kike yi fah duk abanza ne inde akan yaran nan ne, kuma nasan babu_ _wani dukanta da Abbas yayi dan tunda muke dashi agidannan banta6a ji ko ganin yasa hannu ya_ _ta6a_ _lafiyarta ba duk kuwa da irin rashin ji da Fateema keyi_ _agidannan, ko yanzun ma nasan iskancin Teemah ne kawai ki rabu dasu."_ !
Kauda kai Ummah tayi gefe kamar bataji ba ga dukkan alamu maganar mummyn be wani shiga kanta ba, sai mummy ma tayi murmushi kawai ta ta tashi ta bata wuri.
Da Teemah ta tashi zuwa 'kiran da Ummah keyi matan gaba 'dayan su suka taho da sauran friends 'din nata dan cewa sukayi suma zasu wuche gida ganin lokaci ya 'dan ja.
Da fara'ah dukkansu suka shigo 'dakin saboda ragowar dariyar dasukayi duk be bar kan fuskokinsu ba, Naanah ce take kwatanta rawar da zatayi wai agurin bikin Teemah gashi bata iya rawar ba abin dariya kuma wai ita adole sai tayi ,Fauzee kuwa data kare mata kallo sai tace _wai_ _rawar Naanahn_ _tamkar agwagwa na tafiya_ hakanne yasasu dariya gaba 'dayan su shiyasa suka zowa Ummahn da murmushi akan fuskokinsu.
Ummah idanunta akan Teemahn yafara sau'ka da har yanzu takasa ri'ke tata dariyar idonta har yana hawaye tsabar dariya, aduk lokacin da ta tuno maganar Fauzee sai kawai taji sabuwar dariya ya kamata.
Mamaki Ummah tayi sosai kuma sai alokacin ta yadda da maganar mummyn data gama fa'da yanzun kafin ta tashi, yanda taga idanun Teemahn badan taga tana dariya ba da sai tace kukan dukan da Abbas din yamata ne amma ganinta tana dariya sai ya wanki ranta ta 'danji wasai.
Sallamansu kawai tayi batare da ta tambayi Teemahn abinda yafaru ba, haka suka je suka yi musu rakiya awurin gate suka musu sallama tare da godiyan ziyaran dasuka kawo musu daga nan su Fauzee sukayi gaba sukace sai nan da kwana biyu kuma idan sunzo shan shagalin biki.
*****
*LAGOS*
Mahmud kullun addu'ah yake kar Allah yasa Abbah yasake tunowa da maganar zuwa yoben nan dan shi ba son zuwa yake ba, Allah kuwa ya taimakeshi Abbah be sake bi ta kai ba, sai kawai yaci gaba shiryen shiryen dake gabansa.
Anty kuwa zuwa yanzun hankalinta inyayi dubu toh ya gama tashi, dan ganin yanda shirye-shirye ya kankama gashi Anty chideh ta 'ki bata ha'din kai suje gurin neman maganin har yanzu, ta ro'ki Anty Chidehn iya yanda zata iya amma sam ta'ki yadda har Anty ta ha'da da cewa zata iya samo mata 'yan mata duk irin wanda take so wanda suka ri'ka awannan harkar ko guda nawa ne matu'kar zata amince ta kaita wurin 'dan ogah, amma Anty Chideh ta'ki yadda tace ita kanta zata iya nemowa kanta indai tana da bu'katar su wannan ba matsalarta bane ayanzu.
Anty kuwa tace ita sam bazata iya aikata lesbian ba, bata ma son ko ka'dan taji ana labarinsa ji take yi kamar zatayi amai tun ranar data ga Anty Chideh nayi ta 'kara tsanar abun bata ma ko san tunowa dashi ballantana ita ta aikata shi da kanta, akan hakan ta gwammaci ganin auren Mahmud da ire-iren 'ya'yan Khadija ko da su nawane aduniyan nan indai har sai ta aikata lesbian zata ga rashin yiwuwar hakan.
Akan haka kullun suke dramma da 'kawarta Anty Chideh inda kowa ya kafe akan nashi ra'ayin, duk kuwa da wannan abinda Anty chidehn keyi mata hakan besa daidai da 'kwayar zarra taji haushin Antyn Chideh ba ko ka'dan, ahaukarta ita gani take kamar _so ne_ ai har yasa Anty chidehn taza6e ta akan hakan, sai dai rashin sa'ar da Anty Chidehn tayi shine ita Anty bata da ra'ayi.
