Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
*@Jeeddahmu898* *Facebook:@RealSmasher.* *______________________* *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *_____________________* *LOYAL TO MY SISTER'S♥* بسم الله الرحمن الر حيم. ^^^^^^^^^^^^^^^^^ *ALLAHUMMA BALLIGHNA RAMADHANA BIL IYMAAN.....👏🏻👏🏻👏🏻* ___________________ *Pg 21.* ^^^^^^^^ A d'an tsorace ta juyo dan lokacin saboda tsabar gajiya da tunani ji take kamar bata cikin hayyacinta saboda yadda ta jima a tsaye ita da bata cika jurarta ba,numfashi ta sauke kafin ta d'an saki murmushi tana satar kallon basket en dake gefen ta "Me kike a tsaye a nan ne k'anwata..?? Na ga alamun ke ko ranar nan bakya ji.." Murmushin k'arfin hali ta sake saki kafin ta janyo basket en ta mik'a masa kawai da cewa "Dama Abinci ne na kawo muku,to kuma sai aka hana ni shiga shi yasa ban tafi ba na jira a nan ko Allah zaisa naga wani dana sani na bashi.." Fuskarsa da mamaki ya kalleta kafin ya furta "Me yasa kika taho da kanki bayan mun aika wanda zai karb'o..??" "Ehh! Babban Yaya Ummi ta sanar min yazo amsa,amma kafin na fito na kawo masa sak'on sai na iske baya nan na tambaya kuma kace ba'a san ina yayi ba.Shi yasa kawai naga ya dac nazo da kaina na kawo saboda ban san wane lokaci shi en zai dawo ba.." Murmushi yayi yana jinjina k'arfin hali irin nata "Kuma sai kika ga dacewar tsayawa a rana ko..??" "A'a ba haka bane Babban Yaya,da nazo ne suka hana ni shiga shi ne na tsaya nan kawai.." Da mamaki ya kalleta kafin ya tambayeta "Amma me yasa baki kirani ba da hakan ya faru..??" Shiru ta d'an yi tana sunkuyar da kanta k'asa kafin ta iya bashi amsa "Ai na manta wayan ne yau a gida shi yasa.." Jinjina kai yayi kawai yana fad'in "Shi kenan babu damuwa kawo ko..??" Mik'a masa tayi tana murmushi itama,bayan ya karb'a ta masa sallama kana ta juya zata tafi,da sauri ya dakatar da ita a nan inda take,sai daya fara ajiye basket en a booth sannan ya dawo inda take yana cewa "Muje ko na taka ki.." Babu yadda bata yi da shi ba akan ya je ita zata koma da kanta kamar yadda tazo amma yak'i barinta ta tafin,shi ya sama mata abun hawa ta shiga duk yaba tsaye yana kallonta yak'i tafiya,sai daya tabbatar da sun d'auki hanya sannan ne ya juya ya koma cikin motan,duk abunda ya faru a idon YAZEED akayi,ko da YASEER ya zauna juya kan motan yayi suka koma dan dama a time en fitowa suka yi da niyyan zasu je restaurant saboda sun jira dawowar khadimin da suka aika amma sai bai dawo ba,ba tare daya kalleshi ba ya furta "Me yasa tazo nan..?" Shima YASEER en bai kalleshi ba ya bashi amsa "Wanda muka aika ne ya tafi nasa uzurin,shi yasa itan tazo.." "Babu wasu ne da za'a iya bawa su kawo sai lallai ita..??" "Ni taya zan sani bayan muna tare da kai anan..?" Kallonsa yarima YAZEED yayi ya girgiza kai kafin ya juya yana kallon wani wajen "Ai kai ka cika matsala,babu dama a tambayeka sai ka bada amsar da ba ita aka tambaya ba.." "A gurinka na koya.." Rabuwa da shi yayi dan yasan matuk'ar zai ci gaba da kula shi tofa haka zasu tayi har sai ya gaji ya k'yale shi,dai² sun k'araso bakin k'ofar YASEER ya d'an dakata yana sauke glass en gefensa,saurin tasowa khadiman suka yi dan yadda YASEER ya tsaya a gurin sun san da magana,suna k'arasowa gurin kuwa YASEER ya had'e rai yana fad'in "Daga yau kada wanda ya sake hana wani shiga matuk'ar ya nuna akwai sak'on daya kawo,idan kuma zaku yi haka to ku jira har sai kun samu tabbaci daga gurin wanda aka zo