na san ina da tarin laifuka"
Bayan kamar Minti biyu mahaifinsa ya kalleshi.
"Na yi zaton ba zaka zo ba ai, saboda ban isa da kai ba"
"Ban isa ba, kai kayi kira na kasa amsawa, da baka isa da ni ba da ba za a kawo maka rokon abun da a cikin aikata shi babu adalci ba"
"Wata wuta ce aka ce ta kama a wani gida, aka roki na kasheta, da na bincika dalilin tashinta Sai aka fada min har da ɗana a gurin assasata, shin hakan gaskiya?"
"An riga ni sanar da kai tashin gobarar data haifar da hayakin sanar da duniya abunda ake ciki ne, amman ina da wannan nufin a yanzu da nake ganin lokaci ne daya dace kowa ya san komai"
"Aka ce ka yi aure? Tatsuniya ce ko kuma dai ana kokarin kunna fitina a cikin masarautar ne?"
Turhan ya natsu Sosai ya sanar da mahaifinsa yadda auren ya afku da kuma yadda boye lamarin har zuwa yau. Yayi zaton zai fuskanci fushi da natsa daga gurin mahaifinsa ne sai gashi ya tsinkayo mahaifinsa na murmushin kasaita ya kalleshi cike da alfahari.
"Wani lokacin akan dora mana nauyin abun da ba za mu iya sauke ba, sai da hikima da yawa, na yaba da kokarinka na boye auren kuma na jidadin da yarka take hannunka, jininmu baya zama a ko'ina sai a kusa da mu"
Turhan ya kalli mahaifinsa cike da damuwa.
"Be zama lallai Fatima ta zauna kusa da mu ba, idan mahaifiyarta ta zabi, zama a Nigeria ina tunanin ba ni da zabi da ya wuce na bi ra'ayinta domin gyara laifin da na aikata"
Mahaifinsa ya sake dubansa.
"Baka aikata laifi ba, ko mace bata cancanci auren dole ba balle kuma kai, baka bukatar zama da matar da baka so kuma bata cancanta ba"
"Ta cancanta, saboda kyauta ce daga gurin mahaifiyar da bata jidadin zaman gidan miji ba, mahaifiyar da bayan danta da yi ma kyauta bata da wani, mahaifiyar da aka hanata ganin danta na tsawon shekaru, aka hana ta shayar da shi, na wofintar da Aisha ne saboda tsoron kallon da za'ayi min, da kuma tunanin kamar ni laraben mutum na fi wata fatar matsayi, bayan kuma har a gurin Allah ba haka ba ne, ada can bana son Aisha, amman a yanzu ina jin zan iya mutuwa ita ta rayu, ta ba ni sanyin idaniyar da ban samu ba a gurin matar da nake ganin ta fita matsayi, Ya Abiy ina son Aisha so mai tsanani, ina son yarta son da be da misali, ita ce ta maida ni uba, wannan shaukin ba zai taba gushewa ba, na aikata abun da na aikata ne saboda son zuciya, amman da na runtse ido ban ga kyau a makanta ba, anya idan mahaifiyata aka yi ma ko yata, zan iya jurewa? Amsar ita ce aa, ko ban fada ko na nuna ba abun yana a zuciya"
Sarkin yayi shiru na tsawon lokaci kamin ya ce
"Karka manta da asalinka, kar ka bari mahaifiyarka ta saka maka kalmomi marasa amfani a kanka"
"Ba zan taba mantawa da asalina ba, ni dan wata mace bakar fata ne daga arewacin Nigeria, kuma dan Sarkin Sudan balarabe mai asali, Mahaifinta bata saka min kalmomin manta asalina ba, amman ta fada min yadda mahaifina ya mu'amalance ta, wanda ya sha banban da yan'uwana da nake gani a Masarautar, kuma laifinta shi ne ita bakar fata ce kawai. Bana son yata ta tsane ni, ko kuma ta kalleni da laifin dana aikata saboda son zuciya shiyasa ba zan ki mahaifiyarta ba, mahaifiyata ta cancanci girmamawata a kowane irin hali, duk uwar da zata dauki cikin danta ta raine shi ta haife shi ko wace uwa ce ta cancanci biyayya daga gurin ɗanta"
Sarki Mohamed Abdou ya dauke kai kamar mai jin kunyar Turhan, kuma ya gagara bayyana bacin ransa.
