za mu yi barazana da court order. Wannan cyberbullying ne...."
Bayan sun gama tattaunawar su, daga baya Amal ta sanar cewa zata yi jawabi a tashar su na rayuwa FM..
An shirya zama, Amal na zaune a cikin studio ɗin gidan rediyo. tana fuskantar cemara ba tare da ado ko yanayin farin ciki ba, tana zaune cikin hijabinta, murya cike da natsuwa take faɗin:
“Akwai wani abu da na koya a rayuwa, gaskiya bata buƙatar ihu. Kuma wanda ke da komai a zuciyarsa ba ya jin tsoron ƙarya da aka ɗinka masa daga waje.
Na ga hoton da aka watsa kuma na san me ke ciki. Hoto da aka ɗauka shekaru biyu da suka wuce lokacin da nake hira da wani baƙo a studio. Wani da yake son wulakanta ni ta hanyar shirya ƙarya, sai ya fassara abin da bai fahimta ba.
Ina da iyayen da suka koyar da ni tsoron Allah. Ina da Kakar da ta raineni da hawaye da addu’a. Kuma ba zan yarda a gina sunana a kan ƙarya da hasashe ba.
Amma wannan abu ya koya min abu guda cewa, akwai mata da yawa da ake mana haka kullum ana ƙulla mana sharri saboda kawai muna da tsayin daka da nutsuwa.
Don haka wannan bai shafeni ni kaɗai ba, Ya shafi kowace mace da ta gina kanta akan gaskiya kuma ake neman cin zarafin ta saboda dai ta ƙi lankwasuwa.
Ina tare da ku. Kuma zan ci gaba da wakiltar ku cikin gaskiya da ɗaukaka....”
Dakata wa tayi tare da sakin murmushi kaɗan, ta ƙara da faɗin:
“Ba wai ni ce jaruma ba ku ne jarumai da kuke tsaye akaina. Na gode.”
Ƙarshen tattaunawa...
A kafafen sada zumunta
TikTok, Instagram, da Twitter sun ɗauki bidiyon yana yawo kamar wutar daji.
Mutane da dama sun fara reposting da kalmomin: #DignityNotDrama #AmalStandsTall #VoiceOfDignity
Wani sanannen ɗan jarida ya rubuta cewa:
“Wannan ba kawai magana bace, wannan darasi ne. Amal ta koya mana cewa mace mai gaskiya ba buƙatar shela.”
Wata likita a Abuja ta rubuta cewa:
“Ni ban san Amal da farko ba, sai yanzu ganin farko naji ta burge ni, zan so ƴaƴana su girma su zama kamar Amal.”...
A wani sashen, Maleekh na kallon bidiyon Amal daga wayarsa, yana a zaune a cikin motarsa mai sanyi da leather seat. Ya dafe kansa, yana juyayi...
a hankali ya furta:
"Ta fi kowa. Wannan ba ƴar talaka ce kawai ba... wannan wata Queen ce.
amma hakan ba yana nufin na goyi bayan ta bane...."
Wani babban kamfani da ke da alaƙa da gwamnatin jihar, suna da hannun jari a gidan rediyon Amal ke aiki. Sun ƙira taro a sirrance.
CEO ɗan manyan mutane, mai suna Alhaji Ma’aruf yana faɗin:
“Wannan yarinya tana yawan fitowa da ra’ayoyi masu motsa mutane. Muna son kwanciyar hankali. Idan mutane suna sauraren Amal, ba za su saurari shugabanni irin mu ba.”
Wani daga cikin su ya ce:
“Za mu samar mata da wata hanyar da zata shigo cikinmu, mu rufe bakinta da kuɗi… ko kuma mu wanke ta gaba ɗaya daga kafar sadarwa.”...
Washegari, Amal ta karɓi gayyata zuwa wani taro.
A can ta iske babban mutum Alhaji Ma’aruf yana mata tayin aiki: albashi mai girma, gida, mota, kwangila. Amma da sharaɗi guda.....
Alhaji Ma’aruf cikin ƙwarewa yake faɗin:
“Kina da wayo, Amal. Muna son ki shigo mu gina Najeriya tare. Amma ki rage yawan fitar da abubuwan da ke ɗaga hankali. Duniya bata son masu sa mutane tunani sosai.”
