Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
*______________________* *fαcєвσσk grσup:*https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *_____________________* *LOYAL TO MY FAMILY.♥* بسم الله الرحمن الر حيم. ^^^^^^^^^^^^^^^^^ ___________________ *BOOK 2. 📓* *Pg 15.* ^^^^^^^^ *#Bleakness* Kallonta Malam yayi a d'an kaikaice jin tayi shiru tak'i cewa wani abu duk da irin yadda yake ta nuna mata farin cikinsa akan maganar auren,sam baiyi zaton idan taji baza tayi na'am ba,amma ga mamakinsa sai yaga sab'anin haka daga gareta,sake kallonta yayi yaga still tana a yanayin firginci,cikin b'ata fuska ya dubeta yana cewa "Inno wannan wane irin halin bak'in ciki ne kike neman nunawa..?? Shin ba abun farin ciki bane ace maimartaba ya nemi abu a garemu kuma mun sadaukar masa tunda har Allah yasa muna da iko da abun..?? A maimakon ace kina farin ciki sai naga sab'anin haka...??" Ajiyar zuciya ta saki mai k'arfi kafin cikin kasala ta d'aga kai tana kallonsa "To ni malam yanzun ai bana ce wani abuba duk abunda kaga ya dace ka aikata mu masu bin umarninka ne..!" Tabbas yaji dad'in furucinta sai dai yanayin fuskar ta da babu walwala yasa shi yin shiru bai sake cewa komai ba,a wannan halin jeeddah ta dawo ta iske iyayen nata sun yi shiru babu mai magana,sab'anin wasu lokutan da zata dawo ta riskesu suna kan hira,tun daga shigowar ta da Inno ta d'aga kai ta kalleta ta fahimci ba lafiya ba,dan yanayin yadda ta saba shigowa gida na yau ya bambanta da sauran ranaku,barka da hutawa tayi musu sannan ta wuce zuwa d'aki jiki babu k'wari,har ta bar wajen Inno bata bar kallonta ba,juyawa ta d'anyi bayan ta janye idonta akan jeeddan tana ajiye b'oyayyiyar ajiyar zuciya a hankali kuma ta jirkita zuwa gefe ta mik'e tana bin bayanta zuwa d'akin,can daga saman traditional iron bed d'in ta hangota her eyes were closed,hannunta d'aya ta d'ora saman fuskarta alamun dai tana tattare da damuwa,a bakin gadon Inno ta matso ta zauna tana kamo hannun jeeddan guda d'aya,saurin bud'e ido tayi tana kallon Inno with some glance "Jeeddatu mene ne yake damunki..?? Wani abu akai miki a can d'in..?? Ki sanar min idan akwai wani abu..!" Yadda taga Inno ta rikice cikin k'ank'anin lokaci yasa ta sakin sanyayyar ajiyar zuciya tana b'oye hawayen dake neman zubowa,saurin girgiza kai tayi tana sakin k'irk'irarren murmushi da iya karsa saman lips,her voice were full with some pampering tace "Nifa Inno babu abunda aka min,kawai dai ina jin kaina yanamin ciwo ne kawai shi yasa kika ganni haka..!" Ba don Inno ta yarda da maganarta ba ta girgiza kai tana sakin numfashi "Shi kenan jeeddatu tunda kice haka,maza ki nemi magani ki sha sai ki kwanta ki huta.." "Nifa Inno ba wani sosai ne nake jin ciwonba,naga duk kin damu.." Murmushin yak'e tayi mata sannan ta tashi ta fita tana mata sannu,a hankali tayi moving head asides tana bin bayan Inno da kallo har sanda ta tabbatar ta fita a d'akin,haka nan tana ganin fitarta a d'akin ta fara jin tahowar wasu hawaye,da sauri ta toshe