"Mahaifita ta dandani daci mai tsananin kashe halshe daga gurin mahaifina, a yanzu kuma da ɗanta ya kawo sai take ganin ta cancani kauna da biyayya, da kowace dakika tsoron rasani take, ni ma kuma ina fargabar rasata saboda ciwon dake neman rayuwarta, Ya shugaba kuma mahaifina tambaya ce mai nauyi na amsa cewa ina da muhimmanci a gareka ko akasin haka, saboda na zama farin tuwo daga bakar tukunya, be zama lallai ka kaunaci abun da nake kauna ba, saboda ni ba Laraba ce ta haife ni ba, amman dai bakar matar nan daga arewacin Nigeria tana da matukar muhimmanci da kima a idona, ina kyautata zaton ba zaka hana ni yi mata biyayya ba, domin Annabi S. A. W ma ya ambaci uwa sau uku sannan ya ambaci uba, saboda muhimmancinta"
Mahaifinsa ya kalleshi, hawaye ne suke saukowa a fuskar Turhan ba na wasa ba.
"Idan an yi min izinin ina son na kama hanyar komawa gobe, kuma zan dawo ne kadai idan mahaifiyata ta samu farinciki da ta dade tana nema, kuma na samu matar da ita kadai nake muradi a yanzu"
Ya risina cike da biyayya.
"A gafarci halshena idan yayi kure, na barka lafiya"
Ya mike tsaye ya share hawayensa ya fice daga fadar. Masarautar ya bari gaba daya, ya tafi gurin abokansa da ya nunawa Fatima a waya tun a kamin ya karaso, biyu suka goya masa bayan dawowa da Aisha dayan kuma ya nuna masa ya karbi yarsa kawai ya barta ta yi tafiyarta tun da har ta nuna bata bukatarsa. Ya dawo gidan ya shiga bangarensa sai ya samu an gyara komai an kwashe duk wani abu daya fashe, wasu abubuwan kuma an maida su a muhalinsu.
Ya shiga dakin da matarsa ta fi zama ya zauna a kujerarta sai tunani yake kala kala can kuma ya mike tsaye ya fito daga dakin ya shiga dakin da komai nasa yake ciki, yana kokarin cire rawanin kansa ya hango wani karamin kwali a kan gadonsa, ya karasa kusa da gadon ya dauki kwalin ya bude. Sai yayi arba da ticket din first class na jirgin da zai tashi daga Khartoum zuwa Abuja a gobe, ga kuma manyan kudi mai kauri a ciki da wata yar karamar takarda.
"Rihla sa‘īda, Allah yisahil tareeqak"
(Safe journey, may Allah ease your way)
_Ṣāḥib al-Jalāla Mohammed ʿAbdou_
Turhan ya kai zaune da jallabiyar dake jikinsa yana murmushi, ya dade zaune yana sake karanta kalmar da ba zata canja daga haruffa ko ma'anarta ba, sake shiri yayi sannan ya fita zuwa bangaren mahaifinsa sai ya samu an shirya liyafar abincin dare da yaran da suke gidan ya zauna aka ci abincin tare da shi, bayan an gama ya shiga bangaren mahaifinsa duk yadda ya so ya samu wata dama ya yi kibabbantacciyar magana da mahaifinsa be samu dama ba, domin mahaifinsa be ba shi wannan damar ba. Daya fito sai ya dauki motarsa ya tafi gidan iyayen matarsa ita ma dai be samu ganinta ba domin ko kofar gate di gidan ba a bar shi ya shiga ba.
