Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
d'in Fulani ina daf da isa b'angaren ta,na zo ina k'ok'arin giftawa ta jikin wani kusurwa dake tsakanin b'angarorin Ummi da Fulani sai naji muryan mutum na tashi a gurin,a time d'in na so wucewa kasancewar dare na sake yi amma yadda zuciyata take bani umarnin tsayawa,sai yasa na dakata da tafiyan da nake sannan na d'an sakaye ina sauraron abunda mutumin yake fad'a,,lokacin ko da naji irin kalaman da yake ambata zuciyata ta matuk'ar tsorata,haka kuma naji ilahirin jikina ya bani dole ba shi kad'ai ne yake shirya wannan tuggune ba,ban tsaya dogon nazari ba dan yadda zuciyata take bani son ganin fuskar ko waye wannan mutumin,cikin rashin sa'a daya faru a dai² wannan lokacin duk iya yadda naso naga wane ne wannan mutumin abun ya gagara,,dan haka ko dana tashi barin gurin a wannan lokacin bayan shiga ta apartment d'in Ummi'n ina cikin damuwa ne gashi ban samu damar ganin fuskarsa ba,,bayan shigowa na na iske Ummi zaune kamar wane lokaci har tayi ta tsokanata a lokacin saboda Ummi mace ce mai yawan barkwanci kuma hakan d'abi'arta yake,,sai dai ko da ganin duk yadda nayi shiru nak'i sakewa haka nan ban iya kula irin barkwancin taba a ranar sai ta zuba min ido tana nazarin dalilin da yasa na kasa amsa mata,,ni kuwa a wannan lokacin ba komai ya hana ni amsa mata ba face irin tashin hankalin da nake ciki na wannan maganar dana ji tana fitowa daga bakin mutumin da ban samu damar sanin ko waye shi d'in ba,,nayi zurfi cikin tunanin anya kuwa bazan sanarma wani abunda ke faruwa ba..?? Kwatsam kuma sai tunanin idan har na fito na fad'a bayan ban san waye wannan mutumin ba kuma bani da shaidar da zan bayyana idan an sani bayyana wanda na gani d'in..?? Duk sai kwakwalwata ta sake rufewa a lokacin har na gaza tab'uka komai,wannan tunanukan sune suka yi tasiri a zuciyata har suka sa zuciyata ta rinjayeni na kasa fad'awa kowa tun a wannan lokacin,,ina cikin wannan tunanin ne a dai² lokacin sai naji Ummi ta tab'a ni had'e da jehomin tambyan me yake damuna..?? Na so ace na daurewa zuciyata na sanar da ita abunda ke shirin faruwa amma sai naji bazan iya yin hakan ba,,badan komai ba sai don kasantuwarta macen dake d'auke da juna biyu,na tabbata a wannan lokacin matuk'ar na sanar da ita wannan maganar da zuciyata ke son na fitar tofa babu abunda zaisa bata shiga mugun halin daya shallake wanda ni na tsinci kaina a ciki ba,wanda idan ba'a yi sa'a bama nak'udan dole ta taso mata,kuma dai kamar yadda likita yake yawan sanar damu ne cewa ba'a son macen da take da juna biyu ta dunga shiga damuwa ko saka abu a ranta,wannan dalilin yasa sai na kasa fad'a matan na kuma sanar da ita da cewar babu komai,,tayi iya k'ok'arin ta na ganin na sanar da ita damuwata amma sai na danne zuciyata nak'i fad'an,,ba don ta yarda ba sai don bata son takuramin yasa ta hak'ura ta barni akan babu komai d'in muka yi sallama da juna bayan ta dad'a min nasihan na daina saka damuwar komai a raina,,nan dai nayi mata godiya muka sake yin sallama na kama hanyar gida zuciyata babu dad'i,,a