gurinsa.." "In sha Allah ranka ya dad'e za'a kiyaye,ayi mana afuwa.." Ba tare da yayi magana ba ya rufe glass en sannan yaja motan zuwa ciki,lokacin da yayi parking ne YAZEED ya kalleshi "Me hakan yake nufi kuma..?" Cike da rashin fahimta YASEER ya juyo yana kallonsa "Mefa..??" "Ina nufin abunda kayi yanzun..?? "Ohhh! Wai kana nufin yanzun kafin shigowarmu..??" Jinjina masa kai YAZEED yayi yana lumshe ido "Hanata shigowa suka yi lokacin data zo.." Tsaki YAZEED yaja wanda yayi sanadiyyar dakatar da YASEER daga niyyan fita da yake yana sake kallonsa "Lafiya malam kake irin wannan tsakin ..??" "Ka bari kawai ni harkar sautar nan ne yake bani haushi wani lokacin,shi kenan komai kake da masu sa maka ido." Dariya YASEER yayi kana ya fice a motan yana bashi amsa "Kai dai ka sani..! Ni babu abunda zance a nan,kaima kuma kasan wannan ba abune da zaisa ka dunga irin wannan maganar ba,dan wata rana war haka kaine *SARKI...!"* Wata juyowa YAZEED yayi yana kallonsa fuska cike da b'acin rai "Amma dai kai sam baka san me ya kamata ka fad'a ba wollahi.." Dariya ya sake yi ba tare daya tanka ba ya wuce abunsa ya barshi nan tsaye yana kallonsa. ^^^^^ Dai² bakin k'ofar gidan aka ajiye ta tana sauka ta wuce abunta zuwa gida dan huta gajiya tunda Allah yasa ta kammala duk wani aikin da yake kanta a ranar,sanda ta bud'e k'ofar gidan ta shiga direct da zuwanta ta hau cire uban kayan data laftawa jikinta kana ta kwanta a kan gadon tana rufe idonta,sai lokacin tunanin had'uwar ta da Aisha ya fad'o mata,nan take tayi saurin bud'e idonta tana mik'ewa zaune,zuciyar ta duk ta cunkushe da tunanin abunda ya had'a Aisha da gidan sarautar,amma abun d'aure kan shi ne duk sanda zata yi tunanin wani abu sai taga sam ba shi bane,ko da ganin ta kasa gano alak'ar tasu duk kuwa da yadda tayi iya yinta sai dai bata gano komai ba,k'arshe kuwa kan dole ta hak'ura ta koma ta kwanta tana sakin murmushi zuciyarta na k'isima mata abunda ya dace tayi,nan take ta furta "Koma wace irin alak'a ne saina nemo.." Har ta rufe idonta ta sake bud'ewa a fili ta sake furtawa "Gaskiya ban yarda da Aisha ba,shin me zaisa duk wad'annan abubuwan da suka faru yanzun kuma na ganta cikin family'n maimartaba,shin da can maimartaba bai santa ba sai yanzun ko kuwa..? Anya babu WANI b'oyayyan AL'AMARI a tattare da ita...!?" Shiru ta sake yi tana tunani "Dole ne na bincika na gano,amma lallai ne akwai wata a k'asa...!" Tajima tana tunani kafin bacci ya d'auke ta mai cike da mafarkai masu dad'i da kishiyar haka. ^^^^^ A b'angaren Aisha kuwa tun data shiga gefen hajiya tayi ta damun Adda akan lallai saita tashi sun tafi,tun Adda'n bata d'auki maganar tata serious ba har kuma ta fara gasgatawa dan yadda taga Aishar duk ta koma wata sukuku da ita,haka nan dan babu yadda za tayi ta shirya suka yiwa hajiya sallama suka fito,lokacin da Adda ta nunawa Aisha su shiga gefen Fulani da Ummi suyi musu sallama k'i tayi,haka babu yadda Adda'n bata yi da ita ba amma fir tak'i ta kafe akan lallai sai dai itan taje ta dawo,itan tana jiranta a mota,haka nan Adda'n ta wuce tana girgiza kai saboda tsabar takaici gami da mamakin abubuwan da Aisha'n ke yi yau kamar wata wacce ta samu matsalar shafar jinnu. Bayan fitowar Adda daga gefen Ummi saboda ita ce ta k'arshe a zuwa yi musu sallaman data je,dan sai data fara zuwa gurin Fulani sannan ta biya b'angaren Ummi'n,nan ta iske Aisha ta kwantar da seat idanunta a rufe ta dafe kanta da hannunta,kallonta Adda tayi tana fad'in "Anya kuwa Aisha zaki iya driven en nan yau..??" 