Da ya dawo sai ya hada kayansa da abubuwan bukatunsa tsab cikin akwai har biyu sannan ya kwanta, washe gari da wuri Khadima ta kawo masa abun karyawa ya karya yana video call da Fatima saboda ta fitini Ammy da kukan rashin Turhan da Emily a kusa, sannan yayi wanka ya shirya ya sake kiranta video call be kashe kiran sai da suka shiga jirgi aka umarci kowa ya saka maka wayarsa a airplane mode.
AMMY POV.
"Jirgin nan zai zo?"
"Eh"
Ammy ta amsa mata tana shafa kanta.
"Zai tafi biya ya dauko Momy ne? I miss her so much"
"Aa Momy sai idan ta huta zata zo"
"When?"
"Ban sani ba tukuna, amman a yanzu idan ana son ganin mahaifiyarki ko kuma a daukota a ina kike tunanin za a same ta sanyin idaniyata?"
"A waya"
"Bayan waya"
"Gidan gurin Uncle Aliyu, ko Vito"
"Aliyu yana ajeta a gidansa ne? Da kuka zo garin nan a gidansa kuke zaune?"
"Aa"
"To da kuna PH ma a gidansa kuke zaune?"
"Aa a gidan Vito ne, shi yana dukan Momy ne shiyasa bana son shi, kuma baya so na yana hade rai"
"Shi Viton Momynki ta aure shi ne?"
"Aa ba zata aure shi ba, ba zamu koma gidan ba, za mu zauna a nan da daddyna ko? Da Momy ko?"
"Haka muke fata"
Fatima ta mika mata wayar da har yanzu bata san yadda zata sarrafata ta kira ba, amman ta iya shiga YouTube da Gallery ko Camera.
"Zaki iya kiran Momy? Ita ma zan yi magana da ita"
Ammy ta karbi wayar ta shiga gurin kira ta gwada kiran Layin Aisha da sunan da Aliyu ya saka mata a wayar wato Emily, sai ta ji wayar a rufe.
"Ba a samu"
"Sake kira"
Ta sake gwadawa"
"It the same thing"
"To kira Uncle Aliyu ki ce ya bawa Momy"
"Basa tare, kin san a ina za a iya samunta?"
Ta yi shiru can kuma ta ce gurin Vito. Ammy ta yi shiru tana nazari.
"Amman Momy ma zata dawo? Ina son na ganta?"
"Zata dawo Fatima"
Ammy ta amsa mata sannan ta sauke ajiyar zuciya.
KAMEELA POV.
Ta shiga bangarensu da mamaki tun a falo ta labarta musu komai, sai Hajiyarsu taja tsaki.
"Aikin kenan, daga Aliyu sai abun da ya shafi Aliyu"
Anty Shafa ta kalli Mahaifiyarsu.
"Hajiya, abun be baki mamaki ba?"
"Miye abun mamaki a ciki? Wata kila ta fadi hakan ne saboda Kameela ta daina zuwa can, daman idan ba neman suna ba yaushe zaka kashi sirrinka ka fadawa kishiyar uwa?"
Kameela ta ce.
"Ba wai ta fada ne kawai saboda na daina zuwa mata da maganar ba ne, domin na ga tsananin bacin rai a tare da ita, har fa marina ta yi, kuma idon ta ya kumbura kamar ta yi kuka"
Can kuma ta juyo har lokacin tana dafe da kuncinta.
"To kuma ma idan ba tsananin bala'i ba ta ina Mama Baraka zata zama mahaifiyar tsinaniyar Emily nan? Ta ya ta ina? Kwata kwata ma basa kama fa, kuma ita Emilyn nan ma fa ruwan turawa ne da ita, fara ce sosai mai jan gashi da blue eyes, amman dai ga dukanin alama akwai wata a kasa"
Hajiya ta tabe.
"Ita fa kishiya ba yar'uwa ba ce, ba mamaki wani abun ta shirya, amman dai anjima idan Alhaji ya dawo, zan kwankwasa kofar na ji ko zata yi kara"
Kameela ta haura sama ta shiga dakinta da mamaki da kuma tsananin kishin ace Emily yar Mama Barakat ce, idan har wannan abun da hankali ba zai dauka ba ya tabbata ai ita kam an gama da ita gamawa ta musamman.
