aka yi ma mutuwa.
"How are you Emily"
Ta daga kafadunta ta tabe baki kadan kamar mai son fashewa da kuka.
"Na shiga damuwa, komai ya chabe min"
"Is okay"
Ya rika hannunta yaja ta tafiya mai nisa sannan suka isa entrance din shiga falon ya taka yana rike da ita ya tura kofar falon ya shiga yana janye da hannunta, falo ne babba mai dauke da kawa da abubuwan burgewa amman Emily bata kula komai ba, ita dai tana biye da shi har suka haura sama hawa na farko ya tura wani daki ya shiga da ita, da kansa ya zaunar da ita kan gadon dake dakin.
"Nan ne dakinki, akwai bandaki ki shiga ki yi wanka wardrobe tana cike da tufafi ki saka marar nauyi, za a kawo miki herbal tea ki sha, kamin ki ci abinci, zan tafi asibiti ana jirana daman saboda ke na dawo"
Ya mike tsaye ya dauke hannayensa daga kan kafadunsa.
"Na gode"
Ta furta, sai ya juyo ya kalleta cike da tausayi be ce komai ba ya fice daga dakin. Kwantawa ta yi akan gadon tana tunanin duk wani abu da ya faru da ita na farinciki wata rana da ta yi farinciki sai fa Emily ta tuna ta a ranar sai gata tana murmushi da hawaye, can kuma ta kai hannunta ta murza wuyan hannun tana tuna agogon da Aliyu ya bata ko a ina ta jefar da shi bata sani ba. Ta mike tsaye ta share hawayenta ta shiga bandakin ta tube tufafin jikinta ta kunna shower ta zauna a kasa ruwan yana dukanta ta rufe ido tana maida numfashi a hankali. Ta dade a haka sannan ta yi wanka har kanta sai da ta wanke sosai sannan ta fito daure da tawul ta bude wardrobe din ta cire doguwar riga mai yalwa marar nauyi ta saka.
Wata Cristian maid ce ta shigo sanye da short skirt da bakar riga ta kawo mata tea, daga baya kuma ta shigo mata da abinci da ruwa. Emily ta dauki tea ta shanye ta zauna bakin gadon tana jin ina ma bata jefar da wayarta ba da ta kalli hoton yarta ko zata ji sanyi. Bata ankaro ba ta fara jin bachi sai ta kwanta tana lumshe ido da hamma kamin kace me bachi yayi gaba da ita.
Bachi ta yi sosai na tsawon awa hudu ko da ta farka yamma ta yi sosai. Tashi ta yi zaune tana murza ido madadin ciwon kan ya sauka sai ta ji ya karu, ta sauko da kafafuwanta kasa kenan AB ya turo kofar dakin ya shigo rike da leda, ya zauna kusa da ita.
"How are you feeling now?"
"Kaina yana ciwo sosai"
"Yeah saboda kin kwanta da tunani ne, kuma bachin be isheki yadda ya kamata ba, amman ga magani zaki ji sauki"
Ya bude ya dauki wani sabon Water bottle da aka kawo mata ta bude ta dauki cup din ya zuba ruwa ya balla maganin ya mika mata ta karba ta sha tare da ruwa, sannan ya bude sabon abincin da aka kawo mata tana bachi ya zuba mata kadan ta sauka kasa ta zauna ta ci, bayan ta gama ya sake bata wani maganin.
"Ki wake shiga ki yi wanka, amman da ruwan normal ba mai dumi ba kuma ba mai sanyi ba, za a sake kawo tea anjima ki sha, zuwa gobe da safe idan kin huta stressed din ya rage sai ki gaisa da Momy"
Ta daga mishi kai, ya mike tsaye ya kunna tv dake dakin ya kama channel din dake nuna abubuwan ban dariya, ya rage sanyin ac sannan ya kalleta ya sakar mata murmushi ya fice, ta bishi da kallo tana mamakin yanzu shi baya cikin wata damuwa shi sam be san wani abu damuwa ko rashi ba, ba kamar ita ba dake da tarin matsaloli. Yadda ya fada mata haka ta yi bayan ta gama ta zauna tana kallon tv sama sama bayan magari aka kawo mata fruit sai madara da ruwa ta ci fruit din rabin plate sannan da shanye madarar da bata da yawa, after like one awa aka shigo mata da tea ta shanye, nan ma babu jimawa ta yi bachi.