'Dagowa tayi tana bud'e lumsassun idanunta ta kalli Adda had'e da sakin murmushin k'arfin hali tana bata amsa "Ehh! Adda zan iya maida mu gida.." "A'a fa Aisha naga alamun jikin nan da gaske kike bakya jin dad'insa,gaskiya idan da hali ki bari kawai a samu wani ya maida mu,bana son a samu matsala ne.." "Zan iya Adda babu matsalar da za'a samu.." Badan ta yarda ba ta hak'ura ta shiga tana fad'in "Shi kenan Allah ya kaimu gida lafiya.." Amsawa tayi da ameen sannan tayiwa motar key suka bar gidan,har suka koma gida ba'a samu wata matsala ba haka babu wata hira data wakana tsakaninsu,sanda suka isa suna shiga gida Aisha bata iya zama a parlour anyi hiran ranar da itaba,tunda suka shigo ta saita k'afafunta tayi sama sai d'akin ta,tana shiga kuwa nanma en ta maida k'ofa ta kulle tana ajiye mayafi da jakarta,a gefen bed enta ta zauna tana tura head tie enta baya zuciyar ta duk a cunkushe saboda tsabar fargabar data addabi zuciyar ta "Me yasa zan ganki..?? Me yasa..? Me yasa².??...wayyooo Allah na..! Gaskiya ban so ba..me yasa sai a wannan lokacin zaki bayyanar min lokacin da kwanciyar hankali da nutsuwa suka same ni..? Gaskiya jeeddah ganinki sam bai zame min alkhairi ba,me zaisa mu sake had'uwa bayan a bayama ba alkhairi ya had'a muba..?? Shin wannan karon ko same kika zo min...??" Ire²n tunanukan da suka dami Aisha kenan a yinin ranar,yini guda tana cikin d'aki k'ofar ta a kulle ba tare data ko iya sake sakkowa k'asa ba bare asa ran zata iya tsinana wani abu.Adda kuwa koda taga haka nan tasa Ladidi a gaba akan lallai sau ta duba mata halin da Aishar ke ciki,lokacin data je ta tarar da d'akin a kulle komawa tayi ta sanarma da Addan abunda ta gani,rabuwa da ita duka suka yi dan a yanayinta ta gama fahimtar damuwa ce kawai a tattare da ita,hak duk sai basu sake kawo komai ba suka zuba mata ido har zuwa dare. Kwanaki biyu Aisha ta d'iba tana jinyar zuciya da gangar jikin ta,dan gaba d'aya cikin kwanakin ganin da tayiwa jeeddah sosai ya haddasa mata wani irin ciwon jiki mai tafe da zazzafan zazzab'i,cikin kwana uku duk ta zama wata iri,a kwana na uku ne shima da kyar aka samu ta ware bayan da Adda ta kaita aka mata allurai,bayan warewarta babu jimawa Adda ta b'illo mata da wani salo,haka nan suna zaune a parlour dukkan su,Aisha tayi nisa cikin tunanin daya zame mata jiki a cikin kwanakin,Adda ta waigo ta kalleta sannan tana cewa "Shin kinyi tunani akan maganar da kuka yi da sajida kuwa..??" Shiru Aisha tayi ta zubawa guri guda ido ba tare data bata amsar tambayar data mata ba,sake maimaita mata tambayar tayi,amma nan enma sai gajiya tayi da magana dan yadda a lokacin shima Aisha'n tayi shiru,fusata tayi ta kai mata mangari cikin zafin nama dan tsabar takaicin data ji,zafin dukkan daya sauka jikinta ne yasa ta firgita tana sosa gurin,harara Adda ta watsa mata cikin masifa ta hau ta da fad'a "Idan ba iskanci ba kina ji ina miki magana amma sai kimin banza kamar ina magana da gini.." Kanta ta sauke k'asa kana ta furta "Kiyi hak'uri Adda wollahi ban jiki ba.." "Dama taya zaki jini tunda kin sawa ranki jaraba da masifa,dama² ma ace kinyi tunani ne akan abunda ya dace da rayuwarki,amma saboda sakarci da rashin sanin ciwon kai kin nuna hakan bai miki ba,yarinya k'arama ta iya tunanin abunda ya kamata amma ke da yake sakara ce kin kasa fahimtar inda ya kamata kiyi tunani,sai neman jefa kanki a wahala da kike yi,ai wollahi