mahaifin Mahmud ya hana shi sai yace matu'kar na aikata wani abu da be kamata ba toh be yafemin ba.
Wannan kalmar batasa na yi wa kaina fa'da ba, mahaifiyata matayi 'ko'karin jan hankalina amma na nuna mata bata isa ba dole itama tazuba min idanu ta 'kyale ni.
Ko bayan auren nayi ta neman hanyan dazan rabasu amma narasa yadda zanyi, ni kaina bansan me yasa na tsani auren ba, bansani ba ashe shai'dan ke ingizani, dan Fateema bata ta6a 6ata raina ko sau 'daya ba amma duk da haka banji amincewar barinta ta zauna amatsayin matar 'dana ba.
Hakan nema yasa da 'kawata ta nemi ha'din kanta izuwa aikata alfasha nice na tsaya tsayin daka wajen ganin faruwar hakan, akan haka Mahmud yazo yau 'din nan dasafe yana kuka Khadija, yana hawaye yake ro'kona akan meyasa nayi haka, meyasa zan bada irin wannan gudummuwar wa rayuwarsa, banji komai araina ba face 'karin haushin matarsa araina hakan yasa nafa'da masa maganganu son raina wanda be kamata ni in fa'da masaba amatsayina na mahaifiyarsa,
Kinsan me yace min ?
"Cewa yayi zai 'dauke matarsa su bar min garin yace inyafe masa in Abbahn sama yadawo ince ya yafe masa laifukan daya masa daga nan yatafi yana share hawaye, ashe 'karshen Mahmud kenan, 'karshen rayuwarsa kenan, ban masa adalci ba koka'dan amma duk da haka yace ya yafemin yace in yi masa addu'ah kawai Mahmud yatafi ya barni da ba'kin cikin rasashi da muguwar dana sanin da bazata ta6a amfanata da komai ba, kaicona nikam wallahi dana kasance me tsananin son kaina, inama zaka dawo Mahmud mu sake rayuwa dakai da sai na so ka na sada ka da 'yan uwanka na kula da kai yanda se ka zama abin kwatance zan zame maka uwa yanda kowa sai ya yi sha'awar rayuwarka, da kai kanka sai kayi alafahari da kasancewata uwa agareka, amma babu dama, ni da kai na nasan ni ba uwa tagari bace, ban kasance acikinsu ba face masu cika rayuwar 'ya'yansu da 'kunci, wahala da azaba gashi ni da kaina nayi sanadin rayuwarka.. inasonka yarona, inason ka Mahmud bansan me ya 'dauke hankalina na manta cewa kai 'din amana ne agurina ba, amanarka Allah ya bani gashi sanadina kabar duniya da tarin ba'kin ciki azuciyarka, Allah kaji'kan yarona kayi masa rahama, Allah ka hasakaka kabarinsa kasa shi 'din me rabone"
Ta 'karashe da kuka me ciwo tana dafe 'kirjinta, kusan dukkan wa'danda ke cikin 'dakin sai da suka zubda hawaye tsaban yanda Anty tacika zuciyoyinsu da tausayi.
Cikin kukan tace
"Khadija dan Allah ku yafemin, tun da sauran rayuwata, Mahmud ya tafi ya barni batare da yabani damar da zan ro'ki yafiyar sa ba wanda inajin ciwon hakan har azuciyata nasan wannan nawin baze ta6a barina in rayu cikin salama ba, Khadija idan ke ma kika 'ki ki yafeni bansan ya 'karshen rayuwata zata kasance ba, na tabbata nayi babban hasara dana 'dauki tsana mafi girma na shinfi'da atsakaninmu, gashi nan shine sanadin komai nice nayi hasara arayuwata gaba 'daya, Fateemah ki yafemin kinji dan Allah ku yafe min ko Allah ze ji tausayina "
Mummy kuka take tayi harda sheshsheka har maganar ma kasayi tayi gaba 'daya jikinta yayi sanyi da al'amarin Anty duk da yake dama ita bata wani ri'keta da haushi azuciya ba, kullum addu'ah take faman yi akan Allah ya shiryata yasa tagane cewa ita 'din bata nufinta da komai, tagane cewa 'dan uwa ba abin yarwa bane, amma hakan be samu ba har se da rai yabi al'amarin kafin nan, yanzu kam se fatan Allah ya jikan Mahmud yasa aljannah itace makomarsa muma Allah yasa mucika da imani Allah yasa kalmar shahada itace 'karshen kalmarmu.
