abinda yacanja daga yanayin tsayuwarshi.
Sai ta yi tunanin ko beji ta bane sake bu'de bakinta tayi da niyyar sake 'kiran sunan nashi
_" Yah Mahm............_
Da wannan lion voice 'din nasa ya daka mata tsawa
_"Shut up da Allah"!_
Ya fa'di maganar tare da juyowa.
*Hi every one!* πββ
_Naga sakonninku readers da dama wasu a groups nagani yayin da wasu suka yiyyi min magana ta private, duk kanku nagani kuma na yaba da 'ko'karinku kuma ina godiya da dukkan addu'o'in da kuke bina dashi, nima ina muku fatan alkhairi.Ha'ki'ka me son ka shike iya bu'dan bakinsa ya zanzaro_ ma _addu'o'i nagartattu batare da haufi ba, duk da yasan Allah na iya amsawa ako wani lokaci, gaskiya godiya nake 'yan_ _uwana_ . *(ALLAH YA* *BAR 'KAUNA).*
*FEELING* *THANKFUL* ππ»
_Gareku commenters kuma inajin da'di sosai da yadda kuke bawa littafin nan kulawa harma idan kunga shiru ku tambaya ko lfy, agaskiya hakan ba 'karamin sani farin ciki yake ba, harma yake kuma 'kara min 'karfin gwiwa, as u can see last week akwai ranar da nayi posting 2pages saboda jin_ _da'din_ _ku kawai masoya na._ *( NIMA INA SONKU ADUK INDA* *KUKE).*
_Nagaji ne amma badan haka ba da na lissafo suna yenku koda ka'dan ne, sai dai duk da haka bazan manta daku ba insha Allahu nayi al'kawarin jero_ _sunayanku koda ba dukkan ku ba aduk lokacin dana samu_ _chance_ _insha Allahu._
*'KORAFI* ππ»
_Sai dai kuma naji wasu daga cikin ku suna ganin kamar wai ni ina team 'din_ _Mahmud_ _ne_ π€.
*SUGGESTION* !ππ»
_Azahiri bahaka ba ne kar ku manta fa ni na kowa ne dukkan su ina son su babu wanda bana so aciki, kuma ai ba lallai bane arayuwa ace wanda kafi so kuma shi yafi tara dukkan abubuwa in dai hakane ashe za'a iya cewa 'dan Adam_ _batara yake ba yacika goma cif-cif, ba dole bane ace Star 'din littafi shi yafi iya komai acikin littafin tunda kowa ma mutun ne, kuma kowa nada tashi irin baiwar Allah yayi masa kunga dole sai ansamu similarities da difference sannan asamu best_ *.(hakane)* β
_Dan haka karku manta wannan littafin sunan shi_ *CAPTAIN* *ABBAS* _kuma star_ ' _dinku a_ _littafin sunanshi_ *oga* *ABBAS*ππ»π
_dan haka_ ππΌ
π€π» *ACIGABA DA*. *GASHI KAWAI* ................... β
_Comment_
_Vote_
_Share_
*Salmerh* π
[10/2, 6:01 PM] Ummiyo: π *CAPTAIN ABBAS* π
By
*Salmerh MD*
Luv storyπ
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
π« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
π«
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_Dedicated_
_2 all masoyan_ _cApTaIn_ _AbbAs._ π
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
_If you donβt care about what people think about u, you already passed the first step of success._
π
Ώ *46*
Cikin firgita Teemah ta matsa baya ka'dan tare da furta _" Yah Abbas "_ asaman la66an ta.
Ganin yanda idanuwan sa suka koma tare da irin kallon da yake mata ma ka'dai abin tsoro ne ballantana kuma irin ihun da ya daka mata aka.
'Kasa tayi da idanuwanta da har sun fara 'ko'karin tara ruwa shikuwa sai ya tako ahankali zuwa gabanta tamkar wani abin arziki zai mata sai kuma yasa hannu ya 'dago habarta zuwa sama dolenta ta 'dago kannata batare da taso ba dan ita yanzu tsoro ya Abbas yake bata sak ya juya mata wani irin halitta daban mai abin tsoro.
Rintse idanuwan nata tayi da 'karfi jikin na rawa saboda lokacin da ya 'dago kannata tayi zaton sau'kar mari zataji amma kuma sai taji shiru.
