Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
biyu da tsayuwar motar sannan taga anbud'e marfin motar,ta 6angaren da suke tsaye,ita da habibun. "Wow" Tace azuciyarta tareda kwalalo ido waje tana kallonsa. Gani tayi yayi kyau da sky blue d'in shaddar dake jikinsa tare da farin glass a idonsa,iyah abinda ta lura dashi kenan ajikinsa amma ba k'aramin kyau yayi mata ba. Abbas kuwa tun tsayu warsa agurin yake kallon su hannunsa nakan stairy,kallonsu yake musamman ma ita, tare da mamakin tsayuwar uwar me take yi awurin,gashi jikinta sanye da uniform. Dayake tinted glass ne da motar shiyasa babu wanda ya hangosa,motar daddy ce dayafi amfani da ita,duhun glass d'inne yahana su ganshi ,duk da lura da yayi duk hankalinsu naga motar dayake d'inne da alama duk ak'age suke suka fitowar tasa. Hakan ne yasa shi fitowa. Yana fitowa bayan ya maida k'ofar ya rufe, gurinsu yanufah direct,hannu yad'aga sama, tana ganin haka ta rintse iso da k'arfi,dan atunaninta sauk'ar mari zataji,murshi yayi dayaga yanda ta tsorata d'in,sai ji tayi yakam kunnanta irin yanda daddy yamasa,harya fara tafiya sai kuma yajuyo,yah wullo wa Habibu key d'in motar,sannan yacigaba da tafiyah. Cafe key d'in Habibu yayi sannan yacigaba da kallon bayansu tunani yake aransa taya akayi wannan yazama Abbas? Abbas ai bay kyashin yiwa mutane magana,amma wannan sai zafin kai,d'azu da kar6ar abu zaiyi awurina ai yamin sallama,amma ganshi yanzu ko kallon arzik'i ma bansamu ba,ballantana sallama. acewarsa fah😏 Teemah kuwa Zafi taji kamar tayi tsallen wahala,harda guntun kwallarta,shikuwa k'in sakinta yayi har se da ya isa d'akinsa yatura k'ofar bayan sun shigo,sake kunnan nata yayi,sannan ya tsaya agabanta yana k'are mata kallo. K'asa tayi da idanunta tare da turo baki gaba,hannunya d'aya kuma na sama kan kunnan tana shafawa ahankali, "Mugu" tace acikin ranta Uniform d'in jikinta yasakr kallo,dayake yamma ne,yasan sai dai na islamiya,. Gyara tsayuwa yayi yan kallon nata sannan yace "Anan ake islamiyar ko? Kanta ta jijjiga batare data d'ago ta kalleshi ba,dan muryarsa har cikin kanta take jinsa,lion voice ne da shi mai ratsa jiki,musamman yanzu da yake maganar da ita ,sosai yanayin muryar tasa ta ratsa ko ina ajikinta.take tsoronsa ya shigeta. "Toh tsayuwar me kike yi agun kuma? Yasake jeho mata wata tambayar. Kasa magana tayi dan wannan tambayar bayyanan niyar amsa take da buk'ata.ita kuma sam bazata iya furta komai ba. Yawan hawayenta taji yaqaru akan d'an guntun dayake mak'ale tun d'azun,ta ke suka fara sintiri akan fuskarta. Kallonta yayi da mamaki aransa yace "lallai yarinyar na bazata canja ba" Juyawa yayi yafara tafiyah sannan yace "jeki" Tanajin haka ta juya da sauri ta fice daga d'ajin. Gurin mummy taje ta sameta a babban parlour, fad'awa jikin mummyn tayi tana kuka mai sauti,hankalin mummyn ba k'ara min tashi yayi ba da jin kukan da Teemahn keyi ba. Dan a zatonta ma tuni Teemahn ta tafi islamiyar. Dakyar ta samu tayi shiru sannan ta tambaye ta dalilin kukan, bud'e baki teemah tayi sannan tace '"bawan nan yayan bane yakama yayita jan kunnena ba,kuma