wannan ranar har na isa gida a ban daina tuna maganganun da kunnuwana suka jiyo minba,,in tak'aita muku labari a wannan satin ne saboda yawan damuwar da nake sawa raina na shiga nak'udar dole,wacce sai dana shafe ak'alla tsayin kwanaki goma sha biyu ina fama da ciwo kuma ciwon da nake ba na wasa ba,sai a kwana na sha uku in da Allah maji rok'on bayinsa a wannan ranar ya k'addara na sauka lafiya tare da samun k'aruwa da y'a mace,,lokacin da likita ya tabbatar na sauka lafiya babu wani matsala sai ya kasance tsakanin Ummi da Fulani sunyi shawaran na dawo cikin gidan da zama dan suna ganin zanfi samun kulawan daya dace ace macen data haihu ta samu,,duk abunda ya kamata su suka yi a lokacin suka kuma tabbatar da ganin na dawo d'in,dan haka bada b'ata lokaci ba aka dawo da ni cikin gidan nan da zama bisa jagorancinsu,a wannan lokacin duk wani nau'ikan gata da karamci na gansu daga gurin iyayen gijina dan haka sai ya zama bani da wani damuwa hankalina ya sake kwanciya,,duk da kasancewa ta hadima a gurinsu hakan baisa sun nuna kyamar abunda na haifa ba,wanda kusan a lokacin zan iya cewa ni dai kawai na haifi yarinyar ne amma duk wani abu daya dace ace uwa ta yiwa y'arta a cikin gidan nan ana uiwa yarinyata tana samun fiye da haka,wanda a lokacin sai yasa duk na sake sakankancewa sannan nutsuwa ta sake shiga jikina,sai dai fa duk wannan abu dake faruwa a kanmu,ko kad'an baisa na manta da wannan babban sirrin dana ajiye a zuciyata ba kawai dai na barwa zuciyata ne tare da saka ido a wasu daga cikin al'amuran gidan,,abunda na manta na shaida muku shi ne kwanaki biyu ne tsakanin haihuwana dana Ummi ni na haihu ranar talata ita kuma a safiyar ranar alhamis,,wanda itan babu b'ata lokaci ta sauka sab'anin ni dana shafe sama da sati ina kan nak'uda,,kamar ni itama haka ta haife tsaleliyar jaririyarta mace,kun san dai duk abunda ya kasance mai kyau baya da wuyar ace mutane basu gane shi ba,amma kasancewar a fuskar jariri matuk'ar yana da idanu da hanci to an gama magana,sannan kun san dai yadda kamanin jarirai suke musamman a lokacin da aka haifesu ba kowa ne yake iya bambance kamannin waye suka yi ba a dangi,ko da kuwa ace mutum ya kai ina da son bambancewan dole ya hak'ura zuwa wasu y'an kwanaki,duk da cewa jaririyar Ummi fara ce sol kamar ita haka nan itama Aisha ta kasance sai dai bata kai y'ar da Ummi ta haifa kyau ba,,in tak'aita muku labarin bayan haihuwan Ummi duka sai ya kasance kulawar yaran ta koma k'ark'ashinta,a kullum yaran suna b'angarenta ni kuma aikina kad'ai shi ne na shayar da yarinyata daga nan babu abunda zan sake mata,duk abunda ya dace ko ina nan ko bana nan ana kulawa da ita yadda ko ni dana haifta babu tabbacin na bata irin wannan kulawar,,har zuwa ranar da sati ya zagayo ma'ana ranar suna kenan wanda a bisa shawara aka barshi akan za'a had'e taron sunan ayi a rana guda,,sannan tun a daren wannan rana aka sanar da sunan jaririyar Ummi sunan Hajiya za'a mayar wato HAUWA'U JEEDDAH,dan haka nima sai nayi k'udurin sunan da zamu sawa yarinyar d'ana haifa kenan,ma'ana duka ya zama