bana son zama"
Ya rasa ta ina zai fara rarrashinta ta zauna domin baya son tafiya da ita gidansu Kameela, na farko dai yana ganin hakan kamar cin fuska ne ga Kameela na biyu kuma iyayenta ma ba lallai su fahimce shi ba domin ko kowa be gane yar waye ba Kameela zata gane kuma karamin aikinta ne ta fallasa shi a gabansu.
Ya mika mata dayar wayar da ita ya fi aiki da ita ya dauki wanda ya bata dazun ya saka aljihunsa.
"Wannan baki san me ke ciki ba, na kunna data zaki iya duba duk abun da kike so a YouTube ki kalli cartoon kuma ki sauke duk game da kike so, Momy ki na na san zata kira ta wannan wayar idan ta kira sai ku yi magana kamin na dawo?"
Ya karba ba dan ranta ya so ba, can ta kalli hotonsa dana Kameela dake makalle a falon.
"Waye wannan?"
"Matata ce"
Aiko take ta hade girar kasa da ta sama ya nukokoce kai.
"Ba zan zauna ba, so you have a wife"
"Yes Baby"
"I hate you"
Yayi murmushi
"I know I'm sorry, Bari na tafi na siyo miki chocolate da ice cream kinji?"
Sam ta ki yarda gaba daya mood dinta ya canja daya fada mata yana da mata, ita a tunaninta idan suka saba da shi zata iya dawowa gidansa ita da Emily su bar gidan Vito, amman tun da har yana da mata ai ba wannan damar.
"She's ugly"
"No she's not"
Ya amsa yana dariya.
"I want my momy"
"Bari na tafi na dawo sai na kaiki gurinta"
Daker ya samu ta yarda ta zauna sannan ya dauki dayan key din motarsa ya fice, daga gidan be zame ko'ina sai family house din su Kameela, a bangaren Mama Barakat ya faka ya fito yana tunanin ya kamata ace ya riko musu wani abu, gashi babu enough cash a aljihunsa, sai dai kuma babu yadda ya iya domin ya riga ya zo dama ace be zo ba ne sai ya tsaya ya nema.
Haka dai ya aje komai ya shiga bangaren da sallama, yaranta suka amsa masa suka gaishe shi sannan suka kawo masa drink da abincin, suka fice daga falon cike da tarbiya, babu jimawa Mama Barakat ta sauko sanye da wani lace mai tsada irin na su na yarbawa domin zama a cikin hausawa da kuma auren bahaushe be saka ta jefar da al'adarta ba, yaranta ma yawanci da yaren yarbanci take musu magana shiyasa duk sun iya yaren.
"Maraba maraba da Aliyu"
Ya sauka daga kan kujera ya zauna kasa saboda ta zauna akan kujerar.
"Haba zaunawarka mana"
"Aa nan ma ya wadatar, na same ku lafiya"
"Lafiya Kalau Alhamdulillah, ya hanya"
"Alhamdulillah"
"Maa Shaa Allah baka ci komai ba?"
"Already sai da na ci abinci na fito"
"Tohm, ina godiya dai Aliyu daka saurare ni kuma ka ni umarnina a matsayina na step mother din Kameela, hakan ya nuna kai yaro ne mai jin magana mai biyayya kuma mai tarbiya, na jidadi sosai Allah ya maka albarka"
"Ameen"
"ka shiga bangaren na su ne?"
"Aa na fara zuwa nan ne tukuna"
"To yayi kyau, da har jiya nake cewa ina son na sake kiranka, domin Kameela gaba daya ta fara fita hayyacinta abincin kirki bata iya ci, yarinyar nan tana sonka kai ma kuma na san kana son matarka, ni ban san me yake shiga tsakaninku kuke ta samun matsala ba"
"Kameela ta cika kishi ne, da abun da ya kai da wanda be kai ba duk na kishi ne a gurinta, bata tsayawa ta saurara kuma bata amfani da tunani kamin ta aikata abu, amman dai In Shaa Allahu ba za a sake jin kam mu ba"
"Hakan yayi kyau domin na tabbatar ita ma kanta a yanzu ta dauki darasi kuma zata gyara"
"Allah yasa"
"Ameen"
Mama Barakat ta ji kamar ta masa maganar Emily sai kuma ta ji rashin dacewar hakan, domin be kamata ta shiga tsabgar rayuwarsa ba, bayan kuma ta fada masa Kameela bata fada musu komai ba, sai kawai ta sauke numfashi ta ce.