(Ameen).
Kafin Mummy ta bu'di baki tayi magana sukaji anyi sallama ashe har anfito daga masallaci, anzo fita da gawa, cikin masu shigowan harda Abbas aka shigo.
Anan ne kam koke-koke ya 'karu dan Anty da Teemah kukansu nin kuwa yayi fiye dana baya, banda su Ummah ma da sauran mutane suma sai share hawaye sukeyi.
Anty kam ri'ke shi tayi tana sake zubda hawaye tare da dana sanin abubuwan duk data aikata abaya.
Abbas ne yace su 'dauka su tafi kawai kukan bashi da anfani tunda ba addu'ah zasuyi masa ba.
Haka suka 'dauke shi suka fita dashi zuwa waje.
Teemah kam cak kukanta ya tsaya tabisu kawai da idanu har ta daina hangosu, babu wanda ya lura da ita sai Ummah, itace tazo ta mi'kar da ita tsaye sannan suka koma gefe suka zauna taringa yimata nasiha tare da bata baki har ta nutsu.
Agurin Abbah aka ajiyeshi yayi masa addu'ah sosai hakama Alhaji Muhammad (kakansa mahaifin Anty).
Daga nan akayi masa sallah aka sada shi da makwancinsa na gaskiya.
Abbas kam suna dawowa daga ma'kabarta be wani da'de ba bayan yasamu ya isar da ta'aziyarsa ga su Abbah kawai ya wuche abinsa, dan baze iya shiga cikin gida gurin matan ba a wannan lokacin, bayaga haka ma shi sam ya tsani ganin fuskar Anty ayanzun.
Yana komawa kuwa ya tarar komai ya kammala sai kawai suka 'dau hanya.
Niyyarsa idan yakoma 'din ze nemi pass ne sai yasake dawowa gurin rasuwar amma kuma koda suka koma sai suka tarar da wani mummunan hari da aka kawo, an kashe dayawan sojojinsu aranar, ka'dan ne suka samu rauni inda 'kalilan daga cikinsu kuma suka tsira da rayukansu da 'kyar.
Washegari sauran 'yan uwan su dake 'kauye suma suka iso da 'yan uwan Anty inda so rin'ka tunawa da alkhairin da Mahmud ya musu kwanaki ka'dan da suka gabata, suna jinjina halin rayuwa ha'ki'ka rai ba'a bakin komai yake ba.
*****
Abin ya matu'kar 'kona ransa yanda 'yan ta'addan ke faman wasa da rayukan mutane batare da damuwar komai ba, sun maida rayukan al'ummah tamkar ran kiyashi, son ransu suke 6arna agurare batare da damuwar komai ba, haushin hakan yasa ya manta da batun mutuwar Mahmud kawai yafara tunanin neman mafita.
*BAYAN SATI 'DAYA* .
Kafin a'karo musu wasu sojoji Abbas da kansa yayi shiri sosai jin inda ma6oyar 'yan ta'addan yake acikin garin daga wani majiyar sirri sai ya yi shirinsa sosai musamman dayake akwai kayan aiki agurinsu sai sukayi amfani dasu tare da taimakon wa'dan da suka rage daga cikin battalion 'dinsa suka tunkari wajen da harin ko ta kwana.