bakinta saboda bata son sautin kukanta ya bayyana,alamun dawowar Inno taji da sauri ta goge hawayen tana rufe idonta kamar tana bacci,sanda Inno ta dawo ta isketa a haka sau ta d'auka ta fara baccin ne shi yasa kawai saita sake komawa ta rabu da ita ba tare data yi magana ba. Can a cikin gida kuwa lokacin da Yarima ya fita bayan maimartaba ya sallamesa,apartment d'in YASEER ya nufa kai tsaye,a hankali yayi knocking door d'in yana sakin numfashi,sanda YASEER ya fito ya iske shi a tsaye hanya ya matsa ya bashi alamun ya wuce,ba tare daya wuce ba ya juya yana fad'in "Precedes me!" "Why do i follows u..??" A hankali ya d'an waiwaya ya kallesa sannan ya sake juyawa yaci gaba da tafiya "It's necessarily..kawai kayi abunda nace.." Cikin d'aga murya ya furta "Wai kai haka ake yine..? Kawai sai mutum yana hutawa tare da iyalinsa ka nemi katse masa jin dad'i..??" Cak Yarima ya tsaya a inda yake yana sakin murmushi "U have to obeying me...?? If not I will...!" "Idan nak'i kuma fa..?? Me zaka yi..??" Har lokacin bai juyo ba yana tsaye a inda yake,kai ya girgiza yana cewa "Try me n see..!" Yaci gaba da tafiyan abunsa,girgiza kai shima YASEER d'in yayi lokacin daya tabbatar Yariman ya tafi,sai da ya saki siririn k'wafa kafin ya biyo shi a baya.Bai iya tarar da shi ba sai daya shigo apartment d'insa sannan ya ganshi zaune yayi crossing legs a saman center table hannayensa a had'e ya aza chin d'insa yana sauraren k'arasowarsa,yana shigowa ya watsa masa wani awful look,murmushi Yarima ya sakar masa nan shi kuma ya nemi guri ya zauna yana sake binsa da kallon "what?" D'innan,murmushi Yarima ya sake saki "Dillah malam ka fad'i abunda zaka fad'a ni kana b'atamin lokaci.." Shiru yayi masa kawai ya zuba masa ido,hakan da yayi kuwa ba k'aramin fusata YASEER yake ba,cikin hasala yace "Kasan Allah idan baza kayi magana ba zan tafi,tunda rainin wayo yasa ka kirani.." Still yarima kin motsi yayi bare YASEER yayi tsammanin zai yi magana,a fusace ya mik'e yana cewa "Duk sanda ka samu daman yin magana kamin magana nd bana son irin wannan time d'in coz ina tare da iyalina.." Eyebrow ya d'age sama yana kallonsa ba tare da tsammanin zai ce wani abuba har YASEER d'in ya sake kulewa,a fusace ya juya zai fice abunsa,sai sannan ya motsa daga zaman shirun da yayi yana fad'in "Whenever u go,u will be back..!" Chak YASEER ya tsaya dai² bakin k'ofa da hannunsa ajikin handle d'in ya d'auki y'an mintuna a tsaye a gurin kafin ya waiwayo,kallon me kake nufi yake jifansa da shi nan shima ya sake d'age masa one eyebrow,da ido ya masa alamun ya dawo ya zauna,kamar bazai dawo ba haka yaci gaba da tsaiwa,ganin hakan yasa yarima yin magana ba tare daya kalleshi ba "My friend..! U have to came back.. Tsaiwa ba naka bane a irin wannan lokacin." Sai daya harareshi sannan ya saki handle d'in ya dawo ya zauna yana had'e fuska,yadda yayi yaso bawa yarima dariya amma sai ya dake ya dai saki murmushi kad'an kafin ya fara labarta masa yadda suka yi da maimartaba,da sauri YASEER ya tari numfashinsa