"Kai ba ma gaskiya ba ne, ai ba hadi hanyar jirgi dabam mota dabam"
Ta zauna cike da kewar mijinta da son sanin halin da yake ciki. Wayarta ta dauka zata gwada kiransa sai wani bangare na zuciyarta ya hana ta yi haka sau hudu sai a biyar ta gwada kiransa, wayar na shiga gabanta ya fadi ta mike tsaye tana safa da marwa a dakin, wayar ta katse be daga ba, ta sake gwadawa be daga ba daga karshe sai yayi rejecting kiranta. Ta zauna baki gado tana hawaye domin tana tsananin kaunar mijinta.
_______________________
Sannu ‘yan uwa mata! Kin gaji da kayan da ba su da salo, ba su da inganci? To yanzu lokaci ya yi da za ki sabunta wardrobe ɗinki da kaya masu kyau, masu ƙima daga Khadeeja Candy Store
Muna da abaya masu kyau irin na zamani, masu sauƙin sakawa da jituwa da dukkanin lokaci whether ki je wurin biki, ko casual outing.
Kuma fa, ba abaya kawai ba muna da bedsheet masu launin kwantar da hankali, masu kyau a gani da taɓawa. Idan kina son daki ya zama kamar hotel, to bedsheet ɗinmu sun dace da ke
Kayanmu masu kyau ne, farashinsu? Ai sai kiyi mamaki sauƙi ne sosai. Muna nan a Kano State, kuma muna delivery zuwa ko’ina!
Ki danna follow yanzu, ki biyo mu a TikTok https://www.tiktok.com/@khadeeja_candy_store?_t=ZM-8wBOKC1rSVi&_r=1
da Instagram https://www.instagram.com/khadeeja_candy_store?igsh=bTk2aG13cmFkZjM0
Ki ga sabbin kaya masu kyau da rangwame.
Zaki sami kayan Kitchen masu inganci, kayan sakawa na zamani, da electronics masu ƙayatarwa duk a farashi mai sauƙi.
Za ki iya saka tufafinmu ki fita lafiya, kitchen dinki kuma ki kawata shi da kayan Kitchen dinmu, da bedsheet dinmu kuma za ki yi barci cikin annashuwa komai daga shagonmu!
Baki da lokaci? Muna da sauƙin oda ta waya ko WhatsApp - 08036126660 muna aika kaya zuwa ko ina!
To me kike jira? Biyo mu yanzu a WhatsApp https://chat.whatsapp.com/HGRV2NYIoaCF7SIvPOIv08
Ba kawai kaya ba ne salo ne, ƙima ce. A Khadeeja Candy Store.
Ki zo yau, ki ɗanɗani bambanci, Khadeeja Candy Store inda kyau da salo ke haɗuwa.
[7/29, 10:20 PM] 𝗞𝗵𝗮𝗱𝗲𝗲𝗷𝗮 𝗖𝗮𝗻𝗱𝘆: https://chat.whatsapp.com/GATlsEHRyd2HW1OjrdF5AL?mode=ac_t
*🍒 ABOKIN RAYUWA 🍒*
*© Khadeeja Candy*
Page 5️⃣9️⃣
BAYAN WATA UKU...
ALIYU POV.
Ya sauke wayar tare da sauke kafafuwansa dake kan karamin taber.
"Tun da aka sallamoka asibitin nan baka zauna ba Aliyu kullum cikin neman yarinyar nan kake"
Ya kalli Ummi.
