Abbas beyi ba yayi shigewar sa ciki.
Teemah kam bata tashi ba sai da ta gama da shayin ta dire cup 'din, tayi zaman jiran sa na mintina, 5, 10 zuwa 16 mins zaton ta ko zai fito ne, ganin shiru har yanzu sai kawai ta mi'ke itama.
'Kofan taje ta duba sai taga ya kuma sake saka lock, inda taga ya 'dau key 'dazu nan taje ta duba amma bata ga komai ba dan haka itama sai ta koma bedroom 'din ta same shi.
Ganin sa tayi kwance yayi 'da'd'daya agado, haushi yasa ta isa gabansa da sauri kamar wacce zata 'dau wani mataki amma tana isa kansa sai taja ta tsaya tace " _Yayah_ !
_Yayah dan Allah ka tashi ka rakani mana, su Ummah fah zasu_ ta _nema na, haka ma Hannah"!_
Shiru yayi tamkar beji ta ba sai tafara bubbuga 'kafafu a'kasa.
Tashi yayi ya zauna, da taga haka sai ta sake fa'din " _Nifah Yayah bacci nakeji kuma ka'ki ka rakani ni atsaye zan kwana_ _ne toh_ ?
" _in zaki iya kwana atsayen bismillah ai ban hanaki ba_ "
Hawaye tafara tana 'ku'k'kuni 'kasa-'kasa.
" _banji ba_ " yace da ita yana kallon ta.
Kauda kai tayi gefe tace " _Allah Ummah fah da su Anty zasuyi ta nemana_ "
'Dan 'karamin tsaki yaja dan harga Allah rigimartan yafara isan shi sai ya fara
'Ko'karin sake kwanciya tare da fa'din
" _Idan bazaki kwanta ba ki kama hanya kiyi tafiyar ki dan ni babu inda zani_ "
Yana gama fa'din haka ya koma yayi kwanciyar sa tare da juya mata baya.
Tsayuwan mintina sun kai ishirin tayi ahaka sannan a hankali ta shiga bayi, wani sabon brush data gani ba'a bu'de ba ta 'dauka tayi amfani dashi sannan ta fito.
'Dayan 6angaren gadon ta kwanta nesa dashi sosai tawani 'dosa na jikin ta kamar ace fita ta zura da gudu.
Abbas kuwa be kula ta ba ko da yaga ta kwanta 'din ma sai da ya bata tazarar kusan rabin hour kafin ya tashi bayan yaji ta sauke ajiyan zuciya .
Kakkashe dukkan hasken yayi sannan ya dawo gaban gadon, ganin har ta fara birgima yasa shi fa'din " _fitinanniya kawai_ "
Space sosai yabada atsakanin su sannan ya kwanta.
ππ»
*HA'KURIN NAN DAI DANA SANKU DASHI SHI NAKE SO KU 'KARA YIMIN, NASAN KUN SHA JIRAN GANIN POSTING AMMA KUKA GA SHIRU, NI KAINA KUNA RAINA....BA NUFI NA IN BA'KANTA MUKU BA KOKA'DAN, PLZ AYIMIN UZURI SABODA ALLAH*
_Comment_
_Vote_
_Share_
*Salmerhn ku ce* π
[10/2, 6:03 PM] Ummiyo: π *CAPTAIN ABBAS* π
By
*Salmerh MD*
Luv storyπ
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
π« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
π«
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
*Bismillahir rahmanir raheem*
_If couples who ar in love ar called *LOVE BIRDS,* then couples who always argue should be called *ANGRY BIRDS*..........._
π
Ώ *77*
Abbas kam ko daya kwanta 'din ma bacci kasa 'daukan sa yayi har kusan 'karfe 12:00 na dare.
Tashi yai yayi alwala ya dinga jero nafilfili tare da addu'o'i sosai sannan ya kwanta.
'Bangaren Teemah kuwa bacci ya mata da'di sosai har bata san lokacin da ta gangaro jikin captain ta shige jikinsa ba.
Har alokacin kuwa baccin be 'dauke shi ba, ganin ta dawo jikinsa ne yasa shi sakin ajiyan zuciya, kanta akan hannun sa ta 'dora, sai hakan ya bashi dama yake sha'kan dadda'dan 'kamshin da jikin ta ke fitarwa da kuma gashinta, a haka bacci yayi awon gaba dasu gaba 'daya.
