Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
jin ransa na baci saboda kalaman da take furtawa ga Ammy. "Aisha da ni kike da matsala ba da Ammy ba, wannan...." Be karasa ba ta dauke shi mari, Ammy ta rufe baki Turhan kuma ya runtse ido ya bude ya kalleta idonsa har suna canja kala. "Har yanzu haukarka na baka zaka iya kiran sunana? How dare you? How dare you zaka tsaya a gabana har ka ambaci sunana? A tunaninka har yanzu wacan yarinyar ce da ka maida baiwa a bakar masarautarku? Ka fadawa kowa kurma ce? Ka hana ta magana? Hadiman matarka suke dokanta? Matar da aka sadakar a matsayin baiwa ga wasu mutanen? Ai Abun kunya ne aji kana nemanta, ko da yake mutane irinka ba su da kunya" "Aish..." Yana sake bude baki ta sake dauke shi da mari. Sannan ta kalli Ammy ta ce "Ina yata take?" "Tana nan lafiya ki yi hakuri ko dan ita ki saurara ni" "Baki da wannan matsayin Ammy, kin rusa wacan kallon da nake miki, saboda kin nade bakin maciji a farin kyale kika damka min, saboda na yarda da ke kuma ya tsare ni, ban mutu ba sai dai wani abu da ya alakance ki da zuri'arki ya mutu tun a wacan ranar, baki da wannan kimar a ido na yanzu, saboda haka ina Yata take?" "Aish..." Turhan na bude baki zai furta sunanta Emily ta sake juyowa ta dauke shi da wani mahaukacin mari sai da ya nisa "Ahhhh" Ya cije hakora ji yake kamar ya rama amman ya kasa. "Huhmmm Aliyu yana ba ni mamaki, indai Har zai iya boye min inda kike da kuma alakata Fatima to zai iya komai" Yayi furucin da yakinin shirya mata komai aka yi aka hure mata kunne domin sanin da yayi ma Emily ba zata iya tsayawa tana fada masa magana haka ba, amman gashi har da mari, kuma ya san ba kowa zai yi haka ba sai Aliyu mutumen da ya dauka a matsayin aboki ashe makiyinsa ne be sani ba. "Kana nemana saboda ka maida ni masarautarku na cigaba da bautawa matarka? Idan akana akwai wata alaka ta nesa ko ta kusa tsakaninka da Fatima to hauka kake yi" Ta nufi kofa zata fice Ammy ta riko jacket din Dr A-B dake hannun Emily tana rokonta. "Ina zaki je? Aisha dan Allah ki saurare ni ko dan shekaruna?" Emily ta tsaya kamar abun arziki ta juyo. "Danki ya kamata ki fadawa wannan, shi ya kamata ya fi kowa sanin daraja da kimarki ya kyautata miki ya riฦ™e amanarki, shi be yi ba sai ni da ban hada komai da ke ba?" Ammy ta girgiza kai. "Wannan ba Aisha da na sani ba ce" "Wacan Aishar da kika sani ai ita kika aurawa mutumen da ya tsoratata tun gabanin a daura masa aure da ita, mutumen da ya gargadeta kar ta yarda ta aure shi, ita kuma a kokarinta na maida alheri da alheri ta danna komai ta aureshi, wacan Aisha itace Aishar da ya tofawa yawu a fuska a ranar da aka daura aurensu, ita ce ya kira ranar da aka dauranta da shi a matsayin bakar rana a gurinsa, ita ce macen da ya maida baiwa ya masarautarsu, take bautawa matarsa, ita ce ya gabatar a matsayin kurma a masarautarsu kuma ya cilasta mata amsa haka, wannan kuma Emily ce ta sha banban da wacan" Ta fisge rigar ta fice abunta, Ammy ta kafe idonta akan danta cikin wani kalar yanayi na bakinciki da takaici, matsawa yayi kusa da ita kamar zai mata bayani amman ya kasa cewa komai sai motsa baki yake. "Da gaske ne abun data fada?" Yayi shiru kamar ba zai amsa ba. "Duk abun da ya faru Ammy kuskure ne" Tasssss Ammy ta wanke shi da mari, hawaye na sauko mata. "Allah ya wandaranka, wace irin zuciya ce a kirjinka? Ba ni da Martaba da zaka mutunta ni ashe? Ashe karyar biyayya