Sai tara ya shigo dakin ya kashe tv ya lullube ta ya rage hasken dakin sannan ya fita. Washe gari kamin kowa ya shigo dakin shi ya fara shigowa sanye da kayan bachi, shigowar shi ce ta tasheta daga bachi ta farka.
"Good Morning"
Ya fada da murmushi a fuskarsa sai ta murza idon ta tashi zaune. Ya zauna kusa da ita.
"How are you feeling now?"
"Much better"
"Kan yana ciwo?"
Ta girgiza kai.
"Good, me kike so for breakfast?"
"wannan tea din ina son na yi bachi"
"Zaki yi bachi, ana bin ka'ida ne ba a son bachin yayi yawa ne, kina cin kwai? Domin shi ne best abun da nake son ci da safe kwai sai tea"
Ta daga kafadunta.
"Okay, za akawo miki amman yanzu ki fara shan maganin nan"
Ya dauko maganin ya bata kamar dai jiya ta karba ta sha.
"idan kin karya ki sha irin wanda na baki jiya, zan fita aiki kin san bama samun zama, ina son ko da zan dawo na same ki kin shirya sai ki haura sama ki gaisa da Momy"
Ta daga mishi kai.
"Na gode"
When ever she says ta gode sai ya ji zuciyarsa ta tsinke. Ita kuma tana jin ita din ba dole ne a kula da ita ba, domin mahaifiyar data haife ta ma ta jefar da ita, duk wanda zai ganta ya taimaka mata ya cancanci godiya a gareta.
"Idan na dawo zamu gaishe da Momy karki manta"
Ta daga mishi kai, sai ya ja kumatunta yana murmushi ya mike tsaye ya fice. Be dawo ba sai after ta yi lunch sannan ya shigo da ice cream da chocolate ya kawo mata, sai da ta ci sannan ya riko hannunta suka fito, ta yi zaton kasa za su sauka sai ta ga sun haura hawa na biyu a nan ma wata duniyar ce mai zaman kanta, wani apartment ne guda mai dauke da komai daya yafi na kasa kyau da tsari, banbancin falon kasa ya fi fadi da yalwa ma sama kuma ba wani mai girma ne sosai ba, falo ne har biyu ga kuma dakuna da suke cikin falon, ta cikin falon akwai view din falon kasa da kuma gefe dayan gefen kuma harabar gidan ce.
Ko'ina na view din glass ne da manyan curtains da aka sako aka bude su da wadi sosai iska na kadawa, dama da falon kuma wani center ce mai dauke da books ga chairs na zama, dayan gefen kuma dinning area ne an yi shi sama kadan sai ka tara stairs biyar sannan ka hau guri. Ga wani katon Tv mai kamar majigi, ta ko'ina sanyi ke bugowa, ya zaunar da ita kan kujera sannan ya shiga one of the bedrooms da suke falon babu jimawa ya fito tare da wata mace da gani daya Emily ta yi mata ta gane wacece.
"Barka da zuwa gidanmu"
Emily ta mike tsaye, matar ma kallon Emily take har ta zauna tana sanye da short gown da sarkar cross a wuyanta, AB ya zauna kusa da ita.
"Zauna mana, ni sai nake ganin kamar na san fuskarki"
Emily ta zauna tana rike da hannayenta.
"Mun taba haduwa wata rana a Sudan, ke kika zo da ni Nigeria"
Da mamaki matar ta sake kallon Emily.
"Anyi haka, ke ce? Wannan baiwar da aka ba ni sadaka?"
Emily ta daga kai, AB kuma ya shiga rudani.
"Kun taba haduwa?"
"Yeah, kai ya ka hadu da ita?"
Ya fada mata, sai ta kalli Emily tace.
"Meyasa kika gudu a gidan matar da na hada ku?"
"Saboda na miki karya a wacan lokaci na fada miki an siyar da ni, ba siyar da ni aka yi ba, wani na aura dan sarki garin shi kuma yaje da ni a matsayin baiwa"
"Zan iya saninki? I want to know more about you, why do you lie"
Emily ta fara hawaye.
"Saboda ba zaki yarda da ni ba idan na fada miki dan gidan nake aure, kuma ba zaki yarda ki taimake ni ba"
Dr AB ya kalli mahaifiyarsa.
