a irin wannan gabar? Alkawari ma daukar mata kuma zan cika"
Ya kasa hade abincin dake bakinsa sai dawowa yayi da shi ya zuba a plate din.
"So nasty"
Fatima ta fada tana daukar plate dinta ta bar dinning din sai yamutsa fuska take saboda ta yi arba da kazanta. Be kula ta ba sai kallon Ammy yake.
"Idan har zan sake ta to miye amfanin nemanta da aka yi ta yi? Kin ce na gyara abun da na bata idan na rabu da ita ta ina zan gyara abun da na bata? And Fatima za a raba mata hankali, bana son ta yi irin rayuwar da na yi"
"Daman ai ba sonta kake ba ka fada min, nemanta kuma ya maka rana tun da ka samu Fatima, daman ni burina a nemi yafiyarta kuma asan halin da take ciki, ita ma kuma ba sonka take ba"
"Na ji ita tana da hujjar da zata ki ni, ban damu ba idan tana sona ko akasin haka, amman ni nace bana sonta wannan a baya ne, kuma na fada ne kawai saboda ta ji haushi ke ma kuma ki kyale ni, amman yanzu ne lokacin da zan gyara komai, taya kuma zaki ce na sake ta? A yanzu babu wanda nake son farantawa rai kamar ita, Fatima da ke"
"Idan kana son faranta mata to ka sake ta mana, bata bukatarka a rayuwarta"
"Ni ina bukatarta, idan na sake ta ai ban gyara lafina ba, na kara batawa kenan, kawai ranki ne a bace Ammy amman ni ba zan saki Aisha ba noooooo"
"Ka sake ta idan kana sonta kuma ka yi nufin gyara laifinka zaka gyara ko baka tare da ita, ka sake ta sai ka sake bibiyarta idan zuciyarta ta natsu ta yafe maka zata iya amincewa ta sake aurenka"
"La la la lala lalala idan na saki Aisha ba zata zabe ni, ta sake aurena ba ko da kuwa maza sun kare a duniyar nan, a yanzu ni nake bukatarka ba ita take bukatata ba, la la la Ammy laa ba zan saki Emily ba, ki can ba ni umarni na bi amman ban da wannan la Ammy laaa"
Ya mike tsaye.
"Kina cikin fushi zan tafi sai kin huce"
Ya nufi yarsa dake zaune kasa tana cin abinci tana game sumbance ta ya hada goshinsa da nata ya lumshe ido yana jin wani irin sanyi da be tana ji ba a duniyar, sanyi rahama na arzikin samun haihuwar da yake nema ido rufe. Sai da ya sake sunbantarta sannan ya mike tsaye ya juya ya kalli Ammy.
"Zan yi magana da Aisha, zan dawo da ita kusa da ni, a masarautarmu za mu yi rayuwa mai kyau, idan na sake ai wani banza ne zai aureta, idan mahaifina ya jure ni ba zan jure kallonta a gidan wani ba, zamanta da Aliyu ne su suka kitsa mata komai ni kuwa sai na nuna masa ni namiji ne"
"Babu wani hucewa da zan yi, wajibi ne ka sake ta wannan dole ne"
Ammy ta fada tana dukan dinning din da karfi. Turhan be sake cewa komai ba ya haura sama ya dauki keys dinsa ya sauko ya fice daga gidan gaba daya.
[7/16, 10:07โฏPM] ๐๐ต๐ฎ๐ฑ๐ฒ๐ฒ๐ท๐ฎ ๐๐ฎ๐ป๐ฑ๐: https://www.wattpad.com/story/215276233?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=KhadeejaCandy
๐ ABOKIN RAYUWA ๐*
*ยฉ Khadeeja Candy*
Page 5๏ธโฃ2๏ธโฃ
Nafisa ta shiga ta sanar da Ummi hukuncin da Aliyu ya yanke akan Khaleefa, Ummi ta dan yi jimmin sannan ta ce.