Da asuba Abbas ne ya rigata farkawa ganin bata motsa ba sai ya sau'kar da kanta dake kan hannun sa ahankali ya mayar mata kan 'karamin sweet design pillow dake kan gadon madadin hannun nasa sannan ya tashi.
Alwala yayi ya wuche masallaci domin gabatar da sallar asubah.
'Karfe biyar da rabi ( 5:30am) Teemah ma ta farka.
A hankali ta bude idanun ta sai taga ita 'daya ce a 'dakin, tashi tayi da sauri ta nufi bayi ta 'dan kintsa kanta a gaggauce sannan ta fito da sauri ko mayafi bata tsaya nema ba ta fice abinta.
Allah ya taimake ta kuwa daya fita abu'de ya bar 'kofan hakan sai ya bata daman fita cikin sau'ki.
Har a lokacin gari be gama yin haske ba amma a hakan da duru-duru ta nufi 'dakin su.
Hannah na kan sallaya bayan ta idar da sallan asubah sai taji an turo kofa an shigo, waigawa tayi sai taci karo da ita
kamar an koro ta ta shigo kanta ko 'dan kwali ma babu.
Tashi Hannah tayi da sauri ta tareta tana murmushi tare da zaro idanu tace " _Ah'ah amaryar Yayah ya haka da sassafen nan kuma kamar an koro ki_?
Teemah ko kula Hannah batayi ba ta wuce kan gado ta kwanta tare da jan blanket ta rufe jikin ta dashi, tana shirin juya wa Hannah baya sai Hannah ta dakatar da ita da fa'din " _Haba Amarya har da nine a fa'dan amarcin_ ?
Sai yanzu Teemah ta bu'di baki tace
" _Hannah plz ni ki 'kyale ni, Allah bansan damuwa ki barni nayi bacci na, ina kam jiya 'kin_ _zuwa nema na kika yi dagangan kika barni na kwana acan bayan sarai kin san halin Yayah da masifa ba rakoni zaiyi ba_ "!
" _Yanzu dana barki kika kwana acan din me yasame ki? Baga shi kin 'debo lada ba, ke dama zaku tafi tare da shi toh miye abin fushi dan kin kwana 'daya awurin sa_ ?
Hannah tace tana kallon ta.
"Bazaki gane ba ne ai Hannah dan ba ke bace"
" _oh o o'oh barni da Bilalu na ni kam kuje can ku 'karata keda wannan dodon mijin naki_ "!
Hannah tayi maganar tana kokarin tashi tsaye.
" _ai naje amma Yayah ya hana ni ganinki sai ma ya wani ce dani bacci kike yi irin ke ga me mijin nan.....nima ai barina kika_ _yi anan 'din na kwana ni ka'dai bayan kinsan su Rauda ba kwana zasu yi anan ba_ _amma kika tafi, in hakane nima nayi fushin mana_ "
'Kasa-'kasa tace
" _Sai kije ai ki gaya masa wannan kuma, dan nima tsintar kaina kawai_ _nayi acan_ "
Juyawa Hannah tayi tana wa Teemahn murmushi irin na tura haushi tace " _may be sace ki yayi babu wanda ya sani_ !"
" _Mtheww_ "
Teemah taja tsaki tare da gyara kwanciyar ta da kyau.
'Karfe shida cif Abbas ya dawo sai ya tarar bata nan, amma be wani damu ba dan dama yasan matu'kar tasan cewa 'kofa abu'de yake toh bazata zauna a dakin ba.
Kai ya jijjiga kawai lokacin da ya ga yanda ta tafi ta bar gadon batare da ko gyara shi tayi ba, yasan duk cikin saurin barin 'dakin ne yasa ko tsayawa ta gyaran batayi ba.
" _Allah ya shirya_ "
Yace a zuciyar sa, da kansa ya kintsa akin sannan ya koma parlour ya 'dau ko wayar sa da tun jiya ya barta anan.
Ogansa ya 'kira suka gaisa inda yayi masa murna tare da sanya masa albarka acikin auren da yayi.
