Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kamata ki aikata ba, akwai illa ciki? Fadin amfanin me zai mata? Shikenan kin bude mata cikinki ta san sirrinki ta san sirrin mijinki, yadda muke mu'alama da komai ta sani, ban jidadi ba kuma in miki daukar mace mai hankali ne mai sani ya kamata, ban yi tsammanin zan ga haka ba, kuma ban jidadi ba” Ya karasa da dan fada domin ya fahimci kamar bata dauki abun a wani abun ba, ganin haka ya saka jikinta yayi sanyi, shi kuma be sake ce mata komai ba ya tashi ya fice daga dakin. Da kallo ta bishi har ya fice sannan ta dauki wayar felling guilty ta bude chat din tana dubawa tare da mayar da amsar tambayar da Huda take mata, kamin da kara da. “Ke yau ya duba wayata ya ga chat dinmu” Sannan ta kashe data ta gyara kwanciyarta da kyau, domin abu ne da ta sani idan suka samu tsabani shi yake bata hakuri, shi yake nemanta. Ba dabi'arsa bace bawa miji hakuri idan ta yi laifi, haka kuma ba mace ce mai saurin karbar laifinta ba, idan ma har ta aminta tana da laifin kenan. And to her hira da kawa ko a group chat da mata yan'uwa Normal ne domun suna suna fadar yadda suke tasu mu'alamar kuma dukansu mata ne babu maza, bugu da kari tana ganin aminci da jindadi ke saka irin wannan chat din. Bayan duk wannan ma why zai dauki wayarta ya shiga chat dinta da kawarta ko kawayenta har ya ga abun da suke tattaunawa, a ganinta a nan kam shi yake da laifi, kuma dai chat irin wannan tsakanin mata ai ba wani abu ba ne, dan haka bata shirya ba shi hakuri a yanzu ba. Yadda ta ayyana haka ne ya faru domin bayan ta yi bachi ya dawo dakin ta kwanta a kusa da ita, daman can no matter how suka samu tsabani baya taba raba gado da matarsa balle kuma har ta kai ga ya raba daki. Yayi bachi not like usual yadda ya saba, domin yana son ya nuna mata illar abun da ta yi, dan haka be shirya abun karyawa ko ya jira ta shirya masa ba yayi wanka ya yi shirin office ya fice daga gidan at early morning. [4/20, 9:58 AM] 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆: *🍒 ABOKIN RAYUWA 🍒* *© Khadeeja Candy* SARAC STARS. C - Pen... ✍️ Page 7️⃣ TURHAN POV. “Shikenan zan jiraka a waje” Ya aje wayar ya nufi gurin da suitcase dinsa yake ya bude ya ciro wani karamin roll on ya murza a wuyan hannunsa sannan ya aje a mirror dake dakin ya sake nufar wayarsa ya dauka ya saka aljihu ya dauki key din dakin ya fice ya rufe dakin. Stairs ya bi har ya sauko daga hawa na uku zuwa na daya, kamin ya karaso kasa ransa ya gama baci domin Turhan ba mutum ne mai son motsa jiki ba sai dole, ko kadan baya son aikin wahala balle kuma wahalar ita kanta da baya hada hanya da ita. Harabar hotel din ya fito yana kallon yadda tsari da kawar babbar hotel din take daga kasa, domin sun sauka sa dare ne a jiya, gajiya bata bashi dama kamar yadda hutu ya bashi a yau da safe ya kalli ko'ina ba. Kusa da wata flower ya tsaya yana kallon ko'ina da kyau, kyam idonsa suka sauka akan wata hallita mai ban tsoro, mutum ne irinsa namiji mai kirar mazaje da jarumtaka, Turhan ya dauke idonsa daga kallon mutumen da shi ma kallonsa yake babu kyabta ido. Ganin sarkar Cross a wuyan mutumen da murdaddiya fuska irin na wanda baya sha'awar dariya, ya saka shi fahimtar addininshi da nasa akwai banbanci, tattoo jikinsa ma ya sanar da hakan. Feeling awkward ya saka shi ciro wayar dake aljihunsa ya fara dannawa, ya dauki lokaci a haka kamin ya sake dagowa ya kalli harabar, a karo na biyu ya sake kallon gurin da mutumen dazun yake tsaye yana kallonsa and wannan karon ma yana