"Momy wannan ba lokacin da ya kamata ayi wannan maganar ba ne please"
"Why? Ya kamata mu san wacece ita, saboda ita ka yi ma mijina karya ya bada jirgi aka dauke ta, and because of her ka roki mijina ya kula da duk wani responsible nata tun daga kaduna har zuwa nan, ya kamata mu san da wa muke zaune a nan"
"Yeah amman ba yanzu ba, she's Cristian"
"Matsalar bata addini ba ce, idan kana son mu'amala, kawance ko aure musulma ko wanda ba musulma ba, wannan ba matsala ba ce, matsala shi ne mu san wacece ita"
"Zan iya baki labarina idan kina so"
Dr A-B ya mike tsaye da sauri ya koma kusa da Emily ya zauna tana hawaye ya rumgume ta.
"No ba yanzu ba"
Momy ta kalleshi kamar bata jidadin rungumar da yayi ma Emily ba ta mike tsaye.
"I'm sorry Son bana nufin bakanta mata, kuma karki dauki hakan a matsayin wani abu, as long as my only son was the one bought you here you're welcome"
Dr A-B ya bata rai alamar be jidadin Momy ta yi ba, ita kuma bata sake cewa komai ba ta koma dakinta. Emily ta daga kai ta kalleshi.
"Ya zan yi da rayuwa? Ji nake kamar zuciyata zata tsaya"
Ya kara rumgume ta.
"Ya isa haka"
Ta share hawayenta ta raba jikinta da na shi.
"Zan iya komawa dakin da ka sauke ni"
"Yeah"
Ya bita da ido har ta fita falon, sannan ya mike tsaye ya shiga dakin da Momynsa take. Tana fitowa falon ta fara saukowa kasa tana hawaye madadin ta tsaya hawa na biyu inda ya sauke ta sai ta sauka kasa gaba daya tsabar hankalinta baya jikinta, ta shiga wani dakin dake falon na farko tana shiga ta ga ba nan ba ne ta fito ta bude dayan dakin nan ma ba sha ba ne nan ma kuka ya ci karfinta ta durkusa tana kuka, laifi take dorawa kanta domin da ace bata biyewa so ba da yanzu Khaleefa be kaita ya baro ba domin shi ne silar faruwar komai.
"Ba haka ake tarbar bako ba, abun da kika yi a yanzu kin kara jefata ne a damuwa kuma baki san iya halin data shiga ba, ba ita ta nemo ni ba ni nake ta kokarin shiga rayuwarta"
Ta aje littafin dake hannunta.
"I didn't ask her to leave, i didn't say she's not welcome, all what i asked her is who she is, ya kamata musan idan ya cancanci duk abubuwan nan da kake mata, kuma ya kamata mu san da amintacciya muke zaune"
"Kina da gaskiya, amman ba a irin wannan lokacin da yanayin ya kamata ki yi wannan maganar ba, kina ganin ganin yarinyar nan kin san akwai damuwa a tare da ita, ni na san yadda damuwa take, ta kan saka mutum ya hauka ko ya fita hayyacinsa, wani ma baya iya bayyana matsalar sa saboda yana jin kamar ba za a fahimce shi ba, tun farkon haduwana da yarinyar nan Allah ya hada wata alaka mai karfi a jinina da nata, na ji ta yi min ta kwanta min a rai, and duk lokacin da zan sake haduwa da ita sai na karanci damuwa a tare da ita, shiyasa nake ta shiga rayuwarta saboda ma taimaka mata"
"Aikinka shi ne duba masu damuwa ka ba su magani not to take their responsibility"
"I thought you want me to get married? Ko da yaushe kina fadar kina son na canja, why all this now?"
Ta yi shiru kawai tana kallonsa. Sai ya juya zai fice.
"I'm sorry Son I'm sorry, bari na yi magana da ita a falo"
"Already ta sauka, ba sai kin yi ba i will talk to her"
"Bari na sauka da kaina na yi magana da ita"
Ta mike tsaye ta aje littafin dake hannunta fice daga dakin ta fito falonta, ta sauka hawa na farko Dr A-B yana biye da ita, shi ya fara shiga dakin ya duba ya duba be ganta ba, ya leka bandaki bayan yayi knocking nan ma bata ciki sai ya fito ya duba sauran dakunan da suke jere da nan bata cikin ko daya ya sake sauka kasa gaba daya ya ya bude dakunan dake falon na kasa, yana bude daki na biyu ya same ta kwance a kasa tana hawaye.
"Emily"
Ta dago da sauri ta kalleshi tana jin zuciyarta na mata wani mugun ciwo.
"Na manta dakin ne I'm sorry"
Ya karasa inda take ya rikota ya mikar da ita tsaye, sai Momy ta karasa kusa da ita.