"Tashi ka tafi, ka yi hakuri da duk abun da zaka ji ko ka gani gurin Hajiya, kasan ita uwa dole ta nuna bacin rai idan aka taba mata ya, balle ma Kameela bata fada mana dalilin dawowarta gida ba, amman dai duk yadda zaka yi ka yi iya kokarinka ka tafi da matarka, Allah ya kawar da fitina a tsakaninku"
"Ameen na gode Mama, tafiyar ta zama ta gaggawa ban riko komai ba, sai dai idan na koma In Shaa Allahu"
"Haba ina ce ai an zama daya, idan zaka zo gida sai ace dole sai ka riko wani abu? Yanzu ai mun zama iyayenka ba surukai ba, saurarena da kai yi kawai ka bi shawarata Wallahi ya fi duk wani abu da zaka ba ni na gode"
Yayi mata sallama ya tashi ya fice ta bishi ta kallon burgewa tana jin ina ma ace daya daga cikin yayanta yake aure yadda yake da biyayya da jin magana haka. Motarsa ya shiga ya yi mata key yayi reverse ya shiga bangaren mahaifiyar Kameela yana faka motarsa tana fitowa tare da kanwar Kameela cikin shirinta da alama fita zata yi, Aliyu ya fito mota ya nufo inda suke sai Hajiya ta yi kamar bata ga Aliyu, sallamar da yayi ma kanwar ce ta amsa masa shi ma cikin rainin wayo domin basa kallonsa da daraja gaba daya, ya mika mata gaisuwa bata amsa ba sai kokarin shiga mota take.
"Hajiya Gurinki na zo"
Ya dago ta kalleshi a wulakantacce kai kace ba shi da gata ko kuma dan talakawa ne.
"Ina jinka?"
Ya danna tafarfasar da zuciyarsa ke yi.
"Na zo ne akan maganar Kameela"
"Ina jinka bani da lokacin batawa fa fita zan yi, kuma saboda kai ka san ba zan fasa fitar da zan yi ba"
Ya hade yawu zuciyarsa na bugawa da karfi.
"Ina son na dauke ta mu koma ne"
"Kam uban nan"
Kanwar ta fada Hajiya kuma sai ta fito motar
"Ka dauke ta ku koma saboda a titi ka aureta? Ko kuma an fada maka bata da kowa? Ai ko baranta muka yi aka ba mu ita sadaka ba zaka shigo haka nan kawai ka dauke ta ku tafi ba, kuma ta inda aka hau ice ai ta nan ake sauka, kai karan kanka baka isa ka zo na tsaya tattaunawa da kai akan matsalarku ba, idan ma bikonta za zo toh ba kai ya kamata na gani ba, domin kai ka maida auren kamar wasan yara, haka kawai dan ta maka dadi zaka turo yarinya gidansu, yanzu kuma da ta yi maka dadi ka shigo kana fada min zaka dauke ta ku tafi, ai ba ni na baka aurenta ba ubanta ya baka aurenta kuma shi kansa yanzu yadda ransa ya bace ba lallai ne ya yarda yarsa ta koma inda ba a san darajarta ba, daman can abu ne da Allah ya riga ya tsara babu yadda za'ayi, amman da na san idan ka aureta haka zaka wulakantata kai da iyayenka ba zan yarda Kameela ta aureka ba ko zata mutu"
"Iyakar abun da zamu tattauna tsakanina da Kameela ne Hajiya ban da iyayena, domin iyayena babu abun da suka mata sai alheri, kuma ina tunanin da ace baki ga alamar za a rike Kameela da daraja ba, da ba za ku ba ni aurenta ba"
A take Hajiya ta zaburo masa da fada.