Amal cikin kwanciyar hankali ta ce:
“Ina son ƙasata, kuma ina son gaskiya. Amma idan wannan tayin yana nufin in yi shiru akan abubuwan da ke damun mutane to ku ci gaba da neman wata mafita....”
Ta miƙe cikin natsuwa ta bar wurin, kowa yana kallonta cike da mamaki...
Bayan kwana biyu da faruwar haka..
Wasu saƙonni marasa suna sun fara shigowa wayarta:
“Kada ki ɗaga murya fiye da haka…”
“Ki zabi zaman lafiya, ko zaman lafiya ya ƙi ki.”
“Mun san inda tsohuwar da ta raine ki take.”
Inna jin labarin tashin hankalin da suke shirin shiga, sai kawai ta fashe da kuka...
Amal fashe wa tayi itama da kuka tana rarrashin Inna tare da faɗin:
"Inna in sha ALLAH babu abinda zai faru da mu, muna kan hanyar gaskiya, kuma Allah yana tare da mai gaskiya, ki kwantar da hankalin ki Inna...."
Itama Inna kuka take tana rawar murya ta ce:
"Amal ina tsoron wannan rayuwar da kike gudanar wa, ina tsoron rasaki Amal, in da hali ki bar aikin gaba ɗaya kizo mu zauna a gida..."
Amal ta ce:
"Kar ki damu Inna akwai lokaci..."
Da haka Amal ta rarrashi Inna har suka yi bacci...
★★★★★
Maleekh kuwa cike da jin haushin Amal yake kwana yake tashi, gaba ɗaya ya tsani yarinyar har cikin ransa, cike da damuwa yake faɗin "Ni zata tozarta a idon duniya? ballagazar yarinya ƴar talakawa..."
Cikin zafin rai ya nufi gaban mirror, nan ta ke ya fara farfasa mirror yana ihu, yana tarwatsa kayan ɗakin sa...
Jin ihu yasa mahaifiyarsa ta shigo da gudu tare da ƙannen sa mata, daƙer Uwar ta riƙe shi tana rarrashin sa domin tinda abun ya faru ya kasa kwantar da hankalinsa, ko ci da sha baya samu damar yi, kullum a cikin tunani yake, takaicin sa tinda yake babu macen da ta taɓa tozarta shi sai Amal da take talaka faƙiriyar yarinya....
Sai da iyayensa suka tura shi England kafin ya samu kwanciyar hankali, domin a Nigeria kullum zafin takaicin Amal hana shi sukuni yake, da ya koma wa can kuwa sai abubuwa suka fara fita masa a rai, ya rage damuwa amma ya kasa manta da Amal...
Dake a can akwai masu kula da shi sosai, basa barin sa yana shiga damuwa, da haka ya koma normal kamar bai je Nigeria ba, amma idon sa akan Amal yake a TV da laptop ɗin sa......
★★★★
Washegari bayan Amal ta kammala aikin ta na yau a gidan rediyo Rayuwa FM......
Amal ta fito daga gidan rediyo Rayuwa FM tana shirin tsallaka titi domin komawa gida, sai ga wata baƙar mota ƙatuwa tazo ta sha gabanta tare da jan yo ta ciki suka wuce da gudu ba tare da mutane sun an kara ba,
Wani tsararren gidan gomnati aka kaita wurin da Governoni da manyan ƴan siyasa suke taruwa,
Zaunar da Amal akayi a ƙasin carpet an rufe mata baki da fuska gam, a lokacin aka cire mata baƙar hular da suka rufe mata fuska da baki, idonta ne suka sauƙa akan wasu manyan ƴan siyasa wanda bata taɓa ganinsu ba sai a poster da kuma jin labarin su, yau ta gan su a zahiri,
Ga wasu manyan security a tsaye a gefe guda suna riƙe da bindigun su,
an tsawatar wa Amal sosai tare da barazanar zasu sa a kasheta idan ta cigaba da fito da gurɓatattun bayani akan su,. Suka zazzage ta tare da ƙiranta da ƴar talakawa, sunyi barazanar zasu kashe ta kuma su kashe Kakarta kuma babu hukumar da ta isa ta hukunta su domin sune suke riƙe da hukuma,
Amal ko kaɗan bata ji tsoron su ba ko fargaba haka ta tsaya tana musayar yawu da su, cikin jarumta.....