Ya 'kara da fa'din be samu ya halacci bikin ba lokacin yaje duba yaron sa ba lafiya ne shiyasa amma yayi ha'kuri. Godiya Abbas yayi masa dan ya tura masa sa'ko musamman yasa aka kawo mishi.
bayan haka ne suka yanke 'kiran.
Daddy ya kuma 'kira suka gaisa shima yayi musu ban gajiya tare da fatan alkhairi wa auren da suka je 'daurawa.
Yana shirin ajiye wayar sai ga 'kiran Saleem kamar yasan yana kusa waya a dai dai lokacin, domin tun jiya yake 'kira amma Abbas 'din be 'dagawa.
Yanzun kuwa 'dauka yayi ya kai kunnan sa tare da yin shiru dan yasan meze biyo baya, ai kuwa Saleem 'din cewa yayi " _Girman ka ne yalla6ai ,gaskiya najinjinawa zumuncin ka_ "
Shi kansa Abbas yasan be kyauta ba amma sai ya basar yace dashi
" _Ya akayi ne Saleem ka 6uya fah?_
Ya fa'da a wani tsare.
" _Kai ka bari kawai maza sai a hankali wallahi, amma gaskiya ni banji da'din abinda kamin ba, ya za'a yi auran ka amma kawai sai de inji anyi ba wani labari_ !"
Shafo kansa yayi tare da fa'din
" _ohh sorry Saleem abin ne yazo unexpected in just 1 week Daddy ya yanke lokacin shiyasa, amma agafarce ni"_
Saleem cemasa yayi
" _Bakomai Cpt. yawuce girman kane ai, me ake shirya mana ne ina fatan za'a yi Sword_ _crossing kasan mu ta nan muka fi 'karfi_ "
Juya kai Abbas yayi yace " _gaskiya bawani COS da za'a yi nima yaushe na nutsu Saleem, an shirya a Rivers amma inajin ba zai yiwu ba dan bazan samu zuwa ba. Amma may be ayi dinner yau in ya yiwu a nan Abuja inaga shi ka'dai ma ya isa nagaji da hayaniyan nan Allah gaba 'daya Saleem_ "
" _Haba mana Captain......ko da yake bari sai na iso kawai nima da yaddar Allah yau_ _zan shigo_ "
Cewar Saleem.
Abbasa ma sai yace masa
" _okay, ba matsala, sai ka iso_ "
Yana cire wayar a kunnen sa yaja tsaki aransa yace " _bawani crossing na sword da za'a yi, haka kawai gardawa daku_ _ku saka yarinya atsakiya kuna faman 'karewa halittar jikin ta kallo_ _a banza_ "
*****
Ba Teemah ta tashi daga baccin ba sai 'karfe tara na safiya ta gota, tana tashi kuwa Anty kamar jira take tazo ta ha'da mata ruwan wanka na ha'din turare tace tayi dashi.
Zama tayi bayan shigan Teemah wurin wankan ta tallafi kanta da hannayen ta duk biyu tana tunani.
Anty na jin 'kunci azuciyar ta fiye da zaton mutun musamman da tasan cewa yau Abbah zai yi aure abinda be ta6a ko kwatan ta zancen shi ba tun farkon rayuwar su har Allah ya kar6i ran Mahmud sai gashi Allah cikin ikon sa rana tsaka kamar wasa ana shirin 'daura auren sa da wata daban.
Bazata ta6a fasa yi musu fatan alkhairi da zaman lafiya ba, dan koma menene yafaru laifin tane, she caused everything, dan haka ita a yanzu bata da wani buri illah taga 'karshen rayuwar ta tayi kyau kawai fatan ta Allah ya fe mata kurakuran ta na baya.
Tana zaune tana tunani har Teemah ta fito daga wanka bata sani ba.
Teemah tayi mamaki sosai da taga ta 'kira ta har sau biyu amma bata amsa ba hakan kuwa yasa ta matso dab da ita ta furta " _Anty_ "!
Da 'dan 'karfi.
Firgigi tayi tare da sakin ajiyar zuciya kana tace
" _har kin gama wankan ne? Kinyi da kyau kuwa?_
Tayi maganar tare da 'kwa'kulo murmushi ta sanyawa fuskar ta.