"Tun kamin na dawo daga Asibiti abun da nake ta kokarin yi kenan, kuma ai baki yarda na bar asibitin ba sai da na ji sauki radau idan ma akwai abun da ya fi jin garau na ji"
"Allah yasa a dace har yanzu babu wanda ya samu labarin Emily"
"Ameen, zan tafi gobe, tare da Mama Barakat ki taya mu da addu'a"
"Allah ya tsare amman da ka hakura har sai ka samu kwanciyar hankali tukuna, bana son ka jefa kanka a cikin wata matsala"
"Babu wata matsala In Shaa Allahu, kwanciyar hankalina yana tare da samun Emily matukar ban san halin da take ciki ba ba zan taba samun kwanciyar hankali ba, wata kila tana cikin mummunan yanayi shiyasa har yanzu bata waiwayi yarta ba, wata kila kuma ta gaji da rayuwar ne ta hakura a haka"
"Jikina ya fi ba ni kamar tana tare da yaron nan da ya saka aka doke ka"
"Abu ne mai wahala ta koma gurinsa, balle kuma shi da a yanzu yake boya? Daddy ya fada min dan Information kadan ake nema ana samu za a kama shi domin an tara masa duka laifukan da ya aikata kuma yake aikatawa, kin ga abu ne mai wahala ace yana tare da ita"
"Haka ya fada min, yanzu haka baya gidansa, babu wanda ya san inda yake, shiyasa nake jin tsoron tafiyarka Aliyu, kar ace shi ma yana nan yana neman hanyar da zai cutar da kai"
"In shaa Allahu babu abun da zai iya"
"Idan ka je a kwana daya zaka dawo?"
"Eh zan dawo a kwana daya saboda ke Ummi saboda ki samu natsuwa"
Cikin yanayin damuwa da rashin son tafiyar Ummi ta ce
"Tohm Allah ya tsare, ya kaika lafiya amman da jami'an tsoro zaka je?"
"Aa zan tafi da addu'a dai"
Ummi bata sake cewa komai ba ta mike tsaye ta.
"Aliyu kana son yarinyar nan ne?"
Ya daga kai ya kalli Ummi sai kuma ya kalli wani gefen alamar nazari.
"Aa iyakar abin da na sani shi ne, ina matukar tausayinta, ta shiga mawuyacin hali tun daga haihuwa uzuwa yanzu, kuma ina ganin a yanzu babu wanda ya kamata ya kyautata rayuwarta irin musulmi, ya kamata ta san muma akwai na gari cikinmu, ban ce zan iya ba amman ina son na ga na maye mata gurbin wasu abubuwan da ta rasa ne"
Ummi ta sauke numfashi a hankali ya fara takawa cike da girma ta fice daga garden din. Ta yi mamakin ganin bakuwar mota a gidan, duk kuwa da ta san gidansu gidane dake yawan samun baki koda yaushe amman wannan motar ta musamman ce domin sunan mahaifin Kameela ne a jikin number motar, hakan yana nufin motar gidansu ce daman su plate din motarsu ma da sunan familysu ake yi.
Ta hau entrance din ta tura kofar falon da ba a gama rufewa ba ta shiga, ta gangan ta yi kamar bata san da kowa a falon ba har sai da Kameela ta mika mata gaisuwa.
"Ummi ina wuni?"
Ummi ta kalli gefen da Kameela take zaune.
"Kameela? Ina ce dai lafiya?"
Cikin yanayin damuwa Kameela ta amsa.
"Lafiya kalau Ummi, na je asibiti ne gurin Aliyu aka ce an sallamo shi, shiyasa na zo gida"
"Okay, akwai wani hakki naki da yake kansa da be sauke ba ne?"
Ta girgiza kai kwalla na taruwa a idonta.
"Aa na zo na duba lafiyarsa"
"Baki bukatar duba lafiyarsa Kameela domin a yanzu babu wani abu a tsakaninku, amman duk da haka mun gode da ziyara zaki iya tafiya"
"Sau ba goma ina zuwa ganinsa asibiti ba su bar ni na shiga ba, yanzu kuma na zo gida ba zaki bar ni na ganshi ba Ummi? Wata uku har da sati a sama ban saka Aliyu a ido ba wannan ma azabtarwa ce, saki daya yayi min Ummi ba uku ba akwai sauran gyara"
Ta fada cikin kuka. Ummi ta taka zuwa inda take tana kallonta.