"Alherin me suka mata? Me suka kulla mata tun da aka yi auren? Duk tsabanin da kuke samu ummi ta taba tako kafarta gidan nan da sunan danta yayi ba daidai ba zata bada hakuri? Mahaifinka ma harkokin siyasarshi kawai ya saka a agaba, yanzu din ma ai ba kai ya kamata ka zo ba iyayenka tun da ba daga mu sai kai muka baka aure ba, kuma Kameela ba daga sama ta fado ba tana da gata, kar na sake ganin kafarka gidan nan da sunan biko wannan iskanci da tsageranci na surukan zamani ni ba zan dauke shi ba, kana neman bata min lokaci ina da abu mai muhimmamci a gabana"
Ya koma cikin motar ta shige direbanta ya rufe sannan ya shiga motar yaja suka bar Aliyu tsaye kunshe da bakinciki kamar ya kashe shi, meya ma ya zo tun farko meyasa ya kawo kansa? Sai a yanzu yake bakincikin neman auren kameela tun farko, domin auren macen da iyayenta ba su dattijai ba ne abu ne mai illa sosai ko da kuwa ita yarinyar tana da tarbiya. Shi aka yi ma laifi ya daure a haka ya zo bikon matarsa amman mahaifiyarta take fada masa magana son ranta.
Juyawa yayi ya shiga motarsa ya kama hanya yana yi ma kansa alkawari na damuwa ba ko cewa aka yi Kameela zata mutu akansa ba zai dawo bikonta ba. Yana hawa titin unguwar kiran Emily ya shigo wayarsa. Fakin yayi gefen hanya yana maida numfashi a hankali wani irin tafarfasa zuciyarsa take be san lokacin da ya daki sitiyarin motar da karfi ba tsabar bacin rai. Ya sauke ajiyar zuciya ya fi a kirga sannan ya bi kiran Emily da already ya yanke bayan ta yi ringing be daga ba.
KAMEELA POV.
Tana can kwance dakinta bata san wainar da ake soyawa ba har sai da Hajiya ta kirata tana mata gargadi wai karta kuskura Aliyu yace ta zo suke ta bishi daga ita sai shi ko saukowa ma kar ta yi ya ganta ko da ya kirata.
"Aliyu ya zo ne?"
"Eh wai wani ya zo bikonki a nan na bar shi na tafi gurin sabgogina"
Kameela ta bude baki kamar ta yi magana babu hali, domin ita kadai ta san yadda suka tsara da Mama Barakat har aka samu kansa ya zo, kuma ta san ita ce mai laifi amman be fada a gidansu ba kuma be fadawa iyayenta ba haka kuma ya danne komai ya zo bikonta meyasa Hajiya zata mata?
"Hajiya kuma kika ki saurarensa"
"Ke dalla can rufewa mutane baki, shiyasa yake wulakantaki ai, saboda baki san daraja kanki ba kina nuna masa rawar jiki da shegen so shiyasa yake gallaza miki yadda ya ga dama har da wani turo ki gida tsabar rainin wayo da wulakanci, kar na ga kafarki waje dan na san halinki shiyasa na kira na gargade ki"
Ka kashe ta tashi ta sauri ta leka windows dakinta bata ganshi ba balle motarsa, saukowa tayi kasa ta shiga bangaren Mama Barakat ta tambaye ta ko Aliyu ya shigo bangarenta.
"Ya shigo baki gan shi ba?"
"Kai..."
Ta juya ta fita da sauri tana kiran layinsa bugu daya aka daga sai ta yi shiru tana jiran ya fara magana.
"Hello."
Ta ji muryar karamar yarinya.
"Wacece wannan?"
"Hello can you hear me"
Fatima ta sake fada domin bata fahimci yaren Kameela da kyau ba.
"Yes who are you?"