"I'm sorry, bana nufin bata miki rai, ki yi hakuri na yi kuskure, amman ina fatan zaki fahimce ni bari na rakaki dakinki"
Ta kama hannun suka fara tafiya.
TURHAN POV.
Shiru yake a jirgi har suka sauka, saboda ya bar zuciyarsa a gidan Ammy be tafi da ita ba, wato Fatima ko da ya bar gidan ma tana bachi bata san ya tafi ba, sai sumbantarta yayi ya dauki hotonta ya tafi shi ma baya son ta ga tafiyarsa tace zata bishi Ammy ta hana. Ya sauka airport din yayi waya aka zo aka dauke shi kamar yadda aka saba, sai dai abun da be saba ba shi ne fara ganin mahaifinsa bayan sauka gida, a yadda al'adarsa take idan ya dawo yana shiga bangarensa ya huta ne sannan ya fito gaishe da mahafinsa, amman wannan karon motar na isa masarautarsu ya umarce direban ya faka harabar fadar mahaifinsa, yana jin kamar ba shi da natsuwa idan be ji dalilin kiran da mahaifinsa yake masa ba.
Ko da ya shiga fadar ya samu mahaifinsa da baki, haka ya zauna har sai da mahaifinsa ya samu sarari sannan ya doshi can cikin fadar bayan ya saka an sanar masa da bukatarsa ta son ganinsa. Kamin ya karasa Ammy ta kira wayarsa ta fada masa Fatima ta fara kuka saboda be dawo ba, ta mata karya cewar ba nesa ya tafi ba.
"Kuka take ne?"
"Eh tana tashi bachi dakinka ta fara lekawa ta fito baka ciki sai na fada mata ka tafi ka dawo, tun dazun take tambaya yanzu kuma ta fara kuka"
"Bari na kira Video Call sai ki ba ni na yi magana da ita"
Ya katse kiran ya kirata FaceTime sai ta kara masa Fatima dake kuka yayi magana da ita yana rarrashinta Ammy na fassara mata har ya samu ta yi shiru. Ya tabbatar mata da gobe zai dawo.
"Idan ka dawo ba zaka sake tafiya ba?"
"Eh, ba zan sake barinki ba Fatima na yi alkawari, i love you"
"I love you too"
"Zaka zo tare da momy? Zamu zauna a nan?"
"Eh, zamu zauna a tare Fatima zamu zama Family daya"
"Okay bye"
Ta masa waving shi ma ya daga mata yana jin kamar yayi kuka domin yana matukar son yarinyar nan fiye da komai, sai da ya maida wayar aljihu sannan ya kunna kai a karamar fadar mahaifinsa cike da amsar tambayoyin da ya san mahaifinsa zai masa.
_________
Ayi hakuri, muna biki ne. 🙏
_______________________
Sannu ‘yan uwa mata! Kin gaji da kayan da ba su da salo, ba su da inganci? To yanzu lokaci ya yi da za ki sabunta wardrobe ɗinki da kaya masu kyau, masu ƙima daga Khadeeja Candy Store
Muna da abaya masu kyau irin na zamani, masu sauƙin sakawa da jituwa da dukkanin lokaci whether ki je wurin biki, ko casual outing.
Kuma fa, ba abaya kawai ba muna da bedsheet masu launin kwantar da hankali, masu kyau a gani da taɓawa. Idan kina son daki ya zama kamar hotel, to bedsheet ɗinmu sun dace da ke
Kayanmu masu kyau ne, farashinsu? Ai sai kiyi mamaki sauƙi ne sosai. Muna nan a Kano State, kuma muna delivery zuwa ko’ina!
Ki danna follow yanzu, ki biyo mu a TikTok https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1
da Instagram https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0
Ki ga sabbin kaya masu kyau da rangwame.
Zaki sami kayan Kitchen masu inganci, kayan sakawa na zamani, da electronics masu ƙayatarwa duk a farashi mai sauƙi.
Za ki iya saka tufafinmu ki fita lafiya, kitchen dinki kuma ki kawata shi da kayan Kitchen dinmu, da bedsheet dinmu kuma za ki yi barci cikin annashuwa komai daga shagonmu!
Baki da lokaci? Muna da sauƙin oda ta waya ko WhatsApp - 08036126660 muna aika kaya zuwa ko ina!
To me kike jira? Biyo mu yanzu a WhatsApp https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08
Ba kawai kaya ba ne salo ne, ƙima ce. A Khadeeja Candy Store.
Ki zo yau, ki ɗanɗani bambanci, Khadeeja Candy Store inda kyau da salo ke haɗuwa.