Shikuwa Abbas kallon fuskar tata ya tsaya yi, sosai yaga yarinyar ta rame masa amma be tsaya yabi takan ramar tata ba sai hankalin sa ya tafi ga rintse idanuwan da tayin, haushin hakan yaji, shi tunaninshi tayi hakan ne dan bata so taga ko da fuskar ne while bahaka bane ita ta rufe idanun ne saboda tsoronsa, tsoron ha'da idao takeyi dashi.
Sake mata fuskartata yayi sai yacigaba da 'kare mata kallo, be kawar da idanun sa daga kannata ba yace _" lover girl !_, _" kin zaci saurayin ki ne yazo ko"?_
Be jira jin amsarta ba yajuya mata baya ya fara taku ahankali hannunsa 'daya har yanzu na acikin aljihunsa kamar an ce kuma yajuyo, sai ya dawo inda take tsayen ya cira hannunsa yaja hannunta da 'karfi.
Be zame ko'ina da ita ba sai a wajen kujera ya wani jefata da 'karfi ya tsaya akanta yana huci, ita kuwa sai ta kudun dune jikinta wuri 'daya yayin da hawayen da ya taru acikin idanunta 'dazun yasamu damar gangarowa abinsa, ci gaba tayi da zubda hawayen helplessly kanta acikin tafin hannunta.
Sau'kan duka kawai take jira awurin yah Abbas 'din dan zuwa yanzun gaba 'daya ta saduda da wannan alamarin, bata san laifin data yi masa ba, dan ita bata masa laifin komai ba a iya saninta amma ga dukkan alamu ranshi a6ace yake da ita.
Ko kuma cewa da taji akeyi anawa sojoji allura wata'kila gaskiya ne, gashi yau tashiga hannunsa Allah ne ka'dai zai 'kwace ta yau ahannunsa, ahankali cikin kukan ta fara fa'din _" Yah Abbas... dan Allah.....dan Allah kayi ha'kuri, wallahi bazan sake ba, dan Allah karka dake ni, in ka dake ni_ _mutuwa zanyi Yah_ _Abbas........"_
Ahankali take maganar dan in ba akusa da ita kake bama bazaka ta6a fahimtar me take fa'di ba saboda cikin shashsheka tayi maganar.
Shi kanshi Abbas yanda tayi sai da ta bashi tausayi amma sam yakasa jin nutsuwa acikin azuciyarsa, yakasa bawa kansa ha'kuri akan abinda yakeji, aganinsa ai shi rani masa hanakali kawai take shirin yi kamar yanda tasaba abaya, azahiri shikanshi be san laifin data yi masa ba she looks innocent, amma shi aransa ji yake tamkar wani babban laifi tayi masa da babu wanda yata6a aikata masa irin laifin akaf fa'din duniya.
Da 'kyar yasamu ya 'dan sassauto ya 'daidaita nutsuwar shi, sai ya yun'kura da niyyan zama agefenta akan kujeran daya jefa tan.
Teemah kuwa na ganin haka ta zamo da sauri ta dawo 'kasa akan carpet kusa da kujerar taci gaba da rera kukanta.
Gira 'daya Abbas ya 'dage da mamakin abin da tayin yana kallonta.
_"meke nan wai "?_
Ya tambayi kansa azuciyarsa.
Teemah kuwa tana sau'ko wa taci gaba da bashi hak'uri " _Nifa banyi laifin komai ba Yayah dan Allah kabarni na tafi, inbaka yadda ba ka tambayi mummy kaji Allah banyi mata laifi ba "_
Rashin sanin amsar da zai bawa tambayar tasa yasa ya watsar da tambayar kawai ya dawo da dukkan hankalinsa gareta yaci gaba da sauraransa ha'kurin nata tana dasa aya yayi murmushin takaici tare da 'dan rankwafo da kansa daf da ita
" _Fatima_ " ya 'kira sunan ta cikin natsuwa.
Shiru tayi bata amsa ba duk da tayi mamakin hakan domin ayanda taganshi 'dazun batayi zaton zai sau'ko so soon haka ba, yau de _" Allah kai ka'dai zaka fitar dani_" ta fa'di aranta sai ta 'dan 'dago kanta ka'dan amma bata kaiga duban fuskarsaba.