"Sunana Fatima Aisha Emily"
Kameela ta sauke wayar daga kunnenta ta duba layi ta ga na Aliyu ne sannan ta sake maida wayar.
"Ina mai wayar?"
"Ya fita ya siyo min ice cream"
"Ke kina ina?"
Ta dayan bangaren Fatima ta kalli inda take.
"Ina falo"
"Falon wa? A ina?"
"A gidan Uncle Aliyu"
Da turanci Fatima take amsa mata. Kameela ta kashe wayar tana jin wani jiri yana debanta zuciyarta ma tafasa numfashinta har sama yake yana dawowa. Ta nufo bangarensu tana mamakim abun da ya kai wayar Aliyu hannun yar Emily domin ta san suna da ya kuma gashi yarinyar ma ta ambaci sunan mamanta.
"Wato Aliyu ba zai rabu da matar nan ba, kuma be shirya rabuwa da ita ba, wai da ita ya zo ne ko kuma yaya? Ni ban gane ba?"
Ta haura sama tana magana da kanta kamar wata mahaukaciya. Sai kuma ta sake kiran Number Fatima ta dauka kamar zata yi kuka.
"Kina damuna ina kallon Cartoon ne"
"Ke fada min a wane falon? PH ko Kaduna?"
"Kaduna jirgi muka shigo muka zo Kaduna ko da muka zo ina bachi ma"
Kameela ta kashe wayar tana jin kamar ta haukace tsabar bakinciki wato har Kaduna ya zo dayar Emily saboda ya raina aurenta kuma ya raina mata hankali, hijab dinta ta dauka ta saka ta fita dakin ta shiga dakin Hajiya ta dauki makullin mota ta sauko kasa ta fice falon babu wanda ya sani ta shiga motar Hajiya ta dauki hanyar gidan Aliyu, yau kam ta shirya ayi ta kare domin ba zata juye wannan wulakanci da Aliyu yake mata ba akan wata kafirar banza da ba matarsa ba.
EMILY POV.
Ta sauka Airport around 5:02 tana fitowa ta kunna wayarta kamin ta kira Aliyu sakonsa ya shigo wayarta, bata wani tsaya duba sakon ba ta danna masa kira ringing daya aka daga.
"Aliyu ina yata take?"
"Hello"
Muryar Fatima na dira kunenta ta tsaya cak ta lumshe ido.
"Fatima my beautiful baby girl"
"Hi Momy"
"Ina kike?"
"Ina falo"
"Falon waye a ina? Ina Aliyun yake ina ya kaiki"
"Gidanshi ya fita ya siyo min ice cream"
"Momy ki daina damuna ina kallon cartoon ki kira dayan kira dayan wayarshi"
"Okay my Love, i love you okay"
Bata tsaya amsawa ta kashe wayar ta cigaba da kallonta, hawaye ya saukowa ma Emily sai kuma ta ji wani iri idan ta yi arba da Aliyu me zata fada masa bata yarda da shi ba? But she has no other choice dole ta sanar masa tana Kaduna kuma hankalinta zai fi kwanciya idan yarta na kusa da ita. Ta gwada kiran dayan layin nasa wayar ta yi ringing har ta katse be daga ba, kanta ta sauke kai ta kalli jacket din Dr A-B dake daure a jikinta sai kamshin turarensa take, kira ne ya shigo wayar ta dago da sauri a zatonta Aliyu ne sai ta ga Vito a nan ma bata daga ba har wayar ta gama ringing sai ga kiran Aliyu ya shigo.
"Hello"
"Aisha"
"Naam"
Sai kuma ta yi shiru.
"Na gwada kiran wayarki bata shiga kuma na miki text baki maido min da amsa ba, lafiya?"
"Lafiya ฦalau, hankalina ne ya tashi da kace min ka tafi da Fatima na kasa natsuwa kuma na kira wayarka ban same ka ba..."
Magana take a shagwabe tana yi tana yankewa.
