Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ficenta duk sai ya zamana yana kan idanunsu ne,,wannan karon kam Ubangiji ya ara musu lokaci nd duk burinsu da mummunan nufinsu sun aikata kuma sunyi nasara,a wannan lokacin ne har suka sami damar sace jaririyar da take kan kwanaki arba'in da zuwa duniya ba don komai ba sai don azabtarwa da zaluntar wanda baiji ba bai gani ba,,wannan jaririyar da nake magana ba kowa bace face jaririyar da Ummi ta shaida muku ta rasu nd ta shiryata tun a daren,shin kun san mene ne yasa ta fad'a muku haka..?? Kasancewar ta uwa mahaifiya da baza ta so wani mummunan abu ya faru ahalinta ba shi yasa a wannan lokacin ta b'oye muku gaskiyan abunda ya faru a wannan daren,haka nan duk da tsananin tashin hankalin da take ciki a sakamakon neman jaririyarta ta rasa hakan baisa ta shaidawa d'aya daga cikinku ainihin labari ba,sai tayi k'ok'arin dannawa duk da ciwon da take ji a k'asan ranta,buh sai dai na tabbatar d'aya daga cikin amintattun hadimansu ta san komai,,da fari Adda sun sone su k'ullawa wannan gidan bak'in ciki wanda bazai tab'a gogewa ba ta hanyar kashe yarinyar da aka d'auko,daga baya a time d'in da suka tabbatar sun same ta sai suka fasa ta inda suka yanke shawaran su raineta sannan su rik'e ta a matsayin makamin su na shirya duk wani zaluncin da zasu kasance suna yak'ar wannan gida da shi,,bayan sace Jaririya Jeeddah a gidan nan,wacce tun asalin taci sunan Hajiya sai suka yi niyyan d'auketa daga garin gaba d'aya,sannan suka yi nisa da ita nd suka canja mata suna da duk wani abu da suka san zai janyo a gane daga HAUWA'U JEEDDAH zuwa AISHA,ba don komai ba sai don son cimma manufofinsu da kuma son aiwatar da duk wasu mugayen al'amuransu akan wannan ahalin,,tun da suka bar garin nan da ita,basu sake waiwayarsa ba sai bayan ak'alla shekaru goma sha hud'u,wanda tun daga nan ne sai ba'a sake jin d'uriyarsu ba haka nan babu wanda suka aminta yasan labarin inda suke rayuwa,wanda akan wannan dalilin ne yasa wasu a cikin ahalin gidan nan suke tunanin ko sun rasu ko kuma wani mummunan abu ya same su. A wannan lokacin da ake fama da wannan irin tunanukan na tabbata babu wani d'aya da zuciyarsa ta kawo masa kan wani abu sab'anin mutuwa,saboda tun a bayan barin su gari babu wanda suka nema kuma babu wanda yasan ainihin gaskiyar lamarin shi yasa babu wanda yayi tunanin suna rayen,,buh ni na san da zamansu saboda yadda muke da Adda tunma a wancan lokacin ku kanku kun san abune da yake matuk'ar wahala ace ban san da zaman su ba,sai dai ganin nima ban fito na nuna nasan inda suke ba shi yasa babu wanda ya tab'a nufoni da batun ko nasan inda suke,,,kwatsam a wani lokacin can bayan tsayin shekarun da aka shafe ba'a ji labarin suba sai muke magana da Adda inda a nan ne har take shaida min bata k'asar ta je Saudi Arabia buh ta bar Ladidi da Aisha a nan k'asar mu Nigeria a can yankin garin Bauchi,harma take sanar dani dalilin da ya janyo tayi fushi ta bar k'asar,wanda ba komai bane face irin rashin nasarar da suke yawan samu,,sai dai abunda ban sani ba shi ne lokacin