tsaye and still kallonsa yake har yanzu, irin kallon nan mai daure kai ga wanda ake yi ma shi, da mace ce take kallonsa sai yace ko tana sonsa ne, amman namiji kamar wannan da zai yi wahala su hada hanya da imani abun tambaya ne a kallon da yake masa, zuciyarsa ta raya masa wata kila yayi masa kama da wani ne da ya sani ne, idan ba haka ba kallon da yake masa yayi yawa, and babu wani dalili da zai saka yayi ta kallonsa haka. Kallo ne mai rikitarwa da mamaki ga wanda ake yi ma shi, hakan ya saka Turhan jin babu dadi kuma ya dan tsorata, ganin ba garinsu ba ne, haka kuma ba gurin da ya saba mutanen ba ne, ko be taba zuwa ba, ya kan ji ana fadar bad side na Lagos, dan haka dole ne yayi taka tsantsan. Takawa ya fara yi cike da izza da takamar da suke zame masa jini ya isa gate din hotel din hannayensa rumgume a bayansa sai kamshi yake zubawa tafiyarma ita kanta ta karbe shi kana ganinsa kasan babban mutum ne kuma dan babban gida. Sai da ya fice daga katon gate din dake bude sannan ya juyo kadan ya kalli mutumen dazun domin jikinsa ya ba shi har lokacin yana kallonsa, ga mamakinsa sai ya ga mutunen yana kallonsa har yanxu, kusan kallon yanxu yafi muni fiye da na dazun, domin a yanzu yana iya hango tsana da harzuka a idanuwan mutumen da be san waye ba, be kuma san dalilin haka ba. Wannan karon Turhan be tsaya shawarta zuciyarsa ya daga wayarsa ya kira Faruk. “Wai baka karaso ba har yanzu? I'm not safe here fa, ina jin tsoron irin mutanen da suke a nan gaskiya” “Gani isowa ranka ya dade, na kusa karasowa, ka kwanta da hankalinka babu komai In Shaa Allahu, Hotel din da ka sauka hotel ce mai tsaro sosai, ba wani matsala In Shaa Allahu, da akwai matsala ai oga Aliyu ba zai bari na sauke ka a wannan hotel din ba” “Ina fatan haka” Ya fada sannan ya sauke wayar tare da jan dogon numfashi, wannan karon be yarda ya sake juyawa ya kalli bayansa ba, balle ya san da wanzuwar mutunen dazun ko akasin haka, sai ya cigaba da tafiyarsa. Kamin ya sake daga wayar ya kira farar uwar data kawo shi duniya. Ringing daya biyu ta daga, daman bata ignoring call dinsa idan tana kusa da waya, tun a lokacin da suke shiri da juna da kuma yanzu da ta sauya mu'amala da shi, banbancin wacan kiran da kuma yanzu, idan ya kira bata kusa bata mayar masa da kiran, kamar yadda ba zata amsa kira da saukin kiransa ba, ba kamar can farko ba da take daukin kiransa da far'a da na jindadi kuma yake kiransa idan ta samu miss calls dinsa, a yanzu sai dai ta amsa masa duk abun da zai fada ne ba a cikin dadin rai ba. “Ammy ina kwana?” “Lafiya Kalau” “Ammy na sauka Lagos jiya da dare sosai, na yi tsammanin ganin kiranki ki tambaya ko na iso lafiya” “Gashi ai mun yi magana yanzu, kuma da ba lafiya kake ba dole za a kira a sanar min” Wani abu na rashin jindadi ya ji ya ratsa zuciyarsa, jiki a sanyaye ya furta. “Haka ne, Ammy na zo nan ne neman Aisha kuma duk saboda ke ne, ba dan ke ba ba zan yi haka ba, ina fatan dacewa ki taya ni da” Kalmar duk saboda ke ne, ya tsayawa Ammy a rai lallai ne ta sani danta yana son farincikinta da albarkarta haka kuma yana nuna cewar har a yanzu bana son zabin nata kawai dai zai nemi Aisha ne saboda gyara laifina ba dan tsantsar nadama da kaunarta ba. “Fatan nasara Turhan Mohamed Abdo” Tana fadar hakan ya aje wayar. Ta lumshe ido ta hade bakinta guri daya ta gumɗe tana maida numfashi a hankali. Jawahir ta rufe magazine din dake hannunta tana kallon Ammy cikin yanayi na damuwa. “Ammy kina daukar abun nan da zafi ne sosai, ni da Maama dukanmu yayane a