karkashin Vito amman har yanzu ba ki yi ba"
Emily ta dube ta.
"Zan yi Fatima zan nema har ma dace zan zama miki irin rayuwar da kike so, ba ni da wani nauyi da ya rataya a wuyana yanzu sai na ki, amman ki daina abun da kike yi, ba haka yara suke ba, meyasa ke kika fita dabam?"
Ta yi shiru tana turo baki, Emily ta ja jikinta ta rumgume tana jin rashindadin fadan da ta yi mata a yanzu.
"Momy, yanzu tun da London ya mutu zan iya amfani da sunan mahaifinta a makaranta? So that yan ajinmu su daina min dariya?"
Ta tambaya murya kasa kasa, Emily ta hade wani abu daya tsaya mata a makoshi ta lumshe ido.
"I miss him"
Cewar Fatima cikin sautin kuka. Emily ma kukan take.
"I miss him too"
Ta kara kankame yarta hawaye masu zafi na sauko mata. A haka Chidimma ta zo ta same su bayan direban dake gidan Vito ya kawo ta.
"Zan yi kokari na baki rayuwa mai kyau Fatima, ni kam ba zan miki abun da iyayena suka min ba, ba zan taba bari ki ji cewar baki da kowa ba, ba zan taba wulakanta ki kamar yadda mahaifin London da naki suka yi ba, ina son jini ko yaya yake"
"Momy waye babana? Baki san bani da baba ba? To waye kuma baba na?"
Fatima ta tambaya tana lafe a jikinta. Emily ta share hawayenta da sauri.
"Idan kina son uba to ki rike Vito a matsayin Ubanki"
"Bana son shi"
Emily ta dago ta.
"Baki da hujjar tsanarsa, kalli gidan da kike zaune, makaranta mai kyau ya saka ki, ya dauki mai girka muku abinci, tufafi sai wanda kika zaba kike sakawa, a ciki wadanda na aura akwai wanda ya bani rabin rayuwar da kike ciki yanzu?"
Ta dauke da mari tana daka mata tsawa.
"Karki sake min maganar abun da ya shafi ubanki"
Fatima ta saka wani irin ihu ta dafe kunci, Emily ta tashi ta bar mata falon. Sai dai bata iya fushi ba dan haka ta dawo ta rarrashi yarta saboda tana jin babu mai rarrashinta sai ita ta rumgumeta, a tare suka kwana kamar yadda ta saba mata a yanzu tun bayan mutuwar London kullum a gado daya take kwana da Fatima.
Washe garin ranar bayan Fatima ta tafi makaranta Chidimma tana ta aikin gyara gida Emily ta shirya ta fita saboda tana jin gidan ya mata babu dadi. Taxi ta shiga ta tafi gurin sabuwar kawarta Tasmia daman bayan can ai bata da wani gurin zuwa. Bata same a apartment din nata ba dan haka ta zauna a gurin har sai da Tasmia ta dawo. Da gangan ta yi kamar bata gane Emily ba.
"Malama lafiya?"
"Lafiya kalau"
"Toh na ga kin zauna a nan ne"
"Ina jiranki ne"
"Kina jirana? Kin san ni ne? Wani abun zan miki ne?"
"Haba Tasmia"
"Malama ni fa ban san ki ba ban taba ganinki ba"
Emily ta mike tsaye.
"Karki fara wannan wasa"
"Fine na gane ki, amman fa gaskiya ba zaki zo ki janyo min matsala ba"
"Bana fatan janyowa kowa matsala, kin tsorata ne?"
"Yanzu dai ba wannan ba me kika zo yi nan"
Ta yi shiru na mintuna.