ni babu abinda namasa". Tsaki mummyn taja kad'an sannan ta kauda kanta daga kallon temmahn "Yah kyauta ai,bake rashin ji ba" Shine harda zuwa kisani agaba da irin wannan kukan Teemah"? Ke kinmanta d'azu ba dariyarsa kika yi tayi ba dan iskanci"? Baki teemah ta turo gaba jin mummy bata goyi bayan ta ba. "Toh islamiyar fah? Mummyn tsake tambayarta. Teema ta bud'e baki zatayi magana kenan sai idonta ya hango mata mutum atsaye daga bakin k'ofar shigowa parlourn. Suna had'a idanun da ita sai ya ce "Assalamu alaikum" Mummy ce kawai ta amsa masa sallamar tasa.Teemah kam kyautar harara ta bashi,amma sai yayi kamar bai gani ba,hakan yabata damar cigaba ta hararsa har ya iso gefensu ya zauna. Gaida mummy uayi bayan ya zauna,daganan suka cigaba da hirarsu da mummy babu wanda yasake bi takanta. Haushi kamar ta sa hannu ta buge sa,abinda ya zaunar da ita ma jin da tayi suna hirar su Hannah ne lil sister d'inshi,da badan hakan bama da tuni tabar inda suke d'in, Ji tayi hirar tafar dawowa kanta,abin sai yafara bata haushi,wai ita ai ta tsaya canje canjen makaranta ne shiyasa har yanzu bata yi nisa ba ga Hannah nan tana SS2 yanzu,mummy ne tafad'i hakan jin datayi cewa wai Hannah na SS2 daga bakin bakin Abbas. sannan tak'ara da fad'in ai Daddyn naku ne ma dayake biye ta wlh duk laifinsa nake gani" Ga dukkan alamu dai wannan abin ya sosa ran mummy, dayake daman tun sanda sukeyin abin tana tsananin jin haushi,ganin cewa duk makarantar da aka kaita sai tace wai bai mata ba,ba taso,daddy kuwa yabiye mata ya canja mata wani da kyar akasamu ta zauna awannan d'in da ke yanzun,kusan makarantu hud'u tacanja. Teemah najin haka ta mike ta fice daga d'akin afusace. Dan tasan anta6o mummy kenan indai akan makarantar tace. Binta suka yi da kallo dukkansu kowa da abinda ke ransa har ta 6acewa ganinsu.sannan suka ci gaba hirarsu. Ita kuwa tana shiga d'akin ta fincike hijab d'in da ke kanta tare da rigar sanna ta cire wandon ma duk ta watsar dasu,sai kace sune sukayi mata laifin. *share pls,nd ur* *comment is needed* πŸ‘ŒπŸ» *in ba* *haka ba zan d'au* *hutu* . *Salmerh* 😍 [10/2, 5:53 PM] Ummiyo: πŸ’• *CAPTAIN ABBAS* πŸ’• By *Salmerh MD* Luv story😍 *Wattpad @* *Serlmerh-md* πŸ’« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS* πŸ’« We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all..... *DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO* Dedicated 2 *Safiyyah Aliyu* *Wakili* . & *Khadija candy* I heart u guys tnx 4 ur luv nd suppoart_ 😍 *Bismillahir* *Rahmanir Raheem* A Mistake increases your experience & experience decreases your mistakes. You learn from your *mistakes* and then others learn from your *success* .