sunansu d'aya kuma sunan mutum d'aya aka maida musu,,kamar yadda na sanar bayan an tambaye ni hakan ce ta kasance a lokacin dan haka sunan da muka yanke za'a sawa yarinya dan haka ko dana sanar sunan Hajiya ne da yarinyar babu wanda bai yi farin cikin wannan karamcin da muka nuna ba,amma mu mun san cewa halacci da aka yi mana a wannan gidan shi ne yajamu ga k'ok'arin mayar da alkhairi da halaccin da aka yi mana,,,tun daga wannan rana aka ci gaba da kula da jariran biyu wad'anda suka kasance masu suna d'aya daga nan har zuwa lokacin da suka cika kwana arba'in a duniya inda Jeeddah y'ar dana haifa ina nufin Aisha kenan take da kwanaki arba'in da biyu ita kuma Jeeddan Ummi take da kwanaki arba'in,,a wannan ranar ne da dare wannan gagarumin *AL'AMARIN* ya faru,,kamar yadda ya kasance tun daga haihuwan su a guri guda suke rayuwa ina nufin a b'angaren Ummi kenan,,bisa yadda ya zama sabo bayan na shiga kamar yadda na saba zuwa a lokacin da niyyar shayar da ita,,bisa sabo na a kullum na kan tarar da su a kwance a saman y'an gadaje a cikin d'akin to a wannan daren sai ya kasance a lokacin ko dana shiga saina iske jaririya d'aya ma'ana Jeeddan Ummi kenan babu tawa Jeeddan,,da fari nayi tunanin ko Ummi ta zo ta d'auke ta ne kafin na iso,dan nayi tunanin ta tashi tana neman abincinta shi yasa ta d'auke ta da nufin rarrashi,amma kuma daga baya koda na sameta da batun jaririya sai take bani tabbacin ai duka yaran suna cikin d'akin itama bata jima da fitowa ba,fad'a min haka keda wuya nan take sai tsoro ya bijiromin dan kuwa ina da tabbacin AL'AMARIN nan da na jima ina boy'ewa a kwanakin baya shi ne ya afku,duk da tsakanin mahaifi da d'a sai Allah haka nan duk uwa tana jin ciwo idan akace wani abu ya samu d'anta amma ni a gare ni a wannan lokacin maimakon ace naji bak'in ciki da faruwar lamarin akaina sai banji irin mugun damuwan dana shiga ba a sakamakon jin maganar da nayi tunma kafin a haifa su duka,abunda ya kamata ace naji tsoronsa amma sai na kasance ina sake yiwa Allah godiya daya zama k'addarar akan tawa jaririyar ta fad'a ba wacce ake nufi da sharrin ba,dan haka sai kawai na juya da niyyan fita daga gurin Ummi,a son raina a wannan lokacin shi ne na kama hanyar gida kai tsaye,amma kash sai Ummi ta dakatar dani sannan ta sakani gaba da tambayoyin abunda yake faruwa tunda taga fuskata babu wani damuwa,still har lokacin ban so fad'a ba dan haka saina sake nufin b'oye mata,wannan alamun na son boy'e abunda ke raina da ta gani shi ne yayi sanadin da tayi min barazanar ko dai na sanar da ita gaskiyan abunda ke faruwa ko kuma zata had'a ni da maimartaba,,ni kuwa tsoron abunda zai iya faruwa take ya shigeni nan take ba tare dana sake yi mata musu ba na shiga zayyana mata labarin duk abunda ya faru tun daga wayar dana ji ana yi akan sace duk abunda ta haifa har zuwa shigowata da nufin shayar da yarinyata,,ban gushe ba ina bata labari har saida na kai kan zuwana ban samu jaririyar ba,lokacin dana gama fad'a mata labarin nan naga tashin hankali ya bayyana akan fuskarta dan take taja ni muka je d'akin da