Wani dattijo mai tumbi wanda ta taɓa ganinsa a poster na zaɓe, ya buɗe baki cikin murya mai cike da izza ya ce:
"Kece Amal Abdulsamaad? Wannan baƙin ciki da kike yaɗawa a radio da social media zai ƙare yau. Mun gaji da sharrinki!"...
Wani ɗan siyasa ya ƙara da zazzafar murya cewa:
"Ƴar talakawa mai rainin hankali! Me kika sani game da mu har kike shisshigi cikin rayuwar mu? Mu muke riƙe da wannan ƙasa!"
Amal ta ɗago kai, tana kallon su ba tare da rawar murya ba, duk da hannunta a ɗaure yake. Muryarta cike da ƙwarin gwiwa ta ce:
"Na sani, ku da kuke cewa kuna riƙe da ƙasa, ƙwarai kun riƙe da zalunci. Amma Allah yana kallon ku. Ku ne kuka haddasa halin da talakawa ke ciki, kuna sace hakkin marasa galihu kuna fakewa da dokokin da kuka rubuta da kanku."
Wani daga cikinsu ya ce:
"Zamu kashe ki! Kuma ba wani hukuma da zai sani balle yayi bincike!"
Amal ta ce:
"Ku kashe ni, amma gaskiya ba zata mutu ba. Ina jin kunyar cewa ni marainiya ce kuma talaka wanda bani da halin taimaka wa talakawa, amma ni ba zan ji kunyar faɗin gaskiya ba. Ku ne matsalar ƙasar nan, kuma ku ne dalilin da yasa yaran da ke da basira kamar ni ke cikin wahala. Sai ku ke raina mu, kun hanamu ci gaba a rayuwa!"...
Wani babban jami’i ya matso da bindiga a gefe yana huci, yana kallon Amal cikin ƙyashi.
Amma Amal ta cigaba da magana cikin fushi da karyewar zuciya:
"Idan da gaske kuke kuna da iko, to me yasa kuke tsorata da murya ta? me yasa baku so na bayyanar da gaskiyar halin da mutane ke ciki? Wannan ƙasar ba mallakin ku bace. Ku ne kuke damun ta!"
Sauran 'yan siyasan ne suka fara kallon juna cike da mamakin ƙarfin gwiwar yarinyar. Ba yanda suka iya da ita haka suka bada umarni a ɗaure ta a ɗaki har sai sun yanke hukunci akan rayuwarta....
An nemi Amal an rasa, Inna ta shiga damuwa, gidan rediyo Rayuwa FM tayi sanyi jin labarin anyi kidnapped Amal...
A Rayuwa FM, ma’aikata sun ruɗe.
Sun katse shirye-shiryensu, suka bada sanarwar bacewar Amal. Jama’a sun fara magana a gari, an fara ƙirarin za'a yi zanga-zanga na rashin tsaron lafiyar marubuta da 'yan jarida masu gaskiya.
A gefe guda... Inna tana kuka a gida, tana addu’ar Allah ya fitar mata da Amal....
"Ya Allah ka dawo mun da jikata lafiya... Amal, ki dawo gida mana."
A nesa, cikin ɗaki a ƙasar england, Maleekh ya zuba coffee a cikin cup, yana sanye da singlet da 3quarter.
Ya kunna laptop, yana kallon rahoton da ke cewa Amal ta ɓace. Sai ya saki wata ƙaramar dariya mai cike da izza yana faɗin:
"that's good! Nasan wannan lokacin zai zo, yarinya marar kamun kai, zaki gane da ruwa ake shayi a hannun manyan mutanen Nigeria....
Ya yi wasu maganganu da rashin damuwa akan abinda ya faru da Amal,
Sannan ya furta:
"Let her learn the hard way, This is Nigeria, ba wani yanki bane inda 'yan talakawa ke zagin manya su tsira lafiya."