πŸ‘ŒπŸ» πŸ…Ώ *9* Zama tayi abakin gadonta daga ita sai pant da bra ranta amatuk'ar 6ace,asama take jin ran nata,"wai wannan shine yah Abbas d'ina kuwa anyah? "Ayanda mummy take fad'a min ai yah Abbas baya min mugunta,amma shi wannan daga zuwansa gidanmu har ya iyah bayyana nashi salon muguntar,kamar fah yasan abinda nafi tsana kenan arayuwa ta wannan jan kunnan,don ko mummy duk ranar da ta min ma wuni nake bana kulata,shiyasa ma ban fiyah yin abinda nasan zai sa ta min irin hakan ba,sosai nake kiyayewa,Ai kuwa da daddy zan had'a shi ya ramamin abuna. Murmushi ne ya kwace mata dalilin tunowa datayi da sanda daddy ke jan kunnansa, "Allah shi kara" Tace afili.harda cije bakinta irin na muguntan nan. Daga nan ta ta shi ta nemi kaya tasaka sannan ta fito tasamu Mummy da Baabah Lami a kitchen ko kulasu ba tayi ba,ita adole fishi take yi an mata ba daidai ba,mummy ma ko inda take bata kallah ba,Sai Baabah Lami ce ma tayi mata magana,ita ma maganar tata k'ara 6ata ran Teemahn yayi, dan cemata tayi "Fatun daddy ya akayi ne naga kinata shan k'anshi haka? Bata kulata ba sai baki data k'ara turowa,dan ta tsani wannan sunan wai "Fatu," Fuuu......ta juya tafice daga kitchen d'in aikin da batayi ba kenan,daman mummy ce tace matuk'ar tana gida lokacin yin girki yayi toh dole ne tashiga kitchen d'in ayi da itah,shiyasa yanzun ma ta zo,toh amma tun kan ma takama aikin Baabah Lami ta kunnata dayake daman a 90 take,kuma dama tun asali ta tsani "fatun" nan, abakin Baabah Lami kad'ai tafara jinsa kuma suna yawan shan rigima da baabah Lami d'in akan sunan,kwanaki harta da'n daina fad'ar sunan sai gashi kuma shi yau kuma ta tuno dashi,kawai sai ta fake da hakan k'ara gaba abinta,dama ba son yin girkin takeyi ba tsoron mummy yasa tafito. Murmushi mummyn tayiwa Baabah Lami tana kallon fuskar ta tace "kin k'ara rura mana wutar kuma ai inaga" "Aikuwa dai,naga alama"cewar Baabah Lami d'in tana d'an dariyah. Mummyn ce ta k'ara da cewa "fushi takeyi wai yanzun da yayanta,amma inaga abin kowa ma bai tsirah ba." Murmushi sukayi dukkan su,daga nan suka ci gaba da sabgoginsu akitchen d'in suna yi suna d'an ta6a hira jifa-jifa. Basu k'ara had'uwa ba sai bayan isha'i,dasuka zo cin abincin dare,Nan ma mummy tace taje maza tak'ira shi. Tana jin abinda mummy tafa'da ta fara bubbuga k'afafu ak'asa,tana fad'in "haba mummy shi wai bazai zo da kansa ba sai ank'irasa"? Tsawa mummy ta daka mata "bana son rashin kunyah Teemah,aiken nawa ne bazaki ba ko kuwa shid'inne kika fi k'arfin ki k'irashi" Tana jin haka ta juya ta fara tafiyah zuwa d'akin nasa, "mthww" mummy taja tsaki biyan tajuya d'in, ita kuwa haushi kamar ya kasheta sai mita takeyi k'asa-k'asa ahankali "wlh mummy duk so take yi ta zubar min da ajina agun wannan mutuminπŸ˜…,so take ya raina ni gaba d'aya.(kujimin yarinya fahπŸ€”πŸ˜) Bakinta kuwa kamar na 6era tsabar yanda ta turo shi gaba. Duk da ran mummy a6ace yake,amma bata kasa fahimtar yanayin Teemahn ba,kuma duk tasan bazai wuce akan abinda yafaru d'azun bane,take wannan abun. Haka taje k'ofar d'akin ta tsaya daga waje tana knock in d'in k'ofar,jitayi babu wanda yace mata ko cikanki ne,sake bugawa tayi da 'dan k'arfi,amma still shiru taji, babu alamun ma anjita. Hakan yasa ta tura k'ofar azuciye,tashiga cika batare ma da sallama ba. Gani tayi yanzun d'akin da haske ba kamar d'azu da ta zo ba. Ta6e baki tayi tare da rarraba idanu ad'akin dan bata ga alamar mutun ba aciki.Komai nakin tsaf dashi tagani,babu gurin data isa ta kushe ad'akin,sai uban