da muke kan yin wannan maganar da Adda,ita Ladidi'n tuni har sun dawo cikin garin kano kuma a cikin gidan nan harma sun nemi gida suna zaune ba tare da kowa ya gane su ba a matsayin jinin wannan ahali,,,wannan shi ne farkon alak'ar su da gidan nan a bayan sake dawowarsu,sannan shi ne asalin lokacin data k'ullawa Yarima mugun *K'azafin* da har ya janyo masa zuwa gidan kangararrun yara,,wannan yarinyar da take tare da su itace asalin yarinyar da aka haifa aka ce ta rasu,wannan itace ainihin gaskiyar wannan labarin.." Gefen Aisha ta kalla tana mai cewa "Aisha yau Allah ya nufa,ya kuma kawo mu ranar da kika san ko ke d'in wace ce,a yau kinji cikakken asalinki da danginki,,,sai dai ina sake neman afuwarku akan sanin wannan gaskiyan da nayi amma sai na kasance mai binnewa ba tare dana sanar da kowa ba,,na tabbatar ba komai ne yaja ni ga aikata haka ba sai a sakamakon k'ulla auren SAJIDA da Yarima da akayi ba tare da an nemi jin shawaran bakina ba a matsayina na uwa mahaifiya da take da nata hak'k'in akan y'ay'anta,wanda ni kaina a wancan lokacin saboda ban tsayi nayi tunani ba nayi ta biyewa mugayen shawarwarin Adda tana sake zuga ni kan kada na amince,,abunda ban sani ba duka a wannan lokacin ashe tana amfani dani ne kawai akan son cimma muradinta,na tabbatar a wancan lokacin data samu damar had'a aure tsakanin Aisha da Yarima babu abunda zai hana basu ruguza rayuwar duk wani mutum d'aya da yake cikin wannan gidan ba,sai dai hak'ik'a Allah ya fita dan ya sake gwada mata cewan bata isa taja da lamarin ba,saboda haka bisa ikonsa sai magananma duka baije ko ina ba,tunda kowa yak'i accepting,wannan dalilin yasa ta dad'a fusata a sanda taji labarin za'ayi auren Yarima da SAJIDA,hakan ne yasa ta shiga min zuga sosai akan kada na amince da batun neman auren,nd har aka yi auren nima sai duk tashin hankali da nayi ta yi Ubangiji ya k'addara sai anyi auren,buh duk da hakan bata hak'ura ba inda ta d'ora da mugun sihirin da har ya janyo musu yim wani irin rayuwar da babu komai ciki sai zallan bak'in ciki,wannan shi ne abu na k'arshen daya janyo muka yi rabuwa mara dad'i a tsakaninmu nd sune suka yi sanadin da yasa ZAHRA y'ar gidan ambassador Abdulmalik ta turo maganar ta fasa auren,sune suka sa duk neman auren da aka yita masa a wannan lokacin yak'i tabbata duk inda aka je sai an dawo ba tare da nasara ba,,duka baryinsu akan wannan gidan shi ne ya dawwama ba tare da farin ciki ba..Wannan shi ne dalilin su na k'ulla duk wannan abubuwan..Idan nayi wani maganar da ba shi ne ya faru ba akan wannan lamarin gasu nan duka suna kallo kuma sun sauraren duk abunda na fad'a,idan har nayi musu k'arya ne zasu iya musawa ko kai tsaye su kalle ni su ce nayi musu k'arya..!" Kowa a parlor'n yayi wani irin shiru mai tattare da d'umbin mamakin yadda aka yita shirya irin wad'annan al'amura ba tare da sanin kowa ba,sannan babu wani wanda ya fahimci yadda duk wannan al'amuran suke tun gabanin yanzun,,nd kowa kuma a wani bigiren na zuciyarsu suna mamaki kan yadda akayi Yarima ya iya gano wani abu a cikin irin tuggunsu har