ko dai kiyi hankali ki san inda nutsuwa da hanakalinki suke ko kuma ni dake musa k'afar wando tare.." Ladidi ce ta kalli yadda Adda take ta faman fad'a bakinta har kumfa yake saboda bala'i, cikin sassauta murya ta fara bawa Adda'n hak'uri kafin ta tambayeta abunda ke faruwa "Yo ba dole kiga ina wannan bambamin ba,yarinyar nan tana neman yi mana bak'in ciki,fisabilillahi ki duba kiga yada alkhairi ke neman samunmu amma tana neman yi mana sakiyar da babu ruwa.." Jinjina kai Ladidi tayi kafin tayi magana "To ni Adda ai ban san duk akan abunda kike magana ba,in banda ke da ita babu wanda yasan akan abunda kuke magana fa.." "Yo dama ai dole ne nayi fad'a saboda Allah ki duba ki gani,nan wai sajida y'ar wajen Matawalle tasa yarinyar nan a gaba tana nusar da ita hanyar alkhairi amma bud'ar bakin y'ar banzar sai ta nemi gayawa sajidar ma magana..Saboda Allah mene ne laifi dan tace sun dace da YAZEED..???" K'ik'k'ifta ido Ladidi tayi kafin ta bud'e baki kalmomin ta na tsinkewa ta furta "Aaa..Adda.da wane YAZEED kike magana ne akai..??" Kallon rashin fahimta Adda tayi mata kafin cikin jin haushin ta itama ta furta "Wane YAZEED ko nake nufi idan ba d'an gidan maimartaba ba..Ko kuwa akwai wani YAZEED da kike tunanin zanyi maganarsa..??" Saurin girgiza kai tayi tana bawa Adda'n amsa "A'a Adda babu.." "To ai shi ne na fad'a miki saboda tsabar wauta irin ta yarinyar nan take neman ta cucemu duka,idan ba dama irinsu marasa tunani ba ta ina mutum zai samu wannan damar ya nuna baya muradinta..??" "Haka ne Adda maganar ki nima na tabbatar babu wanda zaiyi hakan..??" "Ganemin hanya dai y'ar gari,ita kuwa ai kinga ta tsaya shirme,ke idanma bakya so wollahi ta dole sai kin koyawa ranki dan ni dai wannan maganar ban d'auke ta abar wasa ba,kuma yanzun nanma bada b'ata lokaci ba zan yima hajiya magana akan ta tuntub'i maimartaba da maganar kawai tun kafin a samu wasu suyi mana shigar sauri.." Babu wanda ya iya koda tari a cikinsu saboda yadda take ta fad'a kamar zata aro baki a wani gurin,haka ranar Adda tayi ta fad'an ta,babu mai tanka mata sai dan kanta kuma data gaji ta bari,sai dai abu kad'an za'ayi yasa ta sake taso da kwantacityar masifar data adana. Da dare bayan sun gama hirarsu Adda tayi musu sallama da ta shige d'akinta ta barsu nan parlour suna kallo,a hankali Ladidi ta juyo ta kalli Aisha da duka cikin kwanakin bata cika wata walwala ba bare fara'a ta dafa kafad'ar ta kana ta fara magana "Aishatu lafiya kike dai ko..Naji kinyi shiru.." Murmushin k'arfin hali tayi mata tana girgiza mata kai "Ehh! Baba ina lafiya.." "To Allah yasa haka ne,amma idan kinji kina da wani damuwa kada ki b'oye min kinji ko.??" Toh tace kafin ta yunk'ura zata tashi,dakatar da ita Ladidi tayi tana fad'in "Ni kuwa da naso muyi wata y'ar magana dake idan ba abunda za kiyi yanzun.." Kamar Aisha tace wa Ladidi tana jin bacci sai kuma ta fasa kawai ta koma ta zauna tana kallonta da cewa "To Baba ina saurarenki.." "Shin mene ne ya faru tsakanin ki da sajida da har ya janyo Adda take irin wannan fad'an..??" Shiru ta fara yi kafin daga baya ta fara bawa Ladidin labarin duk abun daya faru tsakanin su a ranar,tana gama bata labarin ta kalleta da fuskar tausayi tana cewa "Shin dan Allah baba ta yaya zan aminta da wannan had'in bayan duk abunda ya faru a baya,na tabbata matuk'ar yasan nice har kuma ya shaida ni da duk abunda ya had'a mu a baya,ina da tabbacin babu yadda za'ayi ya amince matuk'ar dai yana cikin