k'anshin turarensa mai dad'in shak'a. Ita kuwa dan iskanci sai ta d'aga hannunta ta toshe hancinta da su,harda ta6a fuska,adole wai turaren bai mata ba ita. Dai dai shima yabud'e k'ofar d'akin ya shigo,ga mamkinsa sai yaga tana toshe hanci,k'arasa shigowa yayi a mamakance idonsa na kanta,so yake yaji menene dalilinta na toshe hanci a muhallinsa,tunda yasan bai bar komai ad'akin da zai sa har aji wani abu makamancin wari ba,dan ko bayin dake cikin d'akin ma atsaftace yake,ko abinci inta kama sai ka iyah ci aciki,balle ma shi bayaga wanka babu abinda ya had'a sa da bayin tunda yazo gidan sai ko alwala. Bin d'akin ya sakeyi da kallo akaro na biyu sannan ya kalleta, wuri-wuri tana rarraba idanu,taku yad'anyi kad'an zuwa inda take,tana ganin haka tayi baya itama da sauri,ganin haka sai ya tsaya a inda yake d'in. "Wani isakanci ne yasaki toshemin hanci ad'aki?" Dan sosai abin yaba shi haushi,ba k'aramin cin fuska bane yin hakan ga wani,babu wanda zai so ace anji wani abu da ya danganci hakan a inda yake rayuwa,balle mutun irin Abbas da tun tashinsa da tsafta aka sanshi,tun yana yaro ya tsani k'azanta..................... "Ba tambayarki nakeyi bane" Ya fad'a atsawace dan jin bata amsa masa tambayar farkon ba. Muryarsa na razana ta amma,dan jikinta har rawa ya fara,amma haka ta dake ta bashi amsa da "d'akin yana wari ne" Ranshi a6ace yake amma baisan sanda ya zaro idanu waje ba tsabar mamaki, "Wari kuma.......? "Warin me toh? Ya tambayeta. " *Turare* " Ta bashi amsa kanta tsaye. Tsabar takaici kasa yin magana yayi,illah kallon daya bita dashi,amma dai yad'an ji nutsuwa datce warin turare ne,abin takaici kuma har yanzu bata bar toshe hancin ba. Gani da yayi still tana rufe da hancin ta ai sai ya yunkura zai kamota,tana ganin ya nufota kuwa ta juya baya,dagudu tabar d'akin,cikin sa'a ma abud'e tasamu k'ofar,dan mamakinta ne yasa daya shigo ko k'ofar bai mayar ya rufeta ba,shiyasa tasamu sauk'in gudu,fit ta fice abinta batare da ta tsaya jan k'ofar ba. Sai da ta tsaya wani lungu ta daidaita numfashinta kafin ta isa wurin mummyn, "Mummy wai yana zuwa" "Uhm" mummyn tace sannan ta k'ara. Da fad'in yakin da'de, "Bansame shi ad'akin bane mummy" tafad'a kamar wata mumina, dan ji take ranta wasai yanzu dalilin wannan abin data yimasan. Shikuwa bayan fitar ta ad'akin sai yaje ya tura k'ofar tare da fad'in "useless kawai" sanin da yayi wa kansa, k'anshi ko wari ko yaya suke kuwa sai ya jiyosu indai wad'annan abubuwan ne,bata isa ta nuna masa jinsu ba. Dawo wa yayi cikin d'akin yatsaya ya sake k'arewa ilahirin d'akin kallo,sai kuma yayi murmushi, "zan had'u da ke ne yarinya" afili ya fad'i hakan sannan ya ka'rasa bakin gado ya ajiye wayarsa. Shima ya zauna ya fara 6alle botiran rigarsa, har ya kusan 6allewa sai kuma ya tuna k'ila aikota akayi, tunda yanzu lokacin cin abincine agidan kamar yadda yasani tun ada, take sai ya mik'e ya fice daga da'kin. Ya nufi main parlour................. Drop ur comment pls readers🀞🏻,inkuna son ku faranta minπŸ™ˆ *Salmerhn* 😍 ku ce πŸ‘ŒπŸ» [10/2, 5:53 PM] Ummiyo: πŸ’• *CAPTAIN ABBAS* πŸ’• By *Salmerh MD* Luv story😍 *Wattpad @* *Serlmerh-md* πŸ’« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS* πŸ’« We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all..... *DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO* Dedicated 2 _Friendy like no_ _other_ ....... ( *Mamee Hafsat* *Ndahi) I hrt u baby* *girl* ._ 😍 *Bismillahir* *Rahmanir Raheem* Ego is just like a dust in the eye ….... without clearing the dust you can’t see anything clear........,. *so clear* *the ego* *and see the world.* πŸ…Ώ *10* A dinning ya same su gaba d'ayansu har daddy amma basu fara cin abincin ba har yanzu,da alamu jiransa suka tsaya yi. Teemah na ganinsa tafara zare idanu tayi k'asa da kanta sarai tasan tayi masa laifi kuma bata kyauta ba,don babu wanda zai so a kushe masa muhallinsa ballantana ma ita na raini tayi. Ko kallon inda take ma baiyi ba yaja kujera ya zauna tare da yiwa su daddy barka da gida. Amsawa sukayi daganan suka yi bismillah auka fara cin abincin su. Teemah yau kam har mamaki ta bawa iyayenta ganin yanda ta ke cin abincin,ita kuwa cin k'arfin hali ta ke yi,don so take ta riga kowa barin kan table d'in tagudu d'akinta ta kulle kafin yah Abbas ya cafkota. Kusan duk kaiwa spoon d'inta baki toh sai ta kalleshi,amma ko sau d'aya basu ta6a had'a idanu ba. Taci abincin yakai rabin plate sannan ta tashi awurin tsam ko sallama bata musu ba. Babu kuwa wanda yah tankata dan mamakin da ta cika su dashi,Abbas kuwa ko ajikinsa,cin abincinsa yake yi cikin kwanciyar hankali,yi yayi kamar bai san ma da ita awurin ba,koda ta mik'e d'in kuwa k'in d'aga kai yayi ya kalleta, amma tak'asan ido babu abinda ya wuce wa ganinsa,ta k'asan idanu yake ta kallon duk abinda takeyi harta gama ta tashi d'in. Tashin bata wani dad'e ba shima yaji ya k'oshi hakan yasa ya wa su mummy sai da safe ya wuce abinsa. Ita kuwa Teemah ruwa ma sai data bi kitchen ta d'auka sannan tawuce d'akin ta da shi,tana shiga kuwa ta danna key tana Hamdala,murna fal cikinta dan tana ganin ai ta tsira. Ruwan tasha ta ajiye ragowan agefen gadonta,sannan ta d'an rage kayan jikinta,school bag d'inta ta d'auko ta dawo ta hau tsakiyar gadon ta barbaza takardu wai nan karatun Test takeyi,batajima ba ta fara hamma,minute-minute kuwa hamman ke zuwa,tsaki tafar jerawa itama aduk sanda tayi hamman,haushin wannan cin abincin datayi yau sosai d'in nan takeji, "ai duk wannan mutumin nan ne yasani" tayi maganar azuciyar ta tare da biyoshi da wata doguwar tsuka. Takai 1hr tana karatun sannan ta tattare shirgin takardun akan gadon,daga nan tayi addu'a adaddafe ta kwanta. Washegari tana tashi kuwa sai da tayi sallah kafin taje ta yi wanka,zaman shafa mai tayi bayan ta fito daga bayin,sai da ta gama goge jikinta tukunna ta kai hannu ta d'auko man nata datake shafawa kullum. "Awsh namanta ashe ban fad'a wa mummy ba" tafad'i tare da dafe goshi. Da kyar tasamu tashafa man kasancewar babu ya k'are acikin robar,shiri tayi cikin uniform d'inta,tafito ta nufi d'akin daddynta,dayake daman idan daddy yana gari shi take fara zuwa gaisarwa kafin mummy,gani tayi baya nan,hakan yasa