Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta d'ago idanu ta kalli Anty chidehn sosai. Sam Anty takasa daina mamakinsu dan ganin datayi su kwata kwata abin bai wani damesu ba kamar ba abin jin kunya tasame su sunayi ba. Dariyah kad'an Anty chidehn tasaki ganin yanda Anty ta kasa daina yi mata kallon tuhuma. Sai ta mik'a hannu ta d'an kamo hannun Antyn atake kuwa Anty ta wafce hannunta da k'arfi domin zuwa yanzu in akwai abinda tafi kyama toh itace babbar aminiyar shawaran tata wato Anty chideh. " come on, feel free mana mum mamud bakomai fah" Tafad'i da dukkan gaskiyarta tana kallon Antyn ita adole in anbarta ba abin damuwa vane hakan, ganin Antyn bata kulata ba sai ta k'ara da fad'in " sucking kawai nake sata tamin when I'm in need but nothing else". "hmm" kawai Antyn tace tare da mik'ewa daga kan kujeran datake tace tatafi gida. Magana taso suyi akan maganin da aka kawo mata d'azu amma wannan 6oyayyen halin Antyn chidehn data gani yau yasata fasa yin maganar ma gaba d'aya kawai ta koma gidanta. Anty chidehn ma batawani damu ba dan tasan damuwar na yanzu ne kawai dakanta ma zata dawo kodan wani dalilin na daban. Anty kuwa koda takoma gida tunanin abun yakasa barinta sam bata ta6a kawo hakan ga k'awartanba duk da yake ahlul kitabi ce ita amma sam bata kawo cewa rashin imanin Antyn yakai har haka ba. Wannan dalilin ne yasa tad'an d'aukewa Anty chidehn k'afa na kusan kwana biyu, yayin da Anty chidehn tabata chance itama akan ta huce tukunna tasan cewa akan hakan bazasu rabu ba sai dai akan wani dalili daban domin bak'aramin sanin sirrin juna sukayi ba, ko wannan d'inma Anty Chidehn ta 6oye mata ne dan ganin kamar ita ba ra'ayinta bane yin hakan shiyasa bata ma bayyana mata ba. Shima Mahmud zuwan Munira da kwana biyu yace shikan zai koma ana nemansa Daddynsa ma baya gari amma ya tattara yakoma yobe state d'in abinsa domin jiyayi sam zaman chan d'in yadaina yimasa dad'i. Da farko Anty taso ta hanashi komawa dan ita afad'anta wai sai ya jira Abbansa yadawo tukunna. Mahmud kuwa yak'I amincewa da batun nata don dolenta ta kyaleshi yatafi badan ranta yasoba. A week d'in daya koma ne Munira tasake dawowa gidan amma wannan karon tafiyar kanta ce ba aike ba ne, koda tazo suka gaisa da Anty kamar yanda suka saba suka d'an zauna suna ta tad'i tsawon mintina bataga Mahmud ba bakuma taji Anty ta ambace shi ba a maganar dasukeyi d'in. Kasa hak'uri tayi sai da ta tambaya tace " Anty ina yaronki"? Dariya Antyn tasaki kad'an sannan tace kardai kice min tafiyar batawa bace ta Mahmud ce"? " murmushi Muniran ma tayi tare da fad'in haba shikuma ? " kedai fad'i gaskiya yarinya" Yanda Antyn ta ke sakewa suyi hira da kuma yanda tayi mata magana ayanzun yasata ko shakkun Antyn ma bataji sosai ba dukda yake son d'anta yakama zuciya amma tasan dole sai dasa hannunta sannan zata sameshi inba haka ba kam tasan samunshi zai d'an mata wahala. Sai batayi k'auran baki ba tafara sosa kanta tana sussun kuyar da kai kamar wata mumina, take sai Antyn ta gama ganota aikuwa sai tayi murmushin da kana ganinta kasan farin ciki taji har zuciyarta. Tashin farko sai takamo hannun muniran sannan ta bata assurance akan cewa karta damu indai Mahmud ne kamar tasameshi tagama tadaina ma damun kanta." Wannan albishir d'in ne yasa Munira ta rungume Antyn da k'arfi tana murna da godiya kamar