nufin sake dubawa,sai dai kun san duk abunda aka ce an neme shi an rasa tofa da wuya a iya gano shi,haka muma muka kasance duk iya bincike munyi amma ko wani alaman da zamu iya gane inda aka nufa da ita bamu samu ba,,dan haka muka zauna shiru a cikin d'akin yayin da muka saka jaririya d'aya a gaba da kallo,,mun shafe ak'alla sama da awanni uku a d'akin muna zaman shiru da sak'a zuwa warwara kafin Ummi ta d'ago idanunta da suka yi jaa ta kalleni tana sauke dogon numfashi,, yadda take ajiyar zuciya a lokacin nima shi ne abunda yasa na d'ago ina kallonta,nan take kuwa sai naga tana gyara zama da kallona sannan ta fara min magana cikin wani yanayin dake bayyanar da tsantsar tashin hankalin daya faru "Hak'ik'a Inno nasan cewa komai k'addara ne a rayuwa,amma wannan abu daya faru har da sakacin ki,,da ace tun daga lokacin da kika ji kinyi k'ok'arin sanar da wani a cikin gidan nan babu yadda za'ayi mu kamanta yin sakaci da rayuwar jaririyar yarinya kamar haka,,amma yau bisa tsoro da fargabar da kika sawa ranki yanzun kinga abunda ya faru,,sai dai ni ina da wani shawaran,sannan kuma ina son dan Allah na rok'i wani alfarma d'aya a gurinki koda ace a bayan shi baza kiyi min wani alfarma ba ina rok'on da ki daure kiyi min wannan kad'ai.." A lokacin data ke min wannan maganar nima sai a nan naga rashin dacewar abunda na aikata,tabbas kamar yadda ta fad'a ne,dana sanar d'in babu yadda za'ayi wani abu makamancin wannan ya faru,,amma kuma idan muka duba tsarin rayuwarmu komai yana tafiya ne bisa doron K'ADDARA,wannan dalilin yasa na kalli duk wani abu daya faru a matsayin k'addarawa ta Ubangiji (S.W.T) akan lamarin,,nan take saina kalleta ina mai amsawa kalamanta "Wallahil aziiym ya uwargijiyata,,,yadda nake rayuwa a ban k'asa bisa k'addarawa ta mahalicci,matuk'ar kika nemi abu a gare ni banga dalilin da zaisa ban yi miki shi ba kome ne ne,domin kuwa kin wuce neman alfarma a gare ni,mufa hadiman kune,saboda haka umarni ya dace ki bayar bawai ki ntambayi alfarma ba,saboda dukkan mu a k'ark'ashin ku muke,, ki fad'i duk abunda kike buk'ata ni kuma da sannu zanyi k'ok'arin aiwatar da duk abunda kika ambata koda kuwa ace hakan zaiyi silar rasa rayuwata.." Wannan furucin nawa shi ne ya bata k'warin guiwa harta samu damar yin murmushi duk da damuwar da take ciki dan haka sai ta samu damar sake yin magana "Na gode sosai da wannan karamtawa taki Inno,iya tsayin shekaru naga hadimai da dama ko a cikin gidan nan,amma ban tab'a ganin kamar ki ba,wannan dalilin shi yasa na yanke shawaran zab'ar ki a matsayin wacce tafi cancanta dana damk'a amanar yarinyata a hannun ta.." Cike da firgicin jin maganganun ta nayi saurin tambayarta a lokacin "Yaa uwargijiyata shin me kike son cewa ne..?? Ban fahimci akan abunda kike magana ba.." Nan take sai naga ta sake yin murmushi sannan ta ce "Na san kin fahimci magana ta,dan haka abunda na fad'a shi nake nufi,kuma shi ne alfarmar da na rok'a daga gareki,na sani cewa wannan abu daya faru akan yarinyata yaso faruwa amma bisa k'addarawa ta ubangiji sai yasa aka d'auki taki jaririyar,akan