ta fito ta nufi d'akin mummy. Daddy kuwa tafiyace tasame shi ta gaggawa,tafiyar bazata dan jiya kusan 10:15pm aka k'ira shi,Allah ma yasa yana da passport d'insa ,so tun adaren ya k'ira yayi booking flight,6:30am yabar gidan,kasancewar 10:00am zasu tashi. Gaishe da mummyn tayi sannan ta tambayeta "ina daddyn ta yake? "Yayi tafiya ne" Mummyn tabata amsa. Sai cewa tayi "aida ya fad'a min ma da da tare zamu" Kallonta mummyn tayi da mamaki sannan tace "Toki bishi mana,ai baki makara ba" Dariyah tayi kad'an "Allah kuwa mummy da binsa zanyi da nasan zaiyi tafiyah,in bahaka inaji ina gani zaman gidannan sai ya gagare ni saboda wannan........,.......sai kuma ta kasa k'arasawa. Mummyn ce takar6e zancen da fad'in " ahh toh in juninki rashin kunya ne da tsokana aikuwa ba ruwana ni,dan ni nawa ido" "Mummy hakama zakice"? "Toh me zance Teemah? "Bake rashin ji kika ce shine halinki ba? Fushi tayi data gama jin abinda mummyn ta ce. Tea kawai tasha shima sama-sama daga nan ta tashi tsaye. "Mekenan" mummyn ta tambayeta tana kallonta. "Ni na k'oshi mummy" D'auke ido mummyn tayi daga kallonta kafin tace "Ke kika sani ai",kije jakata bak'an nan ki d'auki Kud'i aciki" fara tafiya Teemah tayi zuwa d'akin mummyn sai tajiyo muryar mummyn na sake fad'in "Kuma yanda kika saba tafiyah dashi zaki d'auka, bance ad'auki harda na shan kayan zak'i ba,sai wata yayi ki takura min da fitina" Karaf akunnen Abbas da shima ya zo dan ya gaida mummyn. Kuma atake ya fahimci me mummyn take nufi,mamaki yafara yi ashe yarinyar nan har haka ta girma amma shine bata da wayo har yanzu? Da wannan tunanin ya k'arasa inda mummyn take,tana ganinsa kuwa ta sake fuskarta dan mummy ba dai son jama'ah ba,sam bata da wannan al'adar ta k'in dangin mijinta. gaida ta yayi shima,sannan yad'an zauna kamar mai jiran wani abu, nan kuwa zaman jiran fitowar Teemah yakeyi agurin. Koda mummy ta masa maganar break fast d'inma cemata yayi a'a bayanzu ba sai zuwa anjima zai ci. Teemah da batasan da shigowarsa ba,tafito kenan daga d'akin mummyn taganshi zaune, Turus taja ta tsaya dan jitayi zuciyarta ta tsinke daganin nasa,dayake baya ya juya mata,so bai ga fitowar tata ba ,mummy ce dai ta lura da ita,kallonta tayi suka had'a idanu take sai tayi k'asa da kanta kamar mara gaskiya. Dayake kuma daman da rashin gaskiyar,sai ta taho ahankali izuwa inda suke d'in. "Ina kwana yayah " Sai da ya d'an juya kansa sannan ya kalleta, dan bata gama k'arasowa daf dasu ba ta masa gaisuwar, "Lafiya"ya amsa mata dashi,sannan ya dawo da kansa saiti suka ci gaba da maganar su da mummy. Tana ganin haka ita kuwa tafice taje dakinta ta d'auko school bag d'inta sannan ta dawo zata wuce, gani tayi yanzun baya zaune awajen, mummy kad'ai ne azaune, "Na tafi mummy" Tafad'a sanda take gyara zaman jakarta akan kafad'arta. "Adawo lafiyah" kawai mummyn tace mata. Harta fita sai kuma tadawo tasake dawowa ta tsaya daga bakin k'ofa tace "Mummy mai na ya k'are fah" D'aga kai mummyn tayi ta kalleta batare da magana ba. Teemah kuwa ta juya tafita abinta don tasan ai mummyn taji me tace d'in. Tana isa wajen motar