Maimakon ta 'dan ja baya da Anty chideh a'a sai ma wani sake lalla6a ta data keyi akullum, saboda tsoron kar ta ce zata fita aharkanta ta rabu da ita gaba 'daya wanda take ganin kamar in hakan yafaru ba 'karamin asara tayi ba tana ganain cewa wahala zata sha in Anty Chideh bata tare da ita, gani take zata shiga uku domin Anty Chideh itace idanun ta afa'din garin Lagos, duk wani damuwarta, farin cikinta, ba'kin cikinta samu da rashin ta kafin kowa yasani sai Anty Chideh tasani.
Inkuwa matsala ce ta kunno mata kai bata san ta tsaya ta kaiwa Allah kukan ta ba, sai de Anty Chideh, zuciyar Anty gaba 'daya ya lalace da zuwa gurin bokaye da 'yan tsibbu harma tana ganin kamar matu'kar kana da 'yan canji toh baka da matsala da komai arayuwa inhar bokaye na existing toh damuwarta ka'dan ce, bata san tasaka Allah a lamarinta ba sai dai bokaye sosai tayi amanna dasu da ayyukansu.
Wata 'kawarta ce ta ziyarce ta asatin bikin tasame ta cikin yanayi na damuwa anan tabata shawaran cewa wai tasaki ranta kawai asha biki agama lafiya duk da baso takeyi ba ta 6oye hakan aranta tunda yanzu tarasa mafita inyaso bayan bikin sai ta shi tsaye ta nemi hanyar 6illewa tayi maganin su gaba 'daya.
Aranar da matar ta fa'di haka Anty kamar zata cinyeta 'danye dan masifah, da 'kyar matar tasamu ta fita ta wuce inda ta fito tana mai dana sanin kawo wannan shawaran datayin, Anty cewa take wai dan me matar zata ce haka, tana nufin ta tsaya kenan har sai angama bikin tana kallo, tana nufin idanu zata zuba kenan tana gani 'danta ya auri waccen _banza_ _dangin mayun_ , tajima tana kunfar baki baub wanda ya tankata agidan, dayake ma Abbah baya nan alokacin, house maid ne ka'dai da ita agidan, da 'kyar Anty tasamu ta lallashi zuciyarta tayi shiru.
Sai dai wani abu da batasani duk wannan dramar da Anty keyi akunnan Mahmud kaf aka yi su har sai da yaga matar tafita sannan shima yakoma 6angarensa, dama shigowar sa gidan kenan yanufo parlour daniyar duba ta, sai kuma yaji suna wannan maganar.
Hawaye yake ta faman sharewa na ba'kin ciki da takaicin halin da mahaifiyarsa ta cusa kanta 'karfi da yaji, har yaushe Anty zata gane ta dawo kan dai dai, har yaushe zakace a kullum sai kayi jayayya da lamarin ubangiji bayan shike da kai ba kai kake dashi ba.
Hawaye Mahmud yake sharewa yake wannan tunanin, babban dalilin dayasa tun farko yanuna baya son auren nan kenan, dan bazai iya tsayawa ya juri ganin Fatima awani yanayi ba, dan yasan Anty bazata ta6a saduda taso zuri'arsu ba, wannan wani irin rayuwa ne?, karo na barkatai kenan daya ke jin irin mugun alkaba'in data ke bin danginsa dashi, bayan yasan ako ina zasu tsaya ko suje ita ce abin zagi basu ba ga duk wanda yasan halinsu gaba 'daya.
Darajar haihuwa kawai Anty take ci amma wani lokaci Mahmud jiyake tamkar ya sha'keta saboda kawai ya huta da ganin ba'kin ciki awanan gidan.
Duk da lokuta da dama yana tanka mata akan abinda takeyi 'din sai de baya jan maganar sosai sai ya 'kyaleta haushi ma baya barin sa ya 'dau dogon lokaci tare da ita, haka kuma be fiya son suna jayayya da ita ba akan abu.
Bayan fitan matar ne kuma sai Anty ta zauna tayi tunani da kanta akan maganar matar sai kuma taga hakan kuma fah yafi mata, saboda bata san ta ina zata fara ba yanzu kam amma bayan angama biki hankalin munafukai ya kwanta asannan ne ita kuma zata bayyana nata haukan.
