Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_. "Jajirtattu mu ne ƙarfi a zuciya, hikima a magana, jajircewa a aiki. Ba mu ja da baya, ba mu faɗuwa. Mu ne tarihi da ake ginawa!" 💪🔥✨ BOOK ONE page 27 to 28 🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹🌹🌹🌹 🌹🌹🌹🌹 🌹🌹🌹 🌹🌹 🌹 Ammy tana so ta tambayi ina Farha take zata zo sai kawai taji wayar ta katse. Ta sake ƙira, ta sake ƙira, amma babu wanda ya ɗauka… duk ƙiraye-ƙirayenta suka ci tura. Misalin ƙarfe biyu na dare Farha ta fara motsawa a hankali daga suman da ta tafi. Idonta ya fara motsawa cikin rauni, numfashinta na fita sama-sama.. Kowa a gidan ya kasa bacci. Amal ta kasa runtsa ido, kuka kawai take yi tana durƙushe a gaban Farha da ke shimfiɗe a ƙasan carpet. Inna kuwa ta zauna gefe cike da fargaba, zuciyarta na bugawa da sauri, haka ma masu aikin gidan suna ta kai komo, kowa hankalinsa a tashe. A dai-dai lokacin, suka ji jiniyar motoci na tsaya wa a bakin get ɗin gidan. Saƙon firgici ya ratsar da Amal, ta zabura ta ɗago tana kallon Inna da ido zuru-zuru, muryarta na rawa ta ce: "Innaaa… taya ƴan sanda suka sani?..." Inna ma jikinta ya ɗauki rawa, ciki ya tsure, ta kasa bawa Amal amsa. A bakin get kuwa, ƴan sanda ne tare da Ammy suka iso, domin Ammy ta samu damar gano inda Farha take ta hanyar tracking ɗin wayarta. Ƴan sandan suka fara knocking da ƙarfi, ƙarar ƙwanƙwasa get ɗin ya razana mai gadi wanda ya taso a tsorace. Cikin zuciyarsa yana tunanin ko ƴan fashi ne suka iso a wannan daren. Sai dai kafin ya yi wani yunƙuri, ƴan sandan suka tsawatar masa da ƙarfi, suka nuna masa hasken torchlight ɗinsu tare da rera sunansa. A firgice ya buɗe musu get ɗin. Kai tsaye cikin gidan suka nufa da sauri. Ammy kuwa bata ma san gidan waye bane, kawai dai ta bi ƴan sandan da zuciya cike da tashin hankali. Sai suka kutsa cikin falon gidan ba tare da bata lokaci ba… Ƴan sandan da suka shigo falon sun tsaya cak ganin wata yarinya a kwance a ƙasan carpet, fuska kumbure, jiki a sake. Amal na kuka tana jijjiga ta. Inna kuma na tsaye gefe jikinta na rawa. Masu aikin gidan suma suna gefe da rawar jiki, kamar wanda aka kama da laifi. Ammy ce ta fara zabura, ta nufi wurin da Farha take kwance tana ihu tana ƙiran sunanta: “Farha! Farhataaa! Kece nan?! Me aka miki haka?!” Ta durƙusa tana jijjigata, idonta cike da hawaye. Ganin Farha ba ta motsi sosai sai ƙaramin numfashi kawai take yi yasa zuciyarta ta ji wani irin sanyi mai sosa rai. Ƴan sanda suka matsa, suka rarrabe su Amal da Inna da masu aikin. Ɗaya daga cikin su ya kalli Amal cikin tsattsauran ido yace: “Ke ce kika yi wannan laifin?” Amal ta ɗora hannaye a kai tana kuka tana girgiza kai: “Wallahi ba ni na kashe ta ba… ni ma ban san ta faɗi haka ba. Na shiga uku, Allah ya sani ban yi niyyar kashe ta ba…” Inna da sauri ta durƙusa tana roƙon ƴan sandan: “Don Allah kuyi hak’uri, ku barta, komai ne ya faru dai matsala ce ta afku, kar ku ɗauki ƴar matashiyar yarinya ku jefa ta cikin kurkuku…” Ammy ce ta