wannan dalilin ne yasa naji ina son dank'a tawa yarinyar da ragamar kulawa da ita ga wani ba don komai ba,sai don na san matuk'ar aka san cewa ba itan aka d'auka ba za'a sake dawowa,wanda mu kuma bamu san mene ne zai iya faruwa ba,dan haka ni a yanzun zanyi k'ok'arin bincikawa na gano inda aka kai yarinyar ki sannan zanyi k'ok'arin ganin na dawo miki da ita,amma ina rok'on ki alfarma d'aya kawai,da ki tafi da tawa y'ar har zuwa lokacin da al'amura za su yi sauk'i.." Ba don na so ba sai don tun a farko nayi mata alk'awari wannan tasa na yarda na karb'i tata JEEDDAN,inda a nan tun kafin mu bar gidan ta sake rok'ona akan duk yadda zanyi nayi akan rayuwar jaririyarta dan na b'oye ta daga idanun al'ummah,sannan kada na bar wata kafa da zata sa a gano itan ba y'ata bace,bayan nan kuma ta ce nayi hak'uri na zauna a gida na wasu y'an kwanaki kafin na dawo bakin aiki na,da wannan alk'awarin na d'auki Jeeddah na goya sannan muka kama hanyar barin cikin gida muka nufi ainihin namu gidan,na kuma duk'ufa kan addu'ar Ubangiji ya kub'utar min da yarinyata a duk inda take,idan da halin mu sake had'uwa to idan kuma babu Ubangiji ya tsare min ita daga fad'awa mummunan hannu,wannan addu'ar ita na kasance ina yi a duk lokacin da nayi ibada,,,tun daga wannan rana ne sai ya kasance rainonta,kulawa da duk wata kariya yaci gaba da zama aikina har zuwa lokacin da naga ta fara girma,,ko da naga a lokacin yarinyar ta fara k'ok'arin bambance iyayenta da sauran al'ummah sai nayi nufin mayar da ita gurin mahaifiyarta, amma abunda ya faru tsakaninmu da Ummi lokacin dana sanar da ita abunda nake nufi,nan tayi ta rarrashina akan nayi hak'uri na k'ara mata lokaci har yanzun tana kan bincike ne amma tasan wanda suka sace y'ata suna nan a kusa damu dan haka ko da zata karb'i yarinyarta sai dai nayi hak'uri har zuwa lokacin da aka san ko su waye suka aikata wannan d'anyen aikin,,dan haka nima tun daga lokacin dana fahimci dalilin da yasa ta fad'in hakan sai ban sake tuntub'arta da maganar lokacin da zata karb'i yarinya ba naci gaba da boy'e duk wani abu nata da zai iya sawa a fahimci asalinta...Wannan shi ne tak'aitaccen abunda ya faru,,amma Aisha ita ce y'ata dana haifa aka rab'a ni da ita a lokacin da ake k'ok'arin d'aukan JEEDDAH..! " Gaba d'ayan gurin idan aka zare Yarima da Ummi dukansu sun shiga wani irin mamakin da yake kama da sun fad'a comma dan yadda suke jin labarin kamar wani irin epic,shi kam Yarima wani kwantaccen murmushi ne a fuskarsa dan dama ya jima da fahimtar Jeeddah tana d'aya daga cikin ahalin su buh bai san yaya al'amura suka faru ba,shi yasa ko daya sani d'in sau bai tunkari kowa da batun ba,yayi keeping secrecy d'in in his mind da tabbacin zai binciko komai da sannu,sai kuma ga shi Ubangiji (S.W.T) ya dube shi yakawo masa komai da sauk'i,,Fulani ce ta kalli Inno bayan tagwayen ajiyar zuciya data sauke sannan ta ce "Yanzun Inno kina son sanardamu ne cewa JEEDDAH ita ce jininmu ba Aisha ba..?? Idan har kin ce ehh mene hujjarki akan haka..??" "K'warai ranki ya dad'e na tattabar JEEDDAH ita ce