"Shikenan zan yi magana da shi"
Ummi ta tashi da kanta ta dauko kudi mai kauri ta sauko kasa sai kyalli take tana zuba kamshi saboda kwalliyar da ta yi ma mijinta kai kace ba ita ya haifi Aliyu da Yayansa Yusuf ba saboda yadda take kula da jiki, kuma bata taba yarda cewar ta tsufa da yi ma mijinta kwalliya ba.
Kamin ta karasa fita falon aka turo kofar falon aka shigo daman ta ji tsayarwa mota. Yusuf ne tare da matarsa suka shigo, Ummi ta saki baki
"Ah ah ikon Allah yanke tafiyar kuka yi kuka dawo??"
Ummi ta rumgume surukarta tana murmushi, Khadija ta yi dariya
"Shi yace kar a fada miki, wai zaki ce ba sai mum dawo ba"
Ummi ta dago tana kallonsa da harara.
"Daman baka yi nufin hutun ba ko?"
Yayi dariya.
"Ummi ke da kike mahaifiyarsa kika gagara jurewa ki zauna Abuja sai da kika zo nan balle ni da nake yayansa na san zafinsa fa, ita kuma wannan kin santa da lakuwa duk inda ta ji dake a guri sai ta zo"
Ya karasa yana nuna matarsa.
"Eh mana ai ita ce yata, kai miye hadina da kai"
Yayi murmushi ya daga kafadunsa ya nufi cikin falon.
"Toh ga ka ga guri nan, barka da zuwa"
Ummi ta fada tana murmushi ta kalli Yusuf kadan ta dauke kai domin bata wasa da shi sosai, ba kamar Aliyu ba da ta dauka tamkar kanenta, Yusuf ta aje shi a muhallin ษan fari ne. Shi ma kuma ya dauke ta uwa ya dauki mahaifinsa aboki shi kansa ya fi sakewa da mahaifinsa kusan duk wani abu da ya shafi kasuwancin mahaifinsa shi yake tafiyar da shi, sukan tattauna abubuwa da dama ba tare da Aliyu ko ita kanta Ummi ta sani ba.
"Zauna Khadija bari na sallami wani na dawo"
Ummi ta nufi kofa ta fita, sai da ta fita harabar gidan daya daga cikin yaran gidan ya zo da sauri yana tambayar wani abun za'ayi mata.
"a Khaleepa nake nema direban da muka zo da shi ina yake?"
"Oh Khaleefa"
Yaron ya kwala masa kira, sai ga Khaleefa ya fito daga BQ da saurinsa ya karaso gurin Ummi ya gaisheta. Ta amsa sannan ta ce.
"Ai kauyenku a Kaduna nan ne kace ko?"
"Eh Hajiya"
Ta mika masa kudin hannunta.
"Ga wannan, ka yi na mota ka tafi gida ka duba su kuma ka tsaya a can ka kwana biyu, har sai ka ji daga gareni"
Gabansa ya fadi ya kalli kudin jiki a sanyaye.
"Hajiya wani laifin na yi?"
"Aa ba laifi kai yi ba, ba korarka aka yi ba, za'aci gaba da biyanka albashi nan da kwana biyu kuma zaka dawo aiki"
"Hajiya saboda na yi magana da Emily ne? Wallahi baki san abun da yake tsakanina da ita ba wata kila da ba ki fusata har haka ba"
"Ba saboda ka yi magana da ita ba ne"
"Ku kuke da komai na ku, duk hukuncin da kuka yanke yayi daidai, amman ina rokon alfarma daya dan Allah a ba ni damar magana da Emily akwai abubuwan da nake son na tambaye da yawa, kuma akwai wadanda nake son fada mata"
"Ita ce bata bukatar ganinka shiyasa aka bata hutu"
Khaleefa ya zube kasa ya hada hannu biyu.