miƙe tsaye cike da haushi, fuska a ɗaure, tana kallon Amal ta wutsiryar ido tana huci tace: “Wallahi ba zan lamunta ba. Wannan matsiyaciyar yarinya ba zata kashe min ɗiya ba ta ce zata tsira. Sai dai ku kama ta, ku tafi da ita yanzu! Ni da kaina zan tabbatar ta ɗanɗani ɗaci irin wanda ta jefa ni a yanzu.” Ƴan sandan suka yi wa Amal dirar mikiya, suka kama hannunta da ƙarfi. Amal ta fashe da kuka mai ban tausayi, tana faɗin: “Don Allah ku yi hak’uri, ban kashe ta ba. Ku tambayi Allah! Ku tambayi zuciyar ku. Na shiga uku, ni Amal, babu kokai a wannan rayuwar sai sharri?!” Ammy ta ƙara tunkarar ta da magana marar daɗi, tana harara tana faɗin: “Ke matsiyaciya! Kina tunanin Maleekh zai aureki? To idan mafarki kike ki tashi kiyi sadaka, domin bazan taɓa aurawa yarona tsiya ba....kina burin zama matarsa ko? Sai dai ki lalace a kurkuku wallahi...” Ƙirjinta ya buga, zuciyarta ta narke da baƙin ciki. Amma saboda tsoron abin da zai biyo baya, Amal tayi shiru da sauran ƴan gidan. Jigum-jigum suke kallon yadda ƴan sandan ke jan Amal kamar wata barauniya. Hankalin Amal ya ƙara tashi ganin suna shirin ficewa da ita. Ta zube a ƙasa tana roƙo cikin kuka: “Don Allah kuyi hak’uri, ku kyaleni, ba ni na kashe ta ba… wallahi ba ni ba ce!” Sai dai Ammy ta ɗaga hannu ta tsawatar musu da cewa: “Ku ɗauke ta! Sai ta ɗanɗani ɗakin kurkuku, sai ta gane shiga rayuwarmu ba abu ne mai sauƙi ba...” Ƴan sandan suka ja Amal suka nufi ƙofar fita da ita, kukan Amal yana cika ko'ina, idonta cike da hawaye, zuciyarta cike da tsoro da baƙin cikin zargi… Inna zama tayi tare da fashewa da kuka... Maleekh yana nan a ɗakinsa, yana zaune a gefen gado, idonsa jajur saboda kwanaki yaƙi bacci. Zuciyarsa cike da ɓacin rai da ruɗani, bai san meke faruwa ba a waje. Kamar kullum sai juyi yake yi a kan gado, yana tunanin yanda zai kuɓuta daga wannan kulle da Farha ta tsare shi. Bai ma san cewa a wannan daren rayuwar Amal za ta sauya ba. A can waje kuwa, ƴan sanda sun ja Amal kamar wata 6arauniya, kuka take tsaye tana roƙo amma babu mai sauraro. A cikin mota suka sata, suka kaita police station, suna isa suka jefa ta cikin cell mai ƙunci da wari, tare da wasu mata masu laifuffuka daban-daban. Hawaye ke zuba mata ba tare da tsayawa ba, zuciyarta na tsinke-tsinke da baƙin ciki. Amal ta kwana daren nan cikin kuka, cikin tsananin tsoro da fargaba. Bata taɓa tunanin rayuwa zata jefa ta irin haka ba. Tana zaune a tsugunne, hannayenta riƙe da ƙafafunta, idonta a rufe, zuciyarta cike da addu’a: “Ya Allah! Ka tsare ni daga sharri. Ka kawo gaskiya fili. Ka tabbatar da cewa ban taɓa kisan kai ba, Allah kai ka san ni marainiya ce. Kada ka bar ni a wulakance a duniya.” A gefe guda kuma, Farha wacce ta fara motsawa daga sumar da ta kwashe lokaci mai tsawo, sai ranta a ɗaure da ciwo da wani irin kasala. Numfashinta na fita a wahalce, idanunta a lumshe, jikinta kamar wanda ya sha miyagun ƙwayoyi. Ammy na tsaye a kanta tana kuka tana girgiza ta: “Farhata, ki buɗe