Yariga yasawa ransa cewa ze yi ya'ki dasu da dukkan 'karfinsa da zuciyarsa hakan yasa be ji ko 'dar ba ya tunkare su da zuciya 'daya Allah kawai ya mi'kawa dogoransa, abu 'dayane dama abin tsoron shine mutuwa shikuwa be dame sa ba, yasan ko mutuwa yayi awanan halin Allah yasani, bashi da alhakin kowa dan haka no retreat no surrender.
Basu fi su goma ba, ha'di da armourtank guda biyu suka tunkari sansanin.
Allah cikin ikonsa kuwa gaba 'daya suka tada gurin suka 'kona komai, kafin hakan sai da yayi ko'kari wajen ganin ya kama director 'din su dake gurin araye, sai de kuma shima Abbas 'din an kashe kusan bakwai daga cikin sojojin nasa befi su biyar bane suka tsira da rayukansu.
Wannan abin da Abbas yayi ba 'karamin girma ya 'karawa hukumarsu ba, dan kuwa aganinsu yayi abinda bakowa ne ze iya yi ba sosai sukayi farin ciki tare da alfahari dashi, hakan yasa duk su biyar 'din da suka rage aka yi musu albishir na 'karinum girma.
Hutu aka basu na tsawon wata 'daya dan su koma ga iyayensu da matayensu.
*CONDOLENCE*π
Sa'kon ta'aziya ga dukkan 'yan uwa musulmai da suka rasa yan uwansu da 'ya'ya yensu, ubangiji Allah yaji'kansu da rahama (Ameen).
Kuyi ha'kuri kuma masoyana, ha'ki'ka ni kaina naji mutuwar Mahmud sosai kamar yanda naga wasu dayawan ku ma suke fa'di , amma ya zamuyi , mutuwa dole ce akan kowa, kuma ahaka labarin yazo tun asali, kunga sai de muyi hakuri....
Dafatan zaku ci gaba da bina har akai ga ci........π€π»
ππΌ
Fatan zaku cigaba da min uzuri na jinkiri danake yi kafin kuga update musamman Wattpad reader's wlh abubuwa ke min yawa amma kullum kuna raina ban ta6a mantawa daku ba.π
_Share_
_Vote_
_Comment_
*Salmerh ce*π
[10/2, 6:03 PM] Ummiyo: π *CAPTAIN ABBAS* π
By
*Salmerh MD*
Luv storyπ
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
π« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
π«
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_Dedicated to u my lovely fans.....Allah ya bar min ku_.π₯°
*Bismillahir rahmanir raheem*
_Failure is only a temporary change in direction to set you straight for your next success. Only_ _those who dare to fail greatly can ever achieve greatly_ .
π
Ώ *68*
Abbas ma porthacourt ya koma ya 'dan huta tukunna sai da yayi kwana biyu kafin yakoma Abuja.
Daddyn Abuja yaji labarin abinda sojoji suka aikata a Borno akafan ya'da labarai amma be ta6a zaton 'dansa Abbas bane ya jagoranci abin har se da Abbas ya dawo gida yake sanar dasu 'karin girman da za'a yi masa.
Mamaki sosai Daddyn Abuja yayi har yake tambayarsa dama haka akeyine, daga shigan mutun sai 'karin girma yabiyo baya.
Anan Abbas yayi masa bayani atakaice akan abinda yafaru, ai kuwa anan Daddyn Abuja yafara masa masifa akan abinda ya aikata 'din yake cewa yanzu badan Allah yarufa asiri ba inda sun kashe shi awurin fa, yace shi sam baya son rigima da tashin hankali yace shiyasa tun farko ni hankalina be wani kwanta da wannan aikin ba in ban dama Yayah Kabiru ya sa baki da wallahi bazaka yi wannan aikin ba ballantana har kaje kana rigima irin wannan, 'karin girman banza da wofi salon cuta, aidan sunga kana bada rayuwarka ne shiyasa inda bakayi hakan ba da bawani girma da sazu 'kara maka"
Shiru Abbas yayi yana sauraronsa sai da yaji yayi shiru kafin ya fara bashi
ha'kuri amma kamar 'kara zugashi yakeyi sai sake 6allewa yakeyi yana bu'de sabon salon masifa ta inda yake shiga bata nan yake fita ba, shi tsakaninsa da Allah yaji haushin
abinda yafarun.