ya janyo a sanadin hakan asiruinsu ya tonu,Abba Galadima kam Ummi yake kallon yana kuma sake kallon Aisha da aka ce y'ar suce yana jinjina AL'AMARIN,haka nan yake jin zuciyarsa ta masa wani irin haske a ranar yau buh yana zaunen ne kawai ba tare daya aminta da kasancewar Aisha y'arsa ba dan yadda yake ganin abun kamar wani dramatizes kuma kamar hallucination,shi dai kawai ga shi nan ne amma ya kasa tantance yanayin dake cikin zuciyarsa,exultant or sadness nema duk he can't even contrast,,Maimartaba duka zuwa su Hajiya kowa dake gurin kallon Aisha yake da wani irin courteous manne a fuskokinsu,ba komai suke kalla a tare da ita suke jin tausayinta kamar haka ba musamman yadda ta rayu tun tana jaririyar a tsakanin mutane irin su Adda da suka kasance marasa imani da komai zasu iya yi akan cikar burinsu ciki kuwar harda zare jariri d'an forty days daga bakin nonon uwa,tabbas sun san dabara ko k'arfi bai isa k'watanta a hannunsu ba haka nan sun san ba komai ya ceci rayuwarta daga fad'awa halaka ba face Ubangiji (S.W.T) wanda ya rubuta hakan a littafin k'addararta,ya kuma zana cewa sai ta rayu ta kuma taka doron k'asa da k'afafunta,ya kuma k'addarawa tun a wancan lokacin tana da sauran rayuwa agaba,shi yasa Ubangiji hana su damar hallakar da rayuwarta yasa suka raineta bayan tasowanta a gurinsu,yanzun kuma ikonsa da k'arfin mulkinsa suka sa asirinsu bankad'ewa ta san asalina a dai² lokacin data gama fidda tsammanin samun hakan,kamar yadda ya raya Annabi Musa (A.S) a gidan fir'aun,,ita kuwa Aisha dake zaune gefe wacce tunda Hajiya Suwaiba ta fara shek'a jawabi,ai tunda ta tsinto labarin asalinta a yau da inda ta fito da abubuwan da suka faru da rayuwarta tun kafin wannan lokacin tuni har hawaye sun jima da b'allewa a idanunta,kuka take tamkar zata cire ranta ta yar duk badon komai ba sai don irin yadda aka d'inta using nata ana cutar da ahalin data kasance itama daga cikinsa ta fito,,duka da suke zaune a gurin babu wanda bai tausaya mata ba,musamman irin su Jeeddah,Abir da ABEELA kuwa tuni fuskokinsu sun jima da jik'ewa da hawayen tausayinta,,Fuskar Yarima kuwa a lokacin a d'aure take tam,zuciyarsa da gangar jikinsa kuwa ko sofanen tausayin Aisha babu a cikinsu bare asa ran nan da wani lokacin zai yi magana ko wani abu makamancin haka,yadda duk sheshshek'ar kukansu ya cika masa kunne ne yasa shi d'agowa yana kallon yadda suka dage sai kuka suke kamar wad'anda aka aikowa da sak'on wani nasu ya rasu,nan da nan yaji zuciyarsa ta sake hawa da b'acin rai gami da jin wani haushin su na lokaci guda har bai san lokacin da wani tsaki yayi escape a bakinsa ba,ai kuwa nan duka yaja hankalin jama'ar gurin da suka yi shiru na tsayin lokaci,,Inno ma tana zaune duk wannan dogon sharhi da Hajiya Suwaiba taja tana saurare sai dai mamakin yadda taji ance yarinyar da aka sace na raye yasa ta daskarewa a nan tamkar wani daskararren ginin daya shekara hamsin bai motsa ba "Suwaiba..! Kin tabbatar da abunda kika fad'a gaskiya kika sanar damu...??" Hajiya da take cikin wasu commotions tun farkon bada labatin ta fad'a