"Hajiya ki dubi girman Allah ki taimaka ki roki Emily ta saurareni, kusan rabin rayuwar nan na karar da ita gurin neman Emily ne, dan Allah Hajiya ki taimaka min na yi magana da ita, akwai zuri'a a tsakaninmu ina son na tambaye ta, kuma Wallahi a musulma na santa ya aka yi ta zama haka? Dan Allah Hajiya ki ba ni dama"
"Damar ba daga ni ba ne, daga ita ne bata bukatar magana da kai a yanxu, ka tafi gida idan ta bukaci hakan zan maka waya, yanzu dai ka tafi dan Allah kar na fito na same ka a nan"
Ummi ta duka ta aje masa kudin ta juya yana ta mata magiya kamar zai zauce har da kwalla a ido. Ko da Ummi ta shiga falon ta samu Yusuf ya haura stairs, sai Khadija a falon da Nafisa suna hira.
"Ke baki kawo mata komai ba? Ke kuma kamar bakuwa ba zaki shiga ki dauko ruwa ki zuba abincin ba"
"Ni na ci abinci, Abban Maama ne dai be ci komai ba"
Ummi ta zauna tana tambayar jikokinta.
"Ni na manta ina kuka bar yaran?"
"Suna can gida, tare da nanny"
"Wai ku wannan rayuwa da kuka daukarwa kanku anya zata yi? Ku gaba daya rayuwar turawa? Komai dai nanny? Haihuwar ma tun da aka haifi biyun nan shiru ba kari? Kuma kuna kallon yadda muke a gidan nan daga Aliyu sai mijinki sai Ramla da bata yi aure ba, Aliyu kuma shi Allah be ba shi haihuwar ba, ku kuma daga yin yan biyu sai ku tsaya haka? Muna son zuri'a gaskiya"
Khadija ta yi murmushi.
"Allah ne be kawo ba Ummi"
"Ku yaran zamani masu dabi'ar turawa ta ina za a gane ko daga Allah ne ko kuma daga ku ne, mu dai na mu daga Allah ne ai"
Ummi ta mike tsaye tana murmushi domin ta ji tsayarwa motar mijinta, da ganganta ta fada ma Khadija haka domin tana son ta ga tarin jikoki saboda Allah be fata yara da yawa ba, ba kuma zata iya zauna da Yusuf ta yi wannan maganar ba amman zata iya da matarsa.
A ranar gidan ya cika da jama'a saboda dawowar Daddy masu zuwa gaishe shi da suka zaba suka zo, wasu ba su san ma abun da yake faruwa ba sai da suka zo wasu kuma yan'uwa ne da abokan arziki suka zo masa jaje, da yammancin ranar Yusuf ya tafi asibitin duba dan'uwansa tare da matarsa da wasu daga cikin yan'uwa, Daddy kam sai dare ya samu zuwa tare da Ummi saboda mutane ba su bar shi ba sai bayan sallah isha'i.
Aliyu ya gaisa da mutane ciki har da abokai wasu ma ba a bar su sun shigo ba, yayi farinciki sosai da ganin dan'uwansa, Khadija sai zolayarsa take tana tambayar ina Kameela domin bata san wainar da ake toyawa ba, Aliyu dai daya gaji da tambayarta a fada mata sun rabu.
Subhanallahi daga haka bata sake cewa komai ba, daga asibitin suka wuce gidansu dake Kaduna daman suna hutun Anniversary ne abun da ya faru da Aliyu ne ya saka suka yi dawowar gaggawa.
Da dare Ummi suka zo duba shi tare da Daddy Ummi ta zo masa da wani abincin da ta girka masa, sun sha hira da daddynsa sosai na abun da ya same shi da wanda yake zargi da kuma abun da yake hararowa nan gaba, har statement din da police suka dauka sai da ya fadawa Daddynsa kuma a kaurara lamarin saboda yana son a dauki babban mataki. Daddy ya shaida masa already hukuma sun fara aikinsu, a nan ya kara warwarewa Ummi zare da bawa a game da Emily sannan ya kara fayyace musu abun da ya faru tsakaninsa da Kameela.