"Na zo da ita ne saboda na san kina bukatar space, kuma zuwa da ita ba wani abu zai haifar ba In Shaa Allahu lafiya kalau zan dawo da ita, gobe ma zan dawo, I'm so sorry na tafi da ita ba tare da neman izininki ba"
"Aliyu ina Kaduna fa..."
"What? Wasa kike yi?"
Ta girgiza kai.
"No da gaske ina Kaduna ina Airport ma yanzu haka, hankalina ya tashi ne please ka fahimce ni ina son yata ba zan taba samun natsuwa idan bata kusa da ni ba"
Mamaki ya hana shi kara tambayarta wani abu.
"Kina ina a airport din"
Ta fada masa sai ya kashe wayar, guri ta samu ta zauna tana ya kallon mutanen dake kai da kawo feeling so guilty kamar wanda ta aikata wani laifi. Tana zaune a gurin har sai da ya sake kiranta ya fada mata inda ya faka ta daga kai tana kallo har ta hango shi tsaye jikin motar sanye da manyan kaya da hula.
"Na ganka gani nan zuwa"
Ya rike wayar yana ta kalle kalle har ya hangota tafe sanye da riga da wando sai kuma jacket din dake daure a kugunta, gashin kanta ya rabo gida biyu sai bin iska yake tana tarewa. Idan yace Emily bata da kyau yayi karya ta ko'ina ta kai mace duk wani abu da namiji zai kalla a jikin mace ya sota Emily tana da shi, a kokarinsa na haramtawa kansa kallonta gudun wuce gona da iri ya saka shi kawarda idonsa sai ya lura mutanen dake tsaye kusa shi ma kallonta suke, na nesa da ita ma kallonta suke domin ta ko'ina mace ce mai jan hankali, ko ba dan jikinta da kyauta ba dole a kalleta domin gashinta da idonta da kuma hasken fatarta. Hakan ya saka shi jin babu dadi domin a musulunci mace mai kima ce suturta ake.
"Hi"
Ta fada tana kallonsa a yayinda take tsaye a gabansa, ya kalleta karab idonsa suka fada cikin nata idanuwan masu matukar daukar hankali, sai ta sakar masa murmushinta mai sanyi da kyau, duk wani bacin rai da damuwa dake tare da shi sai ya ji yayi kasa kamar an jefa dutsen kankara a rijiyar dake cike da ruwa take fitar da kara tit tit tit haka zuciyarsa ke bugawa a hankali ba bugawar tsoro ko fargaba ba.
"Wane irin dress ne haka? Kin sake komawa Emily dinki kenan nan?"
Ta kalli jikinta sai a lokacin ta saka hannunta kwance jacket din Dr A-B dake daure a jikinta.
"Haka na zo, Dr Adam Bello ne ya daura min wannan jacket din tasa"
Ta yi zaton yadda ta dauro jacket din ne be masa dadi ba.
"Waye Dr Adam kuma?"
Ta fada masa shi ne likitan da suka hadu asibiti da Tasmia ta kwanta kuma ta fada masa irin hidimar da yayi mata a yanzu har ta samu sauka a airport din. Aliyu ya dan ji babu dadi kadan ko ba komai uwar yar abokinsa ce be kamata ace tana mu'amala da maza anyhow ba, ya san ta dana kyau karamin aikin yan'uwansa maza ne su kawo mata hari da alheri ko da sheri.
"I thought i warning you about this, ko ba komai ke fa mace ce kuma uwa, idan ma baki duba duk wannan ba why not ki girmamani kamar yadda kike yi a wacan karon ki saka tufafi masu kima? And baki fada min matsayin wannan Likitan a gurinki ba har kika karasa labarinki"
"Ba shi da wani muhimmanci a gurina wannan ne haduwata da shi ta uku"
"Me ya same ki a fuska"
Bata amsa masa ba ta ce.