gurinki, be kamata ki yanke shawara ko ki yi wani hukunci mu saka baki ba, amman bahaushe yace mai shawara aikinsa baya baci, sai dai ba shi da sirri, kuma mai shawara ba ya nadama, amman na san ranki ya bace sosai akan Yaya Turhan amman ya kamata ki yi hakuri...” Bata karasa ba Ammy ta bude idonta ta kalleta, tsoron furuci ko fadan da zai fito a bakin Ammy ya saka ta yanke maganar da bata karasa ba. Ammy ya gyara zamanta da kyau tana kallon Jawahir. “Jawahir mahaifinki ya taba baki labarin cewar bayan haihuwar Turhan ban sake haihuwar kowa ba?” It take her 5 seconds to answer. “Ammy abu ne da kowa ya sani a familynmu bayan Turhan baki sake haihuwa ba” “Amman ya taba fada dalilin da ya saka bayan Turhan ban sake haibuwar kowa ba?” “Aa be taba fada mana ba, Abba baya zama yayi hira da mu yadda kike yi Ammy” Ammy ta yi shiru tare da dora hannunta daya akan daya. “Dauke breakfast din nan” “Baki ci komai ba Ammy” Ammy ta daga mata kai, Jawahir ya tashi tsaye da dauke breakfast din ya fice, Ammy ta mike tsaye ta nufi karfen dake balcony din ta tsaya yana kallon harabar gidan. Ammy na jin lokacin da Jawahir ta bude kofar falon ta fito balcony din da Ammy ta fi yawan zama musamman da safe idan zata karya ko kuma da yamma. “Mahaifinku ya taba fada muku cewar na zauna a gidan kaso?” Mamaki ya cika fuskar Jawahir. “Gidan kaso kuma? Yari fa kenan Ammy” Ammy ta daga mata kai ba tare da ta juyo ba. “A zamanin da na yi yan matancin, a cikin yayan sarakuna musamman na yankin arewa bana jin anyi wata yar sarki mai farinjini irina, ba nufin sarautar gidanmu ko kudin mahaifina ba, ina maganin farin jini ne wata baiwa da Allah ke hallita bawa da ita” Ammy ta juyo tana murmushi ta kalli Jawahir dake tsaye. “Ba ni da kyau sosai, haka kuma ni dan ba za a kalleni ace min mummuna ba, kamar yadda ni ba fara ba amman ba fi fararen matan kyau da shiga zuciyar maza, bana zama a guri na tashi wani be so ni ba, na yi farinjini sosai, yayan manyan mutane da manyan mutane sa kansu sun nuna sha'awar kulla danganta da mahaifina ta hanyar aurena, a lokacin da ace za a titsi ni na fitar da wanda nake so ba zan iya ba, domin hankalina ba a kan soyayya yake ba, kuma dukan masu neman aurena suna kyautata min yadda ya kamata na so su, mahaifina kuma yana alfahari hakan” Ta nufi kujerar data tashi ta zauna Jawahir ma ta zauna a kujerarta tana kallon Ammy fuskarta fal da mamaki. “Wata rana mahaifina ya karbi babban abokinsa kuma babban sarki garin Khartoum, masarautarmu ta san da zuwan sarkin kusan kasar ma ta san da haka, domin ya gana da shugaban kasar wacan lokaci kamin ya iso masarautarmu, bayan tafiyarsa mahaifina ya shigo cikin masarauta ya saka aka kira ni, na zauna a gabansa kaina na kasa ya sanarmin cewar ya kyautar da ni aure a gurin dan Sarkin Khartoum, a wacan zamanin idan iyaye suka yanke shawara ba a musawa ko da a gurin bayi ne balle kuma yayan sarakuna, wacan lokacin yayan sarakuna basa aure sai yayan sarakuna yan'uwansu, na amsa masa babu musu, a lokacin ba zan iya amsa cewar ina son kyautar da mahaifina yayi min ko akasin haka ba, iyakar abun da zan iya shaida an aurar da ni ga mutanen da ba su san darajar dan'adan ba, mahaifina ya kulla alakar ne saboda ya karfafa zumuncinsu, kuma yayi bugun kirji cewar Balarabe ya auri yarsa Maryam ta yi farinjini, sai dai mahaifina ya manta cewar balaraben Asali baya son kowa sai balarabe dan'uwa, kadan ne suke son wani yaren, sai dai ko kadan basan son bakar fata, kuma basa son girmama ra'ayinsa, basa kallonsa