Abbas dayaga haka sai yayi shiru kawai yaci gaba da sauraransa.
Allah sai ya taimaki shi ya kawo masa Daddy Babba dayake shi be baro wajen ta'aziyar Mahmud ba sai yau kasancewar Abbah babban abokinsa ne dole ya kasance dashi a kowani irin hali.
Yana shigowa kuwa yaji me suke tattaunawa akai sai da yaji Daddyn ya kasa fahimtar Abbas ne kafin ya jefo nashi da fa'din
" _haba Hassan, ya zakayi haka kuma? dama ya shiga aikin ne dan ya zauna yaga ana abinda bashine ba_ _ya kuma sar'ke hannuwa yana kallo?_
" _Ai kamata yayi ka 'kara masa 'karfin gwiwa tare da godewa mahallici daya sanya ya tsira da ransa, bawai kasashi agaba da bambami irin haka ba, da wanne zaiji?_ "
Shiru Daddyn Abuja yayi ya kauda kai gefe, hakan yasa Daddyn Teemah 'karasowa ya zauna shima.
Dan ya fahimci ran 'kanin nasa a matu'kar 6ace yake tunda har ya nuna halin ko in kula da zuwansa.
Da 'kyar yasamu yashawo kansa ya sassauto.
Amma be wani saki jiki sosai ba, duk lokacin dayaga Abbas 'din sai kawai ya tuna da abubuwan da yayi taji a labarai sai yaji ransa ya 6acida hakan.
Kusan kwana uku da dawowar Abbas amma maganar bata wuce ba, su daddy suka koma Dubai da Mummy sai daga baya da ya samu Daddyn nasa yayi wata tafiya kafin yasamu ya 'dan sake a Abujan.
Sai da su Mummy sukayi kwana biyar da tafiya kafin yasamu suka zauna da su Ummah har suka 'dan tattauna akan rasuwar Mahmud wanda dukkansu abin ya ta6a rayukansu ciki harda Hannah ma da ita bataje ba kuma ma bawani sabo tayi dashi ba, amma yanda Ummah ta ke basu labarin yasa duk takejin tamkar tana gurin akayi komai, dataji batun saka Teemah ta aikata lesbian da Anty taso yi da wata mata wacce bama musulma ba ce yasa tunanin Hannah yayi saurin kawo mata cewa waccen matar ne data ganta ranar da suka kai Teemah gidan uwar mijinta dan taga yanda matar take kallon Teemah alokacin tamkar zata cinyeta 'danye bata ta6a raba 'dayan biyu itace.
Hannah ce ta tambaye Ummahn tace da ita " _toh meyasa kuma aka baro Teemah acan bayan duk faruwar wa'dannan_ _abubuwan, basa jin tsoron abinda ze biyo baya ne_ ?
sai Ummah tace
" _Antyn yanzu tana bata tausayi ne sosai kuma ita ta ro'ki abar mata Teemahn saboda_ _ka'daici_ "
Ummah tace itama bata amince ba da farko 'ki tayi dan taga yanda yanayin Teemahn yake har yanzu bata saki ranta ta sosai ba, taso a 'dan nesantata da garin ko zata samu ta warware da wuri, amma se Mummy tayi saurin amincewa da batun Antyn.