bazata daina ba, tana sake Antyn kuwa ta tashi ta zari key d'in ta da gudu ko kunya bataji tayi waje wai bari takaiwa mummynta albishir mai dad'i. Da murmushi Anty ma tarakata yayinda tana fita itama Anty ta zari mayafi ta tafi gidan aminiyar ta Anty chideh shab ta manta da batun lesbian d'in tsabar farin cikin datake ciki. Kuyi hak'urin rashin jin update da dawuri da bakuyi ba pls abubuwane suka min yawa. Vote, comment and share pls🀞🏻 *Salmern ku ce* 😍 [10/2, 5:59 PM] Ummiyo: πŸ’• *CAPTAIN ABBAS* πŸ’• By *Salmerh MD* Luv story😍 *Wattpad @* *Serlmerh-md* πŸ’« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS* πŸ’« We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all..... *DA BAZARMU* * *MUKE TUNK'AHO* _Dedicated to_πŸ‘ŽπŸ» 😍 *Salmerh nayi muku* *fatan alkhairi* *Bismillahir* *Rahmanir Raheem* When people walk away from you, let them go. Your destiny is never tied to anyone who leaves you, and it doesn’t mean they are bad people. It just means that their part in your story is over. πŸ…Ώ *30* Koda Anty chideh taganta murmushi kawai tayi, daman tasan dolene zata dawo kodan yanda sukayi sabo sosai ma. Haka Anty ta kora mata bayanin abinda yafaru tare da nuna tsantsar farin cikinta afili. Dama tun asali tafison ita taza6awa Mahmud matar aure da kanta sai kuma akayi sa'a fad'uwa tazo mata daidai da zama Munira ta nuna tana ra'ayinsa. Munira y'ar k'awar Anty ce dasuka had'u sanadiyyar maganin mata. Domin duk wani nau'i na magani da suke anfani dashi ita da Anty chideh Mahaifiyar Munira ke musu order daga sokoto kuma sunajin dad'in maganin shiyasa suke shiri sosai. Anty tana gani kamar samun Munirah amatsayin matar d'anta wata dama zata samu dazai sa zumuncinsu da mahaifiyar Muniran ya d'ore sosai. Anty chideh ma sai tayata murna tare da k'arfafa mata gwiwa akan hakan. ***** Mahmud kuwa koda yakoma bai wani dad'e agidan ba yawuche inda aka turashi awani d'an k'auye ne zaiyi bautar k'asan. Da farko Teemah murna takeyi sosai data ga yadawo d'in dan azatonta yanzun agida zai zauna amma sai yace mata ai shi tafiya zaiyi take sai murnar tata ta koma ciki. Dayaga haka sai ya mata alk'awarin zuwa duk weekend yana dubata sai da taji haka kafin tad'an sake fuska. Haka sukayi ta dashi aranar daya sauk'a d'in kuma duk hirar bata wuce ta Abbas ba. Shima sai ya ringa biyeta ganin hakan tafi buk'ata. Harda yayi niyyar k'ira mata Abbas d'in su gaisa amma sai ya fasa daya tuno cewa Abbas d'in yanzu yana bakin aiki ne. Haka suka gama hirarsu suka rabu, yana komawa d'akinsa kamar Abbas d'in yasani sai ga k'iran sa ya shigo. D'auka Mahmud yayi yana murmushi yace " d'an halak" "Allah ko"? Cewar Abbas d'in slowly Mahmud ne yaci gaba da fad'in wallahi nake gaya ma yanzu muka gama hirarka da lil sis harfa da zan k'ira layinka in had'a ku sai kuma nayi tunanin ko kana aiki ne" " hmm ai gara ma baka k'ira ba, bayanzu zanyi magana da ita ba tukunna da sauran lokaci" Mahmud na dariya yace "Kai oga Abbas hukunci ne wannan ko kuma ra'ayine? " duka biyun" Abbas ma yafad'a atakaice. Kafin Mahmud yasakeyin wata magana sai Abbas d'in ya k'ara fad'in yaushe ma kadawo ne bansani Mahmud? " Yau-yau d'in nan na iso amma inajin gobe ko jibi ma zan shiga wani k'auye" " owk Allah ya kaimu" da " Ameen" Mahmud ya fufe maganar sannan sukayi sallama da juna. Washegari da yamma Mahmud yawuche