"Bana da gurin zuwa ne kawai na zabi na zo nan, kuma na ji anje nemana gida na yi zaton ko kece ko Aliyu"
"Ba ni ba ce, ni ba zan tafi gidanki ba yanzu kam, Aliyu ma ba shi ba ne domin be taba zuwa nemanki ba"
"Okay zan tafi, duk lokacin da kika ji zuciyarki ta natsu da ni, kin san gidana kuma kina da number da wayata, sai anjima"
Emily ta tafi ta barta tsaye a gurinta tana binta da kallo. A taxi ta dawo kamar yadda ta tafi a taxi ta shigo gidanta tana share hawaye. A falo ta samu Vito zaune Chidimma na zuba masa ruwa a cups.
"Do you take my phone?"
Ta tambayi abun da yafi zame mata wajibi a yanzu, domin jiya ta duba ko'ina bata ga wayarta ba. Vito ya kalli Chidimma yayi mata alama da kai sai ta tafi dakinta ta dauko wayar ta mikawa Vito da hannu biyu be karba ya aje cups din dake da sauran ruwa ya kalli Emily, sai ta juya da wayar bangaren Emily da hannu daya ta mika mata.
"Akwai wata number data turo miki sako har sau hudu wai ki kirashi ya damu da ke"
Emily ta karbi wayar da hannu daya sannan ta ware dayan hannunta ta wanke fuskar Chidimma da mari.
"How dare you take my phone? Har ki karanta min sako?"
"Ta saman screen na karanta sakon ni ban san password din ba ma, shi ma na kunna wayar ne kawai saboda na tabbatar tana yi saboda faduwar da ta yi a hannuna, bayan haka kuma na kashe ta kamar yadda take"
Cewar Chidimma cikin kuka.
"Waya aikeki daukar min waya? Tsawon kwanakin nan da na yi ban damu da wayata ba ashe tana gurinki?"
"Ba ita ta dauki wayar ba, ni na bata ta aje, amman me zai saka wani ya turo miki sako? Miyasa zai damu da ke?"
Vito ya bata amsa sannan ya dora mata da tambaya, Chidimma kuma ta fashe da kuka har da zubewa kasa.
"Burinka kai ka raba ni da kowa, so kake ka ga ina rayuwa cikin kunci, matar da na samu mai kyakkyawar zuciya ta rike ni a matsayin kawa yau naje ta nuna bata san ni ba, saboda ka lalata tsakaninmu ka firgitata"
Ta dauki ragowar ruwan da ya sha ta watsa masa a fuska.
"Ni na saka ya damu, zo ka kashe ni ka huta"
Ta wuce fuuuu ta haura sama, binta yayi da kallo sai kuma yayi murmushi ya kalli Chidimma dake ba shi hakurin ruwan da Emily ta watsa masa, ya rikota ya mikar da ita tsaye.
"Karki damu"
Ya fice ya bar falon. Emily ta shiga dakinta ta zauna tana ta haki kamar wanda ta yi yaƙi, ta kunna wayar ta cire Password ta shiga messages box dinta na sms sakon Aliyu ne kadai sakon da ya banbanta da sauran sakwanin dake wayarta na Mtn. Ta karanta duka sakwanin sannan ta gwada kiran numbersa.
ALIYU POV.
"Wato baki ma wani damu da ni ba kalli yadda kika yi kiba kika yi fari"
Yana maganar yana kai mata abincin da ta shirya masa a karamin falon mahaifinsu. Ita kuma tana rike da wayarsa tana abun da ta saba yi masa a waya, wato bincike amman har ta yi ta gama bata ga wani abun da zata zarge shi da shi ba.
"In ji wa? Wannan kibar fa ta haihuwa ce kowace mace tana yi da muke Video call baka gani ba"
"Aa waya ai rage miki kyau take rabin raina"
Ya sake kai mata wani spoon din.
"Kina nan kina cinyewa Alhaji abinci ko?"
Ta yi dariya tana kallon wayar da kira ke shigowa da number da babu suna a jiki, a take ta amsa kiran ta kara a kunne.
"Hello... Aliyu..."
Ta ji muryar mace tana ambaton sunan mijinta.
"Wacece wannan?"
"Emily ce"
Mai kiran ta amsa mata kai tsaye.
"Emily....?"