yana tambaya "Wace yarinya ce..?? Ya fad'a maka ko y'ar waye ne..??" Kai ya kad'a masa alamun "A'a" da mamaki ya kalleshi "Kai d'in kuma u have no idea da zaka tambaya ba..??" Sake kad'a masa kai yayi alamun haka ne,siririn tsaki ya saki kafin ya tambaye shi "To da baka tambaya ba what's the meaning of telling me..??" "I dunno..!" Ya fad'a yana d'age shoulders sama,"Ok" kad'ai YASEER ya fad'a kafin ya mik'e tsaye a hankali yana cewa "Whenever u find who she's..Nd from where she becomes,,sai ka sanarmin ko..??" "Dallah malam ai kai zaka nemo bani ba.." "Saboda nine zan zauna da ita kome kake nufi.." "U are not..buh u have to find..!" "Look my friend..u have to know...am not the one who stay with her..!" "Yeah! I knows.. But kuma dole ka bincika nd make sure ka fad'a min akan lokaci..!" Sakin baki YASEER yayi kawai yana kallon yadda yarima ke wani commanding nasa kamar yaro da uban gidansa,hannayensa goye akan chest ya zuba masa ido,yadda yaga Yariman ya d'aure fuska shima haka yayi yana ci gaba da kallon k'arfin halinsa "What do u mean..??" "I means whatever u mean..!" "U are not..! Ya za'ayi kana commanding d'ina sai kace wani yaronka..Why tun farko baka tambayi Abiiy ba sai yanzun ka zo ka nemi takurani.." D'an k'aramin tsaki yarima ya saki "Dillah malam jeka to tunda bara kayi min abunda nace ba..!" "Dama ka isa ka dunga min magana a haka ne sannan kayi tunanin zanyi,kawai dai dama ka rok'e nine saina tausaya maka nayi amma kana mandate nawa kayi tunanin zanyi maka abunda kake so.." Banza Yarima yayi bai sake tankawa ba dan haka shima YASEER ficewa yayi a apartment d'in yana mitan abunda Yariman yayi masa. ^^^^^ Misalin k'arfe 9:15pm Baba ya shigo gidan,tun daga shigowarsa daya kalli Inno bai sake magana ba sai cewa da yayi mata "Ina jeeddatu..??" A hankali cike da rashin walwala ta d'ago tana cewa "Tana d'aki malam,amma ta sanar min kanta na ciwo..!" Bai damu da abunda ta fad'a ba,saima umarnin kiranta daya bata,cikin rashin kuzari ta mik'e ta nufi k'ofar d'akin da jeeddan ke ciki,sarai tunda Baban nata ya shigo taji har kiranta da yasa Inno tayi duk akan kunnenka ne,dan haka tana jin yace a kira tan ta mik'e,tana niyyan fitowa suka had'u da Inno a k'ofar d'akin,komawa da baya Inno tayi itama ta biyo ta,har k'asa ta durk'usa daga d'an nesa kad'an tana yiwa baban barka da dawowa,cikin walwala ya amsa mata yana sakin fuska,kafin ya mata izinin zama,a hanakali ta zame ta zauna tana sake sunkuyar da kai k'asa,sai daya kira sunanta kafin yace wani abu "Shin duk abunda na fad'a zaki yi na'am da shi ko kuwa..??" Ya tambaya yana mai kallon sashen da Inno take ta rafka tagumi "Ehh baba..In sha Allah zaka same ni mai yi maka biyayya akan duk umarni da zaka bani..??" "Da kyau..! Shin akwai wani wanda kuke tare a yanzun..? Ina nufin saurayi..??" Nauyin bashi amsa taji da farko,har sai da ya ce "Ina fatan babu saboda a yanzun ina son sanar da ke na riga da nayi miki miji,,idan akwai wanda kuke tare ina mai umartarki da kiyi maza ki