yabar Teemah da kewa. Amma wannan karon bata wani damu sosai ba dan zuwa yanzun tafara sabo da irin hakan. Tafar gane cewa dole ne irin hakan sai ya faru tunda suna da 'yan uwa kuma dole a ziyarci juna. Bazai yiwu ace kowa yazo sai ta yi kewarsu ba saboda ba kowane zai zo yakuma zauna mata agida ba dolene atafi tunda kowa nada muhallinsa koma badan hakan ba kowa nada abinyi. Haka tacigaba da zuwa makarantar ta harsun kusa kammala S S 2 d'in sai Daddynta yace waec zata rubuta kawai bazatayi SS3 ba. Itama dataji datayi farin ciki sosai dan dama tagaji da zaryar zuwa makarantar nan. Shikuwa Daddyn ganin girman data ke k'arawa ne yasashi yanke wannan hukuncin, dan Teemahn akullum kamar hurata akeyi haka ta k'ara k'iba dukta cicciko. Yayinda Mummy sam hakan bai mata ba, inda asonta taso Teemahn ta kammala gaba d'aya kafin sai ta rubuta waec d'in, amma koda ta gwada sanar da daddyn Teemah k'i yayi ya amince dan acewarsa bata da hujhan da zai sa dole sai anyi hakan, dolenta ta hak'ura ta zuba musu idanu. Ana cikin hakan ne wani matashi yabi ya uzzura ma rayuwarta yahanata sakat. Akullum inta fita zuwa islamiyah sai ta ganshi yasha gabanta da niyyar yimata magana. Itakuwa kokad'an bata so daya takurata ma sai ta daina zuwa da k'afan datake zuwa dayake dama itace tace zata na zuwa dakanta bama sai ankaita ba, amma dataga matsin yayin yawa sai ta ce Habibun yaci gaba dakaita kawai. Amma me.....gudun gara take ganin kawai tayi domin tana fitowa zata ganshi tsaye ajikin motarsa yana rarraba idanun ta inda zai ganta. Rashin sa'an datasake yi kuma shine wani lokaci Habibu baya isowa da wuri har sai an d'an fara watsewa yayinda wasu lokuta kuma har jiranta yakeyi tatashi kafin su wuce gidan. Aduk ranar da Habibun bai iso dawuri ba haushi sosai Teemah keji kamar tayi fiffike yayinda ga matashin kuma abin farin ciki ne dan yana samun chance d'in zuwa kusa da ita harma yayi mata magana, dukda bawani kulashi takeyi ba amma dai yana jin dad'in hakan sosai. Ranar kuwa da bai samu daman mata magana ba yakan bisu abaya har sai sun shiga kafin yake wuchewa shima. Sai dai bai ta6a gangancin shiga musu gida ba yakanzo ya tsaya na tsawon wasu lokuta a k'ofar gidan daga d'an nesa batare daya nemi kowa ba shidai akullum burinsa yaganta koda sau d'aya ne. Yau ma takama ranar Sunday, koda Habibun ya sauk'eta gida yakoma suka fita da mummy kuma basu dawo dawuri ba har aka tashi a islamiyar dan siyayyar mummy baya k'arewa matuk'ar tashiga kasuwa shiyasa suka 6ata lokaci sosai. Tsaye take ak'ofar makarantar tana ganin duk kowa na tafiya amma ita sam ba Habibu babu alamarsa, zuciyarta nagaya mata cewa tabi ayarin masu wucewan itama suwuce tare sai dai tana tsoron kar kuma waccen mayen yabiyo su abaya abinda ta tsana kenan. Kafin ta ankara sai taga har ankusa watsewa gaba d'aya domin d'ai d'aiku ne kawai suka rage dan dolenta tafara tafiyah da niyyar cimmah way'anda suke gabanta su had'a hanya amma taku biyar me kyau batayi ba sai kawai taga mutun tsaye agabanta yana murmushi, kallonsa ta tsaya yi da mamaki hankalinta kuma yana ga wad'anda takeso su tafi taren daya fahimci haka sai ya d'an k'ara matsowa kusa da ita hakan da yayi sai ya hanata ganinsu ma gaba d'aya sanasiyyar katangan ta yayi musu. " kiyi hak'uri ya kad'ai nakaiki gida" Yafad'a yana kallon fuskarta. Muryarta na rawa