Sosai tayi na'am da wannan shawarar da zuciyarta ta batan, takuwa bishi dan Abbah da kansa yayi mamakin yanda farat 'daya Anty ta sau'ko ta zubda dukkan makamanta na ya'ki ta kama shirin biki babu 'ka'k'kautawa, yanda ta nuna tana son auren ma har in baka sani ba zakayi zaton ko tafi Abbah ma burin son ganin anyi auren angama.
Mahmud ne ka'dai yasan dalilinta shikuwa akullum addu'ah yake kar Allah yabata sa'an cutar da kowa, dan yasan ha'ki'ka sihiri gaskiya ne, tsafi gaskiyar mai shi.
*INAJIRAN GANIN MUHAWARAR KU READERS.........* π€π»
ππ»
_Comment_
_Vote_
_Share_
*Salmerh ce*π
[10/2, 6:01 PM] Ummiyo: π *CAPTAIN ABBAS* π
By
*Salmerh MD*
Luv storyπ
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
π« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
π«
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_Dedicated_
_2 all masoyan_ _cApTaIn_ _AbbAs._ π
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
_Happiness is not a goal, but a way of life._
π
Ώ *48*
Anty da kanta ta 'dauki driver suka je da Abbah gidan abokin Abban ta sake duba kayan da aka harha'da 'din, anan ta nuna cewa wasu abubuwan ai sunyi ka'dan ya kamata a'kara gaskiya saboda wannan bikin na _kai_ _da kai ne_ .
Speechless Abbah ya zauna yana kallon iyayin da Antyn keyi, take kuwa ta sake tura ku'di wa Hajiya Aisha tace a'karo kayan tanaso bikin 'danta ya kasance fitattace wanda za'a jima ana kwatancensa aduniya.
Hajiya Aisha kanta tayi mamakin yanda abin ya dawo, domin ba haka labari ya iso mata ba da farko ganin alokacin Abbahn shine tsaye akan komai, sosai tayi mamakin yanda Mum Mahmud 'din ta canja cikin 'kan'kanin lokaci, dan akwanakin baya ka'dan kafin zuwan yau akullum in suka yi duba da yadda Abbahn yayi ruwa ya kuma yi tsaki akan lamarin auren ba sa cewa komai sai dai suce Allah ya shiryi Mahaifiyar Mahmud 'din, Allah da ikon sa kuwa ashe shiriyar tata na kusa yanzu kam sai dai suce _"ALHAMDULILLAH"_ dan Mum Mahmud tabawa kowa mamaki alokacin da basu zata ba.
Aranar Anty bata koma gida ba kasuwa ta wuce tayi siyayyah sosai ma kanta, kaya tsadaddu ta siya ta bada 'dinkin express a inda tasan bazasu bata matsala ba, bata damu da tsadan 'dinkin ba ita damuwar ta tasamu adai dai lokacin da zata bu'kace su.
Ta dawo gida da sauran ragowar siyayyan data yi ni'ki-ni'ki a hannu.
Tun daga ranar Anty bata 'kara nutsuwa guri 'daya ba akullum tana hanyar fita, kasuwa da sauran abubuwa.
Haka duk mutanen data san zata gayyata duk ta gayyace su daga 6angarenta, 'kawayenta ma wasun sunyi mamakin canjuwarta ta amma koda sukayi magana sai tabisu da murmushi kawai batare da ta basu gamsashshiyar amsar da suke son ji ba.
Akwana biyu kacal da sa'k'kowar Antyn har gida yafara cika da wasu daga cikin 'yan uwa da abokan arzi'ki, hatta 'yan uwan Abbah da suke 'kauye 'kalilan daga cikin su sun samu sun zo hakama yan uwan Antyn.
Abin mamaki Anty duk ha'dasu tayi tai musu sau'kar bangirma, bata nuna mugun hali ba koka'dan bata bari sun samu 'kofara da zasu zageta da ita ba wanda hakan duk yana cikin target 'dinta ne nagaba.