"Tafiyar ta gaggawa ce shiyasa ban yi tunanin saka wani kayan ba, ma tsorata ne na yi tunanin... I'm sorry ka fahimce ni please, ka san halin da na shiga ba wai ina nufin ban yarda da kai ba amman hankali zai fi kwanciya idan Fatima tana kusa da ni, na zo na dauke ta ne sai mu koma gobe dan Allah karka min rashin fahimta"
Ya motsa bakinsa a hankali har wani iri yake ji saboda yadda ta marairaice murya da fuska tana masa magana sai ya dorawa kansa laifin tayar mata da hankali na tafiya da yarta ba tare da amincewarta ba.
"Ma fahimta, shiga mota mu tafi"
Ya bude bangaren da yake tsaye ta zagaya ta shiga baya ta zauna gudun kar ayi masa mummunar fahimta domin ta fahimci shi din mutum ne mai mutunci kuma kai addinin. Be ce me yasa kika zauna a baya ba yaja motar suka fara tafiya be yi nisa ba ya samu kansa ta saita madubin gaban motar zuwa saitin da Emily take zaune a baya ba dan komai ba sai dan yana son karantar yanayin da take ciki, jikinsa na bashi wannan kwancin jinin dake fuskarta dukanta Vito yayi ko kuma wani abu ya faru tsakaninta da Dr A-B din ne, waya sani ma ko Vito ne ya cilasta mata zuwa ta tafi da Fatima, sai tausayinta ya kara kamashi, mutanen da babu zumuntar nesa ko ta kusa suna ta juyata yadda suke so saboda rashin dangi da wanda zai tsaya mata.
"Shi likitan yayi kokarin taba mutuncinki ne?"
"Aa"
Ta amsa tana kallon titi.
"Ba zaki fada min abun da ya sami fuskarki ba?"
"Duka ne"
Tun da ta amsa da duka ne ya fahimci wanda yayi mata dukan ba sai ta fada ba.
"Saboda na taho da Fatima ne?"
"Ba yau ba ne tun wacan ranar ne da na saka Abaya"
"Shiyasa kika hana na ganki? Karya Tasmia ta min kenan?"
Ta yi shiru idonta na cika da hawaye ta share, be sake cewa komai ba ya cigaba da tukin har ya iso gida yayi horn mai gadin ya bude masa ya shiga ya faka motar harabar gidan ya fito, Emily kuma ta zauna domin bata san su waye a gidan ba kuma be ce ta fito ba. Zagayawa yayi bangaren da take ya bude kofar bayan ya bar kofar a bude ba tare da yace mata komai ba. Tana ganin haka sai ta sako kafafuwanta kasa ta fito tana rike da jacket din.
"Na taho?"
Ta tambaya kamar mai jin tsoro, Aliyu ya juyo ya kalleta ya girgiza mata kai.
"Bari na daukota"
Ya shiga ciki ita kuma ta tsaya a gurin ta rumgume hannayenta, ba a dauki lokaci ba ta ga ya fito da sauri ya nufi gurin mai gadi.
"Malam Tahir ka ga wata karamar yarinya ta fito nan waje?"
"Eh sun fita ita da Hajiya, ba su ma wani jima sosai ba Hajiya ta zo da mota ta dauke ta suka fita"
"Hajiya? Wace Hajiya?
" Hajiya ta gidan nan"
"Kameela"
"Eh ranka ya dade"
"Me ya faru"
Emily ta tambaya tana karasowa inda suke tsaye. Aliyu be ce mata komai ba yayi hanzarin ciro wayarsa aljihu ya kira Kameela kusan 3 missed call bata daga ko daya ba.
"Ina Fatima? Ni fa ban gane ba"
Ta tambaya hankali a tashe
"Kameela ta dauke ta"
"Kamar ya Aliyu karka min haka idan ma wasa kake dan Allah ka daina ba haka muka yi da kai ba ina yata take?"
Bata tsaya jiran amsarsa ba ta nufi kofar falon ta shiga da gudu. Aliyu kuma ya bude motar sa a fusace ya shiga yana jan numfashi da karfi ya dauki hanyar gidansu Kameela.