★★★★★★
A cikin ɗakin da aka ɗaure Amal...
Tana zaune a ƙasa, an ɗaure hannayenta da ƙafafunta, amma zuciyarta bata ɗaure ba. Kamar mai jin ƙarfin wata iska daga sama, ta ɗago kai tana sauƙe ajiyar zuciya. A hankali ta fara karanta addu’o’i da ayoyi cikin ranta, ba ta yi kuka ba sannan ba ta girgiza ba, amma jikin ta yana bada wani sanyi da tsantsar jarumta. ɗaya daga cikin jami’an tsaro ne ya matso da abinci ya ajiye a gabanta ba tare da ya kalle ta ba, ya since mata hannaye tana gamawa aka ƙara ɗaure ta ..
A lokaci guda a waje...
Wasu daga cikin ma’aikatan gidan gomnati suna ta waya da mutane daban-daban suna yunkurin ɓoye labarin bacewar Amal. Amma a waje, duniya ta fara motsawa.
Rayuwa FM sun fitar da sanarwa cewa:
"Mun rasa ɗaya daga cikin ƙwararrun ma’aikatan mu, Amal Abdulsamaad, bayan fitowarta daga ofis jiya da yamma. Muna ƙira ga hukumomi da jama’a da su taimaka wajen gano inda take..."
Social Media ta karaɗe da hoton Amal da rubuce-rubucen:
#FreeAmalNow
#JusticeForAmal
#TruthIsNotACrime
Gaba ɗaya gari ya ɗau zafi.
Ƴan jarida da kungiyoyin kare hakkin ɗan adam sun fara yawo da labarin. Wasu fitattun mutane suna wallafa goyon baya gareta, wasu suna cewa: “Kalmar gaskiya duk wanda ke faɗin ta sai an ɗauke shi”, hakan ya jefa tsoro cikin zukatan wasu, amma ya ƙara juriya cikin zukatan wasu da dama.
A wani ɓangare kuma...
Maleekh yana zaune yana kallon wannan hayaniya a tv. Cikin zuciyarsa yana fargaba amma a fili sakin murmushi ya yi,
Ya ƙira Rikky Blaze ta video call yana faɗin
"Rikky, ina so ka kawar da wancan yarinyar daga labarai... ba damuwata me za ka yi ba, amma dole muryarta ta ɓace!"
Rikky ya ce:
"She’s already disappeared, boss. The problem is people won’t shut up."
Maleekh ya ce:
"Then shut them up. Everyone has a price....
Bari ta gama shan wahala, zata gane rayuwa ba wasan yara ba ne. A Najeriya take ƙasar da ‘yan ƙasa irin ta ba su da wata kima idan sun raina manya. Wacce 'yar talaka ce za ta fito tana zagin giwa ta kuma yi tsammanin zata tsira? Ai sai ta ɗanɗani azaba, ta gane cewa hauka da raini na da farashi mai tsanani!"
Rikky ya ce:
"Ogah! Yarinyar tana da taurin kai ne, sannan tana da jarumta dubi yanda ta tozarta sunan ka a ƙasar...."
Maleekh cike da mugunta yake faɗin:
"Zata sha wahala ne, zan koya mata darasin da zai ɗaure mata kwakwalwa har abada. zan nuna mata cewa ƙasata ba kasar tatsuniya bace, Najeriya ne! Inda ‘yan talaka ba su da murya idan sun taka layin manya. Wacce ce ita? Wacce 'yar raini ce da za ta fito tana zagin giwa a gaban jama'a? Ai sai ta ɗanɗani wahala, ta gane cewa a Najeriya, rainin hankali yana da farashi. Kuma wallahi, zan tabbatar an biya wannan farashin sau biyu!...."
Yana huci ya kuma cewa: "ƴar matsiyata jikan talauci, ban da talakawa wa zai tsaya ɓata lokacin sa wurin sauraron ta...."
Rikky ganin yanda ran Maleekh ya yi matuƙar ɓaci yasa shi cewa:
"Sorry Ogah...."