Aliyu yana son ya tambaya ya Emily take yana gudun Ummi ta masa fahimta ba daidai ba, alhalin shi kuma ya damu ne kawai ya san halin da take ciki.
"Idan ba mataki aka dauka ba ita kanta ba zata samu salama ba"
"Ai dole ne wannan, indai har aka tabbatar shi ne to ya kai karshe, ni da har na fi zargin Kameela saboda yarinyar bata da hankali, indai har zata iya saka maka guba to zata iya komai"
"Abu ne mai wahala Kameela ta yi haka, kuma bana zargin Turhan even though yana cikin bacin rai, amman bana tunanin zai saka ayi min haka, domin na fito gidan kenan ma ba a jima ba, lokacin be isa ace ya je ya samu wasu su yi min wannan dukan ba, na fi zargin Vito ne yake bibita saboda na zo da yarta kuma gashi ta biyo bayana and ita kanta ya saba dukanta balle kuma wani"
"Bincike dai zai tabbatar da komai In Shaa Allahu"
Ummi ta fada sai Daddy ya ce.
"Yanzu ita yarinyar tana Lafiya?"
Aliyu ya kalli Ummi da sauri yana jin amsar da zata bada daman tun shigowarsu yake son ya tambaya sai kuma ya danne zuciyarsa saboda Ummi.
"Tana lafiya"
"Amman ta fito waje?"
Aliyu ya tambaya, sai Ummi ta yi kamar bata ji shi ba. Daddy ya ce.
"Amman Aliyu kana tunanin Turhan zai fahimce ka kuwa?"
"Abu ne mai wahala mahaifiyarsa ma dazun sai da ta fada min magana"
Ummi ta fada, Aliyu ya tambaya.
"Me ta fada miki?"
"Shirmen mata ne, kasan mu sa kananan maganganu"
Aliyu yayi shiru slowly slowly ransa ya fara baci amman be ce komai ba. Daddy kawai ya koma gida Ummi a asibitin da kwana tare da dan'uwansu Muktar duk kuwa da irin yadda Aliyu ya so ta tafi ta bar Muktar din ya kula da shi, Daddy har zolayarta yayi wai ta zabi ษa ta bar miji, ta fada masa ana canja miji ba a canja ษa ba.
EMILY POV.
Wannan ne dare na farko da bata ji dadinsa, saboda ta kwana da kewar Fatima sosai, gashi ta yi bakunta a gidan da mutumen data sani baya cikin gidan sai bakin fuska. Abincin ma bata wani ci abun kirki ba abun duniya ya taru yayi mata yawa. Tun gabanin Asuba bachi ya yanke a idonta sai hawaye ne suke ta aikinsu ta yi iya tunanin ta yi iya hangenta amman ta gagara samun mafitar da zata iya amfani da ita yarta ta dawo gareni. Wannan dalilin ya saka duk yadda ta hana zuciyarta daga ganin laifin Aliyu sai ta kasa domin shi ya janyo mata komai. Ba zata hana zuciyarta aminta da shi ba, amman bata da tabbacin abun da yake zuciyarsa da na mahaifiyarsa, domin Ammy da Khaleefa darasi a rayuwarta.
Bata sauko kan gadon ba har sai da Ummi ta dawo daga asibiti ta leko dakin daman tun fitar Nafisa a jiya babu wanda ya sake lekota duk wani kai da kawo da ake a gidan bata fito ba. Ummi ta kunna wutar dakin ta kalleta.
"Kin tashi lafiya Emily?"
Ta tashi zaune.
"Good Morning"
Ummi ta karasa kusa da ita ta zauna tana kallonta da murmushi.
"Kin tashi lafiya?"
Ta daga kai kawai tana boye idonta.