cikin fizgo maganar tana sake kallon Aisha,sai da Hajiya Suwaiba ta jinjina mata kai sannan ta furta "Na rantse da Allah.! Yadda kuka ji nayi rantsuwa tsakanina da mahaliccina haka wannan maganar take babu sofanen k'arya a cikinta,,amma matuk'ar kun nuna baku yarda ba kuna iya bincikawa ku tabbatar da gaskiya.." Kowa sake jinjina maganganun yake a ransa,nd Ummi kam tana zaune ne a gurin amma zuciyarta cike yake da taradaddin anya ta yarda da wannan batun kuwa..?? haka ma YASEER shima irin tunanin dake zuciyarsa kenan buh duk cikinsu babu wanda yayi ko tari a bari ya furta abunda ke k'asan ransa sunyi shiru suna bin kowa da kallo "Zo Aishatu..! Ki daina kuka haka nan kinji..!" Muryan Umma'n YAZEED ta ratsa kunnuwansu,dukan su da mamaki a fuskokinsu suka juya suna kallonta coz babu wanda yayi tunanin Ummah Fulani zata yi makamancin hakan musamman data riga tasan ko wace ce Aisha har ma da farkon alak'ar ta da gidan,,kai Aisha ta shiga girgizawa muryanta cike da tashin hankali tana fad'in "Ban cancanci zama d'aya daga cikinku ba,,na tashi tare da mutanen da ban san ko su d'in su waye a rayuwarta ba,duk da sun d'auke ni akan wani manufar su,bana son rab'ar wannan gidan da kowa,ku barni nayi nisa da ku,dama can ban san kowa ba,haka kuma baku san ina rayuwa a duniyar ba,besides an jima ana amfani da ni wajen cutar da ahalina duk ban sani ba,na sani a matsayina na musulma sam hakan ba shi ne abunda addini na ya umarce ni nayi ga wanda nake rayuwa da shi ba ko da ace ya kasance mun samu sab'anin zamowa y'an addini guda,,sai dai kash! Maimakon na zama wacce za'ayi alfahari da samuwarta a duniyar sai na kasance wacce za'ayi Allah wadai da ita,,nayi nadama kuma nayi bak'in cikin samun asalina a dai² irin wannan lokacin dana gama zame musu masifa,dan haka nake rok'on ku bana son sake rab'ar kowa,bare na aikata wani laifin kwatankwacin wannan,,dan Allah ina so kuyi hak'uri da ni ku barni nayi nisa da kowa..Amma kada kuce zaku hana ni tafiya.." Nan kuka ya sake cin k'arfin ta "Babu wanda zai hana ki tafiya,,a duk lokacin da kika so kina iya yin k'aura daga duniyanma baki d'aya ba wai iya gidan nan ba..!" Fuskarsa a matuk'ar d'aure yayi furucin yana kuma sake binta da kallon da yake sake jadadda mata irin k'iyayyarsa gareta,murmushi Aisha ta saki mai ciwo,sannan ta sunkuyar da kanta k'asa dan irin kallon da yake jifanta da shi bazata tab'a iya jure masa ba,zuciyarta cike da matsananciyar kunyarsa kan irin laifukan da ta aikata masa ta furta "Na gode sosai YAYANAH bisa goyon bayanka gare ni..sai dai ina rok'on afuwarka,haka nan bazan gushe ba ina sake neman yafiyar laifukana a gurinka har sai ranar d'aka furta cewan ka yafe min..!" Wani uwar hararan daya bankad'a mata yasa ta datse maganarta ba tare data shirya yin hakan ba,tsakin dai still ya sake saki cikin izzar mulki ya sake d'aure fuska,YASEER ne ya d'an tab'a shi cikin k'asa da murya ya shiga masa magana "Man why are u behaving like this ne..?? I think mun riga munji ko itan wace ce a gurinmu nd mun san duk abunda ya faru da dalilinta na