Cikin sanyin jiki Teemah ta amsa mata da fa'din "eh _h nayi mei kyau, Anty me yafaru ne naga kinyi shiru kina tunani?_
" _Hmm, bakomai Fatee na kawai ina tuna halin rayuwa ne yanda duniya ke juyawa damu, yau gashi Fateemah na ta sake zama matar wani karo na biyu"_
Anty ta tayi maganar tana mai sunkuyar da kanta kasa bata so Fateemah taga rauninta koka'dan musanman da yanzu ta tuna da marigayi gudan jininta Mahmud.
Teemah kam tsayawa kallon ta tayi kawai dan sam bata yarda hakan shine a zuciyan Anty ba, domin 'karara damuwar ta ta nuna a fili kan fuskar ta.
Ganin da Anty tayi Teemah tayi shiru sai ta kamo hannun ta dawo da ita gaban mirror ta zaunar da ita kan stool tare da fa'din
" _Zo zauna in gyara miki gashin kin nan kafin mai kwalliyar ki tazo_ "
Teemah yanzun ma shiru tayi ba ta furta komai ba damuwar ta be wuci ganin sauyin yanayin Anty datayi ba, tana so tasan ainihin dalilin hakan amma tasan Anty idan ba tayi niyyah ba bazata ta6a sanar da ita ba, inda tayi niyya ne da tun ma kafin ta tambaya da da kanta zata sanar da ita.
Tsinkayar muryar Antyn ta tayi tana fa'din " _Yarinta ta girma 4d second time, nauyin auren ya sake hawa kanki, amma kin san me nake so dake Mamana_ ?
Kai Teemah ta jijjiga mata ahankali alamar " _ah ah_ "
Rage murya Anty tayi yanda bakowa ne zaiji su ba sai in kana kusa cikin natsuwa tace
" _Kinsan Yayanki Abbas shine mijinki ko?_
Ahankali Teemah ta bata amsa da fa'din " _ehh nasani Anty_ "
Anty cewa tayi
" _Yauwa uwata, ina fatan zuciyarki ta kar6i hakan baki ji cewa an takuraki_ _ko shiga hakkin ki ba ko_ ?
" _Ah ah banajin hakan koka'dan Anty_ "
Da sanyin muryarta ta bata amsa.
" _Alhamdulillah_ "
Anty ta fada harda lumshe idanu dan yanda taji da'di da kar6an auran da Fateemah tayi.
Afili kuwa Antyn cewa tayi.
" _naji dadi Fateemah, nayi farin ciki sosai, ni kaina na rigaki kar6an auren nan tun ma kafin a ha'da shi, da kaina Fateemah na hangi 'kauna_ _da kishin ki tattare da Abbas kuma nasan da iznin Allah_ _rayuwar auren ku sai ta bada sha'awah watarana!, inaso koda kin koma gidan auren ki dan Allah Fateemah ki ri'ki_ _ibadar ki kinji, ki ro'ki Allah akan komai zai miki maganin koma menene, karki yadda ki kai kukan ki wurin kowa koda kuwa meze faru dake domin kuwa Allah kadai_ _ne mai taimakon da babu wanda ya isa ya miki makamancinsa_ _sai shi din nan dai Allah mabuwayi, Fateema rayuwa ta aya ce awurin_ _ki ai nasan kinsan duk abinda yafaru dani, 'karshe wa gari ya_ _waya?_
_Niice da kaina nayi dana sani nayi Allah wadai da halina!Mijin ki mijinki ne Fateema kuma_ _sirrin kine, 'yan uwan sa kema nakine dan ma kinga ai duk dangin_ _mijinki jininki ne dole ne ma ki so su koda babu aure a tsakanin ki da Abbas ballantana_ _kuma aure ya 'kara ha'da ku, ki so su ki kauna ce su sosai, ki girmama 'karfin_ _zumuncin dake tsakanin ku kar kiyi watsi da shi"._
" _Nasan auren ku auren ha'di ne na iyaye wanda za'a ce dukkan ku ba shiri yasame ku, amma dukkan ku kunyi_ _biyayya kuma na matukar jinjina muku, amma ki sani dole ne sai kinyi ha'kuri dan auren ha'di na tafe ne da wasu irin rikitattun abubuwa_ _wa'danda sai wanda ya ta6a faruwa dashi ne ka'dai zai gane su, ba zance bakwa son junanku_ _ba dan ban shiga zu'katan ku nagani ba amma nasan dole ne sai kin fuskanci wani 'kalubale daga mijinki wanda ha'kuri ne ka'dai_ _zai iya magance miki su, Fateema kiyiwa mijinki biyayya, bansan taurin kai da rashin kunya banda_ _musu da jayayya dashi kinji? na tabbata idan kika ya'ki zuciyar ki kika kuma dogara ga_ _Allah komai zai zo miki da sau'ki amma sai kin daure sosai kinji?_
Ahankali ta 'dagawa Anty kanta dan duk kalaman Antyn sun sa jikinta yayi sanyi matu'ka, duk abinda Anty ta fa'da gaskiya ne sai dai ita can 'kasan zuciyarta take jin ta shiryawa zama da shi a kowani irin hali.