idonki, ki dubeni. Don Allah kar ki barni, idan kika mutu me zance wa iyayenki?!” Sai da ta ji Farha ta motsa da ƙyar ta ɗaga hannu, ta sake faɗowa gefe kamar zata sake suma. Da gaggawa Ammy ta ƙira direba, ta ɗauke ta da hannunta ta saka ta cikin mota. “Hospital za mu nufa yanzu! Na rantse sai wannan yarinyar Amal ta biya kuɗin halin da Farha ta shiga,” ta faɗa tana kuka tana riƙe da hannun Farha... Motar ta nufo babban titi da gudu, yayin da zuciyar Ammy take huci da haushin Amal. Ita kuwa Farha sai sauƙe numfashi take yi kamar wacce take kan shan wahala mai tsanani. A haka suka nufi asibiti, yayinda Amal kuwa ta kwana cikin ƙunci a ɗakin kulle na ƴan sanda… Washegari gari na wayewa, ƙarar ƴan ƙiran sallah daga masallatai daban-daban ke ratsa kunnuwan mutane. Amma Amal ta buɗe idanu a cikin ɗakin kulle, babu wani hasken rana face ɗan ƙaramin wutar lantarki mai walƙiya a sama. Tana juyi a ƙasa, ƙasa mai sanyi ga duhu da wari, duk jikinta ya kankame saboda sanyi. Idonta ya kumbura saboda kuka, zuciyarta cike da tsoro da damuwa. Ƴan sanda biyu suka shigo suna mata ihu a kai. “Ke! Tashi ki fito..." Amal tayi tsitt kamar bada ita ake ba sai rawar sanyi take.. Ɗaya ne ya sake daka mata tsawa.. "Ki fito mana! Kin yi shiru kamar gawa.” Amal ta ɗago a tsorace, ta daidaita kanta. Aka ja ta zuwa ofishin DPO, inda aka fara yi mata tambayoyi cikin tsawa: “Wacece ke? Me kika yiwa Farha? Kin bada guba ta sha, sannan kin shaƙe ta, har ta faɗi. Shin kisan mai kike shirin yi ne?” Hawayen Amal suka zubo tana cewa: “Wallahi ban bata komai ba. Gaskiya nake faɗi, mun yi faɗa ne kawai saboda ta zo gidana ta ci mun mutunci. Ni ban san tasha wani abu ba. Don Allah kuyi adalci.” Ƴan sandan suka kalli juna suna dariyar rainin wayo: “Ke yarinya, kin yi laifi kin kawo kanki. Idan ba kin sami wanda zai tsaya miki ba, za ki cigaba da kwana a nan. Kuma idan aka tabbatar ta mutu, to lallai kin shiga uku.” Amal ta fashe da kuka, zuciyarta na karyewa... Sannan aka maida ta cikin cell.. A gefe guda kuma, Maleekh yana zaune a ɗakinsa a kulle, fuskar sa cike da gajiya. Yana zaune a bakin gado, hannunsa na tallafe da kansa, yana tunanin: “Me yasa Mom za ta ɗaure ni haka? Wani hali Amal ke ciki yanzu? Shin tana lafiya? Ko kuwa ta ɗauka na watsar da ita ne?” Ya ɗago yana kallon saman ceiling, zuciyarsa na wani irin bugawa da tashin hankali. Ya tuna da wayarsa da aka kwace masa... “Idan dai suna ƙiran wayata, to nasan zasu yi tunanin na gudu ko na guje su. Ya Allah! Ka fito da ni daga wannan halin.” Ya miƙe a tsorace, ya ɗauki kwalbar ruwa ya sha sannan ya nufi bathroom, ya ɗauroalwala. A cikin ɗakinsa ya tsaya ya tayar da sallah... Bayan ya idar da sallah. Idonsa ya rufe yana jin wani irin zafi a zuciya, zuciyarsa ta cika da tsanar Farha.. Maleekh yana zaune a daddumar sa, sai yaji budar ƙofar ɗakin sa, a zabure ya miƙe tare da nufan falonsa da gudu, Islam ya gani a tsaye da key a hannunta... Haka yayo kanta kamar zai rufe ta da duka.. Islam