kake min? Bayan idona ka aikata abun da zai zubar da kimata? Ka rusa duk wani mafarkina da buri da nake da shi, ban taba tambayar wace kalar zamantakewa kuka yi ba amman raina be taba kawo min irin wannan kazamar rayuwar ba, kalli wuyanta ka gani sarkar cross ce a jiki, ka kalli shigarta ta tashi daga musulunci ta koma kafirci, Allah ya biyaka na gode" Gaba daya jikin Turhan yayi sanyi duk neman Emily da yake saboda Ammy ne, ba dan yana jin be kyauta mata ba, amman a yau ya dan ji wani iri. "Zan gyara komai Ammy na miki alkawari, ko dan yar dake tsakaninmu, kuma na faranta miki" Ammy bata ce masa komai ba ta juya ta fice daga falon ta fita ta shiga motar da aka kawo ta, direban ya juya da ita, Turhan na tsaye a entrance yana kallon motar har suka fice sannan ya juya ya kalli kofar falon yana jin kamar ya bankawa gidan wuta domin a yanzu ba shi da babban makiyi kamar Aliyu. "Ina zata je?" Wata zuciyar ta tambaye shi, sai ya sauka entrance din ya bude mota da sauri ya shiga yayi reverse ya fice yana ta kalle kalle zuciyarsa na raya masa wata kila ta tafi ta samu Aliyu wani gurin ne gashi be san inda zai ganshi ko ita ba. Haka ya bi titi yana tafe yana kalle kalle har Napep idan ya gani lekawa yake duk yake dare ne ba lallai ya ganta ba shi dai ya rike kamanin gashinta da hasken fatarta, kamaninta na baya da a yanzu sun hade masa har yanzu ganin yake kamar ba Aisha da yake nema ba ce ya gani. A hankali yake tuka motar yana bin gefen hanya da kallo idan ya ga napep sai ya mika kai ya leka, idan ya ga mota ma sai kallo yana son tantance motar da Aliyu ya zo da ita gidan domin be rike kamanin motar da kyau ba, yayi tafiya mai nisa har yana shirin juyawa ya koma gidan Ammy saboda wata zuciyar na raya masa wata kila Aliyu ya koma gidan ko kuma ita Emily, sai ya hango mai kama da ita an sauke ta a napep ta shiga wani shago da aka kawata shi da haske, da sauri ya faka can gefe yana kallon shagon. EMILY POV. Tana fita gidan ta samu Napep ta hau ba tare da ta fada masa inda zai kaita ba, kawai ta fada masa su yi ta tafiya, tana zaune a Napep din tana jin kamar ta yi kuka amman ta danne zuciyarta da idonta daga zubar da hawaye, tana jin a yanzu jaruma ya kamata ta zama. Ta ina zata samu yarta shi ne abun da yake damunta a yanzu, ta dayan gefen kuma tana jin tsanar Aliyu a ranta domin shi ne silar faruwar komai, meyasa ma ta yarda da shi tun farko? Gashi yanzu saboda abun da ya aikata har Turhan ya samu damar tsayuwa a gabanta da Ammy su yi magana da ita. "Huhmmm Aliyu yana bani mamaki, indai Har zai iya boye min inda kike da kuma alakata Fatima to zai iya komai" Furucin Turhan na dazun ya fado mata a rai, sai kuma ta tuna yadda yake kokarin fahimtar da ita ba shi ya shirya wannan ba, it could be true amman idan ba shi bane miyasa har yanzu be dawo gareta da Fatima ba? Meyasa be kirata ba? Idan ba haka ba meyasa ya zo da Fatima? Wane irin uzuri ne da ba zai fada mata ba? "Ina zan kaiki Hajiya?" Mai Napep din ya tambaya ganin ana ta tafiya bata ce komai ba. "Ka sauke ni gurin da zan samu mai Pos ba ni da cash" Tayi furucin tana gwada kiran number layi da layin yake hannun Fatima sai ta ji layin a akashe, ta gwada dayan layin na Aliyu da wayar take hannunsa nan ma ta ji wayar a kashe, gaba daya sai ta rasa me zata yi, bata gane gidan Ammy a yanzu balle ta je ya dauko yarta idan ma tana ganewa bata son abun da zai maida ita gidan har abada, wannan