jinin wannan gidan,,kuma zan sake tabbatar da gaskiyar abunda na fad'a yanzun.." Jakar da tun shigowarta take tare da ita ta fara k'ok'arin bud'ewa sannan tasa hannu a ciki,wani d'an k'amin box ta fara cirowa sannan ta bud'e ta zaro d'an wani necklace na yara da yake ciki,kowa dake gurin ita yake kallo har ta gama d'ago shi tana musu showing "Idan har baku manta wannan ba na tabbata babu yadda za'ayi ace kun manta mamallakin wannan abun wuyar.." Da mamaki duka suke kallonta dan babu yadda za'ayi ace sun manta da samuwarsa,musamman Abba Galadima daya kasance shi da hannunsa ya sak'alawa y'arsa ta cikinsa,zazzage sauran y'an kayan dake cikin jakar ta sake yi nan take kayan jarirai ya fad'o da towel na d'aukan yara wanda duka suka kasance na musamman,tsantsar mamakin ganin last dress na jaririyarsu da kuma abun d'aukan ta yasa su fara gasgata cewar lallai Jeeddah ita ce jininsu to amma suna ganin wannan kad'ai bai isa ace sun rik'e shi a matsayin shaida ba dole ne suyi wani abun,,still Fulani ta sake numfasawa tana kallon Inno "Tabbas Inno tsayin shekaru mun kasance tare da ke a wannan gidan a matsayin hadimar mu,kuma bamu tab'a samun ki da wani laifi ko wani maganar banza ba,amma a yau kinyi abunda ya matuk'ar bamu mamaki, sai dai har yanzun bamu gama gamsuwa da batunki na cewa JEEDDAH ita ce jinin wannan gidan ba,dan haka dole zamu sa likitoci a lamarin dan mun san sune kad'ai zasu iya fayyace mana gaskiyan abunda muke nema.." Amsawa tayi cike da yardar ayi hakan,,ba'a d'auki dogon lokaci ba Ummah Fulani ta kalli YASEER tana sanar masa ya kira musu family Dr nasu,tunma bai gama amsawa ba Yarima yayi caraf ya karb'e zancen da cewa "Ba sai kun wahalar da likitoci ba dan kuwa ina d'auke da shaidan da zai tabbatar da abunda ake nema.." Idanunsu duka suka ajiye akansa da mamakin maganarsa,wasu kuwa da suka ga baza su iya yin shirun ba sai data kaisu ga tambayar sa "Shin wane irin shaida ne kake da shi broah..??" Cewar YASEER kenan dake kallonsa,,ita kuwa Umma'nsa cewa tayi "Idan har ka tabbatar kana da shaida maza ka nuna mana ita kowa ya gani yanzun.." Amsawa yayi da girmamawa sannan ya gyara zama tare da fito musu da wani farin envelope ya mik'awa YASEER da yake yafi kusa da shi sosai,cikin nutsuwa ya zaro ninkakkiyar takardar dake ciki ya wareta sannan ya fara bi yana dubawa,sanda ya tabbatar ya gama kuma ya gamsu ya mik'e ya kaita ga Abba'nsa,haka takardar tayi ta zagayawa a tsaninsu hatta da su Adda sai da taje hannunsu,nan take suka fahimci takardar bata komai bace face ta gwajin jini wato DNA,kuma nan take suka ganewa kansu cewar Jeeddan dai ita ce ke da alak'a da masarauta ba Aisha da suka d'auka ba,,kowa idanunsa akan Yarima da tunanin yadda akayi wannan AL'AMARIN ya faru,,sai dai babu wanda ya kaiga tambayar sa yadda aka yi hakan ya faru tunda sun samu tabbacin abunda suke nema,,,awanni sun sake shud'e,wanda bayan da komai ya gama wakana a wannan ranar mai cike da tarihi a kuma wannan gida Yarima ya sake yiwa A.S.P Hood magana akan su wuce da su Adda har ita kanta Ladidi dan kuwa AL'AMARIN a yanzun ya sake zani,dole ne sai an sake k'addamar da hukunci tunda ga wani laifin nasu da aka tono buh not now,,kawai dai sai an zauna kafin a zartar da sabon hukuncin,,nan take kuwa suka zo suka izza k'eyarsu suka wuce da su,,a nan ne kuma aka bar family'n cikin tsananin farin ciki da kasantuwar wannan ranar mai tafe da abubuwan al'ajabi............. #Follow #Vote #Comment. Then #Share. *®ɛąl ʂmąʂɧɛr.