"Haka ne, akwai sauran gyara a halayyarki Kameela, tun da har son zuciya zai iya daukarki ki yi kokarin kashe mijinki, kuma zuciyarki ta raya miki mahaifiyar mijinki zata yarda ki sake zama da danta saboda hauka ce ta haife ni, kuma zuciyarki ta raya miki wai akwai sauran gyara tsakaninki da mutumen da kika so ki shafe rayuwarsa daga doron kasa, har kika ikirarin an azabtar da ke da rashin ganinsa, ada can kina tunanin idan kika kashe shi gawarsa za a aje miki kina kallo?"
Kameela ta kara fashewa da kuka.
"Wallahi Ummi ina son Aliyu... Kishi ne Wallahi, kowa zai iya kuskure ki dauke ni kamar..."
Ummi ta nuna ta da yatsa da taka mata tsawa
"Ke yarinya kama hanya ki fice, idan kishi ne miyasa ita mahaifiyarka bata kashe mahaifinki ko kishiyarta ba? Abunda nake gani a labarai kika so ko wace jarida ta yi ado da fuskar dana a jiki? Lallai har yanzu baki da hankali"
Ummi ta nuna mata kofa da yatsa. Kameela ta nufi kofar tana kuka ta fice, Ummi ta tsaya jiki windows har sai da ta ga ficewarta a gidan sannan ta juyo ta nufi stairs.
TURHAN POV.
Wani irin kuka sosai Fatima take da daukar numfashi tana kiran sunan Momy.
"Momy... Momy..."
Ammy ta kalli Fatima dake kwance kan godonta tana bachi a motse saboda tunani da rashin cin abinci. Sai kuma ta kalli danta da ya fi Fatima rama da shiga tashin hankali saboda damuwarsa da Fatima take da tambayar ina Momynta, ga kuma rashin sanin halin da Aisha take ciki domin tun da ta tafi har yanzu ba a samu wanda ya ji duriyarta ba, kuma bata dawo gurin yarta ba.
"Da ace na san haka rayuwa zata zame maka ta zame mata daban hada auren nan ba"
Ammy ta fada cikin tsananin damuwa, abu ne da yake bayyane a gurin kowa babu wanda zai ce ya taba ganin Turhan a cikin wata matsala da ta haifar masa da rashin cin abinci na kwana daya, sai ga shi a yanzu baya iya cin abin kirki bachi ma wani lokacin sai yayi da gaske yake yi, saboda tunanin tambayar da Fatima take masa, da kuma tunanin a wane hali Aisha take ciki, a dayan bangaren kuma yana auna tsakanin tsanar da ta yi masa, saboda kawai yarta ta zaba shi sai ta tafi ta bar shi da ita har na tsawon lokaci babu sako ba aike babu wata hanya da za a iya samunta.
"Haba Ammy be kamata wannan kalamin ya fito bakinki ba, ai ke alheri kika yi nufin aikatawa kuma shi kika aikata kuma alheri ya samu tun da gashi ina da Fatima, ni ne na kawo duk wata matsala da muke ciki yanzu, tunani ne sai na rasa wane zan yi, kullum da fargaba nake farkawa a guntun bachin da yake daukata a karshen dare, fargabar tambayar Fatima, ga shi ta dauki damuwa ta saka a ranta yanzu ta daina sakewa da kowa ta daina walwala, kuma ita kanta Aisha yanzu ba mu san wane hali take ciki ba, kuma ina fargabar kar ace ta fada wani hali saboda rashin Fatima idan har haka ya faru laifin a kaina zai sake komawa"
Ta kalleshi cike da tausayi.
"Ka yi iya kokarinka kuma na baya ba, ka nemeta a lokacin da baka san tana tare da yarka ba, a yanzu kuma da ban saka ka ba, ka saka kanka ka je har garin da ta zauna baka sameta ba, a garin nan bana tunanin akwai inda kafarka be taka ba gurin nemanta, nan ma baka dace ba, tun da ka baro Sudan baka koma ba saboda Aisha, a haka ma ka biya Turhan kuma ina alfahari da kai, jikina yana raya min kamar tana wani guri kusa ta boya ne kawai saboda ta fitine mu, tun da gashi yanzu Fatima kullum sai ta daga mana hankali saboda neman mahaifiyarta"
"Amman me yasa bata dawo ba?"