ya saka no matter how much she try dole ne ta dorawa Aliyu laifi domin shi ne silar faruwar komai. Mai Napep din ya sauke ta gurin wani katon Shagon pos ta fita ta shiga ciki ta yi musu transfer ta waya suka bata cashi ta sallami mai Napep din sannan ta cigaba da tafiya a kasa bata san inda zata je and bata san me zata yi ba babu abin da take bukata sai yarta, wata zuciyar na raya mata taje office station ta fada musu dauke mata yarinya aka aka kaita gidan sai dai kuma ko ta fada bata san yadda zata kwatanta gidan ba. Guri ta samu da babu haske sosai ta zauna, ta sake gwada layin Aliyu shiru be shiga ba, daga baya kuma ya shiga yayi ta ringing ba a daga ba. Duk abun da take Turhan na can gefe a mota yana kallonta bata sani ba, idan ta matsa gaba sai yaja motar ya biyota, ta yi tafiya sosai akafa tana take tana sake sake ta shafa kanta ta daga kai sama ta sauke ta sauke ajiyar zuciya amman ta rasa samu mafita ko daya. Daga karshe wata zuciyar ta raya ta koma gidan Aliyu wata kila zai dawo ko ya dawo, ko be dawo ba komai daren dadewa dole ya dawo ai, shi ya kamata ya dawo mata da yarta. Fitowa ta yi cikin haske ta isa gaban Titin da kyau ta tari Napep ta hau tana kwatanta masa inda zai kaita domin ba sanin sunan unguwar ta yi ba, mai napep yana tafe Turhan na bayansu har suka isa bakin gate din gidan Aliyu, yana ganin haka wani bakinciki ya sake rufe shi, ba mamaki sun shirya da Aliyu ne yace ta dawo gidan domin ya ga tana taba wayarta a dazun. Sai da shiga gidan sannan ya matsa yayi fakin gaban gate din ya fita yayi knocking mai gadin ya bude. "Aliyu ya dawo?" "Aa be dawo ba tun da ya fita, bakuwar da ya zo da ita ce kawai ta dawo" "Okay" Ya saka kafarsa ya shiga cikin gida sai kuma ya juyo ya tambayi mai gadin. "Dan Allah kwanan bakuwar nan nawa a gidan nan?" "Gaskiya yau ta zo" "Amman kamin yau ka taba ganinta a gidan nan?" "Aa Wallahi ban taba ganinta ba sai yau" "Okay" Ya nufi cikin gidan, sanin idan ya shigo da motarsa zai iya janyo hankalin Emily ta san ya dawo gidan, zata iya ficewa ta sake barin gidan ya saka shi barin motar a waje ya tsaya kofar falon cikin rashin natsuwar tsayuwar what if mai gadin karya yake masa Aliyu yana ciki? Ya duba harabat gidan be ga kamanin motar da Aliyu ya tafi da ita gidansu ba. Ya biyo sawunta ne kawai saboda kar ta bace masa domin tsawon lokacin da ya dauka yana nemanta yanzu kuma ya same shi ta ba zai bari ta masa nisa ba saboda Ammy. Yana jin kamar ya bude kofar falon ya shiga be da kuzarin haka, wayarsa ya ciro ya kira layin mahaifiyarsa ya sauka daga gurin ya nufi gate. "Hello Ammy kar fa Aliyu ya dawo ya lallaba ki ki ba shi yarinyar nan" "Ai ko hauka nake ba zan ba shi ita ba, kai dai ka yi kokari ka gyara laifinka, karka damu da wannan ka gyara kuskurenka" Ya kashe wayar, a gurin mai gadin ya karbi ruwa yayi alwala suka ba shi abun sallah yayi sallah Magariba da Isha'i, mai gadi da yaron gidan suna gefe suna ta shawarar me ya kamata su yi domin sun kira kira wayar Aliyu ta shiga tana ringing amman ba daga ba, gashi su ba su gane kan abun da yake faruwa ba. Turhan ya zauna a gurin har karfe goma sha daya na dare, baya son ya tafi ya barta kar tafita be san inda zata je ba, ko kuma kar ya tafi Aliyu ya dawo, ko da yake yarta na gurinsu ya san abu ne mai wahala ta iya yin nisa. Tunawa da Fatima ya jafashi a wata duniyar tunani, ya tashi ya fita wajen gate din inda motarsa take