a tsorace ta ce "Yaya ka tsaya kaji.." Maleekh yana tambaya "waya rufe ni? Meyasa aka rufe ni har tsawon sati uku?.." Islam ta ce "Yaya Wallahi Aunty Farha ce ta kulle ka, sannan ta hana kowa zuwa yanda kake, ita take ɓoye da key ɗin ka sannan wayarka ma a hannunta yake....yanzu ma tin jiya da safe Aunty Farha ta fita bata dawo ba, har dare Ammy ta fita neman ta, nayi waya da Ammy da safen nan take sanar mun wai suna hospital, Farha bata cikin hayyacinta sakamakon shaƙar da Amal tayi mata a gidanta, yanzu haka Amal tana police station a kulle..." Maleekh jin haka hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ba, jin Amal tana police station, cikin fushi yake cewa "Tin da Farha tayi mun wannan danyen aiki sai na wulakantata, ko tana gadon asibiti sai naci mutuncinta, har tana da kwarin gwiwar rufe ni a ɗaki har tsawon kwanaki? Sannan meya kaita gidan Amal?..." Islam ta ce "wallahi ban sani ba Yaya, yanzu ma ɗakin ta naje na dubo yanda ta ɓoye key ɗin ɗakin ka, nazo na buɗe maka, kasan ina kaunarka Yayana..." Maleekh ya rungumi Islam yana jin daɗin yanda jininsu yazo ɗaya da ƙanwarsa Islam...Yana ji da ita sosai sa6anin Arfat marar kunya... Maleekh ko tsaya gyara kansa baiyi ba ya fita... Yana fita harabar gidan ya nufi wurin parker motoci, ya shiga motarsa sabuwar Mercedes-Benz CLE 450 4MATIC Coupé mai sheƙi, wanda ko a Abuja da Lagos ba a cika ganinsa ba. Duk da yana cikin tashin hankali bai tsaya gyara kansa ba, ko kallon gilashin motar. Zuciyarsa na tafasa kamar wuta, yana maimaita a zuciyarsa: “Amal a kulle? Kuma saboda wannan wautar da Farha tayi? Wallahi sai ta gane ni ba yaro bane.” Kai tsaye ya nufi gidan Amal, ba tare da tsayawa ko’ina ba. Yana tafe da gudu, yana jin kamar hanya ta yi masa kaɗan saboda tsananin fushinsa. Da isarsa gidan Amal, bai tsaya daƙile hayaniyar zuciyarsa ba, ya sauƙa daga motar da sauri, ya nufi ƙofar gidan... Knocking yake da ƙarfi, mai gadi yana tambaya amma Maleekh bai tsaya bashi amsa ba, ganin buga get ɗin yaƙi ƙarewa ne yasa Mai gadin buɗe wa, yana buɗe get Maleekh ya hankad'a shi tare da shige wa... A falo ya tarar da Inna zaune sai hawaye take tayi, Maleekh ne ya rarrashe ta tare da tambayarta "shin wani police station aka kaita?.." Inna cikin kuka tace "Ni ina zan sa ni..." Sai da ɗaya daga cikin masu aikin gidan ta shigo ta sanar masa.. Maleekh bai tsaya jiran komai ba ya miƙe tare da fice wa... A gefe guda kuwa, Amal tana cikin azabar duka a hannun wata ‘yar sanda mace. Ta na ƙoƙarin kare kanta da kuka da magiya, amma taurin zuciyar wacce ke dukan nata ya fi ƙarfin tausayawa. Kowane dukan sanda yana ratsar da ita yana kuma hura mata ƙarin zafi. Duk abin da suke nema daga gareta shi ne ta faɗi cewa wani abu ta ba Farha tasha domin ta mutu. Amal tana kuka cikin wahala tana cewa: “Wallahi ban ba ta komai ba! Na rantse da Allah, babu wani abu a hannuna. Don Allah ku yi adalci!” Amma babu wanda ya saurareta. Sai dai a lokacin, ƙarar motar Maleekh