da kima, balaraben mutum baya son bakar fata ko kadan, da fari sun nuna kamar za su janye, domin mijin da aka ba shi kyautata be shirya karin wani auren ba bayan wanda yake da shi da farko, ban san miya ja ra'ayinsa ba, sai kuma ya amince” Ammy ta share hawayen da ya sauko mata. “Daga lokacin da aka daura min aure, aka dauke ni akai kai a masarautar, sai na fara fuskantar kalubale, tun da na shiga masarautar ban saka mijina a idona ba sai da aka yi sati biyu, idan na fito cikin masarautar sai na fuskanci wulakanci, ba irin wulakanci na bawa da sarki ne, wulakanci irin na banbancin launin fata, wulakanci irin na wanda aka kyauta a gurin da ba a da bukatarsa, na fuskanci tsangwaba domin yarenmu da na su ba daya ba, kusan babu wanda ya san an auro a wajen masarautar domin ba a fita da ni, ba a nuna ni a matsayin surukar gidan, sai matar da na tarar wato uwargidana Maimunatu, surukarna suna wulakanta ni mijina da abokiyar zamana ma haka, ko da rana daya ban taba fadawa mahaifinta halin da nake ciki ba saboda bana son ya ji cewar ya zaba min abun da be dace ba” Ta rufe ido hawaye na sauko mata. “Shiyasa nake matukar tausayin Aysha, ni kadai na san irin tsangwamar da ta fuskanta a masarautar, domin na san yadda abun yake, gashi kuma Turhan ya watsa min kasa a ido ya tsaba alkawarin da ya daukar min” Ta bude ido har lokacin hawaye ke saukowa daga idonta, ta mike tsaye ta nufi kofar falon ta bude ta shiga, kai tsaye ta nufi stairs ta shiga dakinta. EMILY POV. Ta kara minti talatin akan lokacin da Amal ta fada mata na shigowa office, domin ta shigo kamfanin karfe bakwai saura mintuna na safe, a tare suka nufi elevator ita da mutumen da suka shiga wacan karon, wannan karon ma a tare suka shiga, ta rasa dalilin kaddara na hadata da wannan mutumen, ko da yake a kamfanin yake aiki kamar ita, dole za su rika haduwa ko da bata so, kamar yadda za ta yi ta haduwa da mabanbanta mutane a gurin. A yau din bata cikin walwala da zumudi kamar jiya, saboda danta dake can kwance a asibiti, gashi kuma yarta Fatima na fushi da ita, thirdly kuma bata samu wadataccen bachi ba, ga gajiyar aikin jiya tattara a jikinkinta, sai ya zama mood dinta ya canja gaba daya, ta sama silent ba kuzari. “Good Morning” Ta gaishe shi saboda tana son ta yi masa tambayar da ba lallai ne idan ta yi ma Boss dinta Amal ta amsa mata ba. Aliyu ya kalleta kawai ya dauke ido ba tare da ya amsa mata ba, hakan kuma ya harzukata. “Daman fa tambaya ce kawai zan yi, karka yi zaton ko ina son kullum alaka da kai ne ko wani abu makamanci haka, haduwar da mu ke kaddara ce ke hada mu, ba wai dan ina son haka ba, ni maza ba burge ni suke ba, so ka sauke girman kan please” Ya juyo ya kalleta a nan din ma ba zai iya karyata kyaunta ba, amman ba zallar kyaun yake kallo ba yadda take bulbule shi da masifa a duk lokacin da kaddara ta hada su ne yake mamaki. “Daman zan tambaye ka ne, ko bakon zuwa ma'ana new comer zai iya daukar hutu saboda wani uzuri na rashin lafiya” Nan din ma be jin zai iya amsa mata, sai kallonta da yake kamin ya dauke kansa. Da yaren turanci take masa magana, sai dai ganin be amsa ta ba ya saka ta wani furuncin da Hausa. “Wato dai ma'aikatar nan kowa dan iskan kansa ne, kowa jin kansa yake, na tambaya wata kila shi ma sabon dauka ne kamar ni, sai kallona yake babu amsa kamar kurma, idan na sake magana kace min aku” Wannan karon be kalleta ba, be kuma bar murmushin zuciyarsa ya fito a fuskarsa ba har suka tsaya a 4 -floor. Ta saka kafa zata fice “Tambaya kawai mutum yayi