Shima be takurata ba wannan karan dan zuwa yanzun ko ba'a fa'da ba dakansa yafara fahimtar irin tsoratan da tayi dashi, ya gane cewa duk abinda takeyi atsorace take yinsa.
_" Waye yace miki bakiyi laifi ba"?_
Shiru tayi masa wannan karan ma dayaga bazata yi magana ba sai yaci gaba da tashi maganar _" anyway,_ _ki bani_ _labari"_.
Yayi maganar yana duba agogon dake 'daure da tsintsiyar hannunsa sai kawai ya 'kara da fa'din
_" ki ban labarin yanda kike so auren ki yakasance"!._
Ko yanzun ma shiru tayi batayi masa magana ba, kawai sai ta 'kara maida kanta 'kasa kamar yanda yake da farko ko ka'dan bata yi alamar zata bashi amsa ba _" toh_ _me yake so_ _ince masa, har akwai wani yanda nakeso aure na ya kasance ne?.
Muryarsa tajiyo yana fa'din _" idan nayi magana banason ashare ni Fatima wata'kila kin manta da wannan ko?"_
Yayi maganar tare da komawa baya ya jinginu da jikin kujerar tamkar wani basarake.
Kai tayi niyyan jijjiga masa amma da tuno da warning 'dinsa daya ta6a mata abaya akan hakan shiyasa sai ta bu'di bakinta da 'kyar kamar ma bazata yi maganar ba tace " ban manta ba".
Shirun shima yayi idanuwansa nakan la66anta datayi maganar, kukan da tayi gaba 'daya sai yasa suka zama jajir, zuba mata idanu yayi shi ka'dai yasan me yake sa'kawa aranshi.
Tsawon mintina biyu suna ahakan, motsi Teemah tafara sanadiyyan gajiya da 'kafafunta suka yi dayake lan'kwashe su tayi ta zauna akansu, zogi taji sun fara yi mata take sai ta sake yamutse fuska tare da daidaita su yanda zata 'dan ji dama-dama.
Motsin data yin ne ya'dan ankarar dashi daga zuba mata idanun da yayi, sai da ya 'dauke idanunsa ya kawar gefe kafin daga bisani ya dawo da kallon shi gareta.
" kina jina"
Ya tambayeta.
Sai itama ta bashi amsa daidai da yanayinta a'kasan ma'koshi ta amsa masa da " uumm" tare da 'dagowa a'dan sace ta dube shi.
Bata san meyasa ba amma wani 6angare acikin zuciyarta na kwa'daita mata son kallon fuskar sa yayin da 6angare 'dayan kuma tsoro ya rinjayar shi kuma sai tsoron yafi mata tasiri saboda idanun ya Abbas tsoro sosai suke bata ayau 'din aduk lokacin da yake yanayin da ba dai-dai ba ko ada ma da take masa iskanci son ranta dan be ta6a ritsata bane shiyasa, amma duk da haka de sai da ta 'dan saci kallon san wannan karan dan yadda yayi mata maganar cikin natsuwa sai yasata har ta samu 'kwarin gwiwan 'daga kanta ta kalleshi, idanunsa 'kur akanta ita kuwa bazata iya sar'ke idanuwanta acikin nashi ba dan haka sai tayi gaggawan maida idanuwanta ga tafukan hannunta dake kan cinyarta luguden da zuciyarta ke yi mata ma ka'dai ya isheta.
_" dagaske ne wai aure zakiyi Angel 'din daddy"?_
Muryarsa asanyaye yayi maganar cikin nutsuwa sai kace bashine ya daka mata uban tsawa 'dazu ba, sai ta 'dago da kanta ka'dan itama amma bata kaiga fuskarsa ba sai ta sau'kar da idanun nata akan hannunsa 'daya dake ajiye akan hannun kujera, a irin yanayin da yayi maganar itama sai tace
_" Daddy ne nima ya_ _fa'da min haka"._
_" toh meyasa ni baki 'kirani kin gaya min ba a lokacin"._
Sai tayi saurin bashi amsa da fad'in " _Wallahi Yayah mantawa nayi kayi ha'kuri"._ Ta 'karashe maganar da karkata kanta gefe harma ta daure ta sanya idanunta cikin nashi.