Abbah da kansa ya nemawa Mahmud 'din gida flat house mai kyan gaske ya kuma zuba komai na bu'kata dai-dai da zamani sai 'dan abinda ba'a rasa ba, sai dai gidan babu nisa da gidan Abbah yake duk a area 'daya suke, da farko ma Anty takawo shawarar cewa wai ko a side 'din Mahmud za'a kawo amaryar, har Abbah yaso ya amince domin shi be kawo komai aransa ba game da canjawar Antyn zatonsa shiriyah ce kawai tazo mata daga Allah, amma da aka sanar da Mahmud shi kam sai cewa yayi a'a shi ba zai zauna a nan ba gaskiya sai de anemo wani guri daban, jin hakan yasa Abbah ya yarda da batun Mahmud 'din dan shi lalla6a shi yake yasamu yaga de an 'daura auren yasan daga lokacin komai zai wuche yazama tarihi.
Hakan yasa ya nema masa gidan da kansa ya biya ku'din lokacin ma Mahmud 'din be sani ba sai daga baya Abbah ya 'dauke shi ya kaishi gidan dan yaga yanayin gidan ko ya masa.
Shikanshi Mahmud ya yaba da tsarin gidan, dan shi dama yafison gida flat mutun yafi sakewa aciki sai dai kuma duk da haka sai da yayi wa Abbah complaint cewa wai ai sun yi kusa sosai shi fah bahaka yaso ba yafison yayi nisa dasu.
Ido Abbah ya kwalalo yana kallonsa da mamaki " Mahmud wai lafiyarka kuwa"?
Abbahn ya tambayeshi.
Baiyi magana ba illah 'dago hannunsa dayayi yana duba tsadaddiyar agogon dake 'daure atsintsiyar hannunsa.
Cigaba da magana Abbah yayi.
" Babana dan zakayi aure shine zaka guje mu gaba 'daya har baka son zama kusa damu?"
"Bahaka bane fah Abbah"!
Kwafah Abban yayi kana yace "toh menene?"
Shiru Mahmud 'din yasake yi ya sunkuyar da kansa 'kasa.
"Mahmud karfa laifina ni danasa ka kayi aure alokacin da baka shirya ba yashafi wata daban, inaso kaji tsoron Allah Mahmud adukkan lamuranka , wallahi idan ka kuskura ka cutar da yarinyar nan azaman aurenku da ita bazan ta6a yafe maka ba, sanin kanka ne ni...nine na nemi ha'din auren nan da kaina, kuma kasan inde har hakane kuwa bazai yiwu in zuba ido inga ancutar da ita inakallo ba batare da nayi magana ba, dole zan 'dauki mataki matu'kar hakan yafaru koda kuwa waye ne yata6ata"
Mahmud kansa ya 'dago ya kalli Abbahn nasa sannan yace
"Abbah nifah bani da burin 'kuntata wa ko cutar da Fatima arayuwata ko ka'dan............"!
" toh menene "?
Abbahn yatari maganar Mahmud 'din da sauri.
" Tausayinta nakeji ni Abbah "
" you see......,"Abbahn yafa'di tare da nuna Mahmud da yatsansa yakuma cigaba da fa'din.
"Ai shi yasa nake ce maka akullum kaji tsoron Allah, ina son ka sani cewa daga ranar da akace an 'daura maka aure toh nawi ne babba ya hau kanka bana wasa ba, daga ranar amanar Allah ta hau kanka duk abinda ka aikata kai da mahallici ne kar kayi zaton ko babu wanda yaganka, idan tausayin nata kakeji da gaske tun yanzu zakayi 'damar zama da ita idan kuwa tausayin ta dan zata auri wanda baya son aurent ne toh kasanar dani inji...."
Shiru Mahmud yayi yana sauraran maganganun Abbahn, shi kanshi yasan gaskiya Abbahn yake fa'da masa amma shi koka'dan abinda ke ransa beyi matching da na Abbahn ba, taya Abbah zaiyi tunanin shi zai cutar da Fatima dan kawai ansashi ya aureta bada son ranshi ba, ai ko da ace yana bacci ne aka tashe shi aka ce ga matarka an aura maka ita bazai cutar da ita ba ballantana kuma Teemah,! yasani daman idan yace be son zama guri 'daya dasu dole daga Abbahn har Anty sai sunyi tinani daban kowa da abinda zai zo cikin ransa,shi kuwa manufarsa tayin hakan daban ce da tasu.