maka shiru kamar kurma” Ta fada da Hausa. “Aku” Ya furta a daidai lokacin da Elevator ya zo rufewa, ya furta mata hakan ne saboda ta san yana jin yaren da ta yi magana da shi. Sai ta juyo da sauri ta kalli elevator da already ya rufe, zuciyarta na bugawa da karfi, sai a lokacin tunani ya zo mata, what if shi babban ta ne a gurin aikin? Wata kila yana a hawa na 5 ne ma ko kuma sako yake kaina, amman be yi kama da karamin mutum ba. Bata dauka yana jin hausa ba, a tunaninta Igbo ne ko yorba, shiyasa bata yi magana da duka yarukan ba sai hausa, bata yi tsammanin a kusa zata samu mai jin hausa ba kamar ita ba, ko da yake ita ma zama a arewa ne ya saka ta kware a hausar ba mamaki shi ma ya zauna a can din ne. Idan ba haka ba Parthcourt da Zamfara ai akwai nisa sosai, a take ta tunatarta kanta abun da ta manta, kamfani ya kan hada mutane kala kala wasu ma daga wata kasar wasu kuma daga wasu yarukan. Fargabar rasa aikinta ko janyowa kanta wata sabuwar matsalar ya hanata ta sukuni har ta gyara office din Boss dinta ta gama, duk kuwa da wani bangare na zuciyarta yana raya ba wani babba ne a kamfanin ba, domin bata taba ganin wani ya rako shi ba, haka kuma zuwan da yayi da safen nan ya fahimtar da ita haka, domin da babba ne a kamfanin ba zai shigo a irin wannan lokacin ba sai 10 ko 9am kamar yadda Amal take shigowa, wannan tunanin ya yaudari zuciyarta har ta samu sukuni. ALIYU POV. Kusan duk wanda ya san shi fari sani a kamfani ya ga shigowarsa a irin wannan lokacin zai yi mamakin haka domin be saba shigowa a irin wannan lokacin ba. Ya wuni da tunanin matar nan da sake gani a yau, yadda halshenta yake iya furta hausa da kyau haka ya nuna alamar ta taba zama arewa ko kuma daga arewar take ma, sai dai abun da ya daure masa kai siffarta gashin kanta ba sun sanar da duk wani mai kallonta cewar ita din baturiyace, haskenta yayi yawa blue eyes dinta da jan gashinta ya fahimtar da shi haka. Sai dai ya kasa tantancewa shin ita din ce matar da abokinsa yake nema ko mai kama da ita? Idan har kama ce ta ina taya sunan zai zama daya Aisha? Ta ya idon da gashin zai zama hali da jikin ne kawai zai banbanta? Sau hudu yana daga waya zai kira Turhan sai kuma ya fasa domin ba shi da wata kwakkwaran hujjar da zai rike cewar matar da yake gani a kamfaninsu ita din ce matar da Turhan yake nema, idan tsabanin haka ne zai wahalar da abokinsa ne, saboda haka yana bukatar hujja, domin Turhan ya fada masa cewar ita wacan tana da jiki kuma bata da masifa gashi bata yi boko ba, ba kamar wannan ba. Ko dai yan biyu ne, ya tambayi kansa sai kuma ya rasa wa zai bashi amsar. Misalin karfe daya ya shiga bandakin office din yayi alwala ya fito ya kashe Bluetooth din dake kunne yana fitar da kirar'ar Qu'ane ya shimfida carpet yayi Sallah, sannan ya mike tsaye ya fito daga office dinsa. “Nick, if there are any newly recruited employees named Aysha, please bring their files to my office” “Okay Sir” Ya bada umarnin sannan ya fice ya sauka kasa gaba daya, Elevator na budewa yayi arba da mutane biyar masu jiran budewarta ciki har da kyakkyawar karamar yarinya mai goye da jakar makaranta, tana sanye da uniform pink short skirt and White shirt, an yi mata parking din bakin gashinta a baya, tana ta kallonsa da blue eyes dinta kamar yadda yake kallonta babu kyabta ido. Zanen halittar fuskar yarinyar ya saka shi manta mutanen dake mika masa gaisuwa kuma suke jiran fitowarsa domin su shiga Elevator. [4/20, 9:58 AM] 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆: *🍒 ABOKIN