Ta furta da mamaki, Aliyu ya aje Spoon din hannunsa ya mika mata hannu.
"Ba ni wayar"
Ta mika masa kamar ba ita ba.
Aliyu ya dora wayar a kunnensa.
"Emily kina lafiya?"
"Ina lafiya"
"Babu abun da ya same ki?"
Kameela ta zaro ido tana sakin baki.
"Aa na kira ne saboda na riski sakonka a wayata"
"Okay, ina tare da Matata yanzu"
Gudun kar zuciyar Kameela ta sosu ko ta yi zargin wani abu ya saka be ce mata zai kirata ba sai kawai ya kashe wayar. Tsabar mamaki Kameela bata san lokacin da ta mike tsaye tana kallon Aliyu ba.
_______________________
Sannu ‘yan uwa mata! Kin gaji da kayan da ba su da salo, ba su da inganci? To yanzu lokaci ya yi da za ki sabunta wardrobe ɗinki da kaya masu kyau, masu ƙima daga Khadeeja Candy Store
Muna da abaya masu kyau irin na zamani, masu sauƙin sakawa da jituwa da dukkanin lokaci whether ki je wurin biki, ko casual outing.
Kuma fa, ba abaya kawai ba muna da bedsheet masu launin kwantar da hankali, masu kyau a gani da taɓawa. Idan kina son daki ya zama kamar hotel, to bedsheet ɗinmu sun dace da ke
Kayanmu masu kyau ne, farashinsu? Ai sai kiyi mamaki sauƙi ne sosai. Muna nan a Kano State, kuma muna delivery zuwa ko’ina!
Ki danna follow yanzu, ki biyo mu a TikTok https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1
da Instagram https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0
Ki ga sabbin kaya masu kyau da rangwame.
Zaki sami kayan Kitchen masu inganci, kayan sakawa na zamani, da electronics masu ƙayatarwa duk a farashi mai sauƙi.
Za ki iya saka tufafinmu ki fita lafiya, kitchen dinki kuma ki kawata shi da kayan Kitchen dinmu, da bedsheet dinmu kuma za ki yi barci cikin annashuwa komai daga shagonmu!
Baki da lokaci? Muna da sauƙin oda ta waya ko WhatsApp - 08036126660 muna aika kaya zuwa ko ina!
To me kike jira? Biyo mu yanzu a WhatsApp https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08
Ba kawai kaya ba ne salo ne, ƙima ce. A Khadeeja Candy Store.
Ki zo yau, ki ɗanɗani bambanci, Khadeeja Candy Store inda kyau da salo ke haɗuwa.
[5/18, 7:55 PM] 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆: *🍒 ABOKIN RAYUWA 🍒*
*© Khadeeja Candy*
SARAC STARS. C - Pen... ✍️
FOLLOW ME ON 👇🏻
FACEBOOK
https://www.facebook.com/profile.php?id=100008156177914
TIKTOK
https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1
INSTAGRAM
https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0
CHANNEL
https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01
KHADEEJA CANDY STORE
https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08
Page 2️⃣6️⃣
Ya daga kansa kadan ya kalleta irin duban na lafiya?
"a gaban idona Aliyu?"
"Zauna"
Ya mata umarni.
"Wacece wannan miye tsakaninka da ita?"
"Zauna"
Ya sake fada peaceful.
"Na ban zauna ba, wacece wannan matar?"
"Emily ce, tsohuwar matar Turhan ina tunanin min mun taba magana da ke akanta"
"Toh ya aka yi kake Communicating da ita? Taya number wayarka ta shiga hannunta? Har ta kiraka har ka damu da lafiyarta? Na shiga uku kirjina"
Ta dafe kirjin tana numfashi da karfi daman tuni ta fara daga masa murya irin dagawar da kowa zai iya ji.
Kansa ya sauke kasa be sake ce mata komai ba, domin ya san halin matarsa da kishi karamin abu ne ya fita hayyacinta a yanzu nan ta fara masa hauka.