Anty cewa ta sakeyi " _Yauwa uwata Allah ya miki albarka, yasa haske arayuwarku har illah masha Allah_ "
A saman la66a Teemah ta amsa da fa'din " _Ameen_ "
" _Bansan me yasa nake jin da'din wannan auren naku ba har azuciya ta ba, inaji ajikina da iznin Allah auren ku akhairi ne,dan haka_ _ki bawa mijin ki kulawar data dace kinji_ ?
Kai ta 'dagawa Antyn tana me sake sunkuyar da kanta.
Anty data fahimci taji kunya sai ta yi murmushi kafin tasake yin wata magana kuwa sai ga mai shirya Teemah ta iso da sallamar ta abakinta tare da wata mata abayan ta.
Amsawa sukayi dukkan su Anty sai ta mi'ke tare da gabatar musu da kayan da Teemah zatayi amfani dashi a yanzun sannan ta bar 'dakin.
Abbas wanka yayi, ya shirya cikin wani shadda golden brown, ajikin babbar rigan kawai akayi aiki da coffee 'din zare wanda ya 'kara haska kayan sosai hakama a jikinsa sai annuri yake yi da sheki sosai kayan ya kar6i jikinsa, yana shirin fita kenan sai ga abokansa sun shigo, take kuwa suka fara yi masa tsiya akan tun jiya ya tafi ya 'kyalesu ko dai amarya ce ta ri'ke shi.
Shiru yayi musu kawai har suka gama be kula su ba, dan shi be iya irin wasan nan ba be ma san me ze ce dasu ba.
Sai da sukayi suka gaji har sukayi shiru, daga baya suka fara hira normal sannan ne yasaka bakin sa aka 'dan ta6a hirar da shi.
Anan aka kawo musu kayan break fast sukaci gaba 'daya still suna masa tsiyan na gaba sai agidan amarya.
Wannan karan kam murmushi Abbas yayi dan indai akan girki ne bazata bashi kunya ba saboda yasan Mummy bata barta haka nan ba.
'Daya daga cikin su ne mai suna Auwal ya tashi ya shiga ciki dan yana so yayi using bathroom, ai kuwa anan yaci karo da pant 'din Teemah da ke shanye a bathroom 'din,
har Allah-Allah yake kuwa ya fito dan ya baza kanu, aikuwa yana fitowa yaje gurin Abbas ya bashi hannu tare da fa'din " _mazaah!!, ashe angon cewa kayi yau din shiyasa naga kana ta shan 'kamshi!_ "
Kallon _me kake nufi_ yayi masa ha'de da harara yace " _ban son iskanci Auwal toh haramun nayi? Me ma kaje yi min acikin 'daki?_
Dariya duk sauran suka kwashe dashi suna nuna Abbas 'din, sosai yaji haushin hakan duk dama abinda suke zato 'din be faru ba amma ai wannan sirrin sa ne damuwar sa ma shine ya akayi har wannan tunanin yazo ran Auwal har haka, yariga yasan kayan ta data cire jiya ba'a fili yake ba sannan shi be ga wani abu a'dakin da zai sanya har mutun yayi masa wannan tunanin ba.
Basu wani da'de bama suka tafi, Abbas be bisu ba.