aikata maka haka,,why after all thus marveled things da muka ji,muka gani kake k'ok'arin nuna kyamar jininka..??" Alakoron hararan shima YASEER ya tsinto daga gare shi cikin fushin da bai tab'a ganin Yarima a ciki ba ya shiga bashi amsa "I think u have already rushed how i hate her,,ka sani bana ko son ganinta a inda nake,me zaisa ka dunga had'a ni da ita .?? She won't became my sister.. ever..!" "Ok..good buh if u don't..!" "Stop! Man..let us enveloped this phrase.. I don't want it..!" Iya jin haushi a wannan lokacin YASEER yaji haushinsa dan yadda yake nuna zallar k'iyayyarsa ga Aisha abun dole ne ya tab'a duk wani mai alak'a da ita,musamman kuma shi d'in da a yanzun yake ganinta matsayin k'anwarsa mafi kusanci da shi ta yaya ne zai so a dunga nuna mata irin wannan k'iyayyar bayan duk babu laifinta a cikin abubuwan da suka faru,,,Inno ce ta d'ago daga dogon zangon tunanin data tafi a lokacin duka idanunta sunyi wani irin jaa saboda tsanantawa kanta da mugun tunanin da tayi,kamar wacce aka ce dole tayi magana ta kalli Hajiya Suwaiba tana fad'in "Hajiya shin kin tabbatar wannan yarinyar ita ce wacce aka d'auka a gidan nan..??" Idanunsu ne suka yi yuuu duka zuwa kanta dan jin yadda tayi tambayar kamar wacce bata san me ake magana akai ba tun kafin lokacin,sai yanzun take son fahimta "K'warai kuwa..Kamar yadda kika ji na fad'a wannan ita aka d'auka kuma itace ta rayu a hannun Adda.." Kallon inda Hajiya take Inno tayi tana jinjina kai fuskarta d'auke da wani yanayin da zai wahala a gane takamaiman mene kwance a fuskan ta ce "Matuk'ar kuwa akace Aisha itace jaririyar da aka d'auka a wannan daren a wannan gidan,,tofa ina da abun cewa,,dan akwai wani gaskiyar da zan bayyana muku yanzun idan har an bani dama............" *Kuyi hak'uri da wannan aradu da kyar na iya yinsa,,nd ina muku albishir kan cewa in sha Allah muna daf da zuwa k'arshen labarin,,buh ku sake hak'uri da ni..* #Follow #Vote #Comment. Then #Share. *®ɛąl ʂmąʂɧɛr.*😉 💠💠💠💠💠 *©® 2019..*  *WANI AL'AMARIN..!*💥 *(Book 2)* 💣💣 💥 *иα* *♡нawwa м.υ {$mαѕhєr}.♡* *Wattpad&Instagram* *@Jeeddahmu898* *______________________* *fαcєвσσk grσup:*https://www.facebook.com/groups/369678263526212/ *_____________________* *LOYAL TO MY FAMILY.♥* بسم الله الرحمن الر حيم. ^^^^^^^^^^^^^^^^^ _My momma's *Hajiya Maryam (Oum Feedy n Hanan) & Maryam Naseer* ban san da wane irin baki ne ya kamata nayi muku godiya ba,hak'ik'a ku d'in na daban ne a gurina dama zuciya ta,a duniyar gizo² idan har mutum yayi dacen samun irin ku,lallai ne ya kamata a taya koma wane ne farin ciki,,addu'o'inku a koda yaushe suna sani jin farin ciki mara misaltuwa,a kullum ina k'ara godiya a gare ku sosai irin wacce baki bazai iya fad'a ba,hannu bazai iya rubutawa ba,haka nan irin wacce zuciya ba zata tab'a iya k'ayyadewa ba,a kullum ina k'ara yi muku fatan alkhairin Allah yaci gaba da kasancewa tare da ku+tsawon rai mai amfani da fatan Ubangiji ya raya zuri'ah..💝_ ___________________ *Masoya na a duk inda kuke a fad'in duniya bani da tamkar ku,addu'o'inku a kullum suna isowa gare ni,,ina yi muku fatan alkhairin Allah yaci gaba da wanzuwa cikin rayuwarku baki d'aya,,Lurv u with all my heart.