hayyacinsa.." Dariya Ladidi ta saki mai ban mamaki,ko ga ita Aisha tunanin ta maganar tata zata bawa Babar tata mamaki kamar yadda itanma take ciki tun daga sanda suka yi maganar da sajida har zuwa yau da Adda ta tada maganar,mamaki ne ya kuma bayyana akan fuskar Aisha'n matuk'a kafin ta kalli Ladidi tana shirin yin magana,saurin dakatar da ita Ladidi tayi tana fad'in "Tabbas..! Adda tayi gaskiya..Ko kad'an Aisha baki yi tunani ba,shin har kin manta da abunda ya faru ne a shekaru biyar da suka gabata garemu..?? Ko kin manta da adadin masifa da bala'in da aka jefa mu..? wanda duka ta dalilinsa hakan ya faru..?? Aisha kiyi tunani matuk'ar akace kin manta ina mai tabbatar miki da ya zama wajibi ki tuna..Domin kuwa na jima ina rok'on Allah ya aramin dama da lokacin da zan rama abunda aka min bada hak'k'ina ba..Yanzun kuwa lokaci yayi da dama ta samu wacce zamu d'auki *FANSAR* duk wani zunubi da aka aikata mana,ya zama dole idanma mafarki kike ki farka dan wannan dama ce mai kyau ta samu da muma zamu yi amfani da ita wajen rama duk abunda aka mana..." Fanfo babu irin wanda Ladidi bata yiwa Aisha ba a wannan daren,tun babu sha'awar ta k'ulla alak'a da YAZEED en a cikin zuciyar ta,har ta fara jin sha'awar aikata hakan ba don komai ba sai dan tuna mata da irin azabar da aka gana musu a gidan yarin,nan take zuciyarta ta fara bushewa ta shiga tunanin irin hanyoyin daya kamata tabi ta rama duk abunda ya faru,Ladidi kuwa bata barta iya haka nan ba har sai data tabbatar ta gama karb'ar duk wani k'uduri nata,dare daya fara tafiya ne yasa kan dole sukawa juna sallama a lokacin bayan da Ladidi ta tabbatar da Aishar ta dawo kan network sannan ta sallameta ta tafi d'aki ita kuma taci gaba da zama nan tana sakin murmushi mai cike da tunanin irin nata matakin da zata d'auka akan duk wanda yake da sa hannu a ciki. Washe gari tun da safe bayan fitowarsu da niyyan yin break suka iske Adda zaune a parlour ita kad'ai sai faman cika take,daga dukkan alamun da dalilan da suka sata yin hakan kana kallonta kasan bazai wuce akan abunda Aisha tayi ba a kwanakin "Kenan hakan na nufin matuk'ar nak'i amincewa Adda a shirye take data dena kula mu duka ko me hakan yake nufi..??" Aisha tayi maganar ta a zuci,rashin samun amsa yasa tayi ajiyar zuciya kafin ta furta "Nasan abunda ya dace nayi yanzun.." Tana fad'ar haka ta nemi guri ta zauna a kusa da Adda tana y'an kalle²nta kafin ta furta "Adda dan Allah ki dena fushin nan haka kinji..??" Ba tare da Adda ta kalleta ba ta bata amsa "Kina so na dena tun farko kika k'i amincewa da abunda nima nake so..??" "A'a Adda..! Wollahi duka ba haka bane,amma in har amincewata zata saki farin ciki Adda wollahi nayi miki alk'awarin a ko wane irin yanayi a shirye nake da nayi komai domin ki..Matuk'ar amincewata a kan wannan maganar zaisa ki daina fushi Adda na shirya na karb'i duk mataki da kika yanke,matuk'ar zaki yi farin ciki da jin hakan ni kuma na shirya bayyana miki cewa *NA AMINCE......................!"* *Comments ya ragu cikin kwanakin nan saboda haka nima na shirya rage hannu wajen typing...Ko dai a gyara ko kuma ni na gyara..U have to choose...!* #Follow me on wattpad @jeeddahmu898. #Vote #Comment. Then #Share. *®ɛąl ʂmąʂɧɛr.*😉 💠💠💠💠💠 *AWESOME WRITER'S ASSO..🏮* ~_{Palace of excitation & pleasant writer's}._~ *©® 2019..*  *WANI AL'AMARIN..!*💥 💣💣 💥 *иα* *♡нawwa м.υ {$mαѕhєr}.♡* *Wattpad&Instagram* *@Jeeddahmu898* *Facebook:@RealSmasher.