tace" awani dalili". " masoyi" yabata amsa atakaice. Da mqmaki ta d'ago kanta ta kalleshi. "Koba haka bane? Yasake tambayar ta. Bata bashi amsa ba illah hanya da fara k'ok'arin nema dan ta myi wucewarta. Amma mutumin ya hanata wucewa domin duk wani motsin da zatayi sai shima ya motsa ya kuma tare gabanta. Dan dole tasake tsayawa ta wurga masa harara tare da fad'in " wai me kake buk'ata ne"? " ki saurareni"! Kauda kai tayi gefe cikin fushi ranta inyayi dubu toh yau jitake ya6aci saboda mutumin nan sam ta tsami hakan dayayi mata ko tace yake kanyi mata. Shikuwa ganin hakan da k'warin gwiwarsa yaci gaba da fad'in............. Kamar yanda na ta6a fad'a miki sunana Imran dan nasan kin manta tunda ba damuwa akayi dani ba. Kuma ni ba a unguwar nan nake da zama ba, nazo ne duba wani fili sai Allah yasa naganki kuma kika kwanta min araina duba da yanayin nutsuwarki. Dafatan zan sami kar6uwa kodan mu k'ara fahimtar juna da kyau dan ni ji nake nasamu matar aure nagama......... Murmushin takaici Teemah tayi wanda ya tsaya mata a kan le6e kawai....aranta tace su matar aure manya! Horn sukaji daga gefensu take dukkansu suka kallo gurin, Teemah naganin motar gidansu ne tatafi da sauri tana hamdala wa mahallici. Bata kula da mummy acikin motar ba sai da ta shiga ta ja marfin motar ta rufe kafin ta lura da mummyn. Innalillahi wa innah ilaihir raji'un tafad'a azuciyarta dan yau kam tasan me rabata da mummy sai Allah. Baki ta bud'e da niyyar yin magana sai mummy ta dakatar da ita da fad'in " waye shi "? " nima fah ban san shi ba mummy" K'ura mata idanu mummyn tayi tana karantar yanayinta afili zaka fahimci rashin sabo da hakan da batayi ba ga dukkan alamu tilasta ta tsayuwan akayi kodan ganin yanda ta taho da sauri daga jin horn d'in mota duk da bata ma san wake cikin motar ba balle tace danta ganta ne, amma hakan bazaisa takasa yi mata fad'a ba ko dan saboda ta k'ara tsare mutuncinta a matsayinta na 'ya mace. Wannan dalilin ne yasa mummyn ta d'ago hannunta tare da ware yatsa d'aya ta nuna Teemahn dashi kana tafara magana. " kinsan Allah Teemah ki shiga hankalinki banason rashin hankali da rashin wayo, baki san mutun ba shine harda tsaywa dashi a k'ofar makaranta? Owk nagane, saboda ki nuna ke kin isa ko me? Hawaye Teemahn tafara tare da jijjiga kanta Allah mummy bansan shi ba yau ne fah yafara.......... Hannu mummyn ta d'aga tare da dakatar da ita daga cigaba da maganan, sai kawai ta sunkuyar da kanta k'asa tana zubda hawaye, bata so kokad'an mummy tayi fushi da ita akan hakan taso ta yi mata bayanin komai amma mummy takasa tsayawa ma ta saurareta ballantana taji abinda ke faruwa. Takaicin ta d'aya shine akan wanda bata ma ta6ajin zata so shiba mummyn ta na shirin yi mata fushi. Motar shiru baka jin k'arar komai sai na shashekan kukan Teemah har suka iso gida. Koda suka iso gidanma mummy ko kulata batayi ba suka fiffita a motan suka barta, kayayyakin data siyo d'inma Habibu ne da ita suka kwashi abinsu kota kan Teemahn batabi ba. Sai da Habibu yafito ne yazo gurin motar ya d'an bata baki akan tayi hak'uri ta shiga ta bata hak'uri zata sauk'o ai. Da jajayen idanu ta kalleshi tace Mummy tana fushi sosai dani ko ? Yace a'a zata hak'ura ki shiga ki bata hak'uri. Da k'yar ta daure ta fito a motar ta shiga ciki lokacin ma har maghrib ya k'arato, ganin haka kawai sai ta wuce