"Za a kawo miki abun karyawa, asibiti na kwana gurin Aliyu na manta ban fada miki ba, and Aliyu ya bawa Khaleefa hutu saboda ki samu sakewa, zaki iya fitowa harabar gidan ko falo ki shakata, kuma ki saka tufafin da ya miki ki sake jikinki babu wani damuwa"
Nan ma ta daga kai. Ummi ta mike tsaye ta fice daga dakin. Sauka ta yi kan gadon ta shiga bandaki ta yi fitsari ta wanke da ruwa domin ta kasa daina wannan dabi'ar ta musulmai wato tsarki da ruwa ko wanke bayan gida da ruwa, ta wanke bakinta ta fito ta tana jin sanyi na abun da Aliyu yayi mata, ya fahimci feeling dinta tun bata fada masa ba, domin babu fuskokin data tsana a duniyar a yanzu kamar ta Turhan da Khaleefa. Ta zauna saman gadon ta kai hannunta ta dauki katin DR A-B data tsinta a jacket dinsa, ta dadde rike da katin tana kallonsa kamin ta dauki wayarta ta saka number shi duka biyun, sannan ta shiga gallery ta kama hotunan Fatima tana kallo sai ga kiran Aliyu ya shigo wayarta. Ta amaa da sauri tana fatan dayan wayarsa ce dakw hannun Fatima aka kira da ita so that ta yi magana da yarta. Tana jin sallama da muryar Aliyu ta san ba yarta ba ce. Bata amsa sallamar ba bata ce masa komai ba kuma bata amsa Good morning da yace mata ba, hakan ya saka shi fahimtar kuka take ko kuma fushi take da shi.
"Idan akwai abun da kike son aikawa ki aikata, karki bar tunaninki ya hana zuciyarki abun da take so"
"Ina son yarinyarta a kusa da ni, i want my baby"
Ta fada tana fashewa da kuka. Aliyu be ce komai ba ya kashe wayar. Kiransa na sauka kiran Vito ya shigo wayarta cikin kuka ta amsa kiran shi ma bata ce masa komai ba sai saurarensa take.
"Kalle ki Emily, kin yi yaudara kina tunanin kin yi nasara ko? Saboda zuciyarki na raya miki ba zan iya miki komai ba? Mamana ta yi gaskiya kin din ba abar yarda ba ce, idan kina tunanin kin gudu kin tsira to kin yi kuskure, ba'acin amanata a zauna lafiya, sai na ga bayan wannan dan iskan yaron da kike so, kuma sai na maida rayuwarki labari Emily, ba zan raine ki wani ya ci moriyarki ba, no way! Daman kina nemam damar butulce min ne, shiyasa kika karbar soyayyata bayan duk abin da na yi miki? Ban ga laifin komai da yake faruwa da ke ba, saboda ke yar iska ce fuck you Emily"
Maganar yake cikin yanayi na maye. Ta hade kukanta tana jin tausayinsa domin abu ne data sani Vito yana sonta, kuma ya kula da ita irin kulawar da kowa be bata ba, ba al'adarshi ba ce shan kayan maye da safe sai idan yana cikin damuwa, and she knows ita ce silar damuwar tun da har ya kira yana karanta mata wannan bayanan.
"Zan dawo Vito, zan karbi yata zan dawo zamu yi aure zamu irin rayuwar da kake son mu yi, kai kadai ne nauyin da ya rage min na sauke, but don't hurt anyone mutumen da kake kokarin ganin bayansa taimako kawai yayi bashi da wata manufa akaina, ba abun da kake tunani ba ne"
"I don't need you now, i already have Chidimma na yi replace dinki da ita, daman daga ke sai ita nw kuka san sirrina, dan haka zata kasance da ni har abada ke kuma zan baki mamaki, daman haka kike ko? Su ma butulci kika musu shiyasa suka horar dake, to ni horon da zan miki ya fi na su, a hannuna kike ina kallon duk wani motsi naki"
Ya katse wayar sai ta lumshe ido ta cije baki tana jin ba zata iya yafewa kanta ba, domin ta san yadda cutarwa take da ciwo and kasa samun soyayyarta da Vito yayi bayan duk taimakon da yayi mata ya zama kamar cutarwa. Ta kai hannu ta taba zuciyarta tana jin kamar ace zata iya cusawa kanta kaunarsa kai tsaye, tun bayan da Khaleefa ya ci amanar ta bata sake jin tana son wani da namiji ba, Turhan ma ta aure shi ne kawai saboda mahaifiyarsa ba dan tana son shi ba. Sai da ta fara raya ma kanta cewar zata cusa zuciyarta ko bata so ta amince da soyayyar Vito, ko dan rama masa alherin da yayi mata, be zama lallai sai tana son shi ba, zata iya zama da shi su rayu yadda yake so, sai kuma maganar Ummi ta fado mata arai.