ya bude motar ya shiga ya zauna a ciki yayi mata key ya gyara farkin din ya gitta motar ta gaban gate din ta yadda babu wata mota da zata iya fita ko ta shiga sai ya sani, sannan ya kwantar da kujerar motarsa ya kwanta a ciki yana tuna abun da ya faru a dazun na taba jikin Fatima da yayi, gani yake kamar ba gaske ba ne, ace yana da ya, ba dan be yarda ba yarsa even though dna is the best way da zata tabbatar da haka, amman duk sign ya bayyana dake nuna Fatima jininsa ce, yana mamakin yadda yake ta kwadayi da kewar yara ashe akwai jininsa a doro masa be sani ba, lallai Aliyu ba karamin makiyinsa ba ne, yana daukarsa aboki ashe yana nan yana masa Zagon kasa be sani ba, daman duniya ta gaji haka mutanen da ka aminta da su su suke fara cin amanarka. Ya sake kiran Ammy domin idonsa sun soma kaikayin son sake ganin Fatima, and his mine yana jin kamar za'a iya Ammy wayo a karbi yarinyar ba tare da ya sani ba. "Ammy ina Fatima take?" "Gata nan a cinyata tana bachi, she told me everything Mamanta ta fada mata bata da uba! Haka aka haifeta, kuka take daker ta yi bachi ita ma tana son ganin mahaifiyarta" Ya kashe wayar jiki a amace. Sai kuma ya fita ya shiga cikin gidan ya bude gate din da kansa a hankali saboda kar yayi makin sound din da Emily zata san wani ya shigo gidan, mai gadi ya rika masa dayan gate din ya fita ya shigo da motarsa yayi farkin gurin da babu haske sosai nesa da entrance din gidan, ya kwanta jikim kujerar motar, tambayar farko da ya fara yi ma kansa why Emily zata ce mata bata da uba? Kamin ya tuna ranar da alaka ta kullu tsakaninsa da Emily by mistake, ashe be sani ba Allah yayi nufin ba shi ya ta hanyarta ne, ya busar da iskar bakinsa ya kwanta jikin motar yana kallon gate din gidan yana tuna zaman da suka yi a masarautarsu. Abubuwan da suka faru a baya yake ta tariyowa, yana tuna inda ya kamata ya nemeta kuma ya gwada hakan mutanen da suka karbe mahaifinsa ya tabbatar masa da cewar ta gudu, ba zai iya matsawa mahaifinsa lamba a domin yayi masa karya tun farko, amman zai iya tunawa ransa ya bace sosai ya ji babu dadi a lokacin da ya dawo ya samu mahaifinsa ya bada ita a matsayin kyauta, gurin matar abokinsa data nuna tana shaa'war abata ita, kuma ya nuna mahaifinsa rashin jindadin hakan ya nuna masa baiwar daga bangaren mahaifiyarsa take a gurin tana da daraja fiye da sauran bayin da suke nan. Misalin karfe biyu na dare ya fita motarsa ya bar kofar a bude ya taka har gurin Entrance din ya leka windows din baya iya hango komai dake ciki saboda a rufe suke, amman yana iya jiyo sautin kuka, a gurin ya tsaya kansa a kasa yana saurarenta har sai da ta ji shiru sannan yayi jihadi ya karasa gurin kofar falon ya murda a hankali without making a sound ya tura ya leka ciki, sai ya hangota zauna akan kujera tana bachi, janyo kofar yayi ya rufe ya dawo cikin motarsa ya zauna, a gurin ya kwana har asuba, idan bachi ya debe shi sai yayi maza ya bude idon. EMILY POV. Akan kujera ta kwana zaune bayan ta gama zirga zirgar safa da marwa a falon ta yi ta gwada layin Aliyu ba a daga ba, daga baya ma sai ta ji wayar a kashe, bata san inda zata je ba. No matter how much she try sai da ta kasa rike kanta misalin karfe 2 na dare ta fashe da kuka kuka sosai har sautinsa yana fita, sai da ta yi kukan ta gaji sannan bachi yayi gaba da ita. Bata farka sai 7am shi ma ta ji sanyi ya soma mata yawa ne, sai ta warware rigar Dr AB ta saka a jikinta