bashi izinin janyewa..!" Saurin d'agowa tayi ta kalli Inno,sai dai yanayin da taga fuskarta yasa ta sake maida kanta k'asa,ba tare data san me bakinta ya furta ba tace "To baba..! In sha Allah zanyi kamar yadda kace.." "Madallah..! Allah yayi miki albarka.." "Ameen" ta amsa sannan ya sallameta ba tare daya sake cewa komai ba,har ta yunk'ura zata mik'e ya sake kiranta "Jeeddatu..!" "Na'am baba.." Ta dawo tana amsawa,hannu yasa a aljihu ya d'auko #200 yana mik'a mata "Karb'i wannan..maza Kije ki nemo magani,naji Babarki tace kanki na ciwo..Ki samu kisha saiki koma ki kwanta ko,Allah ya k'ara sauk'i.." "Ameen" ta sake amsawa sannan tasa hannu biyu ta amshi kud'in tana masa godiya,d'aki ta koma ta d'auko hijab d'inta,bayan ta sanarwa da Inno zata je chemist ta fice a gidan zuciyar ta cike da damuwa mai tarin yawa.Tunda ta fito a hanya take jin wani irin bak'on yanayi a tare da ita,musamman maganar baba ta yanzun wacce jinta kad'ai ya haddasa mata shiga tsananin damuwa,jin yadda zuciyarta ke faman yi mata k'aik'ayi ne yasa ta dakata da tafiyan,can daga d'an wani sak'o ta mak'ale nan ta fara kukan da bata san dalilin sa ba,shin maganar da babanta yayi mata ce tasa ta kukan ko mene ne,ita dai duka bata sani ba,tana cikin wannan halin ta soma jin tashin scent a kusa da ita,a d'an firgice ta d'ago idanunta dake cike da hawaye tana kallon shadow d'in dake tsaye daf da ita saboda gurin babu haske "K'anwata..!! Me kike anan..?? Me aka yi miki...??" Muryar da bazata tab'a mantawa bane taji ya daki kunnuwanta,sake bud'e ido tayi sosai duk da bata iya ganin fuskar sa hakan bai hana mata fad'in "Babban Yaya..!" "Na'am k'anwata..?? Me akayi miki kika zo nan kika tsaya..??" Mamakinta a lokacin bai wuce yadda akayi yasan itane a tsaye a gurin ba "Babu komai." Ta fad'a tana scrubbing hawayen fuskarta "Babu komai kike kuka..??" Saida taji maganarsa har k'irjinta dan sosai kalamansa suka sa ta firgita,kenan yasan abunda take yi.?? For how long yake tsaye a gurin..?? Ta tambayi kanta "Kinga wuce muje na rakaki hanya ki koma gida..Bana son ganinki da irin wannan lokacin kina fita,ko ke baki san akwai had'ari mace ta dunga fita by this time around ba.??" Hanci ta d'an ja,alamar daya sake tabbatar masa kuka tayi,shiru ta d'an yi kamar baza ta motsaba,can kuma ta sake fashewa da kuka mai tab'a zuciya "Ya salaam..! " Abunda YASEER ya furta kenan yana dafe forehead d'insa da hannu d'aya,a hankali ya furta "Na tambayeki kince babu abunda aka miki,why yanzun kike kuka..??" Cikin sheshshek'ar kuka ta sake cewa "Babu komai.." "Ok..ok..! Ya isa to tunda bazaki fad'a min ba,wuce muje.." A hankali ta d'an matsa daga gurin da take tana cewa "A'a.. Babban yaya,nima ba gida zanyi ba.." "Ina zaki je da wannan lokacin..??" Ya tambaya yana zuba mata idanunsa duk da shima har lokacin baya ganin fuskarta "Zani chemist ne na duba magani.." Jinjina kai yayi yana sauke numfashi "Ok..! Baki da lafiya ne hala shi yasa ki kuka ko..??" Kai ta d'an karkad'a daga cikin duhun da take