Emily ta duba duk inda zata iya na falon domin ba wani sanin gidan ta yi ba, ta kalawa Fatima kira shiru ta shiga har dakunan data gani ta duba bata ta ga Fatima ba ta sauko tana kiranta bata ji ta ba. Da wayar dake hannunta ta yi amfani ta kira layin Aliyu na farkon wanda ta kira da shi dazun har Fatima ta daga. Kiran ya shiga yana bugawa tare da bugun zuciyarta.
"Hello Fatima my baby girl where are you?"
Shiru ba'ace komai ba.
"Hello Baby Girl talk to me, ina kike?"
Shiru ba'ace komai ba. Ta yi zaton Kameela ce dan haka ta fara magana cikin kaushin halshe.
"If you hurt my baby Kameela, sai na kashe ki Wallahi sai na halaka ki"
"Your Baby is in safe hands..... Aisha... Emily..."
Ta ji an fada cikin wani sauti mai kamar rada kamar rarrashi, da wata murya da bata fatan sake jin irinta, dip bugun zuciyarta ta tsaya wayar ta subuce tsakanin hannunta da kunnenta ta fadi kasa...
_________________
Na biya bashin jiya kuma na yi long page
Kar inji wani yace Pim.... ๐
[7/4, 5:08โฏPM] ๐๐ต๐ฎ๐ฑ๐ฒ๐ฒ๐ท๐ฎ ๐๐ฎ๐ป๐ฑ๐: https://www.wattpad.com/story/215276233?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=KhadeejaCandy
๐ ABOKIN RAYUWA ๐*
*ยฉ Khadeeja Candy*
Page 4๏ธโฃ6๏ธโฃ
KAMEELA POV.
Tun da ta fara tukin bata tsaya ko'ina ba sai bakin gate din gidanta, ta yi horn mai gadin ya leko ya ga ita ce ya koma ciki ya bude ta shiga ta faka rai a bace bata ko tsaya kashe motar ba ta fita ta banki kofar falon da karfi ta murda ta shiga, Fatima dake zaune kan kujera ta zabura ta mike tsaye tana kallon Kameela. Kameela ta harari Fatima kasa da sama ta tabe baki.
"Eh lallai ashe da gaske ne, amman Wallahi Aliyu ya gama cin mutumci na, kuma ya nunawa yarinyar shegiyar matar nan ba ni daraja a gurinsa"
Ta yi kwafa ta shiga kitchen din ta duba abincin da suka ci suka rage, ta fito tana tambayar Fatima da turanci.
"Ina Emily take?"
"Tana can ba da ita muka zo ba"
"Ke ma da ganinki zaki yi munarfuci, waya sani ko daukota yayi har uwar suka zo"
Ta fada da hausa sannan ta kama hannun Fatima ta karbe wayar hannunta.
"Ai yau za'ayi ta ta kare, sai na datse duk wata alaka dake tsakanin matsiyarcin uwarki kwartuwa mai bin mazajen mutane"
CONTACT list dinsa ta shiga ta nemo number Ammy ta kirata da layin Aliyu, Ammy ta daga tare da sallama, Kameela ta amsa tana fadar ba Aliyu ba ne.
"Ni ce Ammy matarsa Kameela"
"Maa Shaa Allahu Kameela kina lafiya ya gidan?"
"Ammy ba lokacin gaisuwa kwatancen gidanki zaki min faka faka"
"Lafiya?"
"idan na zo zaki ji Ammy fada min kawai"
Ammy ta kwatanta mata Kameela ta sauke wayar ta kama hannun Fatima sai Fatima ta ficike hannunta.
"My Momy warn me not to talk to strangers"
"Aliyu ne ya ce na zo na tafi da ke yana can wani gida zai siya miki ice din yace ma kawo ki"
Fatima na jin haka sai ta yarda Kameela ta kama hannunta suka fita ta bude mota ta saka ta ta shiga taja motar mai gadin ya sake bude mata ta fita, tana tukin tana bala'i Fatima sai kallonta take domin bata jin yaren da take.
"Ki bani wayar zan cigaba da kallona"
Kameela ta mika mata wayar ko kira zata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 36 Chapter of 63