Yanda tayin ba'karamin birgeshi tayi ba sai kawai ya tsaya yana kallonta kamar baze sake magana ba.
Ita kuwa har godiya takewa Allah dayaga yayi shiru yana kallontan, _"Allah kasa ya ha'kura ya barni na tafi"_
duk zaton ta laifin da tayi masa kenan shiyasa yayi maltreating 'dinta 'dazu har tana tunani aranta " ashe dama akan 'dan wannan abin ne, toh ai in de wannan ne harda kai a laifin, kaima ai baka ta6a 'kirana ba, toh ni meyasa zan 'ki......
Tana cikin tunanin taji ya sake fa'din " _kin_ _manta kika_ _ce_ "?
Ga mamakinta wannan karan atsaye yake hannunsa 'daya cikin aljihunsa harma ya juya mata baya kamar me shirin barin 'dakin.
Mamakinta be wuche na har yaushe yabar nan 'din ba batare da tasani ba.
_" Fatima toh dani kika manta ko kuma da 'kirana a waya?_
Yana gama fa'dan hakan ya juyo ya fuskance ta ga dukkan alamu amsar tambayarsa yake bu'kata gamsashshiya daga bakinta.
Ita kuwa rasa abin da zata ce masa yasa tafara in ina domin ta kamamman abinda zata furta wanda bazai zama laifi ba take so dan ta kar ta 'kara yi masa wani tunda tasamu ya sau'ko, kuma sai tarasa, sai da 'kyar tasamu ta furta _" da wayar"_.
Murmushin takaici yayi inda murmushin ya tsaya masa a iya saman la66ansa sannan ya juyo ya dawo kusa da ita kanta ya 'dago zuwaga kallonshi wannan karan kam jitayi zata iya kallon idanunsa tunda taji ya 'dan sau'ko daga masifar da 'daina shayin ha'da ido dashi aikuwa takalleshin idanun su suka 'sarke cikin na juna
_" ki gaya min gaskiya, ke ma kina son auren nan ko?._
Ita kanta bata san lokacin da har kanta ya motsa ta bashi amsa ba saboda wani bug...bug take jin zuciyarta kamar zata fa'do waje.
_" Fatima kina son Mahmud"_?
Ya sake tambayarta.
Yanzun kam shiru tayi masa sai da ya sake maimaitawa da 'dan 'karfi kafin ta sake 'daga masa kai alamar _"ehh_"
Yagane me take nufi amma dan yasake tabbatarwa yace mata be fahimceta ba dolenta ta bu'di baki ta bashi amsa da " _ehhh"._
_" kin tabbatar "?_
kai ta 'daga masa yanzun ma dan ji tayi bakinta yayi mata nauyi koda zai doke tane bazata iya bashi amsa da bakinta ba.
Yana gama fahimtar ta take sai yasake mata kanta ya koma ya zauna da kyau akan kujera ya lumshe idanunsa tare da jingina bayansa tsawon mintina biyu.
Tashi yayi cak kamar an mintsine shi ya nufi 'kofar fita daga 'dakin, yanda ya buga 'kofar ma ka'dai abin ka juya ka kalleshi ne domin da 'karfinsa ya bugata tamkar tayi masa babban zunubi.
Teemah tana inda ya bartan har ya bar 'dakin bata iya 'daga ido ta kalleshi ba, tana zaune tamkar mutun mutumi, bata san me yasa take jin kamar bata kyauta ba haka kawai sai take jin rashin nutsuwa ga kuma damuwa da tausayin kanta da bata san tushensu ba na ratsata ta ko'ina hakan sai ya 'kara kashe mata jiki tare hana ta motsi agurin banda gudun da hawayen ta ke yi babu abinda ke motsi ajikinta.
Yana fita daga 'dakin sai su kaci karo da Hannah da ta taho da saurinta itama ta nufo dakin, dan tun 'dazu tun fitan Teemah take cikin bayi bata san da labarin zuwan shi ba koda ta fito kuma 'kawayen Teemah basu tuna sun sanar da ita 'kiran da Ummah take yi musu akan lokaci ba, sai da ta 'bata lokaci awurin yin shirin tagama kafin Naanah ta tuna da cewa an'kirasu tun 'dazu.