sannan tace "A'a..ni lafiyana k'alau.." "To fad'amin abunda yasa ki kukan..!" Jimm tayi ta kasa magana dan yadda take jin nauyin sanar masa,wai akan babanta yace zai aurar da ita ne take kuka haka,tabbas tasan abun kunya ne gareta ace tayi kuka saboda wannan dalilin,kome mahaifinta zaiyi akanta bai kamata ace ta kunyata shi ba.Clapping hannunsa yayi a saitin fuskarta,da sauri ta dawo cikin nutsuwar ta "What happens..kike irin wannan dogon tunanin..!??" Yanzunma niyyan ta tace babu komai,sai dai kafin ta k'arasa tuni ya tari numfashin ta "And don't even says u dunno.." Kai ta sunkuyar k'asa ta kasa magana "Zaki iya fad'amin damuwar ki yanzun..ko kuma baki amince dani ba..??" Kai ta d'an d'aga tana satan kallonsa "Bafa haka bane..!" Ta fad'a while her voice were full of pampering,murmushin gefe yayi yana kwaikwayonta "To da yaya ne..??" Mamakin yadda yayi magana tayi har tana sakin blush "Kai Babban Yaya,har da tsokanata..??" Murmushin dai shima ya sake yi kafin yace "Yeah! Ai naga baki so nasan matsalar ki ne,buh babu komai,muje ko na rakaki.." "A'a Babban Yaya..hakama na gode,ai na fad'a maka ba gida zanyi ba..!" "Ok.! To muje dai na rakaki..!" Tsayawa tayi tak'i gaba tak'i baya,ganin haka yasa YASEER matsawa daf da ita,ba tare da tasan abunda zai yiba taji ya kamo hannunta had'e da janyo ta daga inda ta b'uya,dai² ta d'aga ido tana niyyan magana saboda ta tsorata sosai da abunda yayi,hasken flash ya wulga a gurin,a tare suka juya suna kallon inda hasken ya fito cike da son gano me hakan ke nufi........... #Follow #Vote #Comment. Then #Share. *®ɛąl ʂmąʂɧɛr.*😉 💠💠💠💠💠 *©® 2019..*  *WANI AL'AMARIN..!*💥 *(Book 2)* 💣💣 💥 *иα* *♡нawwa м.υ {$mαѕhєr}.♡* *Wattpad&Instagram* *@Jeeddahmu898* *______________________* *fαcєвσσk grσup:*https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *_____________________* *LOYAL TO MY FAMILY.♥* بسم الله الرحمن الر حيم. ^^^^^^^^^^^^^^^^^ *Gaisuwa ta musamman zuwa ga fan's d'ina na Wattpad da Facebook,wannan sak'on gaisuwar daga zuciyata ya fito bawai iya kar harshena ne ya furta ba,,na gaishe ku kyauta mutanena.😄* ___________________ *BOOK 2. 📓* *Pg 16.* ^^^^^^^^ *#Marriage affirms* Iya hange da dubawa sunyi sai dai babu ko alamun mutum ya tsaya a gurin bare suga gilmawarsa,da sauri YASEER ya saki hannunta yana d'an komawa gefe a dalilin jin wani irin fad'uwa da gabansa yayi,ita kam JEEDDAH kai ta sauke k'asa tana scrubbing k'ananun tears dake neman sakkowa saman fuskarta,a hankali cikin wani yanayi ta jiyo muryar YASEER a cikin kunnenta "K'anwata ya kamata kiyi hanzarin barin gurin nan..for now kinga abunda ya faru,buh bamu san me zai biyo baya ba gaba.." Kai ta d'an kad'a masa alamun taji,sannan a hankali cikin rashin kuzari ta shiga d'aga k'afafunta,nan a tsaye ta barshi sai da yaga b'acewarta sannan ya sauke nauyayyun numfashi a hankali kuma shima d'in ya waiwaya yana sake duba gurin da fatan zai samu wani abu a gurin,sai dai har ya gama zagaye gurin bai samu komai ba,haka nan shima d'in ya juya