ta rufe zip din ta saka hannayenta a aljihun jacket din sai tda nufin sararawa sai ta ji abu a ciki, ta lalaba ta ciro arba ta yi da card din Dr A-B mai dauke da email dinsa da number wayarsa da kuma sunansa Business Card mai kyau classic one. Tana rike da card din tana kallo da shafawa kira ya shigo wayarta da sauri ta dauki wayar sai dai ganin number Vito ya katse hanzarinta, bata gama tunanin abun da zata tsara masa ba ta samu kanta ta amsa kiran domin shi ne kadai mutumen da baya betraying dinta. "Hello" "Kina ina?" Ta hade yawu, ta yi shiru. "Kaduna ko?" Ta ji gabanta ya fadi. "Wani abun ne ya taso min da ban yi zato ba shiyasa na tafo" "I can't lie again Emily, wannan ogan na gurin aikin ku kika bi? Butulcin ne kika fara tun yanzu ko?" "No no nooo ba abun da kake tunani ba ne, na san ka yi min gargadi amman kuskure na aikata na bawa Aliyu Fatima ya zo da ita Kaduna va tare da sani na ba, kuma yanzu Turhan ya karbeta ina..." "Good, so me kika son na yi yanzu? Na yi fada da shi? Ko ke na sake yarda da ke? Ko kuma na yarda da duk wannan karyar da kika shirya? Na saka wasu kananan yan iska sun bawa boss dinki warning it's just a warning before i come" "What do you mean?" "Je ki tambaye shi idan rayu" Ya katse wayar. Kirjin Emily ya shiga bugawa da mugun karfi, ta sake gwada number Aliyu a nan ma ta shiga kuma sai ta yi sa'a aka daga kiran. "Hello" "Mai wayar yana asibiti" "Wace Asibiti?" Ta tambaya aka fada mata sai ta nufi kofar falon ta bude ta fitada sauri ta kula da motar Turhan dake can gefe ba domin hankalinta ba a gurin yake ba, ta fita mai gadin na tambayar lafiya bata kula shi ba. "Anya ba guduwa zan yi ba ni ma wannan zirga zirga kar wani abi ya faru ko ya bata a dora min laifi fa" Ya fada yana kallon Turhan daya juyo da mota da nufin bin sawunta. Achaba Emily ta hau ta fada masa inda zai kaita ta hau jikinta nata rawa gaba daya hankalinta ya gama tashi. [7/8, 11:19โ€ฏAM] ๐—ž๐—ต๐—ฎ๐—ฑ๐—ฒ๐—ฒ๐—ท๐—ฎ ๐—–๐—ฎ๐—ป๐—ฑ๐˜†: https://www.wattpad.com/story/215276233?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_writing&wp_page=create&wp_uname=KhadeejaCandy ๐Ÿ’ ABOKIN RAYUWA ๐Ÿ’* *ยฉ Khadeeja Candy* Page 4๏ธโƒฃ8๏ธโƒฃ Ta isa asibitin ya sauka kan achaba ta biya shi kudinsa ta Emergency ta shiga tana dubawa yawo ta yi bata gane dakin ba domin asibitin babbar Asibiti ce Emergency ma biyu ce ta shiga dayar ta nan ma ta binciki bata gane ba sai da ta sake kiran wayar aka fada mata, sannan ta gane dakin bayan ta isa aka hana ta shiga domin dakin na tsare da jami'an tsoro. A dole ta dawo waje ta zauna ta dafe kanta, duk abun da take Turhan na biye da ita, shi dai be san me ke faruwa ba, be san wa aka kawo ko ta zo gani asibiti ba, kuma be isa ya tunkarenta ya tambaya ba, dan haka ya zauna nesa da inda ba zata ganshi ba yana kallonta. Can kuma ya ga ta fashe da kuka sosai hakan ya karantar da shi ko ma minene abu ne mai muhimmancin sosai a gurinta, karfin hali yayi ya tashi daga inda yake ya taka cikin takunsa na kasaita kamar wanda baya son taka kasa ya karasa inda take zaune tana kukan ya tsaya daga gefenta ya kalli mutanen da suke gurin yana kirga mutane nawa ne, domin ya san Emily zata iya disgashi ya lura gaba daya an hure mata kunne, har ya kalli inda take zaune kamar ya zauna amman ba dama ya san zata iya tashi ta bar shi a gurin. Ya tsaya a gabanta kamar wani hoto ya kalleta ya kalli harabar ya kasaita ta hana shi bude