Har Abbah ya kammala da nasihar tashi Mahmud bai ce masa komai ba shiru yayi yana sauraransa, sai daga 'karshene da Abbah yace masa kar yaga kamar yamanta da batun zuwa Yobe ne dan yaga yayi shiru, yace kawai ya 'kyaleshi dan yaga alamar bason zuwa yake ba kuma dan kar abun ya masa yawa shiyasa ya 'kyaleshi amma hakan bawai yana nufin ya bashi 'kofa bane da zai ci zarafin yarinya
ba ko da bayan auren dan bazai lamunci hakan daga gareshi ba.
Aranar akan wannan maganar suka kusan wuni da Abbah dan har suka koma gida Abbah be daina yi masa tuni akan magabar ba haka yake yin ta fa'da-fa'da, nasiha-nasiha, garga'di-garga'di. Tausayintan da Mahmud yace yake jine yafi tsayuwa aransa dan takamamme ya rasa dame zai fassara ma'anar hakan.
Koda Anty tasamu labarin gidan da Abbah ya nemawa Mahmud itama sosai tanuna farin cikinta azahiri harma take nuna musu zumu'dinta nason zuwa ganin gidan itama yayinda take jin tamkar wuta ne azuciyarta yake ci dan ba'kin ciki da takaici, taso Mahmud ya zauna acikin gidan da suke saboda zatafi saurin cimmah burikanta akan auren cikin sau'ki amma Mahmud yayi mata yawa, sai de duk da haka ba ta yi 'kasa a gwiwa ba tace de _" su zuba_ _sugani "_ .
Ana gobe 'daurin auran dasafe Daddy ya 'kira Daddyn Abuja yake tambayar labarin Abbas sai Daddyn Abuja yace ai a kwana kinnan ma yazo amma kwanansa 'daya yakoma bakin aikinsa yace kasan 'dan naka gwani ne wurin bin doka, baya son wasa da aikinsa.
Dariya daddy yayi tare da fa'din ai hakan yana da kyau shine daidai domin sau'ke nauyin daya rataya akansa, ya'kara da fa'din shima yasamu labari agida sunce masa Abbas 'din yazo amma yakoma, yace amma fah dukda haka kar Abbas yace min bazai zo ya halarci wajen 'daurin auren nan ba"?
Daddyn Abuja cewa yayi
"Ehh toh gaskiya bamuyi maganar nan dashi ba amma bari zan tambayame shi naji ya ake ciki".
" yauwa kace masa injini nace auren fah ahannunsa na dan'kata gaba 'daya shine zai bada auren Fatiman ma'ana shi zai kasance _alwali_ agareta.
Baki Daddyn Abuja ya washe tare da fa'din
"Ahh gaskiya abu yayi kyau bari zan sanar dashi yasamu lokaci ya taho kafin goben, nima anjima da yamma insha Allahu ina hanya"
" Toh bakomai Allah ya tsare ya bada sa'a"
Daddyn Teemah ya fa'di tare da yanke 'kiran.
ππ»
_Comment_
_Vote_
_Share_
*Salmerh ce* π
[10/2, 6:01 PM] Ummiyo: π *CAPTAIN ABBAS* π
By
*Salmerh MD*
Luv storyπ
*Wattpad @*
*Serlmerh-md*
π« *DA BAZARMU* *WRITTER'S ASS*
π«
We are here to make you happy,smile,educate and to realized that we are the best among all.....
*DA BAZARMU* *MUKE TUN'KAHO*
_Dedicated_
_2 all masoyan_ _cApTaIn_ _AbbAs._ π
*Bismillahir* *Rahmanir Raheem*
_Trust is like a paperβ¦....Once it's crumpled, it can't be perfect againβ¦......_
π
Ώ *49*
Koda daddyn Abuja ya sanar da Abbas sa'kon daddyn Teemah Abbas ji yayi tamkar zuciyarsa zata fita daga 'kirjinsa ta yo waje tsabar yanda bugunta ya 'karu, shiru yayi batare da ya bawa daddyn nasa amsa ba, ha'ki'ka badan daga bakin mahaifinsa yaji maganar ba da cewa zaiyi tsantsar rainin hankali ne yasa aka za6eshi domin yayiwa Teemah wakilcin auren ta, amma sanin daga bakin mahaifinsa yaji da kuma sanin wanda yaza6e shin shiyasa yayi saurin kauda wannan tunanin azuciyarsa,
Hello!.....