Maleekh Yana magana idonsa na haskawa da ƙiyayyar Amal yana faɗin:
"A gaban duniya za ta fallasa ni? Ni Maleekh?! Wacce ce ita? Wace ‘yar tasha ce zata tsaya a gabana ta ce wai zata yi magana akan gaskiya? Gaskiya? A ƙasar da kowa ke sayar da gaskiya don ceton kansa?"
Zama ya yi daga tsayen da yake ya miƙar da ƙafa tare da durƙar da kansa akan table ɗin gaban sa yana magana yana ƙwanƙwasa teburin da yatsarsa:
"Zan koya mata darasi ta hanya mai tsanani. Zan nuna mata cewa Nima ɗan Najeriya ne, Ba a waje nake ba da ‘yan talakawa ke wulakanta manya su tsira. Wallahi sai ta gane cewa rainin hankali a kasar nan yana da tsada, kuma zan tabbatar ta biya da wahala."
"Ka yi mata fiye da haka,"
Rikky ya ce shima cikin ɓacin rai.
Sannan ya ci gaba da cewa
"Za mu nuna mata yadda ake wasa da wuta a ƙasar da ba ruwan kowa da gaskiya."
Maleekh ya lanƙwasar da kansa, cikin sassanyar murya ya ce:
"Lokacin dariyarta ya ƙare. Yanzu lokaci ne na hawaye. Kuma zan tabbatar hawaye ya maye gurbin karfin halinta."
Daga nan ya kashe wayar, yana kallon fuskar Amal daga wani video da aka ɗora a online yana jin wani abu mai nauyi a zuciyarsa, wanda ya kasa fassara shi, ya ce:
"Me ya sa tunaninta baya barin kaina, duk da irin ƙiyayyar da nake mata?"
---★★★
A cikin ɗakin Amal...
Ƙofar ɗakin aka buɗe da ƙarfi.
An kawo wani babban ɗan siyasa wanda shine shugaban hukumar ɗaya daga cikin manyan bangarorin gwamnati. Ya zauna gaban Amal yana kallonta tamkar ba mutum ba:
Shugaban Hukuma ya ce:
"Idan kin yarda zaki zauna lafiya to ki daina magana, zamu baki gidan zama, mota, da naira miliyan ɗari. Amma sai kin yi alkawarin komai ya ƙare."
Amal ta ɗago kai cikin ƙarfin zuciya tana murmushi ta ce:
"Ba zan siyar da gaskiyata da farashi ba. Ko zaku bani duniya gaba ɗaya, idan talaka yana kuka saboda zaluncin ku, zan cigaba da magana... In har na mutu a haka, Allah zai karɓi hakkin talakawa da bakin da suka nema masa."
Wani security ne ya shaƙeta da hannu yana zazzaro mata ido amma shugaban ya dakatar da shi yana kallon Amal da tsantsar mamaki da takaici ya ce:
"Bata tsoron mutuwa....
Haƙura ya yi, shima ya bata wuri...
A gida...
Inna ta kwanta rashin lafiya. Mutane sun zo suna ɗaukar nauyin kulawa da ita. Tana ta kuka tana faɗin:
"Allah ka dawo mun da
Jikata lafiya... Amal zata iya shiru amma ba zata iya cin zalunci ba..."
Zuwa yanzu...
Gwamnati tana cikin tashin hankali. 'Yan jarida daga kasashen waje sun fara bibiyar batun. Tura ta kai bango. Haka nan mutane sun fara tashi da zanga-zanga a Abuja da Kaduna, suna ɗauke da hoton Amal tare da tambari:
“TA BA Da ƘARFI GA MURYAR MARASA ƘARFI!”....
Wata mace ce ta shigo cikin ɗakin da Amal take,
Tana sanye da kayan masu aiki, ta zauna kusa da Amal cikin sautin muryar da ba kowa ke iya ji ba.
Matar ta ce:
"Sun ce in kawo miki abinci… Amma na zo da saƙo daga waje. An fara neman ki. Duniya na magana. Ki ƙara juriya, zan dawo da labari."