Ummah tace
" _koda muka ke6e ma naso in tuhumi Khadija akan_ _meyasa tayi haka amma sai ta nuna min bakomai ai yanzu Anty tayi_ _nadama ta gane kuskurenta, mutuwar Mahmud ya kasance aya ne agareta me girma, dan haka abar mata Teemahn kawai wai_ _Antyn tausayi take bata sosai itama yanzun_ "
Ta6e baki Hannah tayi ta 'dauki wayarta taci gaba da latsawa tamkar bata damu ba amma Allah ne ka'dai yasan yanda taji haushin hakan azuciyarta, abar yarinya ma da abinda ya dameta za'a wani 'kara barinta agurin muguwar matar nan, itama Teemah ai abin tausayi ce ba wata Anty ka'dai ba, ji take da 'ace tana da iko da sai ta je ta 'dauko 'yar uwarta zuwa gida , yayinda Abbas ya kauda kansa gefe sam yaji nutsuwarsa ta kau, shi ai be ta6a tunanin an baro yarinyar acan ba, taya ma za'ayi ace tana can gurin matar da ta fi tsananta aduniya se kace tarasa 'yan uwa ko kuma tarasa inda zata zauna , wannan ai rashin gata ne akayi mata, sam ya tsani matar nan har zuciyarsa, halinta sam be masa ba, yanzu kuwa dayaji komai kaf sai yakejin ma gaba 'daya itace abu mafi girma dayafi tsana arayuwarsa, tausayin banza tausayin wofi
shi be abin tausayi awurinta ba sam.
Be ce da Ummah komai ba kawai ya tashi yana wani ha'da goshi yakoma 'dakinsa.
Ummah da idanu kawai ta rakashi dan ta fahimci ba'a saiti yake ba.
*****
Yanzu komai ya dawowa Anty sabo fil, ibada kawai tasa agaba tana neman gafarar mahallici tare da yiwa marigayi Mahmud addu'an neman dacewa, kusan kullum sai ta zubda hawaye musamman idan ta dubi Teemah sai taji dama ta bari sun yi rayuwarsu cikin kwanciyar hankali sun haifa mata jikoki masu kyau kamar su, da ma bata shigo da su Munnira cikin rayuwarta ba, tasan da yanzu komai be faru ba,
lallai gaskiya ne da'ake cewa tsalle 'daya tak zakayi kafa'da rami amma fita daga ciki kuwa sai kayi dagaske, yanzu gashi nan ita gari ya waya dan kowa na zaune da 'ya'yansa cikin so da 'kauna ita kuwa babu nata, tsanan data yiwa Khadija na ba gaira ba dalili gashi ita abin ya cutar, awannan lamarin bata tashi da komai ba face hasara me girma, ko Anty Chiddy da take aminiyar tama gashi tun rasuwar Mahmud 'din har yau sau 'daya tak taganta agidan, bata 'kara zuwa ba, ha'ki'ka masoya nada wahalar samu wani lokacin ma'kiya kuwa ko'ina suna nan birjik akewaye dakai, gashi ita masoyanta ma na kusa da ita amma ta rintse idanu ta ringa hango ma'kiyanta dake nesa da ita 'karfi da yaji ta matso dasu kusa da ita, bata sani ba ashe kanta zata cutar, gashi nan Khadija data nunawa tsana muraran itace ta bar mata 'yar cikinta amatsayin sanyin idaniya dan ta rin'ka 'debe mata kewa batare da ta yi musu ko da ka'dan ba, yau da ace burin Anty Chiddy ya cika akan Fateemah tayi lalata da ita da bata san ya zatayi da abin kunya ba, tasan ita kanta da se ta tsani kanta da rayuwarta, Alhamdulillah ma da abubuwa suka 'dan yi sau'ki Allah ya tsare Fateema ya bata kariya.
Abbah kansa yanzu baya kula ta ko da ya shigo sede su gaisa da Fateemah ya 'dan jata da hira da tambayarta damuwarta sannLnan ya yi mata nasiha daga nan ya tafi abinsa ko kallon inda Anty takeyi ma bayayi.