Suna tafiya kuwa yayi hanzarin shiga bedroom 'din yafara investigating 'dakin, still shi be ga komai ba dan hatta su bangles da earings 'dinta da sauran su ma ba'a fili suke ba balle yace ko dan sune tunanin sa ya bashi cewa wani abu yafaru, sai dai ko in Auwal bincike yayi masa har yaga wani abin mace shiyasa yayi masa wancan tonon sililin...
Tunaninsa ya tsaya ne lokacin da ya bu'de 'kofan bathrum idanunsa suka sau'ka cak akan jan pant 'din ta dake shanye tun jiya abayin.
Wani 'kululun ba'kin ciki, haushi da takaici hade da kishi ne ya tokare sa, sai yanzu ne ya fahimci asalin abinda Auwal ya gani da har tunanin can yazo masa.
Tsaki yaja tare da jan 'kofan bayin ya koma parlour.
Waya ya 'dauka ya 'kira layinta ta kuwa 'dauka dan lokacin already an gama yi mata kwalliya tana zaune da wayar a hannun ta.
" _Hello_ "
tace ahankali.
" _Me kike yi_ ?
Yace da ita a kausashe.
itama tace
" _Ba komai_ "
" _maza ki zo yanzun nan karki 6ata min lokaci_ "
Be jira jin amsarta ba ya ending call din.
Teemah baki ta tura gaba ta kalli inda Hannah take tsaye tana rage kayan jikinta sai kuwa suka ha'da idanu, Hannah da bata gani tayi shiru sai tace
" _Ya daga amsa waya kuma kin fara fushi ince dai lafiya?_
Amsa ta bata da fa'din
" _Ba Yayah bane yace wai inje_ "!
Hannah sai cewa tayi
" _Dodo yayi kira kenan, sai ki tashi ki tafi ai kinsan angon naki sai ahankali inajin be gaji da ganin ki bane kika gudo"_
Kalan tausayi tayi tace
" _Dan Allah Hannah kije ko kuma 'kira shi kice masa 'kafata na ciwo....._
Tare ta Hannah tayi da fa'din
" _Ah ah sai de ince masa 'kin zuwa kikayi..._
Sake marairaicewa Teemah tayi tace
" _Haba dan Allah Hannah_ "
" _ni baruwana kinga tsakanin ku ne, yanzu fah mijinki ne kun fi kusa, daina sani a shirgin ku please_ "
Tana maganar ta nufi bathrum.
" _Hannah toh dan Allah tsaya ki raka ni mana_ "
" _Daya 'kira 'din yace miki kije ke da Hannah ne, i thought amarya_ _ka'dai ya nema_ !
Tana gama fa'din haka tashige abinta tana dariyar mugun ta.
Teemah sharewa tayi kawai ta tashi ta wuce wurin Mummy dayake dama tun safe basu ha'du ba, Mummy da bata san me ake ciki ba sai ta zaunar da ita ta ringa yi mata nasiha kawai akan biyayyar aure.
Anan Hannah tazo ta same ta dan tana gama wankan ta taho 'dakin da Mummy take anan take shiryawa tunda aka fara biki, sai kuwa taga Teemah tawani bararraje tana hira.
Hannah cewa tayi
" _har kinje 'kiran Yayan kin dawo ne_ "
Da gangan ta tambaya dan tasan it's hardly ace Teemah taje batare da tayi taurin kan nan nata ba.
Harara Teemah ta banka mata tare da ha'de ranta.
Muryar Mummy tajiyo tana fa din " _na me kenan_ ?
'Kasa Teemah tayi da kanta ta rasa me zatace dan tuni ta hango 6acin rai a fuska da muryar Mummy, gashi ita ba kowani lokaci ta iya shirya 'karya ba ballan tana ta fidda kanta.
Mummy ne tasake fa'din
" _Teemah karki kuskura kice min Ya 'kiraki ne baki je ba kika yo nan"_
"' _Karyan Hannah ne fah...Mummy naje ni... tun 'dazu"!_
Tayi maganar kamar zatayi kuka.
Mummy juyawa tayi ta kalli Hannah ta ce " _da gaske ne wai Hannah abinda ta fa'da_?