*😉 💠💠💠💠💠 *©® 2019..*  *WANI AL'AMARIN..!*💥 *(Book 2)* 💣💣 💥 *иα* *♡нawwa м.υ {$mαѕhєr}.♡* *Wattpad&Instagram* *@Jeeddahmu898* *______________________* *fαcєвσσk grσup:*https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *_____________________* *LOYAL TO MY FAMILY.♥* بسم الله الرحمن الر حيم. ^^^^^^^^^^^^^^^^^ ___________________ *BOOK 2. 📓* *Pg 42.* ^^^^^^^^ *#Raptures* Dukansu da suke zaune a parlor'n idan ka kalli fuskokinsu d'auke suke da wani irin delighted mai wuyar b'acewa,haka nan kowa cikinsu kallon Jeeddah yake cike da tsananin so mai tafe da tausayinta,,ABEELA da Abir kuwa tuni suka sata a tsakiya kowannensu ya rik'e hannunta d'aya suna ci gaba da tsiyayar da hawayen tausayin rayuwar y'ar uwartasu,haka nan suna mata murmushi a lokaci guda,ita kanta ba'a barta a baya ba dan kukan take,sai dai kukanta a wannan lokacin ba wai kuka ne da yake nufin abu d'aya ba,yadda ta tsinci tarihinta a yau ji take duk duniyar ma babu kamarta wajen farin jin nutsuwa had'e da farin ciki mara misaltuwa,haka nan a gefe guda tausayin Inno da Aisha da aka rabasu a dalilin son a d'auke ta ya hana zuciyarta nutsuwa dan yadda take blaming kanta akan faruwar lamarin,,a duk motsawar second ji take wani sabon k'aunar Inno na sake bijiro mata,dan yadda take jinta a zuciyarta ya wuce ta kwatanta da baki,,inda ainihin mahaifiyarta take zaune wato Ummi'n YASEER kenan ta d'ago idanunta masu cike da hawaye tana kallo,itanma Ummi'n ita take kallo idanunta da hawayen tausayawa kansu da kuma y'ar tata,duk da dai da fari ta so hanawa a bada labarin yadda komai ya faru dan yadda zuciyarta ke tsoron abunda zai faru,amma a yanzun kam zamu iya cewa tafi kowa farin ciki da kasantuwar komai daya zo musu da sauk'i,,murmushi tayiwa Jeeddah mai cike da tsantsar so da k'auna irin ta tsakanin d'a da mahaifi,kafin ta bud'e mata hannayenta alamun tana son taje gareta,babu musu ta zare hannayenta a cikin nasu Abir sannan ta nufi mahaifiyarta,ko da zuwanta a kusa da ita nan ta shige jikinta had'e da kwantar da kanta ta saki sabon kuka mai sauti,warm hug Ummi ta sake bawa Jeeddah itama tana hawayen had'e da murmushi duka a lokaci guda kuma tana shafa kanta da fad'a mata "Don't cry my child.. Kuka bai kamace kiba,,a yau ranar farin ciki ne a agaremu,rana ne daya kamata mu nuna godiyarmu ga ubangiji (S.W.T) domin shi yayi nufin wannan AL'AMARIN ya kasance garemu,, Ni yafi kamata na zubar da hawaye a wannan ranar ba keba..domin kuwa nice na amince kuma na janyo miki shiga irin wannan rayuwar.. Ki yafemin yarinyata.. Ki yafe min..!" "Umminah..! Baki yimin komai ba,,duk wani abun daya faru muk'addari ne daga

Chapter 58 of 63