bayi ta d'auro alwala ta zo ta tada sallah. Ba ita ta tashi agurin ba har sai da tayi sallahr isha'i. Addu'a sosai tayi kafin ta tashi ta nad'e abin sallahr. Ko hijabin datayi sallan dashi bata cire ba ta nufi d'akin mummyn ahaka. Da sallama ta shiga d'akin sai ta sami mummyn na shirin kwanciya. Zama tayi ak'asa kanta ak'asa tajira har mummyn ta gama shirin baccin kafin taje gareta da muryar kuka take bata hak'uri. Mumnyn yi tayi kamar batasan da ita a d'akin ba domin kwanciyarta tayi ta juya mata baya, sai da taga kukan da Teemahn keyi kamar zaiyi yawa kar kuma yasata ciwon kai. Koda tayi tunanin nan d'inma sai da k'ara minti guda akai kafin ta tashi ta zauna ta fuskanci Teemahn tare da fad'in " inajinki yah akayi? Vote, comment and share pls🀞🏻 *Salmern ku ce* 😍 [10/2, 5:59 PM] Ummiyo: πŸ’• *CAPTAIN ABBAS* πŸ’• By *Salmerh MD* Luv story😍 *Wattpad @* *Serlmerh-md* πŸ’« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS* πŸ’« We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all..... *DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO* _Dedicated_ _2 all masoyan_ _cApTaIn_ _AbbAs._ 😍 *Salmerh nayi muku* *fatan alkhairi* *Bismillahir* *Rahmanir Raheem* People say, Find good people & leave bad ones but it should be, Find the good in people & ignore the bad in them. Remember No One Is Perfect in This World. πŸ…Ώ *31* Teemah kamar bata ji abinda mummyn ke fad'i ba taci gaba da rera kakanta ahankali kanta akan cinyoyinta. Da mummy taga kamar Teemahn bazata yi magana ba sai ta sakeyin wata maganar da d'an d'agun murya tace " idan zaki bud'i baki kimin bayani toh inkuma bahaka ba ki tashi kiyi tafiyarki" . Daga haka mummy bata k'ara yin wata maganar ba illah ido data zubawa 'yar tata tana kallonta. Ahankali Teemahn ta d'ago kanta suka had'a idanu da mummy, take tausayinta yah kama mummy musamman yanda taga idanun Teemahn sun k'ara girma da jaaa, alamun rashin nutsuwa kaf sun bayyana agareta, sai taji sam bata kyautawa gudan jinin nata ba, bahaka yakamata tayi mata ba tunda bata ta6a samunta da irin laifin ba yakamata tayi mata uzuri, ita kanta sai ta rasa dalilin da yasa ta d'aukewa Teemahn wuta ma, amma yaxatayi, mutunci da darajar y'arta take son karewa bakomai ba. Kauda kai tayi gefe daga kallon Teemahn, yayinda Teemahn ma tak'urawa hannayenta idanu tarasa me zata ce da mummyn, tanaso tayi mata bayani amma sam tarasa abinda zata fad'a. Da 'kyar ta daure ranta tafara magana ahankali cikin natsuwa. " Mum......my kiyi hak'uri dan Allah ki yafemin , kar kiyi fushi dani, ni bansan wayeshi ba, last week na fara ganinsa nima, kuma duk ranar da.......dana fita saina ganshi, shine dakansa yafara zuwa k'ofar makarantarmu amma wallahi mummy ki yadda dani banta6a sauraransa ba yau d'inma bada son raina bane bayadda zanyi ne shiyasa natsaya.............daganan mummy dakatar da ita daga magana inda tace " saurara yah isa". Tsawon mintina biyu kafin mummyn ta mik'a hannunta ta kamo na Teemahn yayinda hakan ya matuk'ar haskaka zuciyar Teemah tare da sanyayawa tasan ko ba komai hakan kad'ai da mummy tayi yana nuni mata ne dacewar mummyn nata ta d'an sauk'o daga fushin data keyi da ita........ Mummy ne taci gaba da fad'in " kina jina ko? Da wuri Teemah ta d'aga kanta alamar " ehhh tanajinta" wa mummyn. " Waye mahaifiyarki? Mummyn ta tambayeta tana kallon fuskarta. " kece". Teemah ta bada amsa a sanyaye " waye ya kamata yasan damuwarki da kuma walwalarki? " kece mummy" " kina ganin zan iya ganin kin hau hanyar da bata dace ba in kuma barki akanta kici gaba dabinta? Kai Teemah ta girgiza tare da fad'in " a 'a ". Toh kin gani ko, ki fahimceni, ba ina nufin k'untata miki ko kuma takuraki bane sam, bani da burin da ya wuce inga kina farin ciki Teemah sannan duk duniya babu wanda zaiso ganin walwalarki sama dani.........amma banda ta wannan hanyar, har yanzu ke yarinya ce, da sauranki, banason tun yanzu ki fara wannan kule-kulen samarin saboda bashi da amfani. kuma ma baki san wani abu ba ayanda kike d'innan duk wani wanda yake ganin sonki yake da gaskiya toh iyayenki zai fara nema ba ya dinga bibiyarki yana tsaidaki a ko ina ba, me sonki bazai ta6a yi miki haka ba ki kiyaye kinji. Kai Teemah ta sake d'agawa alamar toh Sai mummyn tacigaba da fad'in " daga yau karki k'ara kula kowa ki bari ko secondary school d'inma ki k'arasa ta tukunna kinji kafin nan ki,ga awancen lokacin ko auren kikace kina so babu Me hanaki." 'Kasa Teemahn tayi da kanta dan k'arshen maganar mummyn kunya ya bata sosai. Daganan mummyn tasake mata hannu tare da fad'in tashi kije ki kwanta toh. Bata mik'e ba kamar yadda mummyn ta umarceta sai ta jefawa mummyn tambaya kanta ak'asan batare da ta kalli mummyn ba tace " shikenan kin huche mummy" tana murmushi tayi maganar. Mummyn ma murmushin tayi sannan tace mata " zan huce dai idan naga kin kiyaye maganata"! " da sauri ta tashi tana murna har hak'oranta na bayyana afili tace " insha Allahu zan kiyaye mummy" "Allah yasa " kawai mummyn ta'kara fad'i tare da yun'kurin mik'ewa da niyyar shiga bayi. Teemahn ma hanyan fita tayi tana jin ranta fari k'al " Mummy sai da safe " tace wa mummyn tana tafiya ahankali. Mummyn ma na gab da shiga bayin ta amsata da " Allah ya bamu Alkhairi". Koda mummy tagama uzurinta tafitoh ma zama tasakeyi abakin gado tana tunanin hali irin na zamanin yanzu, daga k'arshe addu'a tayiwa 'yarta akan Allah ya kareta ya rabata da sharrin masu sharri yarabata da soyayyar wahala da duk wani al'ummar musulmi. Dan wannan soyayyar wahalan ita tafi lalata al'ummah yanzu, sai kaga matashi ya 6ata lokacinsa da dukiyarsa akan yarinya zai nuna mata so tamkar ya had'iyeta in akayi rashin sa'a itama yarinyar sai ta fara masa mahaukacin so inda wannan son da ta fara yi masan in ba sa'a ba sai ya zame mata abin dana sani agaba. Domin dashi samarin yaudara suke anfani su lalata tarbiyar yara at last kuma su guje su batare da sun aure sun ba. Shiyasa ita tun da idanta yaga 'yarta tsaye da wannan saurayin hankalinta yagagara kwanciyah bawai dan Teemahn bata kai ta tsaya da saurayi, bane a'a kawai dai in so samu ne yazo gida su gana da mahaifinta kafin nan, inda hakan yayi bazata ta6a jin yayi ba dai dai ba ko kuma tayi fargaban ke6ewarsa da y'arta. ( ALLAH YA RABA AL'UMMAR MUSULMAI MUSAMMAN 'YA'YA MATA DA MUGAYEN DAKE CIKIN MAZA,SUMA MASUYIN HAKAN ALLAH UBANGIJI YA SHIRYE SU.). Mummy bata samu tayi bacci da wuri ba aranar dan sai yanzu ta k'ara tunowa da halinda rayuwa take ciki a yanzu, sai ya zamana tana kwance ne amma baccin gaba d'aya ya k'aurace wa idanunta, duk juyin dazata yi kuwa sai ta jefi 'yarta da addu'an kariyar ubangiji haka har kusan k'arfe biyu kafin bacci 6arawo ya saceta. Yayinda