[7/27, 8:34 PM] 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆: https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08
*🍒 ABOKIN RAYUWA 🍒*
*© Khadeeja Candy*
FOLLOW ME ON 👇🏻
FACEBOOK
https://www.facebook.com/profile.php?id=100008156177914
TIKTOK
https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1
INSTAGRAM
https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0
CHANNEL
https://whatsapp.com/channel/0029VaNTEQTFXUuaypyV5O01
KHADEEJA CANDY STORE
https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08
WATTPAD
https://www.wattpad.com/story/215276233?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=story_info&wp_page=story_details_button&wp_uname=KhadeejaCandy
Page 5️⃣8️⃣
Turhan ya zube a gaban mahaifinsa ya gaishe shi, mahaifinsa yayi kamar be san da shi a gurin ba, bayan mintunan da suka bata a zaune wata kalma bata shiga tsakaninsu ba, Turhan ya yankw shirun ta hanyar sake mika gaisuwarsa ga mahaifinsa a nan ma be tanka shi ba. Bayan tsawon lokaci mahaifin ya mike ya shige wata turakar tashi, Turhan ya tashi ya koma bangarensa ya samu balarabiyar matarsa kyakkyawa kamar shi tana zaune cikin bahon wanka tana shuda jikinta da kumfan shower gel mai kamshi.
Ya karasa kusa da ita fuska babu wata walwala ya sumbanci goshinta kamar yadda ya saba, cikin farinciki da zumudi ta mike tsaye ta rumgume shi tana masa barka da zuwa.
"Ban yi tsammanin dawowarka yanzu ba, ya Ammyn take?"
Ya kalleta kawai yana murmushi a zahiri a badini kuma yana hango dalilin Ammy ne aura masa Aisha, tun da yake da matarsa bata taba sha'awa tafi gaishe da mahaifinyarsaba, ko a waya sai idan shi ya hada su take gaisawa da ita, ya taba mata tayin tafiya Nigeria sai ta nuna bata da bukata be sake maimaita bukatar hakan a gareta ba, kuma a wacan lokacin baya ganin illar hakan sai yanzu da ya fi fahimtar muhimmancin mahaifiyarsa...
Ya sake ta juya ya fice hakan sai ya bata mamaki domin be saba ganin jikinta a haka ba ba tare da nuna shaukinsa akai ba, amman yau tambayar ma be amsa ba, a take ta wanke jikinta ta daura tawul ta dayan kuma ta daure kanta ta fito daga Bathroom din ta bullo corridor domin babban bandakin dakinsu ba a daki yake ba a mahadar hanyoyi ne dake tsakanin dakunansu. a ranar dai kam Turhan be samu magana da mahaifinsa domin baya amsa ba. Karamin falon ta fara leka bata ganshi ba sai ta dawo corridor ta shiga dakinsa.
"Turwhan... Kana lafiya kuwa?"
Ta karasa inda yake tsaye yana cire rigarsa tana kallonsa.
"Wata kila gajiya ce, amman idan na huta zan mu wata magana"
"Tana da muhimmanci ne har ka bata rai haka?"
"Zan ki iya hada min wani abu na ci?"
"Shaghala (Mai dafa abincin) zata hada maka"
"Shukuran"
Ya saka bathrobe ya fice ya barta a dakin, tana mamankin yanayinsa a yau. Da dare ma sai da ya koma bangaren Mahaifinsa nan ma be yi magana da shi ba. Haka ya dawo bangarensa ya zauna a inda suka saba cin abincin shi da matarsa ya samu an jera abinci a kasan wani farin kyalle da aka shimfida ta zauna ya hade kafafuwansa yana kallon kayan marmari da ka'ida ce kullum sai an aje tare da sweet kala kala. Be ankaro ba ya ji an zauna kusa da shi matarsa ce fuskarta dauke da murmushi tana kamshin EOS Khumra Al Dufra Perfume Oil.
Ya juyo ya kalleta tana sanye da thobe (or toob / toub / توُب), wata kafaya ce ta al'adar larabawan Sudan, sai ya sakar mata murmushi ya kama hannunta ya rike.
"Kana cikin damuwa ina iya ganin haka daga gareka, ina lura da irin wannan yanayin a duk lokacin da ka dawo daga Nigeria, amman na yau na musamman ne"
"Na kan dawo da damuwa ne saboda neman mafitarta wata hanya ne, a yanzu kuma na samu karshen ta amman ta kasa bullewa da ni"
"Ina gane ko wace kalma da yaren larabci amman ban da tsarke magana a cikin wata magana, fada min Habibi me ya same ka?"