Hellloo Abbas kana jina kuwa?....
hel.....
Muryarsa asanyaye yace " ina jinka Daddy"!
" aww toh naji shirune shiyasa"!
Daddyn Abuja sake maimaita abinda ya fa'din yayi zaton shi Abbas 'din be ji yace dashi 'dazun ba sai de tunkan ya 'karasa maganar Abbas ya tari numfashinsa da fa'din
" Daddy abubuwane agabana masu yawa wallahi, yanzu ma shirin tafiya nakeyi zuwa Kogi state bani da wannan lokacin"!
" toh ya za'ayi kenan"?
Dadyn ya sake tambayarsa.
"Daddy please ka wakilceni ko kuma kasa wani amadadina in babu matsala, zan 'kira Daddy Babban ma nayi masa bayani "
"Toh shikenan ba matsala, Allah ya tsare ya rufa asiri"cewar Daddyn, da "Ameen Ameen "Abbas ya amsa masa sannan sukayi sallama kowa ya ajiye wayar.
Abbas da tsaki ya cire wayar a kunnansa dan ma Daddyn Abuja yariga ya yanke 'kiran badan haka ba babu abinda zai hana shi jiyo tsakin da Abbas 'din yabi bayan wayar dashi.
Baya yakoma ya kwantar da jikinsa tare da 'daga kansa sama yana jujjuya kujerar dayake kai 'din, wani huci yake fitarwa tamkar wani wanda ya dawo daga gudun kilometre.
" kar Allah yasa a 'daura auren in de har sai ni zan bada shi, mthewww"
Ya 'karasa da jan tsaki kana ya sake 'daukan wayar yayi dialling no. tsawon mintina biyu ne ya 'daukesa a maganar yana kammalawa kuwa ya mi'ke tsaye da hanzari yafara rage kayan jikinsa.
Wanka yashiga sharp-sharp ya watso ruwa ajikinsa ya fito, shiri yayi cikin kakinsa na sojoji gwanin birgewa, dan ba 'karamin kar6arsa uniform 'din keyiba, kamar kar ya rabu dasu har abada idan yasaka su.
Zama yayi dan saka socks da takalmi, yana gamawa da shirin yafito ya kulle 'dakin ko wayarsa ma be tuna ya 'dauka ba, hularsa ce kawai ya ri'ko a hannunsa ya tafi.
Taku yake cikin ta'kama da 'kasaita duk da cikin hanzari yake tafiyar amma hakan be hana bayyana isarsa afili ba, Abbas 'karshe ne wajen iya tsarawa kansa komai, ciki kuwa harda tafiya be barta abaya ba, musamman idan ya shiryo cikin uniform 'dinsa jiyake tamkar yafi kowa, jin kansa yake kamar bashi ba, alokacin jin kai da miskilancinsa 'karuwa sukeyi sosai.
Ballantana yanda yake samun girma aduk lokacin da ya fito hakan ba 'karamin birgesa yake ba, dan dayawa daga cikin sojojinsu na girmama shi, ciki kuwa harda wa'danda suka girme wa shekarunsa suka kuma fishi da'dewa a akan aikin nasu, shiyasa akowani lokaci yake godiya ga Allah da kuma daya ya tsaya tsayin daka ya jajirce dan ganin ya samu wannan matsayin daya kai 'din ayanzu.
Ko yau 'dinma daya fito daga block 'dinsa hakanne yafaru, dan duk inda ya ha'du dana 'kasa dashi sai de kaga suna 'kamewa suna mishi gaisuwar ban girma, ko kulasu ma bayyi yake wucewarsa dan abin da ke gabanshi ne damuwarsa awannan lokacin, hakan kuwa bazai hana su cigaba da sara masan ba.
Office 'dinsu direct yawuce ya nemi jin batun tafiya Kogi state 'din da aka ce zasu da kuma lokacin da za'a yi tafiyar, aka sanar dashi cewa nan da 2hrs ne tafiyan, da 'kyar ya samu yayi cancelling sunan shi aciki aka maye da wani daban inda da kanshi ya sanar da wancan 'din cewa akwai tafiya nan da 2hrs dan haka ya shirya ya taho kafin lokacin.