"Ni ban ma yarda ba, mu ga wayar mu gani waya sani ko soyayya kuke ka boye wani guri da ba zan gani ba"
Ya mika mata wayar ta karba ta sake shiga chat dinsa ta duba ta fito ta sake duba inbox dinsa, kamin ta shiga longcalls dinsa ta yi forwarding number Emily zuwa number ta.
"Wai ke da na yi ma alkawarin ba zan miki kishiya ba, miye abun tashin hankali idan kin ga ina magana da wata? Har yanzu hankalinki be kwanta da ni ba? Kuma ko aure zan yi ta ina zan aure matar da abokina ya aura?"
"Aliyu ka ci amanata Wallahi da kake waya da matar nan, ashe ina nan ina wankan jego kana can kana soyayya da wata, jira kawai kake na daga kafa"
Ta fada cikin kuka da hargowa, sai ya mike tsaye ya karbi wayarsa.
"Idan kin huce kin sauko zan dawo mu yi magana"
Ya juya ya fice ya barta a gurin tana gurnanin kuka, wani irin ihu ta saka tana shure shure duk ta watse abincin da suka ci da wanda ya rage a warmers ta watse kayan gaba daya a kasa kamar mai aljannu, da sauri Anty Shafa da Farida suka shigo suna tambayar lafiya sai kuma ta kasa fadar komai saboda bata son su ji abun da Aliyu ya aikata kar su mata dariya ko su ce Allah ya kara.
"Ba komai"
Ta tashi tana cigaba da kukan ta fice daga falon suka bita da kallo.
"Ba komai take wannan kukan"
Farida ta fada sai Anty Shafa ta kyalkyale da dariya.
"Ya gumama ai kadan kika gani daga halin maza, yarinyar da kin yi auren kudi ma da kin more, amman yanzu ai sai bakincikin ya miki yawa ko rabuwa kuka yi ga kiyayyar aure ga ta siyasa"
"Ai dai tun da ta nace sai shi sai ta ga babu dadi kuwa"
Cewar Farida Anty Shafa ta fice domin labartawa Hajiya Asma'u wato Mahaifiyarsu abun da ke faruwa, Farida kuma ta fita kiran mai aikinsu domin gyara gurin da Kameela ta bata.
Kameela na shiga dakinta ta fada kan gado ta fashe da wani sabon kuka tana jin kamar ta shake wuyan Emilyn da bata taba gani ido da ido ba. Ta dago ta nufi wayarta ta dauka ta duba number Emily din ta kira number, sai kuma ta kashe gudun ajin abun da take fada ko halin da take ciki ya saka ta fito dakin ta sauka kasa ta fice daga bangarensu zuwa bangaren Mama Barakat, ta bangaren ma ba shiga ta yi ba waje ta samu inda babu wanda zai jita ta sake kiran number Emily ringing biyu Emily ta amsa kiran da tsoro domin bata tsammani shigowar kira daga bakuwar number.
"Hello"
"Sannu karuwa, yar iska marar aji mai bibiyar mazan mutane, me kokarin raba aure fasika yar titi, kafirar banza yar wuta, saboda ke baki tsaya kin yi zaman aure ba shiyasa kika kokarin ruguza nawa auren ko? Toh Allah ya fiki, Wallahi ki fita sabgar mijina ko na kashe ki, Aliyu ya fi karfinki ba zai taba sonki ba ba zai taba auren mace irinki ba, karki sake kiran mijina a waya karki sake magana da shi idan ba haka ba Wallahi sai na lahira ya fiki jindadi, akan mijina zan iya komai, shegiya marar tarbiya haihuwar hasara, ke je gurin mijinki mana, wato so kika ki kashe min aure kamar yadda ke naki yake kashe ko? Me yasa dole sai Aliyu? To mijina musulmi mai addini babu abun da zai yi da fasika irinki, wato so kike ki lalata masa tarbiyar ko? Ki shige jikinsa da sunan matar abokina ki gwada masa duniya"
Uffan Emily bata ce mata ba har ta yi maganganun da zata yi ta gama.