Teemah ke can ad'akinta tana ta kwasan bacci cikin kwanciyar hankali, tun lokacin data ga murmushi a fuskar mummynta tajita wasai shiyasa koda ta dawo d'akinta cikin farin ciki tayi addu'a ta kwanta dan bata tare da wata matsala a yanzun tunda mummy ta huce. ***** Tun daga wannan lokacin Teemah ta dinga kiyaye had'uwar su da wancen gayen, bama shiba duk wani wanda ya nemi ya tsaya da ita ko wani abu daban kyakykyawan kallo ma baya samu ballantana kuma lokacinta gaba d'aya. Haka saurayi Imran ya gama iyah biye-biyen da zai yi mata dayaga bata da niyyan sauraransa sai ya hak'ura ya daina kulata dama shima bawai son nata yakamashi sosai bane Imran irin samarin nan ne wad'anda a duk inda auka ga yarinya sai sun kulata musamman ma idan ta birgesu , sai Allah ya taimaki Teemah tak'i sauraransa hakan ne kuwa ya ku6utar a ita daga fad'awa tarkonsa. Tsabar yanda take kiyaye wa ma saboda kar ta ringa had'uwa da kowa ciki kuwa harda imran yanzu kwata-kwata ta daina zuwa ko'ina, duk dayake dama itan ba gwanar yawo bace, daga makaranta sai islamiyah, toh su d'inma yanzu bata fiyah zuwa ba, kasancewar ta gama karatun ta yanzu muraja'ah takeyi da kuma gya-gygyara haddanta, boko kuma tunda aka mata registern weac sai ta daina 6ata lokacin ta wajen zuwa, tana d'an zuwa amma ba kullum ba sai ranar da taga dama tukunna take zuwa, kuma ko zata je d'inma amota ake kaita akuma je adawo da ita gida bata ta6a yadda ta matsa ko'ina batare data hango motar gidansu ba tana fitowa kuwa babu 6ata lokaci sai cikin mota. Wannan dalilin ne yasa ganinta yayiwa imran wahalar gaske shiyasa dan dolensa badan yaso ba ya hak'ura da ita. Mahmud kuwa kusan duk sati sai yazo musu week end inkuwa be samu yazo asati d'aya ba toh satin gaba sai yazo ko kuma alokacin da ya samu dama koda ba week end bane sai yazo, kamar de yadda wannan weekend d'inma ta wuce basu ganshi ba haka nagaba ma. shiru gashi kuma gurin babu network me k'arfi ko sun nemeshi bazasu ta6a samunsa ba. Sai da yayi kusan 3weeks kafin yasamu dakyar yazo shi gida sai kawai suka ganshi tsulum kamar anjeho shi. Mummy da Teemah na zaune Teemah na gyarawa mummy farce kawai sai suka ji sallamarsa. Aikuwa dukkansu bak'aramin farin ciki sukayi da zuwan nashi ba ji sukale kamar sun shekara ne basu ganshiba. Koda mummy tayi masa complaint akan rashin jin nasa dasu ba d'in sai ya bata hak'uri tare dayi mata bayanin rashin network d'in da suk ke fama dashi amma yace yakusan barin wajen ma zai dawo gida inyagama abinda yake yyi acan d'in yanzu zai dawo gida inyaso duk sanda aka buk'ace shi sai ya je shi. " sosai sukaji dad'in hakan dayace d'in musamman ma mummy saboda dama tafison ya zauna agida ko dan saboda insecurityn da ake d'an fama dashi alokacin amm shi Mahmud d'in yak'i yadda da hakan yace shidai yana son zuwa k'auyen. Haka suka cika masa gabansa da kayan ciyeh-ciyeh dan acewar mummyn wai rama yayi sosai kamar bashi ba dan ya bud'e ciki yaci abinci ko zai warware tace idan ma yak'i dawowa wannan karon kam dakamta zata je k'auyen ta dawo dashi gida ta k'araseh da fad'in " hab irin wannan wahala haka. Dariyah sukayi mata shida Teemah mummy kuwa sai ta tashi tana mita ta barsu awurin. Teemah dakanta ta rink'a bashi labarin, imran lokacin da suka fita yawo dashi, shikuwa yayi ta kwasan dariyah yana fad'in village girl

Chapter 14 of 67