Uzuri sosai ya basu kafin yasamu suka cire sunan nashi da shara'din cewa ths is d first and d last da zai 'kara yin irin hakan ya kuma amincewa sannan ya 'kara da neman pass na kwana biyu.
Da yamman ranar ya baro Porthacourt ya sau'ka a Abuja, gidan babu kowa ya samu sai me gadi kawai dan daddyn sama aranar suka wuche kuma dawuri suka tafi, tafiyar motan da zasuyi daga Maiduguri zuwa Damaturu ne yasasu tafiya dawuri dan basu so dare ya same su ahanya saboda dokar da ke wannan yankin alokacin mai tsanani ce.
Kaya kawai Abbas ya canja cikin wani kaftan brown colour bayan yayi wanka tare da gabatar da sallan la'asar dake gabansa daga nan ya fita daga gidan yatafi airport da 'kyar yasamu flight 'din da zashi maiduguri 7:00pm, daga can yashiga gari yarage lokaci tare da ziyartan wani abokinsa.
Koda Abbas ya sau'ka a maiduguri hotel ya nema ya yada zango dan bayajin zuwa gidan oga philip wannan karan, duk dama ba'karamin taimakonsa oga philip 'din keyi ba ko ta wajen ha'da shi da driver ma dayake yi, amma wannan karan ya gwammaci ya hau motar haya kawai yafi masa badan komai ba sai dan ji da yakeyi yanajin haushin kowa ma gani yake kowa damuwa ne.
Abbahn Mahmud da shi kanshi Mahmud 'din already sun iso da sauran abokan arzikinsu da suka zo musamman domin halartar 'daurin auren, suma ganin suna da 'dan yawa sai suka taso da wuri cikin sa'a kuwa basu samu matsala da komai ba suka iso akan lokaci kuma lafiya 'kalau, dan har sun riga Daddyn Abuja ma isowa.
Daddy acan wani guest house 'dinsa dake bayan legislative quaters ya sauke su harma da wasu ba'kinsa na nesa da suka samu damar amsa gayyatar daddyn, 'dakuna isassu ne agidan so babu wanda ya takuru da wanzuwar 'dan uwansa anan kowa ya sau'ke gajiyarsa.
Babu wanda yabi ta kan Abbas domin daddy da kansa yayi musu bayanin yanda sukayi da Abbas 'din awanni ka'dan dasuka gabata, zatonsa shi ka'dai ne yasani dan Abbas da zai masa maganan be nuna masa cewa yayiwa Daddynsa bayani ba.
Dukkansu basu damu da rashin sa agurin ba dan sunsan yanayin aikinsa bakamar su bane da su suke sarrafa kominsu yanda suka ga dama.
Mahmud ne ka'dai ya damu da rashin Abbas 'din dan tun safe yake ta trying layin Abbas 'din amma baya samunsa, da farko yayi ta 'kira ba'a 'dauka daga baya kuma not reachable, ko bayan isowarsu ma yayi ta gwadawa amma baya samunsa.
Mahmud bahaka yaso ba, yaso Abbas yakasance tare da shi awannan hidiman dan shike 'kara masa 'karfin gwiwa a kullum.
Amma dayaga be same shi ba dole ya ha'kura da nemansa fatansa de Allah yasa lafiya yake. Sai dai yasa aransa cewa matu'kar Abbas be halacci wurin 'daurin auran nan ba yace da kansa zai je har porthacourt 'din yaji dalilinsa nayin hakan bayan shine yasashi ya amince da auren tun farko.
*****
Washe gari saturday gari na wayewa kowa yafara shirin 'daurin aure.
Abbas da safiyar ranar ya iso around 9:30 am, alokacin kuwa shirye shirye yariga ya kankama kowa harkar gabansa yakeyi, ta 'karamar 'kofan dake bayan gidan yashigo dan baya son kowa ya ganshi shi, gaishe-gaishen damuwan nan ma shi baso yake ba, Allah ya taimake shi babu kowa ta bayan hakan yasa cikin natsuwa ya nufi 'kofar dake kitchen wanda ita zata sada shi da ainahin 'dakunan dake cikin gidan.
Koda yashiga ma wasu mata yagani a a palourn kuma ayanda ya lura duk ba'ki ne be wayi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 24 Chapter of 67