"kina jina dam ubanki ko na sake maimaitawa? Ko da yake ke ai baki da uba ma, baki san zafin hakan ba ko da an zage ki, shiyasa yanzu kike son ki rusa gida ko? Toh ki shiga hayyacinki ni bakar macijiya ce"
Ta kashe wayar tana huci, kamin kuma ta saka ihu ta fashe da kuka, ta dawo main door ta shiga bangare Mama Barakat ta zauna a falonta tana ta rusar kuka, Mama Barakat ta fito Kitchen da saurinta tana tambayar lafiya. Da yake Kameela ba mace ce mai rufin asiri da iya rike cikinta ba sai ta fara fadin.
"Aliyu ya cuce ni, ya ci amanata mutuwa zan yi zuciyata"
Mama Barakat ta yi mata tambayar duniya bayan wannan Kameela bata sake cewa komai ba, ganin haka ya saka Mama Barakat barin bangarenta ta tafi bangaren uwargidanta tana tambayar me ya samu Kameela take kuka da kiran Aliyu ya cuceta. Hajiya Asma'u dake zaune gefen gado tana kwance sarkar zinari ta girgiza kai cikin saurin maganarta ta ce.
"Mu ba mu san me ke faruwa ba, bata ma fada min ba, amman yara sun shigo suna fadin sun ganta tana kuka ta watse kaya, yanzu kuma kuka yake can?"
"Wai ko dai ce mata yayi zai yi aure? Kin san fa yayi mata alkawarin ba zai mata kishiya ba, kuma yadda Anty Kameela take da shegen kishin nan zancen kishiya ne kawai zai daga mata hankali haka"
Farida dake kwance gefen da Hajiya Asma'u take zaune ta fada.
"Aiko da na ci mutuncinsa Wallahi, dan ubanshi har cikin gidan Ubanta zai tarar da ita kuma ya fada mata zai mata kishiya? Kuma fa karamin aikin uwarshi ne ta saka shi kara aure a yanzu, ko dan abun da aka yi a gurin haihuwar nan"
Cewar Hajiya Asma'u, Mama Barakat tace.
"Wata kila dai wani abun ne, amman ga alamu Aliyu yana da hankali ba zai fada mata zai kara aure a gidansu ba, ya kamata dai a bincika"
"Baki gama sanin duniya ba Baraka karki ce zaki fada min mutanen cikinta, ke lokacin da aka rufe idon Alhaji aka aura masa ke ba ido da ido ya kalleni yace zai aure ki ba?"
Ta karasa da hararar Mama Barakat, Mama Barakat ta yi murmushi kawai ta juya ta fice. Hajiya Asma'u ta kalli Farida.
"Miko min wayata na kira shi, ya zo na ji abun da yake faruwa, idan ma wai auren ne burinsa to ko sai dai ya rabu da Kameela dan yadda take da kishi ba zan bari ya halaka min zuciyar yarinya ba shi ya je ya more rayuwa ya bar ni da jinya, ko kuma ya fasa auren domin babu wanda ya masa cilas din yi mata alkwarin ba zai kara aure ba, kuma dan ya kai dan iska ya zo har cikin gidan nan ya fada mata zai kara aure? Aiko yau sai na ci mutuncinsa, yaushe ma aka yi auren da za'ace ya kara aure, duk makircin uwarsa ce na sani saboda ba son Kameela take ba"
Farida ta mika mata wayar, Hajiya Asma'u ta kamo number Aliyu ta aika masa kira.