Amal ta zuba mata ido da hawaye a idonta ba tare da ta iya cewa komai ba. Matar ta latsa mata hannu a asirce, ta miƙa mata ɗan karamin zare alamun cewa ba ita kaɗai bace a cikin gidan da ke goyon bayanta.
A GIDAN GWAMNATI...
Wasu daga cikin shugabannin gwamnati sun fara yin shakkar tsare Amal. Labarai sun bazu zuwa kasashen waje. Ana barazanar dakatar da haɗin gwiwa da gwamnati idan ba a fito da bayanin da ya shafi Amal ba.
Ministan Cikin Gida ya fuskanci matsin lamba.
Ya ƙira taro na manyan jami'an tsaro da 'yan siyasa da su ka tsare Amal.
Cewa:
"Duk abinda za ku yi, ku yi shi da wayo. Idan aka samu gawarta a matsayin evidence, mu ne za mu durƙusa. Kiyasta illar hakan..."
A RAYUWA FM...
An gudanar da wani gagarumin shiri na musamman da aka ƙira "AMAL, MURYAR GASKIYA".
A cikin shirin, an sake kunna sautin wasu daga cikin tattaunawarta da talakawa da labarinta na masoya biyu da aka kashe wanda ya taɓa zuciyar mutane a baya.
A ƙarshe anchor ya furta:
"Idan har gaskiya ce laifi, to duk mai gaskiya zai ɓace kamar Amal... Amma Amal ba zata ɓace ba. Rayuwarta ta riga ta zama muryar al'umma!"
A CIKIN ƊAKIN MALEEKH, ENGLAND...
Yana zaune cikin duhu, kofin coffee yana hannunsa, yana kallon projectorin da ke nuna masa tashar Rayuwa FM da yadda mutane ke zanga-zanga a ƙofar gidan rediyon da hoton Amal a saman banner.
Ya yi murmushi cikin rashin jin daɗi, yana ƙara karanta wani email da Rikky Blaze da ya turo masa:
Rikky yana cewa:
"Sir, we may need to drop the girl soon... The pressure is building. She may die, but her voice won’t..."
Maleekh ya runtse idanu yana faɗin:
"Damn it, Rikky... why is this girl messing with my world?"
Ya jefa glass cup na coffeen a bango yana buga ƙafa cikin fushi.
Daga nan ya ɗauki waya ya ƙira wata lamba yana faɗin:
"Release her. But make sure she learns something first... Let her walk out, but her heart will broken."
TO PAH TASHIN HANKALI, ASHE DAI ƁATAN AMAL DA SA HANNUN MALEEKH🤔🤔
A CIKIN GIDAN GOMNATI...CIKIN DARE!
Amal tana zaune a cikin duhun ɗaki. Aka buɗe ƙofa, wasu mutane biyu masu baƙaƙen kaya sun shigo. Ba tare da an yi mata komai ba, suka kwance ta, suka cire mata ɗaurin baki.
Mutum na biyu ya ce:
"Zaki koma gida. Amma ki sani... wannan ba ƙarshe ba ne. Wannan faɗa ce tsakanin ƙarfi da ƙasa. Ki nutsu, Amal..."
Suka sa mata fuskar rufe ido (eye mask), suka fitar da ita daga gidan.
Sai da suka yi tafiya mai nisa sosai a mota kafin suka fitar da ita a cikin duhu suka cilla ta cikin wata mota, suka bar ta kusa da wani titi mai duhu inda wasu masu mota suka same ta da safe....
LABARI YA KARAƊE KO INA...
An same ta a rana mai ɗumi, da 'yan sanda da ma'aikatan Rayuwa FM suka kai ta asibiti. Ta zauna jinya tsawon makonni biyu sakamakon fesa mata tiyagas da akayi..
Inna ta yi kuka sosai tana rungume da ita, tana faɗin:
"Amal... na riga na sani, ke ba za ki yi rayuwa kamar sauran mata ba... Amma Allah yana tare da mai gaskiya!"
Bayan wasu kwanaki,
A gaban tagar asibitin da rana ke haskawa, Amal na zaune a kan kujera sanye da farin hijabi da doguwar rigar marar ado. Kamar wacce ba ta da ƙarfi, amma idan ka duba cikin idanunta zaka ga karfi da sabuwar fahimta.