Ya juyo ya fuskance ta da kyau.
"Ina fatan zaki fahimce ni kuma zaki min uzuri, lokaci yayi da ya kamata ki san komai..."
Sannu a hankali Turhan ya yi mata shimfidar da zata mikar da ita zuwa cikin ajinsa har ta dauki karatunsa, tun da ya fara bata ce masa uffan ba har ya kai karshen littafin data kasa fahimtar haruffansa balle ta haddace karatun ciki. Ya fada mata ya aure wata mata matar kuma ita ce wanda ya zo da ita a matsayin baiwa haka kuma ya sake ta a yanzu amman zai dawo da aurensa da ita, haka zalika yana da ya a tsakaninsu, sannan ya fada mata yawan zuwan da yake Nigeria har ya dade yana zuwa nemanta ne. Da farko zancen ya rikice mata ne har ta rasa muhallin dorashi kamin hankalinta ya janyo tunaninta bayan ya nuna mata hoton Fatima.
"Mabsoot bikhibalak"
Ta furta tana jefar da hannu idonta ya fara tara hawaye.
"Ka ci amanata Turwhan, taya zaka yi aure bayan idona? Saboda bana haihuwa? Ko kuma saboda mahaifiyarta bata so?"
"Ki zargi komai ban da mahaifiyata, domin bata taba nuna miki kiyayya ba, matar da baki taba sha'awar gani ba?"
Ta tsaya cak tana kallonsa kamin ta mike tsaye ta taba masa.
"Barakallahu fika Turwhan"
Ta juya sai yayi hanzarin mikewa tsaye ya rike ta.
"Idan har zaki ji babu dadi wannan abun da na aikata ki yi tunanin yadda matar da na wulakanta zata ji? Kuma na yi ne ba dan kai na kadai ba har da ke?"
Ta juyo da karfi.
"Idan har baka sonta taya ta haihu da kai? Bayan duk wannan yanzu kuma kana fada min zaka dawo da ita? A tunaninka zan iya zama da kai bayan duk wannan abun da ka yi min? Balle kuma har zaka zauna da matar da bata wuce matsayin mai kula da gidana ba? Aure ya kare tsakanina da kai.
"La la la, khalas al-mawdu‘ intiha. Ana ‘ayza talaaq"
Furta cewar sai dai ya sake ta ya karya masa guiwa sai dai be karya zuciyarsa ba domin a yanzu Fatima kawai yake hange. Ya kama hannunta ya rike cikin sigar rarrashi ya ce.
"Za mu iya fahimtar juna mu gyara komai, ki yi uzuri, ki karbe ni tare da yata"
"Ba zan karbi uzurinka ba, kuma har abada ba zan taba son yar wata ba, har karshen rayuwata, Lihaddy akher nafas fi ḥayāti"
Ta furta hakan har sau uku tana hade hakora, kalmar ba zata taba son yar wata ba har karshen rayuwarta ya saka Turhan ya saki hannunta domin Fatima yarsa ce, ba yar Aisha kadai ba, be ce ya shirya rabuwa da ita ba, ko rusa aurensa ba, domin ba zai yarda ya maimaita irin wacan kuskuren da ya aikatawa Aisha ba, sai dai kuma hakan ba shi yake nufin ya jure a ciwa yarsa ko mahaifiyarta mutuncin ba. Ta kalli hannunta daya saki ta kalleshi fushi ya dauketa ta fara shure kayan abincin da abinci dake ciki tana ihu tana la'antarsa da kalmomi marasa dadi. Kamin ta fara bin sitting room din ta fara hargitsawa tsabar bala'inta be iya kwana a gidan ba sai fita yayi ya kwana a hotel, washe gari ko da ya dawo be same ta a gidan ba, ya samu ta yi ma gidan barna duk wani abu mai glass sai da ta fasa shi hatta kwalbar turare bata bari ba.
Wanka yayi ya canja tufafi sannan yayi ma khadimansa su gyara bangaren, ya fito ya nufi fadar mahaifinsa ko'ina ya bi kallonsa yan'uwansa suke, sauran Khadiman gida kuma sai ya sauke ido ake satar kallonsa, kowa yana mamaki da abun da matarsa ta fada jiya cikin ihu da hayaniya. Yau ma da ya shiga mahaifinsa be tanka masa ba.
"A gafarce ni,
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 46 Chapter of 63