"Kina fifita farincikin wasu akan naki, kina fargaba tunkarar wasu da abun da yake zuciyarki, shiyasa kika cutar da kanki...karki sake tsorata ko cilasta kanki abun da ba shi kike bukata ba..."
Ta bude ido tana ba kanta amsa zuciyarta kuma na raya mata Idan bata amince da soyayyarta ba zai iya cutar da Aliyu.
"But i have to Vito ya cancanci komai daga gareni"
Ta share hawayenta sakamakon turo kofar dakin da aka yi za'a shigo. Mama Baraka ce da lullubinta dauke da katon kwandon abinci yaranta yan mata biyu ma suna dauke da abinci, ta shigo da far'arta ta aje abincin a kasa suma suka duka suka aje Emily sai kallonsu take su ma suna kallonta, Mama Barakat ta zauna a bakin gadon tana kallon Emily.
"Ina kwana, kin tashi lafiya"
Emily bata amsa ba, duk kuwa da tana tunanin ko Ummi ce ta ce ta shigo mata da abincin. Mama Barakat bata damu ba ta gabatar mata da yaranta biyu.
"Kin ga bakuwar fuska ko? Wannan sunanta Misira, wannan kuma Hakima zaki iya kiransu da kawayenki ko kanenki"
Emily ta watsa mata harara.
"Bana son ganinki ba na fada miki ba? Duk wani abu mai alaka da Kameela bana bukatarsa"
Mama Barakat ta girgiza kai da sauri.
"Aa Wallahi zuwana ba shi da alaka da Kameela ba wai ina kokarin gyara abun da Kameela ta bata ba ne, Kameela yar kishiya ta ce kawai bayan wannan babu wata alaka, dan Allah ki yarda da ni"
"Ku ba abun yarda ba ne, ku fita daki nan"
Mama Barakat ta fara hawaye tana bude abincin da suka zo da shi.
"Dan Allah karki tsaurara ganinki da nake ina jin sanyi, kin ga abubuwa na shirya miki na karyawa ban san wanene favorite dinki ba, amman abubuwa sun kai bakwai a nan ki ci duk wanda kike so, jiya kuma na yi waya da ita mahaifiyar yaron da suka rike miki Fatima, da na ce zan je na same ta sai kuma na ga ba zan iya yakin ni kadai ba, dole sai da taimakon mai gidan sai na yanke shawarar na fada masa, kuma na fada masa sai dai ban yi nasara na samun amincewarsa ba, be ma fahimce ni ba, amman... Amman... Dai na san zan samu kansa"
Mama Barakat tana maganar jikinta na rawa kamar wanda aka turke, iya kar kokarin na fahimtar da Emily ne bata nufin cutar da ita.
Cikin daga murya Emily ta dagawa Mama Barakat tsawa domin ta fahimci so take ta shiga jikinta ta cutar da ita, bata san me suke kullawa ita da Kameela ba.
"I don't need your help, bana bukatar abincikin Bana bukatar komai daga gareki, ki fita ki bar nan i don't need you"
Babbar yarta ce misira ta kasa jure yadda Emily take magana da mahaifiyarsu ne ta daka ma Emily tsawa.