zuciyar sa cike da fargabar abunda zai faru. Jeeddah kuwa ko data bar wajen kai tsaye hanyar gida ta juya dan tunda abun ya faru take jin bazata tab'a iya zuwa wani neman magani ba haka nan take jin zuciyar ta cike da fargabar abunda ya farun,dai² sanda ta shigo gida Inno tana zaune a tsakar gidao daga k'asan awning ta rafka tagumi da duka hannayenta kallo d'aya ya isa sawa mutum ya fahimci tana cikin matsanancin damuwa,sai dai duk da hakan ba wai tana tunani bane,kawai dai tayi shiru ne ta zuba idanunta akan hanya nd she was awaiting taga shigowar Jeeddah a gidan,tana shigowar kuwa ta saki wani ajiyan zuciya mai k'arfi sannan ta amsa mata sallamar duk da a ciki² tayi,a sab'ule take tafiya duk wani motsinta akan idon Inno dan haka har ta expiring inda Inno ke zaune ta d'ago tana kiran sunanta,chak ta tsaya a gurin sai data ja numfashi sannan ta iya juyowa dukanta,a gaban Inno ta tsuguna tana sauke kai k'asa "Kin samo maganin..?" Sai da k'irjinta ya buga saboda sam bata yi zaton tambayar da Inno zata mata ba,a hankali ta bud'e baki ta furta "A'a ban same suba.." "To shikenan wuce ki kwanta in Allah ya kaimu zuwa safe zai sauka ciwon,idanma bai daina ba,da safen sai a nemo miki maganin." "Toh...Sai da safe.!" Ta fad'a tana mik'ewa daga gurin da take tsugune "Allahu ya bamu alkhairi.." Inno ta amsa mata tana bin bayanta da kallo har ta shige d'akin amma ita d'in ta kasa matsawa a inda ta barta,sai da ta shafe ak'alla wasu mintuna masu yawa da bata san adadinsu ba sannan ta mik'e tana sakin dogon ajiyar zuciya daga haka ta wuce ciki itama zuwa d'akin mai gidan nata. Washe gari kam tun da safe kafinma ace Jeedan ta kaiga tashi a bacci,sai ga sak'o daga cikin gida gurin Ummi ta aiko a tafi da ita,amazingly nd strains Inno ke bin matan da kallo dan ita dai wannan AL'AMARI ba k'aramin d'aure mata kai yake ba kuma yana matuk'ar bata tsoro,haka tana kallonsu bayan sun gaisa ta kuma ji sak'on uwayen gijin nata ta basu hanya suka nufi d'akin da jeeddan ke kwance,cikin barcinta ta fara jin ana tashinta kasancewar bata wani samu isashshen bacci ba da daren a dalilin abubuwa da dama wanda suka sata shiga matsanancin damuwa,a hankali ta fara ware idanunta a cikin d'akin har ta gama bud'e su tsaf,nan ta sauke su akan matan dake tsaye akanta "Ranki ya dad'e.. Barka da tashi..!" Suka fad'a yayin da ita kuma kanta ya kulle jin abunda matan ke fad'a nan ta shiga tambayar kanta "Ranki ya dad'e..?? A ina kenan..??" Katse mata tunani suka yi ta hanyar fad'in "Idan har kinyi mana izini muna son gabatar da sak'on uwar gijiyar mu gareki.." Kallonsu taci gaba dayi tamkar status har bata san me suke cewa ba sai da taji an kamo hannunta,a hankali tabi hannunta da kallo tana kuma bin y'ar dattijuwar dake rik'e da hannun nata "Ranki ya dad'e,,An umarce mu da kada mu b'ata lokaci wajen tahowa dake..!" Da kyar ta iya had'iye wani abu a bakinta sannan taci gaba da binsu da ido,dai² nan Inno ta shigo jin shiru basu fito ba har lokacin,ko da jeeddah ta hangota tsaye a