RAYUWA 🍒* *© Khadeeja Candy* SARAC STARS. C - Pen... ✍️ Page 8️⃣ “Hi” Ya furtawa yarinyar yana faɗaɗa fuskarsa da murmushi, matsawa ta yi baya ta ta kauce daga mutanen da duke tsaye jiran fitowarsa, hakan ya bashi damar fitowa har ya amsa gaisuwar da ake mika masa, sannan ya kalli yarinyar data matse jikin ginin dake bayanta kamar zata shige ciki, gashi ta hade rai irin na yaron da yayi arba da bakuwar fuskar da be sani ba. Tsayawa yayi a gurin har sai da kowa ya shige cikin Elevator sannan matsa kusa da ita yana murmushi ya mika mata hannunsa. “Hi” Ta hade hannayenta ta kawar da fuska. “Momy na tace na daina magana da wanda ban sani ba, za a iya sace ni” Murmushin fuskarsa ne ya fadada ya gingina kai. “Gaskiya ne, ni ma ta fada min haka ta fada miki shiyasa ba zaki amsa ni ba idan na miki magana, amman na san ki mahaifiyarki ta nuna min hotonki a wayarta tun da dadewa shiyasa yanzu ma ina ganinki na gane ki” Ta juyo ta kalleshi. “Da gaske” Ya daga mata kai. “Uhm-” “To waye kai?” “Ni...” Ya nuna kansa yana tunanin me zai fada mata, sai ta ce. “Are you her new boyfriend?” Ya wara ido. “Boyfriend? No... Karki ji haushi ki yi kishin Babanki” “Ni ba ni da Baba ai, Momy na tace bata haife ni da Baba ba, tsaya ma ka ji sunana Fatima Aysha Emily, amman yayana yana da Baba shi sunanshi Londom Hamza, amman shi babansa ya mutu kamar yadda Momy ta fada, amman ni ba ni da Baba, amman ka ga kowa yana sa baba ko a makarantarmu kowa yana da baba ban da ni, shiyasa na matsu Momy na ta yi new boyfriend so that na samu Baba, saboda na tsani Vito bana son shi shi kuma wai yana son Momy ne, amman ni bana son shi....” Sai da ta kai ayar zancen sannan ta numfasa, mamaki da burgewa ya saka Aliyu jan numfashi. “Hmmmmm wannan yarinyar ya a je da ke Hi-five” Ya mika mata hannu ta mika masa nata suka taba, shi kam abun nema ya samu daman bincikarta yake son yin, sai kuma yayi sa'ar ita din ku ace gurin magana, ya kama hannunta yana murmushi tunawa da yayi da matar dazun wanda tace idan ta sake masa magana ya kirata da aku and he did. “Ciki zaki shiga?” “Eh Momy na tace na zo na same ta a nan saboda yau nannynmu tana gurin London ba shi da lafiya yana asibiti shi sickle ne kuma Autisms, baya yarda da mutane sosai daga Vito sai Nanny Chidimma sai Momy sai ni” Ya nufi elevator ya danna ta bude. Sai da suka shiga sannan ya sake tambayarta. “Shi Victor shi ne Babanki? Ko saurayin Momy kika ce ko?” Ta tofar da yawu. “Allah ya kiyaye bana son shi, sunan shi Vito not Victor Vito sunan yan Italian ne da aka samo daga latin word “Vita” Vito yana nufin rayuwa, sunansa ke nan?” “Amman miyasa kika tsane shi? Ba shi da kyau ne” “Yana da kyau, amman baya yin dariya, and wata rana idan Momy ta bata masa rai sosai yana dukanta, i just hate him, kawai ina zama da shi ne dan dole, amman Momy tace da sabon aikin da ta samu yanzu zata siya gida zamu koma can Vito ba zai sake zuwa gurinta ba” Aliyu ya daga girarsa sama ya sauke yana tan tabe baki kadan. “Wow, okay” “Ina son haka, and na san idan Momy ta bar gidan Vito zata samu Boyfriend sai ya zama Daddyna, ni ina son Daddy” Aliyu ya rage tsayinsa ya kama fuskarta ya rike cike da tausayi, ko bata fada masa uwarta ba ya fahimci akan waye take magana, secondly fuskar abokinsa dake shimfide a yarinyar yake kallo. “Amman kai kana da girlfriend?” Yayi murmushi kawai ya mike tsaye ba tare da ya amsa mata ba. Ita ma bata sake cewa komai ba har suka sauka a 5floor. “Momy na tace a 4 Floor zan sauka office na biyu

Chapter 6 of 63