ALIYU POV
A gidansa dake Kaduna ya koma daman a can yake sauka a duk lokacin da ya zo ko suka zo tare da Kameela, a gidan aka fara kaita lokacin da take Amarya anan aka mata jere da komai, akwai mai gadin gidan da mai share harabar sai kuma mace daya dake zuwa every Friday ta yi mopping din gidan ta saka turare ta gyara ko'ina. Bayan ya faka motarsa ya bude ya fito ya shiga cikin gidan kana ganinsa kasan baya cikin jidadin, ba komai ya janyo masa haka ba sai rashin uzuri da kuma fahimtarsa da matarsa bata yi, yadda take da zafin kishi kuma hankalinta yake gushewa yana damunsa, ga kuma rashin rufin asiri idan ba haka ba miye na daga murya tana ihu da kuka akan abun da be taka kara ba balle ya karya.
Shi dai kam ya so ya samu mata mai fahimta da uzuri, ba laillai sai aure ko soyayya kadai ke shiga tsakanin namiji da mace ba, akwai wanin abun da zai iya hadawa aiki ko taimako ko kasuwanci ko kuma wani abun na dabam kamar dai shi da ya shiga tsakanin Emily da Turhan. Wayarsa ya ciro daga aljihunsa ya gwada kiran Kameela domin ya ji babu dadi a halin da ya barta, sai ya ji line busy ya kashe kiran ya sauke numfashi a hankali ya tashi ya shiga Bedroom dinsa ya zauna sannan ya kira Emily. Kiran farko bata daga ba na biyu ma haka, a ka'idarsa baya yi ma mutum kira fiye da biyu amman saboda yana son magana da ita ta son sanin halin da take ciki sai ya sake kiranta a karo na uku. Ta daga amman ta yi shiru bata ce komai ba.
"Emily?"
Bata amsa ba, shi kuma be damu da hakan ba ya cigaba.
"Daman na aika miki sako ne saboda na damu na san halin da kika ciki, ban sani ba ko Vito yayi miki duka saboda abun da na aikata ko kuma ya kore ko wani abun, shiyasa na aika miki da sakon kuma ina yawan kiran wayarki a kashe, na je gurin Tasmia nemanki ita ma bata samu labari daga gareki ba, amman dai kina lafiya ko? Ba wata matsala?"
Ta yi shiru tana hawaye, kukanta ba shi da sauti amman jikinsa ya raya masa kuka take.
"Emily akwai wata matsala ne?"
"Aa zan yi farinciki idan ka aiko min da motata ba tare da na zo dauka ba ko kuma kai ka zo gidana ba, kuma zan fi kowa farinciki idan baka sake kirana ba, ko neman ji daga gareni, na gode da duk wani taimako da ka yi min tun daga ceto rayuwata da ka yi har zuwa taimaka min gurin rufe London na gode, alakarmu ta tsaya nan"
Ta kashe wayar, mamaki fal a fuskarsa gaba daya ma ta taushe kusurwar tunaninsa, me ya faru? Vito ne na cilasta mata yanke alaka da shi tun a yanzu ko kuma tana cikin wata matsala ne da bata son ya sani? Ko kuma barazana yayi mata da rayuwarsa ko ta yarinyarta? Sai ya ji ya gagara natsuwa da hakan a take ya sake kiransa sai ta ki ta daga.
"Ba kince kina neman hanyar da zaki saka min da abun da na yi miki ba? To yanzu ina son ki saka min ta hanyar fada min me yasa kika yanke alakata da ke? Kina cikin wata matsala ne?"
Ya aika mata da sako, sms din ya fita wayarsa kiran surukarsa Hajiya Asma'u na shigowa wayarsa. Sai ya daga da sallama
"Assalamu Alaikum"
"Aliyu ka zo yanzun nan ina nemanka"
"Hajiya Lafiya?"
"Idan ka zo zaka ji"
Ta kashe wayar, a yanayin yadda ta ji muryarta ta gautsi ya san ba lafiya ba. Ya mike tsaye kenan sakon Emily ya shigo wayarsa.