Da farko tana damuwa da hakan amma ganin dagaske yakeyi yasa itama ta ha'kura ta daina damuwa tasawa ranta cewa girban sharrinta kawai takeyi adun'kule, tariga kuma ta kar6i duk wani 'kalubale da zai zo mata ko da kuwa Abbah zai ce ne yasake ta bazata damu ba in kuwa yankan naman jikinta zai rin'kayi kullum shima bazata yi musu ba, dan tasan ka'dan kenan daga cikin abinda Allah ze mata dan ba 'karamin amanar amintattun bayinsa taci ba.
Abbah kullum idan ze dawo sai ya kawo mata wani abu naci sha kona sawa sannan yayi ta mata hira har se yaga ta 'dan saki jiki kafin ya barta, shi kanshi ma bawai mutuwar bata dameshi bane a'a sosai yake jin kewar 'dansa amma baya nuna damuwarsa afili, sai ko in yana 'dakinsa shi ka'dai kafin nan yake tunani tare da yi masa addu'ah sosai, amma kana ganinsa kasan mutuwar ta bigeshi, musamman idan kayi duba da irin ramar da yayi, tausayin Teemahn yake ji ayanzun ganin cewa wannan lamarin ya sameta ne tun a 'kananun shekarunta, tana yarinya 'karama da ita shiyasa ma kullum yake 'ko'kari wajen ganin ya faranta mata.
Anty kuwa kawai dubanta yakeyi baze iya koda maimaita abinda yafaru abaya da ita, be ta6a sanin haukarta takai hakaba, shi dai baze rabu da ita ba saboda darajar mahaifinta amma bayajin ze 'kara yadda da ita har 'karshen rayuwarsa, tsana me girma yake yi mata wanda baya jin akwai ranar da hakan ze bar ransa.
Teemah har karatu take 'karawa Anty ka'dan dan gaba 'daya ta mantasu duk da ta yi karatun abaya amma rashin kulawa yasa yanzu ko izu biyu bazata iya kawowa da kanta ba, hakan yasa tace Teemahn tana yi mata ko zatana tunawa dasu.
Tanajin da'din hakan kuwa dan kuwa sosai take 'karajin kusancin ta ga mahallici, sai de lokuta da dama sukan bar karatun ne saboda kukan da Anty takeyi musamman idan ta tuna baya ta tuna da 'ko'karin da mahaifinsu yayi tayi akansu amma duk ta watsar, shima yau gashi da fushinta ya yabar Lagos beko tsaya ya saurareta ba, tasan yanzu kusan kowa ya tsaneta tunda gashi iyayenta ma basu saurareta ba, saboda mummunan halayenta.
Anan ne Teemah sai tayi ta bata ha'kuri tana mata nasiha hartayi shiru, gaba 'daya damuwar Anty sai ta nunka na Teemah harma wani lokaci manta nata takeyi sai de Anty.
Itama yanzu sosai Antyn take bata tausayi ganin yanda gaba 'daya take damun kanta alokuta da dama.
Gashi Abbah ma sai ya daina shigowa sai de ya 'kira Teemahn zuwa 'dakinsa suyi hirarsu ya bata duk abinda zai bata sannan ya sallameta, sau tari sai bayan ta fita damuwarsa ke 'kara yawaita addu'arsa kullum agareta shine Allah ubangiji ya bata miji nagari wanda zai so ta ya kuma kula da rayuwarta.
Haka rayuwar Abbah ayanzu sam Anty kwatakwata ta daina ganinsa ma.
Ganin kamar abin ze mata yawa ne yasa Teemah ta 'dan fara yiwa Abbah magana akan ya yafewa Anty kar damuwan yayi mata yawa tunda yanzu ta tuba tace ya yafe mata shima, Allah ma yafe mana yakeyi idan mukayi masa laifi meyasa mu bazamu yafi junanmu ba.
Da 'kyar da su'din goshi Teemah tasamu kyakkyawar kalmah daga gurin Abbahn dan kusan kwana uku sukayi akan maganar kafin yace zai yafe mata amma sai in ya ga cewa tuban
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 37 Chapter of 67