Koda taje gun Ummah kuwa masifah tafara yimata akan wai ina ta zauna tun 'dazu bata je sun gaisa ba alhalin tasan baya da'dewa akan hanya yake, ha'kuri tabawa Ummahn tare da fa'din ai batasan shine yazo ba"
Mummy ce ta tari maganan da fa'din je ki sameshi ku gaisa kafin ya tafi yana can 'dakin.
Toh ita da suka zo jiya Teemah duk tabi da ita ta nunnuna mata ko'ina agidan da 'dakunan yayun tan, hakan yasa da mummy tace mata yana 'dakinsa sai ta nufi 'dakin da Teemah ta nuna mata jiya amatsayin 'dakin sa, amma sai bata ga alamar ma anbu'de shi ba ( ashe ita kuma mummy key 'din 'dakin Mahmud ta bayar aka sau'keshi aciki), ita kuma sai Hannah tayi tunanin ko bata gane lissafin bane tace bari ta dubo 'dayan tagani tukunna ( abinda ya sa tayi delay 'din zuwa da wuri kenan).
Tana zuwa kuma sai ta ha'du dashi harya fito, _"ah ah_Yayah _har tafiya zakayi_ __ne_ _bayan bamu ha'du ba?
_"Sauri nake yi Hannah lokaci zai 'kure min"._
"_Toh yayah kaci abinci ne ?_ "
Duk maganannan da sukayi akan tafiya suka yi ta, Abbas be tsaya ba koda ya gantan sai yaci gaba da tafiyarsa, itama tana binsa abaya take ta faman jero masa tambayayoyin, ganin kamar zata takura shi. Sai ya ce
_" Hannah naci jeki fito da sauran suna ciki"._
Yasan in ya fa'di haka zata koma tayi abinda yace dan yasan Hannah bata ta6a musanta masa magana kowacce irice.
Illai kuwa hakanne, dan yana fa'din haka ta tsaya cak daga binsan da takeyi, ta bi bayansa kawai da kallo daga bisani kuma sai ta juya ta koma 'dakin domin fito da ragowar abincin kamar yadda ya ce da ita.
Tana shiga sai ta hango Teemah a zaune tana zubda hawaye, da sauri ta 'karasa inda Teemahn take tayi zaman dirshan a gaban ta arikice take tambayarta abinda yafaru.
Teemah kuwa bata san da shigowan Hannah ba sai kawai taganta agabanta lokaci guda.
Hawayenta ta fara 'ko'karin gogewa ita adole kar Hannah tagani.
Duk 'ko'karin da Hannah tayi dan taji meyasamu Teemah tayi amma takasa samun gamshashshiyar amsa ko guda 'daya ne daga wurin Teemah.
Data gaji da tambayar sai tace mata
_" nasan me ya faru ai kawai baki san sanar dani ne"_
Shiru Teemah tayi kawai tana kallonta ita kanta so take taji abinda yasame ta so take taji daga bakin HANNAH, dan idan zata tambayi kanta da kanta ma bata san meke damunta ba bata san mezata ce yafaru tsakaninta da Yah Abbas ba.
_" wannan sojan ne nasani, nasan shine yasaki kuka domin shi ne ka'dai naga yafita daga 'dakin nan kuma nasan sarai zai iya"_
Hannah tayi maganar tare da mi 'kewa tsaye ta nufi inda taga tray 'din abincin.
_" gaskiyarki ne Hannah, Yah Abbas ne !,toh amma me zance yamin har nake kuka"?_ azuciyarta tayi wannan tunanin, sannan itama ta mi'ke tabi bayan Hannah zuwa gurin abincin.
Hannah sai da ta zauna kafin tafara bu'de su 'daya bayan 'daya tana gani.
_" 'kila ya tsaya yi miki mugunta ne ma shiyasa ko abincin be saurara ba harda wani cewa wai inzo in kwashe_ _sauran ashema ko bu'dewa beyi ba"_ tayi maganar dai dai tana 'ko'karin rufe plate 'din daya kasance na 'karshe data bu'de " _muje sai na tambayeshi ai laifin me kika masa da har yasaki kuka, innayi sa'a shi zai gaya min tunda ke kin'ki sanar da ni, problem 'din ma miskilancin tsiya gareshi da 'kyar ma yakulani idan yaga dama, amma nasan me zanyi ai in ya'ki bani amsa Daddy zan 'kira infa'dawa ince in yazo nan dukanki yake yi kullum kafin yatafi "_
Suna kan tafiya Hannah take ta jero bayananta batare da Teemah ta fa'di ko kalma 'daya ba sai da Hannah ta dasa aya sannan Teemah tace
_" ke nifah bance miki ya Abbasa ya doke ni ba"!_ awani tsare tayi maganar tamkar wata jaruma.