da za akaitan aciki taganshi a mazaunin driver. kasancewar Habibu ne yakai daddy maiduguri inda zai hau jirgi, da kyar ma in sun isa yanzu ballantana ayi zancen dawowa. Turus tayi taja ta tsaya tana k'are masa kallo. kusan minti biyu shima dagangan yak'i yi mata magana,sai da yaga bata da niyyan shiga ne sannan yace mata "U ar just wasting ur time,let me tell you,ni inada abinyi" Bai kalli inda take ba yayi maganar hannunsa d'aya kuma na kan stairy. Ahankali ta ta ko tazo jikin motar,tana k'ok'arin bud'ewa tashiga ta tsinkayo muryarsa yana fad'in "Habibu kika gani ne acikin motar? Sarai tasan me yake nufi amma sai tayi kamar bataji sa ba harta bud'e k'ofar tana k'ok'arin shiga sai taji wani uban tsawan da ysa take ta firgita ta,balle daman muryarsa razana ta take. Dawani irin b'acin rai yayi maganar "bana son rainin hankali fateema,sa' anki ne ni? Ai tana jin muryar tasa jiki na rawa ta rufo k'ofar ta dawo gefensa tashiga ta zauna. Wani guntun tsaki ya sake sannan yaja motar,wani uban horn yadan na tun kan su isa bakin get d'in,da gudu mai gadi yaje ya bud'e musu suka fice agidan. Bai sarara da gudun ba har saida ya dangana da babban titi kafin nan,kasantuwar bai san inda makarantar ta ke ba,kallon ta kawai yayi sai yaji tace "NANA AISHA" Aransa yayi murmushi dan yanda yaga tsoro kwance akan fuskarta"ga shegen tsoro ga rashin kunya,afili kuwa ko kad'an babu annuri akan fuskar tasa. Daya ke yasan gurin sai bai k'ara ko kallon inda take ba ballantana magana har suka isa,yana yin parking ta fita da sauri tare da rufe k'ofar da iyah k'arfinta kai kace yau ta fara shiga mota,shigewa tayi ciki abinta batare da tasake ko waiwaye ba,bayanta yabi da kallo yana k'ara mamakin duk ina wannan yarinyar ta koyi rashin ji haka,komai na rashin ji salo-salo ta iya su,inbadan mummy tasani ba ma ke kinsa ne na kawo ki makaranta (Kunji yamanta da shekarun bayaπŸ˜…) Jan motar yayi ya shiga cikin gari,bai dawo ba har sai kusan 12na rana. 12:56pm Mummy ce tsaye ajikin mota abakin makarantarsu Teemah tana jiran tashinsu,dayake cewa Abbas tayi ya kaita idan ta tashi zata bi ta 'akota tunda ita zata yi,shiyasa bai koma d'auko tan ba,hakan ma mummy tana ganin kamar ta takurashi amma bata fad'a masa yaji ba aranta ne take jin hakan. Abbas kuwa baisan dan hakane mummyn tace masa zata bi tad'auko tan ba,daya sani kuwa bazai barta ita taje d'in ba. Bata wani dad'e agurin ba aka tashe su,tana ganin hakan sai ta koma cikin motar ta zauna saboda hayaniyar yara da kuma k'ura,kuma atunaninta ai Teemah tasan motar gidansu inta ganta ai zata ganeta. Teemah ma bata san cewa mummy ce tazo tafiyah da ita da ba,bata fito da wuri ba sai da kusan rabin d'aliban suka wuce kafin ta fito, kuma koda ta fito data fito d'inma sai ta wani d'auke kanta daga ganin motar,dan ta zaci Abbas ne yazo yanzun ma. Bakin titi ta nufa da niyyan taran adaidaita amma cikin rashin sa'a sai bata samu ba,don gaba d'aya d'alibai sun tashi yanzu,kuma a irin wannan lokacin samun abin hawa wahala yakeyi,gashi ana zabga rana. Wasu ne 'yan mata su biyu suka zo inda take tsayen,'yan class d'insu ne,suma napep zasu hau,anan suka tsaya surutu,ranar ne yafara isanta,dan tun tana jurewa harta ji inaah bazata iyah ba,da gefen ido ta kallo motar,ga mamakinta sai ta hango mummyn ta zaune aciki. Take taji wani farin ciki ya lullu6eta........ *Drop ur comment* *nd share pls* πŸ‘ŒπŸ» *Salmerhn ku ce* 😍 [10/2, 5:54 PM] Ummiyo: πŸ’• *CAPTAIN ABBAS* πŸ’• By *Salmerh MD* Luv story😍 *Wattpad @* *Serlmerh-md* πŸ’« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS* πŸ’« We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all..... *DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO* _Wannan page d'in_ _naku ne ku_ _d'ai_ πŸ‘ŒπŸ»' _yan_ *CAPTAIN* *ABBAS FANS* *2* , _inajin_ _dad'in comment_ _d'inku har_ _6argona......__ 😍 *Bismillahir* *rahmanir raheem* Worry is a total waste of time. It doesn’t change anything. All it does is steal your joy and keep you very busy doing nothing. πŸ…Ώ *11* Da saurinta ta isa gurin motar,alokacin ma mummy hankalinta harya fara tashi da rashin ganin Teemahn,tana k'ok'arin fitowa kenan ta duba ta dakyau,sai taji muryarta ta k'ira ta "Mummy" Da sauri mummyn ta d'aga kanta ta kalleta kana tace "Haba Teemah a ina kika tsaya fisabilillahi? Karkata kai Teemahn tayi gefe tayi kalan tausayi, Mummyn kuwa tacigaba da fad'in "Wato dama haka kike wa Habibu idan yazo d'aukarki ko kisashi yayi ta jiranki ko? "Ahh fah mummy ni na _d'auka_ wannan yayan ne shiyasa fah nak'i zuwa" Haushi mummy taji dajin abin nan data fad'a d'in,gata gwanar fad'ar gaskiya bata fiye 6oye al'amarinta ba ita. Cikin jin haushi mummy ta bata amsa da " toh ai sai ki _ajiye_ da kika ga bashi d'in bane kuma" "Sorry my mum" cewar Teemh ta fad'a tana zagawa d'ayan b'angaren ta inda zata shiga motar. "Wato ke bazaki bar raini da mugun halinkin nan ba ko? Mummyn ta ce bayan Teemah ta shiga motar "Shiru tayi bata yi magana ba. "Inda Abbas d'inne kenan haka zaki shanya shi? Waini sa'anki ne shi d'in? "Kalli time fa Teemah kusan 1:30 amma sai yanzu zaki taho,kinsan tun yaushe nake anan d'in inaji ranki? "Allah mummy bansan ke bace kika zo da bazan dad'e ba. "Hmm"Allah ya shiryeki " Kawai mummyn tace tare da yiwa motar key,sun iso daf wad'ancan friends d'in Teemahn sai Teemah tace "mummy sabon pegi" tafad'a tare da nuno su. Tsayawa mummyn tayi,Teemah kuma tayi musu magana suka shigo dan har yanzun basu samu abin hawa ba. Gaida mummyn suka yi ta amsa musu cikin sakin fuska daganan ta d'auki hanyar sabon pegin,ba hanyarsu bace amma haka sai da ta kaisu har k'ofar gidan su da taimakon kwatancen da suke mata,har suka isa,godiya sukayi mata sannan suka shiga ciki dan dukkan su 'yan gida d'aya ne. Daga nan mummy ta juyo ta nufo hanyar gidansu dake Nyanya Quaters gujba road Damaturu. "Allah mummy gwanda da kika zo,d'azu da wannan yayan yamin wani tsawa har sai da naji fitsari. "Wataran ma ai har dukan ki zaiyi inde kika ce juninki rashin jine" "nifah babu abinda namasa mummy" Bata kulata ba,dan tasan koma me zata ce toh 6ata bakinta takeyi abanza kawai dan Teemah baji takeyi ba. Horn mummy tayi aka

Chapter 4 of 67