Inna tana gefenta, tana riƙe da hannunta, tana faɗin:
"Na ce miki ki bar harkar siyasa, amma na fahimci ba ke ki ke zaɓar wannan hanyar ba, kamar dai mutanen ki ne ke zaɓar miki wannan hanyar ta fuskar tausayi...."
Amal ta juyo, da hawaye a idanu cikin murmushi ta ce:
“Inna, da ace ba ni aka yi wa wannan ba, wata rana wata ce za ta fuskance shi. Amma yanzu da na riga na faɗa ciki wallahi zan kare kaina, da sauran masu rauni da ba su da murya.”
Inna cikin kalar tausayi ta rungume ta tare da faɗin:
"Allah ya cigaba da tsare mu gaba ɗaya..."
★★★
Kwana biyu bayan fitarta daga asibiti, Amal ta koma Rayuwa FM.
Kowane ma’aikaci ya rungume ta cikin tausayawa suna jajanta mata, Sun ajiye mata wani guri na musamman a matsayin “Mai Tsaron Gaskiya”.
A shirin ta na farko bayan dawowarta, ta fara da ƙasa da murya, tana kallon microphone kamar tana kallon duniya:
Ta ce:
“Na rayu a inda yawancin mutane ke barin ran su. Suka ce zan mutu, amma Allah ya raya ni. Na dawo da murya ta, ba don jin daɗi ba sai don kare gaskiya.”
Jama’a a gari sun fara yi mata kallon girmamawa fiye da da. Tashar Rayuwa FM ta karɓi goyon baya daga ƙungiyoyi na duniya da kafafen watsa labarai na kasashen waje.
Maleekh: Tashin Ƙiyayya da Shirinsa na Dawo Nigeria
A cikin ofishin Cash Empire da ke England, Maleekh na tsaye gaban mirror. Yana kallon kansa da gilashi a idanu, yana sanya necktie. A gefensa Rikky Blaze ya tsaya da wani file mai taken: “Project: CashTalk FM Abuja Launch.”
Rikky ya ce:
"Kafafen yaɗa labarai sun fara canza salo, Rayuwa FM da Amal sun fara samun ƙarfi da motsin da ba kowa zai iya dakatar da su ba."...
Maleekh ya juyo cikin fushi. Idonsa ya yi jajur.
Ya ce:
"Don dakatar da murya, ba sai ka rufe ta ba. Kana nutsar da ita ne da hayaniya mafi ƙarfi. Mu yanzu muna ƙirƙirar murya da ta fi tata ƙarfi...."
Ya kama jacket dinsa, ya fesa turare mai ƙamshi da tsada yana faɗin:
“CashTalk FM za ta zama gidan ‘yan Nigeria masu iko. Ba gidan gajiyayyu ba. Ba wurin kuka da hauka ba .....gida ne na gidan makamai da babbar murya. I’ll give them the opposite of Amal.”
★★★★★
Maleekh ya iso Nigeria da ƙungiyar sa a boye. A wani sirrin fili kusa da Maitama, an fara ginin CashTalk FM. Tashar da ke da fasahar zamani fiye da Rayuwa FM.
Ya sanya mutane su fara neman sabbin masu gabatarwa amma duk wani tallace-tallace yana da manufa guda: Yi wa Amal ƙasa a gwiwa da jawo hankalin matasa daga gareta.
Maleekh yana so ya yi ganawar sirri da Amal...
Yana maganar zuci a yayin da yake zaman kaɗaici shi kaɗai domin a yanzu ya zaɓi ya yi maganar sirrin sa da zuciyar sa a kan ya sanar wa wani, domin ya koyi darasi a gun abokinsa Nasir....
"Ba sai na kashe ta ba. Zan goge ta a hankali… da suna, iko, da tasiri. Kafin ta gane me ke faruwa, zata dawo ita kaɗai babu kowa a gefenta.."
🔊 GIDAN REDIYO RAYUWA FM. ZUWAN MALEEKH CASHBANK A KADUNA
Washegari da safe
Amal na zaune a ofishinta mai tsabta da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 62