* *______________________* *fαcєвσσk grσup:* https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *_____________________* *LOYAL TO MY SISTER'S♥* بسم الله الرحمن الر حيم. ^^^^^^^^^^^^^^^^^ *ALLAHUMMA BALLIGHNA RAMADHANA BIL IYMAAN.....👏🏻👏🏻👏🏻* ___________________ _Hhhhhh..! Wato comments enku akan littafi baya tashi sai kunji marubuci ya sab'a lamba,akwai wani abu a tare daku da yake k'ara min nishad'i shi ne ci da zuci,matuk'ar kuka ga marubuci yayi wani abu a cikin labarinsa abunda yafi kamata kuyi shi ne ku bada k'afa zuwa wasu pages a gaba,idan har kuka ga yayi abunda bai muku ba sai ku magantu anan,nd abu na gaba shi ne damafa shi marubuci a duk lokacin da yayi ba dai² ba comments enku ne ke sawa ya gyara kuskuren,daga zaran kuma babu hakan zaku yi ta cin karo da mistakes a cikin labarin,amma ni kam na tabbata ko da comments ko babu yadda na tsara labarin in sha Allah haka zai kasance,ina da yak'inin d'ari bisa d'ari zaku fahimce ni zuwa gaba,sai dai ina fatan za kumin afuwa yanzun akan duk abunda zaku ga ya faru..Na gode sosai,thanks all for d lurv n care.Ur comments alwayz make me feels like am d best.#tag my Pep's._ *Pg 22.* ^^^^^^^^ Saurin kallonta Adda tayi tana sakin fuska cike da farin ciki mara misaltuwa kafin ta magantu "Y'an nan da gaske kike kin amince,ko kuwa dai kina son yimin wasa da tunani ne..??" Murmushi Aisha tayi mata tana lumshe ido had'e da jinjina mata kai,rik'o ta Adda tayi saurin yi ta mannata da jikinta saboda tsabar farin cikin data haifar mata da shi a lokacin "Amma dai Allah yayi miki albarka Aishatu Allah yasa ki gama da duniyar nan lafiya..Kai y'an nan dama zaki yi saurin amincewa haka..?? Wollahi banyi tunanin haka ba ko kad'an,nima tun farko da banyi miki haka ba..Kiyi hak'uri kinji..??" "Haba Adda me yasa ne zaki na bani hak'uri, ai duk abunda kika yi babu maganar kinyi kuskure,hasalima ni yafi kamata na baki hak'uri saboda na b'ata miki rai,ki yafemin addata dan Allah..!" Hannunta Adda tayi saurin rik'awa tana murmushi "A'a Aishatu dena bani hak'uri ai nima tun farko ba haka ya kamata nayi miki magana ba matuk'ar ina son ki amince,kamata yayi ace na lallab'a ki har ki amince amma sai nabi dake ta hanyar da bai dace ba,ki gafarce ni kinji y'ar albarka.." Tana murmushi ta sake kallon Adda,koda jin abunda ta fad'a tuni yasa ta b'ata rai sannan tayi magana "Haba Adda ni dai dan Allah ki daina bani hak'uri in dai ba so kike nayi miki kuka ba Allah kuwan.." "A'a kar kiyi y'ar albarka idan kika yi kuka ni kuma ina kike so nasa raina..??" Cikin shagwab'a ta b'ata rai tana cuna baki gaba "Shi kenan to na fasa.." "Yawwa ko kefa,nima yanzun tashi zanyi tunda zafi² akan bugi k'arfe,kafin wani abu ya gifta gara tun yanzun na kira hajiya na sanar mata yadda al'amarin yake kafin a samu wata matsalar tasa na manta..Bare ma wannan ba abune da za'a manta dashi cikin gaggawa badan babu mai manta alkhairi sai wawa..." Murmushi Aisha ta sake mata kafin Adda'n ta tashi ta barta nan tana sake sa mata albarka.Bayan tafiyar Adda da wasu y'an mintuna Aisha ta zame ta kwanta tana rufe ido game da sakin ajiyar zuciya mai k'arfi,hannunta ta goya a k'eyanta tana sakin murmushin jin dad'i kafin ta bud'e bakinta tana magana da kanta inda take cewa "Finally dai na amince Adda,nd yanzun komai zai tafi dai²...!" Har tayi shiru ta sake sakin wani murmushin tana jinjina kai game da lumshe k'ananun idanunta "Wahhh! *JEEDDAH...!* yanzun lokacin ya zagayo..!

Chapter 17 of 63