"Saboda ta azabtar mu mana, saboda idan ta waige mu sai mu mika mata Fatima jiki na rawa"
"Da ma dai ban sake ta ba, zata iya zuwa fa ta dawo da auren wani akanta"
"Zuciyar yarinyar nan bata da kyau, duk wata uwar kirki ba zata iya tafiya mai tsayi haka ta bar yarta ba, saboda kawai ubanta yayi mata ba daida ba, ni miyasa ban kyale ka ba? Bayan duk abun da ubanka yayi min? Wani lokacin idan na tsaya ina tunani sai na rika ganin kamar ba Aisha bace ban yi zaton zata iya aikata haka ba"
"Na fi tunanin kamar bata lafiya, ko kuma wani abun ya same ta, wata kila da yanzu ta dawo, domin yadda nake jin Fatima ni kam ba zan ma iya sati ban saka ta a ido ba"
"To ya sani tun da ta zabarwa kanta guduwa? Wani abun ba kaddara ba ce har da hali"
"Kuma ni sai nake ganin kamar Aliyu ya san inda take, kawai dai yana wasa da hankalina ne ko kuma yana jiran na nemi taimakonsa ne wanda abun ne da ba zai taba faruwa ba har abada, gashi ba wani tufafin kirki take sakawa ba yanzu"
Yana maganar cike da zafin kishi marar misaltuwa.
"Idan har abun da kake zargi ya tabbata to ni ina baka shawarar ka hakura da yarinyar Turhan, shi kuma sai mu ga idan dan halak ne"
"Ai be san kunya ba Ammy ina cire kafa tasa zai saka ya taka, da ace ya san kunya ba zai aikata abun da ya aikata min ba, domin no matter what ya fi kusanci da ni fiye da Aisha, amman ya zabi ya ci amanata, na san ban kyautata ba amman dai ai ni abokinsa ne Aisha kuma be da alakar komai da ita"
"A wani mutum makiyinka ne Turhan a cikin yan'uwa ma akwai su kuma munafikin mutum yana da wahalar zama da ganewa, amman ba zaka taba sanin sai wani abun ya faru, wani zaka samu yana maka hassada ne domin idan babu wannan ban da dalilin da zai saka mutum ya zabi bare sama da wanda ya sani ba, kuma har ya nuna maka kirkiri ai kiyayya ta kai kiyayya, sai dai ka yi taka tsantsan"
Turhan yaja dogon numfashi ya sauke, sannan ya mike tsaye ya fice daga dakin gaba daya kansa ya kulle ta ina zai samu Aisha? Ina ta shiga? Tana raye ko kuma tana cikin wani hali? Miyasa zata masa irin wannan horon mai azabtarwa haka? Tsanar da take masa ta kai har can? Amman ta saba guduwa halinta ne. Wani bangare na zuciyarsa ya raya masa, sai dai be gamsu da hakan ba domin yana ganin ga rayuwarta a nan wato Fatima.
Ya jingina jikin mota yana kallon tausarin da suka yi sararin samaniya ido, ya tsada idonsa gurin wata tauraruwa wacce ta fi sauran haske a dare.
"Na zabtu Aisha, na azabtu fiye da yadda kike tunani, na shiga damuwa na rashin sanin halin da kike ciki, fargabar irin tarbar da zan samu a gareki ya hana ni walwala, ban taba sanin muhimmancin wani abu na kimanta shi ba kamar yadda nake jinki a yanzu, na yi iya yadda zan iya na san wane hali kike ciki amman hakan ya gagara, yaushe zaki dawo gareni? Idan kin dawo zaki saurere ni kuma dai yafiyar ba yanzu ba ce? Kin ce baki taba so na ba, kin yi komai saboda mahaifiyata, yanzu miyasa ba zaki yi saboda yarki ba? Ina son ki Aisha ina son kasancewa da ke"
A hankali yake lumshe ido yana budewa zuciyarsa cike da kuna, ya hade yawu.
"Ni mai tarin laifuna a gurinki na sani, amman ki ba ni
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 47 Chapter of 63