💖* ___________________ *BOOK 2. 📓* *Pg 41.* ^^^^^^^^ *#Wonders* Shiru parlor'n ya sake d'auka lokacin da Inno tayi wannan furucin,kowa a zuciyarsa banda sak'a da kuma gagarumin daka had'e da fargaba a wannan lokacin babu abunda take yi,saboda yadda duka wannan ranar ta yau ta zo musu da wasu irin sauyi aikin al'amuran da suka shafi gidan,nd a gefe guda kuma tana sake bankad'a musu wasu big secrecy da duk all these while babu wanda ya iya tunani ko fahimtar wani abu musamman akan al'amuran da suka shafi gidan kuma suke kawo musu nak'asu,,,Yarima daya fisu dakewa ne ya nisa sannan ya amsawa Inno maganar ta coz sauran kam they were feels like jikinsu was knotted da irin metal chain d'innan,shi yasa magana ma yake gagaransu "Godiya nake ranka ya dad'e,,Allah yaja da nisan kwana.." Murmushi ya mata dan shi kam akwai abubuwa da dama a zuciyarsa da yake ji game da furucin da aka yi na kasantuwar Aisha a matsayin wata b'angare nasu,cikin nutsuwa Inno ta sake numfasawa sannan ta fara magana cikin wani yanayin dake bayyana abunda zata fad'a yana da matuk'ar muhimmanci sannan babu alamun wasa ko k'arya a cikinsa "Kamar yadda Hajiya Suwaiba ta fad'a a yanzun bada jimawa ba cewa jaririyar da aka d'auka a wannan gidan a wannan daren ita ce Aisha dake zaune a gaban mu,,tofa ina sake neman afuwar ku duka bisa sanar da ku wannan babban sirrin da zanyi dan kuwa Aisha ko kad'an bata da wata alak'a da wannan ahalin,,,sannan ina da yak'inin sake sanar da ku cewa ba ita ce jaririyar da Ummi ta haifa ba..Hak'ik'a Aisha y'ata ce dana haifa a wannan lokacin...!" Gaba d'ayansu zuciyoyinsu lokaci guda suka saboda jin furucin Inno a gare su dai² yake da tashin thunderstorm,sannan ga wani irin kallon da kowa ke binta da shi na rashin fahimtar inda zancenta ke son kaisu,,irin kallon da duka suke mata yasa ta ci gaba da magana kamar yada ta fara "K'warai kuwa na tabbatar da abunda na fad'a gaskiya ne kuma haka yake,,matuk'ar ace kowa zai kalli fuskar Aisha na tabbatar zai bambance ainihin da waye take kama a tsakaninmu nan da muke zaune.." Tayi nuni da kanta da kuma su Ladidi,kamar had'in baki duka suka yi yuuu da idanunsu akan Aisha'n,burin kowanne daga cikinsu duka a lokacin bai wuce su gano abunda Inno ke nufin su nemo akan fuskar nata ba,,with lots of astonishment suke kallonta suke kuma kallon b'angarorin biyu,ma'ana Inno da kuma su Ladidi,tabbas sai yanzun suka fara fahimtar wani abu game da AL'AMARIN dan yadda a yanzun da suka samu mai haska musu wani abu game da cases d'in dake kan faruwar,nan take sai suka fara hangen kamanin Inno a tare da ita,yayin da a wani gefen kuma suke sake hangen yadda take d'an fizgan kama dasu Adda,buh duka dai har lokacin suna cikin duhuwa babu yadda za'ayi su iya bambance ainihin gaskiya hakama abunda Inno ke son su gane d'in,amma dai tabbas duk wanda ya kalleta zai iya gano d'an kamanninta da Inno,,tambayan farko da kowa cikinsu ya fara bijiro masa shi ne ya akayi duk