Turus Hannah taja ta tsaya
_"Toh yah akayi? fa'damin_ "!
_" ayaya kika sameni"_ ?
Sai da Hannah ta 'dage gira tukunna tace
_"Azaune mana kina_ _kuka"!_
_"Toh abinda yasame ni kenan, gajiya nayi da zaman kuma kafata ta ri'ke sai zogi takemin nakasa ko motsa ta shiyasa ni kawai nafara kuka"_
_" shikuma yatafi ya 'kyaleki ahakan"_?
_"Sai da ya fita sannan na fara jin zafin"_!
_" kin ma rainawa kanki hankali yarinya amma da nazo 'din waye yataimaka miki kika mi'ke?"
Da sauri Teemah tace _" ai lokacin 'kafar ta daina zafi"_
_" kuma hawayen kasa tsayuwa yayi ko"? ,_
Shiru Teemah tayi ta kauda kanta gefe.
Hannah kuwa sai taci gaba da maganarta _" kekika sani wallahi indai juninki wai adake ki 6oye ne kin shiga_ _ukun ki,_ _Yah Abbas fah bashida kara shikan_ _babu_ _ruwansa muguntarsa intazo yinta yakeyi ako ina indai shine, kicigaba da rufa masa asiri wai ke gaki me_ _yayah ko hmm_ , _jiki_ _magayi ai_ _yarinya"__
_"ke kin kasa yadda be min komai ba_ _ko"_ ?
_" ai ko bani ba babu me amince miki Teemah"._
_"Allah kuwa Hannah babu abinda ya min idan abu yamin ai zan sanar dake kinsani"!_
" _ke kika sani fah ni babu ruwana_ "
Hannah tafa'da 'kasa-'kasa.
Teemah kuma acikin zuciyarta tace _"kanki akeji parrot_ _kawai."_
Hannah alwashi tayiwa aranta sai ta bincika ta gano abinda ke faruwa saboda tana ganin kamar Teemah na 6oye mata wani abin ne, kuma batason Teemah ta kullaci Abbas saboda idan ya kasance kullum mugunta yake mata dole zata na jin haushin sa aranta,itakuwa tana son yayan ta batason kuma taji ance anajin haushin wani abu nashi daya dangance shima ballantana shi da kanshi, tafi son taji kowa nason shi, shiyasa ko yanzun ma ta damu dataga Teemah na kuka taso Teemahn tasanar da ita meke faruwa dan tayi maganin abin, amma Teemah ta'ki.
Abbas kuwa tun kafin ya isa 6angaren da yasan zai samu Ummahn ya 'daga waya ya 'kira Mummy..............
*ACIGABA DA KAFTAWA MUTANE NAH...........*π€π»
*Sa'kon Ta'aziya ga 'yar uwa RAHAMA NALELE da dukkan al'ummar musulmi, Allah ubangiji ya ji 'kan magabata yasa alajanna hutu ce. Allah ubangiji ya musanya abinda* *aka rasa da alkhairi* *mafifici.*
_Sorry 4d late condolence._
_Comment_
_Vote_
_Share_
*Salmerh ce*π
[10/2, 6:01 PM] Ummiyo: π *CAPTAIN ABBAS* π
By
*Salmerh MD*
Luv storyπ
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
π« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
π«
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_Dedicated_
_2 all masoyan_ _cApTaIn_ _AbbAs._ π
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
We canβt solve problems by using the same kind of thinking we used when we created them.
π
Ώ *47*
Mummy cewa tayi ya shigo tukunna suyi sallama da mahaifiyarsa mana kafin yawuche 'din, yayi 'ko'karin ce da mummyn ta sanar da Ummahn kawai basai ya shigo ba da 'kyar mummy tayi convincing 'dinsa yashigo koda ya shigonma atsatstsaye yayi musu sallamar yawuche abinsa kafin su Hannah su shigo ma har ya wuche dukkansu sun fahimci 'yar 6oyayyiyar damuwan dake kwance asaman fuskarsa amma basu tsaya sun tambayeshi ba saboda sun san basamun amasa zasu yi ayanda suka san halinsa.