"Ke dan Allah wace irin mace ce, baki san darajar iyaye ba ne da zaki rika cin mutuncin mahaifiyarmu a gaban idonmu? Haba Mama Wacece wannan kika ta rawar jiki da ita ne, duk girkin nan da kika tashi kina yi tun asuba duk saboda wannan banzar ne?"
Misira na rufe baki Mama Baraka ta dauke ta da mari ta nuna mata kofa.
"Fita fita ki ba ni guri"
Misira ta kalli Mama Barakat da mamaki dafe da kumatu.
[7/16, 10:07โฏPM] ๐๐ต๐ฎ๐ฑ๐ฒ๐ฒ๐ท๐ฎ ๐๐ฎ๐ป๐ฑ๐: https://www.wattpad.com/story/215276233?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=KhadeejaCandy
๐ ABOKIN RAYUWA ๐*
*ยฉ Khadeeja Candy*
Page 5๏ธโฃ3๏ธโฃ
Emily ya hade wani kunci daya tokare zuciyarta.
"Kin yi gaskiya, ban san darajar iyaye ba"
Ta juya ta kalli Mama Barakat.
"Kin gani ko? Yarki tana ganin na zafafa, dan Allah bana son na sake fadar wata magana ina girmama mutuncinki ki fita dan Allah karki sake dawowa"
Jikin Mama Barakat ya kara yin sanyi.
"Me kika sani game da uwa?"
Ta juyar da idonta ta wani bangare na dakin tana sosa wani kurji da ya dade yana mata kaikayi.
"Ban san komai ba, saboda tarihin rayuwata be taba wanzuwa da uwa ko uba ba, na tashi ba tare da uwa, uba ko. Yan'uwa ba, dan haka ban san dadin uwa ba sai rashin dadinta, ban san komai game da uwa ba domin tawa uwar bata taba rumguma ta ba, taba nuna min tarbiya ko akasinta ba, bata banbance min yadda zan yi rayuwa da mutane ba, shiyasa ban iya rike halshe ba, ban san zafin da ake ji idan an ci ma uwa mutuncin ba, amman ni ina fatan yata zata sani, domin na tsaya kanta, na iya yadda zan iya na rayu saboda ita, na yi ma kaina alkawari ba zan taba bari ta ji abun da na ji ba, ba zan bari ta yi irin rayuwar da na yi ba, zan hade duk wani bakinciki saboda ta yi farinciki"
Ta juyo ta kalli Mama Barakat idonta na zubar da hawaye.
"Dan Allah ki tafi bana son na sake fadar wata magana marar dadi a gareki"
Mama Barakat ta nufi kofa ta bude ta fice tana zubar da hawayen da suka fi na Emily zafi da kuna a zuci, Hakima na binta a baya. Emily ta daga kanta sama ta shanye hawayenta sannan ta sauke ta shiga bandaki ta yi wanka ta fito ta zauna gaban madubi ta shafa mai ta saka turare kasancewar babu wasu kayan kwaliya ya saka ta lakaci man shafi ta shafa a lebenta ta shace kanta. Wandon balazo da rigarsa da Ummi ta bata ta dauka ta saka blue ne mai wani zane zanen baki sai rigarsa ta yadi baki da karamin dankwali baki, da dankwalin da daure gashinta madadin ribbons sannan ta dauki wayarta ta tsaya gaban madubi ta kalli kanta with full confidence.
Ta yi kyau babu karya, tabon dukan da Vito yayi mata ya bace confidence din data sakawa kanta ya kara mata kyau da kwarjini, bakin data shafawa mai sai shinning yake, ta juya ta nufi inda talkaminta suke ta saka ta bude dakin ta fita, ta sauko falon a daidai lokacin da Ummi ta zauna a kujerar dake facing din ta Mama Barakat tana fadin.
"Ki yi hakuri fa na barki a nan, na tsaya sallamar mai gida
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 42 Chapter of 63