tsayin wannan lokacin babu wanda ya tab'a mata irin wannan kallon da har zai gano ainihin itan y'ar wane ahalin ne,nd ya akayi duka kowa ya kasa ganewa cewa itan ba jinin su Adda bane..?? Ko kuwa dan ta taso a hannunsu ne da labarin da suka bayar na kasancewar ta y'a a gurin Ladidi ya rud'e su duka shi yasa duk suka kasa fahimtar hakan..?? To amma idan har Aisha itace y'ar Inno'n kamar kuma yadda ta fad'a shin JEEDDAH kuma fa a ina ta samota..? Ko kuwa itama ta zama d'aya daga cikin masu safarar jarirai ne..?? Shin rashin y'arta ne yasa ta samo Jeeddan ko kuwa yaya abun yake..?? Duka wannan tarin tambayoyin sune suka addabi zuk'atansu har kowannensu yake kwad'ayin inama ace shi ne zai fara samun amsa,,shirun duka da suka yi suna masu sauraron Inno da tunanin irin wannan surprise da suke ta karb'a daga gurin mutane daban² a wannan wayewar garin yasa har mutum bazai iya bambance wanda yafi wani shiga rud'ani ba a tsakaninsu,,to amma idan har hakan ya faru a yanzun shin wane sabon surprise ne zasu kuma samu anan gaba.?? (Ni dai nace suyi hak'uri za suji koma wane ne bada jimawa ba) Kunnuwansu suka sake bazawa suna masu sauraron jin cewarta dan kowa a takure yake yaji bayani na gaba "Na tabbata duk za kuyi mamakin jin na fad'i haka,amma iya gaskiyan da nayi nufin fad'a shi ne na fara fad'a,in sha Allah kuma yanzun bada b'ata lokaci ba zan baku tak'aitaccen labarin yadda akayi wannan *AL'AMARIN* mai cike da rud'ani ya faru..." Sai data jera ajiyar numfashi kanta a k'asa kafin ta fara magana "Kamar yadda kuka sani a wani lokacin can baya,,a kuma lokacin daya kasance Ummi take goyon ciki,,haka nima a wannan lokacin na kasance ina d'auke da nawa juna biyun,wanda dukan mu a wannan lokacin kusan tare muke komai da Ummi,hatta da awon ciki a lokacin da duk wani abu daya shafi lafiyar mai juna biyu da abun dake cikinta ya zamana likitan gidan nan ya kasance yana kula damu,haka nan idan har zai zo dubata nima baya tafiya har saiya tabbatar da lafiyata da kuma nawa cikin a bisa umarnin Fulani,,saboda haka hatta da watannin cikinmu duka d'aya ne dan haka ya zama tare duk muke goyon cikin,,duk da a wannan lokacin Fulani ta kan hanani yin duk wasu ayyukan da suka jib'inci zasu bani wahala tunda taga cikin ya d'auko hanyar tsufa,bayan nan kuma a yadda taso shi ne ta so ace kamar yadda ta bani damar zama a gida na huta har zuwa bayan na haihu sannan na dawo bakin aiki na sai ni kuma nak'i amincewa da hakan naci gaba da aikina kamar babu wani larura a tare da ni duk da dai ba hakan taso ba sai dai ganin na dage yasa ta rabu dani,,kwatsam lokacin da cikinmu ya shiga watan haihuwa a wata rana daya kasance cikin irin ranakun da nakan yi dare a cikin gidan nan,ina cikin tafiya a hanyana ta fita daga gidan bisa rashin sanin abunda ke faruwa sai na ratse hanya da nufin zuwa b'angaren Ummi,haka nan a wannan lokacin duk da ba sosai nake zuwa ba sai idan wani abu ya kama ko likitan dake dubamu ya zo,,amma ranar sai naji ina son zuwa na yi mata sallama,to a wannan lokacin ne bayan na bar apartment

Chapter 57 of 63