Hannah sai da ta kalle ta suka ha'da ido sai ta kawar da nata idanun tace
" _Bawani nan Mummy yanzun nan ne fa dazan shiga wanka ya 'kiratan_ "
Mummy dawo da kallon ta tayi wurin Teemah tace " _na 'kirashi na tambaye shi kin yarda_ ?
Da sauri ta jijjiga kanta alamar " ah ah"ta 'kara da fa'din " _Allah Mummy Yayah allura yake sawa ayimin fah_ "
" _Bana son maganar banza Fateemah alluran saboda lafiyar waye akeyin ta?_
Shiru Teemah tayi ta sunkuyar da kanta 'kasa tana ta juya hannayen ta cikin juna.
" _Ina tambayarki_ "!
Mummy ta daka mata tsawa.
Afirgice tace " _saboda... nii....ne_ "
" _Toh 6ace min a'daki na tunda ke kullum kunnen ki bana jin magana bane kije kiyi tayi, kuma saura inji cewa baki jeba_ "
Tashi tayi sum-sum ta kama hanya tana bankawa Hannah uban harara kamar idanun ta zasu fito.
Hannah kam sai gwalo take yimata tana 'karawa har suka daina ganin juna.
Aranta tace " _kiyi ha'kuri 'yar uwata ina sonki sosai kuma inason ganin kina farin ciki, amma nasan matu'kar kika ci gaba akan haka toh bazaku shirya da Yayah ba ni kuwa *BURINAH* inga kun gyara auran ku kun rayu kamar kowa"_.
Fitan Teemah kenan sai ta ha'du da Anty, take ta jefa mata tambayar ina zata kuma haka?
" _ba Yayah bane yace wai inje kuma fah Anty allura yake sawa ayi min_ "
Cikin shagwa6a tayi maganar tana turo baki.
Murmushi Anty tayi tace da ita
" _Habah kuma yarinyata da akeyi miki alluran bakiga kin fi samun sau'ki bane, maza kiyi_ _sauri kije kar ki 6ata masa lokaci_ "
Haka ta juya ta tafi tana 'kun'kuni har ta isa.
Ciki-ciki tayi sallama haka kuma shima ya amsa mata ahankali.
'Karasowa ciki tayi sai ta tarar dashi hakimce a kujera tamkar wani sarki, ba 'karamin kyau yayi mata ba amma sai ta ta6e baki tare da kawar da kanta gefe.
Inda yake ta'karaso ta ce " _ina kwana Yayah?_
Abbas kam wani yanayi na 'kauna da shauki ne yayi nisan tafiya da shi hakan yasa be ma ji lokacin da ta gaishe shin ba, ita kuwa bata 'kara ba sai ta ci gaba da tsayuwan ta.
Tunaninsa na dawowa sai ya kauda da kansa batare da ya sake kallon ta ba yace " _kinyi breakfast ko_ ?
" _Uhmm_ " tace dashi.
" _Me kika ci_ ?
" _Chips da...._
Kafin ta 'karasa ma yatare ta da fa'din " _D'auko maganin ki ki kawo ingani_ "
Wucewa tayi cikin bedroom 'din nasa ta 'dauko maganin saman drawer ta kawo masa.
Maganin ya 6alla ya bata ta kar6a tasha, har zata tafi ma ganin cewa dan maganin ne ya kirata kawai sai taji yace da ita ta wuce bathrum ta 'dauke wannan abin nata da bari kuma karta kuskura ta sake amfani dashi, in kuwa ta 'kijin magana shi da ita ne.
Zuwa tayi ta dudduba dan shaf ita ta manta da pant 'din ta nan, tana gani kuwa ta hau gungunin " _ina ruwansa da abuna toh, dama me yakai idonsa wurin da har ya gani._ ?
Haka tazo ta wuce shi tana tura baki.
Shima binta yayi da kallo harta fita, sai ya jijjiga kansa.
*****
'Karfe 11:07am na ranar aka 'daura auren Abbah da amaryar sa Halimatus Sadiya, 'kanwa ga Hajiya Aisha matar abokin sa da tayi siyayyan kayan auren Mahmud.
Anty Sadiya 'yar kimanin shekaru 31,kuma bazawara ce da mijin ta ya rasu ya barta da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 45 Chapter of 67