baki ya tambayi me ya saka ta kuka, baya son ta zubar masa da kimarsa just because yana nemanta kuma yana neman gyara abun da ya bata, sai dai kuma tunawa da Fatima ya saka shi kawar da komai, domin samun Fatima a yanzu yana jin Emily ta gama masa komai, ya hade yawu zauna a gurin, jin alamar mutum ya zauna a kusa da ita ya saka ta mike dago kanta daman tun da ya iso gurin ta ji alamar mutum amman bata dago ba sai da ya zauna kusa da ita. Ganin Turhan ne ya saka ta mike tsaye da sauri sai yayi hanzarin mikewa tsaye ya riko hannunta. Juyowar da zata yi sai ta juyo da shirinta na sauke mata yatsunsa biyar na dayan hannun a fuska, yayi hanzarin saka dayan hannun ma ya rike dayan hannun. "Zaki iya marina ki ci mutuncina yadda kike so idan muna daga ni sai ke a guri a gurin da jama'a suke kai da kawo ba, Aisha kin fa san waye ni na san kina jin haushina amman..." Be kai aya ba ta buga masa kanta a hanci ba shiri ya saki hannayenta. "Ya Rabbi ya Allah..." Ya furta yana jin wani gishirin bala'i a hancinsa yana ratsashi har cikin kai, ya kai hannu ya taba hancin nasa har yana huro iska ya ji ko hancin yayi jini, bata tsaya a gurin ba ta kara gaba, bata wani san asibitin ba da tambaya ta isa gurin da ruwa suke ta tara hannunta ta wanke da kasa sannan ta tara hannunta ta dauraye. Turhan na can daga nesa yana kallonta ganin ta wanke hannun ya saka jin wani iri ya kalli hannayensa even though ya san hannunsa are clean. Karfin hali yayi ya karasa gurin da take duke ya tsaya daga bayanta. Duke take a gurin tana ta kuka, abubuwa sun chabe mata a yanzu, Vito yayi fushi har ya cutar da Aliyu, ga Fatima bata hannunta ga shi ta hadu da daya daga cikin manyan makiyinta wato Turhan, Aliyu yana raye ko ya mutu bata sani ba, but no matter what bata so wani abu marar kyau ya samu Aliyu ba, balle kuma ace sanadinta ne. "Ina son na san dalilin kukan ne wata kila zan iya taimaka miki, ki fada min me ya kawo ki nan kuma me ya faru ba dan ni ba sai dan Fatima" Ta runtse ido cike da bacin rai, yanzu kuma ta rasa dalilin wannan mutumen na bibiyarta, da ace tana da iko da ta toshe kunnuwanta daga sauraren muryarsa. Mikewa ta yi tsaye ta juyo ta kalleshi. "Har abada, har kasa ta rufe idona, har duniya ta nade ba zan taba karbar taimako daga gareka ba, balle kuma har na nema, da zaka iya da ka taimakawa kanka ka nisanta kanka daga ni da duk wani abu da ya shafe ni, idan ka aikata hakan rayuwarka zata tsawaita ka cigaba da zalunci da ka sakawa gaba, kuma saka ceto kanka daga wulakanci, idan akwai muryar da na tsani ji kamar mutuwata to taka ce, idan akwai fuskar da zan iya kwakwale idanuwana na zubar da su saboda kyamar kallonta to taka ce, idan kana kallon Fatima a wani tsanin hawa to ka yi kuskure domin Fatima bata da uba, ko a tsintuwa ta zo ba zata taba zabarka a matsayin uba ba, mutumen da ya kalli uwarta ya aibanta surarta, ya kaskantar da ita a matsayin baiwa a fadar da ya kamata ace an girmamata, ya kira ranar auren uwarta da bakar rana, ya kira ranar da ya kebe da uwarta har aka samu cikinta da bakar rana, ya fadi cewar ba zai taba son abun da ta haifa ba, ya watsa mata yawu a fuska, wai duk saboda kawai ta aure shi dan ta farantawa uwarsa rai, ya kira uwarta da tubabbiya, ya kira dan'uwanta da shege yana musa cewar ta sunna aka same shi, ya bar uwarta ta wahala a titi ta haife ta a titi ta raine ta a titi kuma yana raye yana da hali da

Chapter 38 of 63