"Matarka ta yi min iyaka da kai a yanzu, ta kira ki kafira yar wuta, da fasika karuwa, na ji ni ba musulma bace amman ni ban taba yin fasikanci ba, tace ban san zafin uba ba, ban zauna gidan aure ba shiyasa nake son ruguza nata ka yi hakuri ba hakan nake nufi ba, bana nufin lalata rayuwar kowa, bata fahimta ba tace ina son na lalata rayuwar aurenta, to me zai saka na yi hakan? Miye ribata idan na yi hakan? Bana bukatar wani tashin hankali a yanzu, ban san kana da mata ba, amman zuciyata ta raya min at age dinka daman ba zai yiyu ace baka da aure ba, ka yi hakuri dan Allah kuma ka bata hakuri"
Yana gama karanta sakon ya koma ya zauna yana cire hullar kansa, domin yau shigar manyan kaya yayi. Abun da ya fara zuwa zuciyarsa shi ne a ina Kameela ta samu number Emily ma? Ya fito daga sakon Emily sai ya ci karo da na Kameela dake kasan na Emily a nan ya duba akwai sakwanin da suke turawa juna amman last sakon da ya tura daga wayarsa zuwa nata layi number Emily ce aka yi forwarding, sai ya fahimci dalilin karbar wayarsa da ta yi dazun da sunan bata yarda ba bari ta duba a nan ta tura number Emily.
Sosai ya kai makura gurin bacin rai, kuma ya fahimci idan be yi ma tunkar hanci ba abun zai iya fin haka, domin Kameela bata tsaya ta yi tunanin abun da ya dace da kuma wanda be dace ba, karamin aikinta ne ace ta sanar da iyayenta abun nan da ta faru wata kila ma shiyasa mahaifiyarta take nemansa.
Ya dauki hularsa ya saka ya fito harabar gidansa ya shiga motarsa cikin bacin rai ya dauki hanyar gidansu Kameela, yana isa ya faka a inda ya faka dazun ya fito ya nufi kofar falon, sai da ya boye bacin ran dake zuciyarsa sannan ya shiga falon gudun kar surukansa su zargi wani abu domin be san dalilin kiran da Hajiya Asma'u take masa.
Yan matan da suke falon suka amsa masa suka gaishe shi, sannan ya nemi guri ya zauna yana baza kamshi turare, daman Aliyu akwai kwarjini da cika ido sai idan ba a hadu da shi ba.
Hajiya Asma'u ta sauko fuska a daure tana sanye da Australian Lace mayafinta a kafada ta zauna a kujerar dake facing din ta Aliyu.
Anty Shafa ma ta sauko ta sai ta yi ma kanenta umarnin su fita falon, duk suka watse aka bar Hajiya Asma'u kawai sai Aliyu da Anty Shafa.
Aliyu ya gaishe ta cikin ladabi, sannan ya gaishe da Anty Shafa.
"Aliyu me ke faruwa tsakaninka da Kameela?"
Aliyu ya kalleta da mamaki.
"Ina Kameela take?"
"Tana bangaren Mama Barakat. Anty Shafa ta amsa masa.
"Me ya faru Hajiya?"
Ya tambaya.
"Shi nake son na sani, saboda ta shigo tana kuka yan'uwanta kuma sun ce ta fasa kayan abinci a falon babansu, kuma Baraka ta shiga tace Kameela sai kuka take tana fadin ka cuceta"
Aliyu yayi shiru yana danne abun da ke masa zillo a zuciya.
"Daman dai na kiraka ne na ji ko abun da zamu iya shiga ne a matsayinmu na iyayenta, kuma ba ina maganar saki ba ne, bana tunanin saki zai daga hankalinmu ko na Kameela, tsoron mu kar a karya alkawarin da aka yi mata ne, domin babu wanda ya san kun yi, dan haka be kamata a karya ba, kowace mace da yanayin yadda Allah yake halittarta yara ne ga su nan na haifa amman kowa da halinsa da kuma yanayinsa, ina tunanin ba cilas aka maka ka yi mata alkawarin ba zaka mata kishiya ba, kai ka sakata a daki ka yi mata alkawarin, mace mai irin zuciyar Kameela ni dai a matsayina na uwa da na san darajarta ba
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 63