k'ofa da sauri ta mik'e ta nufe ta,dan har lokacin bata yarda da abunda idanunta da kunnuwanta ke jiye mata ba,hannunta Inno ta rik'o ta jata suka fice tana yiwa matan alamun su d'an dakata,fita suka yi daga d'akin zuwa tsakar gida,sai data zaunar da ita sannan ta zauna itama tana kallon yadda duk take cikin damuwa,a hankali ta ambaci sunanta,sake zuba mata ido jeeddah tayi sai dai bata iya amsawa ba "Jeeddatu..!" Inno ta sake kiranta a karo na biyu "Na'am.." Ta amsa tana jin fargaba na saukar mata "Ina so ki bani aron hankalinki nan,sannan ki saurari abunda zan fad'a miki,duk a yadda zaki ji furucina ina so ki rik'e shi a zuciyar ki sannan kiyi amfani da duk wani shawara nawa,bana so ki biyewa son zuciya domin wata rana zai kaiki ga aikata dana sani,wanda bana miki fatan hakan.." Shiru tayi sai kunnenka data baza tana jin abunda Inno ke fad'a "Na san dai a yanzun da kika tashi ko ban fad'a miki ba idanunki sun gane miki wani abun,sai dai abunda nake so na sanar miki shi ne duk abunda za'a ce miki kibi su da duk yadda suka ce miki kiyi,banda musu ko nuna baza kiyi ba,na tabbata daga yau babu lallai ace mun sake had'uwa,dan zasu tafi dake ne yanzun,ina fatan duk inda kika tsinci rayuwarki zaki yi hak'uri ki kuma karb'i k'addarar da zata same ki,na sani wata rana sai labari,duk abunda zai same ki ina horanki da ki tashi ki fad'awa mahaliccinmu domin kuwa babu abunda yafi k'arfinsa..!" Nasiha sosai Inno tayi mata mai saukar da wani irin yanayi har cikin b'aro,sun d'auki lokaci mai tsayi tan ta mata nasihan sannan ta d'an kalleta tana cewa "Maza Kije ki shirya ku tafi,Allah ya tsare ya kuma kiyayemin ke a duk inda kika kasance.." Kuka ne yayi grabbing mata da take jin inama zata dawwama tana yinsa akan ace taga wannan ranar da za'a rabata da Inno'nta,dai² nan matan suka fito suna yiwa Inno magannar ta basu ita su wuce suna sauri ne nd ance dasu kada su b'ata lokaci,a hanakali Inno ta mik'e ta nufi d'akin jeeddan ta d'auko mata hijab da nik'ab d'inta da sauran y'an wasu y'an kayan data san zata buk'ata a kusa tunda taga alamun idan ta itane bazata yi hakan ba,sanda ta dawo inda take zaune har lokacin tana ta rusa kuka kamar wacce aka aikowa da sak'on Inno'n ta rasu,ita da kanta ta saka mata hijab d'in sannan ta d'aura mata nik'ab d'in da,bayan ta gama d'aura mata hannunta ta kamo sannan ta dank'a a hannun matar tana cewa "Gata nan..Allah ya kiyaye hanya..!" Juyowa jeeddah tayi dai² sanda Inno ke k'ok'arin barin gurin saboda damuwar da take jinta a ciki,ita kanta ji take kamar ta fashe da kukan ko hakan zaisa ta samu sassauci a cikin zuciyar ta,tana ji tana gani Inno ta shige d'aki ba tare data ko bari taga tafiyarsu ba,har lokacin jeeddan hawaye take har suka kaiga fita a gidan suka kama hanyar cikin gida bata bar kukanba. Ita kanta Inno dai² lokacin data tabbatar sun fita a gidan,haka nan ta ji saukar abu mai d'umi a saman fuskar ta,ko data kai hannu ta shafa take taji ruwan hawaye,sai da tayi mai isarta kafin ta goge

Chapter 37 of 63