Hannah da Teemah kuwa koda suka shigo 'din ma sai kowa yabi hanyarsa, Teemah 'dakinta ta wuche wurin friends 'dinta bayan ta daidaita nutsuwa da yanayin fuskarta, Hannah kuwa kitchen ta shiga ta ajiye tray 'din da ta 'dauko sannan ta dawo wurin Ummah tazauna agefenta.
_" Ummah wallahi Yayah ko cin abincin ma beyi ba ya fito kayansa"_
tace da Ummahn cikin yanayi na shagwa6a66u.
Sai Ummahn tace mata
_" 'kila baya tare da yunwa ne shiyasa "._
'Kasa-'kasa tayi da murya dan kar kowa yajiyo ta tace _" Ummah kinsan wani abu"?_
Kai Ummahn ta girgiza mata alamar _a'a_ sai ta cigaba da fa'din
_" kukafa nasamu Teemah nayi a'dakin nasa na tambayeta kuma ta'ki ta sanar da ni_ _abin da yasameta"._
_" nasan za'a rina"_
Mummy tace azuciyarta.
dan duk 'kasa-'kasan da Hannah tayi da muryarta sai da Mummy tajiyo ta batasani ba, dah ita a shirmenta wai ba'a jiyo ta Ummah ce ka'dai kejinta, wannan karan Ummah mantawa tayi da sirrin 'karyar da Hannah take so suyin tace
_" toh me yasame_ _ta"?_ da 'dan 'karfi tayi maganar.
_" oho nima bansani ba, amma inaga itada yayah ne"!_
Hannah ma dolenta ta dawo da muryarta daidai yayin fa'din hakan dan Ummah tariga ta tona ta.
Mummy naji amma bata tanka ba sai da taga Ummah taciro waya sannan taso saka baki amaganar duk da bata so haka ba amma sai taga yazama dole ne tayi maganar, tana shirin yin magana sai Hannah ta rigata tambayarta abinda Ummah zatayi da wayar ganin tana shirin nemo wata number, afirgice tace da ita _"wa kuma zaki 'kira Ummah da wayar"?_
_"Abbas mana, tambayarshi zanyi abinda yarinya nan tayi masa ya daketa"_
Hannu Hannah tasa tana 'ko'karin kar6ar wayar tace _"kai Ummah bazaki ci ribar zance ba kekam, daga magana sai ki 'kirashi kalan yazo yaci 'kaniyata yace ni ce nafa'da miki".?_
_" Toh me yasa zai daketa yatafi abinsa, daga zuwa gaishe shi dan_ _neman fitina da rashin ha'kuri sai yakama ya doketa, yarinyar da ake shirin taron bikin ta shine zai daka tsabar shi_ _ishashshe ko me?"_
Sai yanzu mummy tasamu damar saka baki amaganar tasu ganin Ummah ta 'dau zafi tace.
_" dama kin hutar da bakinki da zuciyarki akan yaran nan, indai Teemah da Abbas ne toh wallahi_ _gajiya zakiyi da magana har bakin ki yayi tsami, haka suke kullum cikin abu 'daya"._
_" toh ai wannan duk rashin ha'kurin na sa ne, taya zai rin 'ka biyewa yarinya 'karama har haka"?._ _mthewww_
Ta 'karashe da yin tsaki sannan ta da dawo da kallon ta da Hannah tace " _kinga Hannah je 'kiramin ita Fatiman, maza yi_ _sauri"._
Tafa'da tare da 'dago hannayen Hannah sai da taga ta tashi tsaye kafin tasake ta.
_" ki sauri mana"_
Ta 'kara cewa da Hannah ganin tana 'daga 'kafa ahankali kamar ba son zuwa take ba.
_" hmmm"_ kawai mummy tafa'di a'kasan ma'koshinta, ganin ko'karin Ummahn takeyi ita.
Ko bayan fitar Hannah Ummah cigaba tayi da surutu tana mita akan lamarin mummy ce ta dakatar da ita da fa'din
_" wannan abinda
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 67