da ya tsaya a gaban police station ɗin ya jawo hankalin kowa, ciki har da wacce ke dukan Amal... Da ƙarfi Maleekh ya tura ƙofar police station ɗin ya shiga, zuciyarsa a hargitse, fuskarsa cike da bacin rai. Ƙarar takalminsa da ke ƙaraso wa da gudu-gudu ta sanya jami’an da ke tsaye kallon sa, wasu daga cikinsu ma suka ɗan ja da baya ganin irin hankoron da ya shigo da shi. Da sauri idanunsa suka sauƙa kan Amal da ke cell, jikinta ya kumbura, hancinta yana zubar da jini. Wata ‘yar sanda mace na tsaye da sanda a hannunta, alamar ba ta kammala dukanta ba.. A zabure Maleekh ya nufe ta yana huci kamar zaki, da sauri ya fisge sandar hannunta ya wurgar gefe, yana ɗaga muryarsa: “Ke wacce irin rashin imani kike yi ne? Wace ƙa’ida ce ta ce ku ci zarafin mace a hannunku? saboda Amal ce shiyasa kuka yi mata haka?” ‘Yar sandar ta ja da baya tana rawar jiki, amma kafin ta ce komai, Maleekh ya wuce wurin Amal. Ya zauna a gefenta, zuciyarsa na tsananta da tausayinta. Ya kamo hannunta cikin tausayi, idonsa cike da hawaye da fushi lokaci ɗaya: “Amal… me suka yi miki haka? duk saboda ni kika shiga wannan hali? Ki kalle ni, wallahi duk abinda ya same ki Farha ce ta jawo amma zanyi maganinta..!” Amal ta ɗago da ƙyar, muryarta a raunane, idanunta sun kumbura da hawaye ta ce “Maleekh… wallahi ban aikata komai ba… suna zargina da wani abu… amma na rantse da Allah ban ba Farha komai ba.” Maleekh ya ɗaga kansa ya kalli jami’an da ke tsaye da ƙarfi, muryarsa na girgiza ɗakin ya ce “Duk wanda ya sa hannu aka ci zarafin ta, sai na sa a bincike shi! Wallahi sai kun gane illar zubar da mutuncinta da ku ka yi...” Yayin da yake magana, manyan jami’an station ɗin suka fito daga ofis ɗin su saboda hayaniyar. Gani Maleekh yasa ɗaya daga cikinsu ya ce cikin ladabi: “Sir Maleekh, kayi haƙuri. Wata matsala ce ta biyo baya, amma za mu warware komai yanzu…” Maleekh ya miƙe tsaye, yana huci, ya dube su da idanun da suka cika da fushi: “Ba ku isa ku ci zarafin ta ba! Da izinin wa kuka yi haka? Amal zata fita tare da ni yanzu, kuma sai na san duk wanda ya bayar da umarnin a daketa.” Ya juya ya dubi Amal, ya kama hannunta da tausayi yana cewa: “Tashi mu tafi, Amal. Wannan wulakanci ba zai sake faruwa ba.” Duk jami’an suka shiga rikicewa, wasu suna ƙoƙarin kwantar da hayaniyar domin sun san halinsa idan yaga ba daidai ba zai iya sawa a cire su a aikin, duk station kowa ya san Maleekh ya shigo, kuma an karya masa zuciya saboda abinda aka yi wa Amal... Police station ɗin ya ɗauki shiru, sai kukan zuciya da Amal ke yi a raunane, tana zaune kamar marar ƙarfi. Dukkan jami’an da suka taru suna sunkuyar da kai suna ba da haƙuri. Wani babban officer ma ya matso da ladabi yana faɗin: “Sir Maleekh, wallahi ba mu yi haka da kanmu ba. Hajiyarku ce ta bayar da umarnin a hukuntata… mu dai umarnin ta muka bi…” Maleekh ya ɗaga hannunsa ya dakatar da shi, idonsa jajir cikin fushi, ya ce da ƙarfi: “Ba ni zaku bawa haƙuri ba! A Amal za ku bada haƙuri! Ita kuka wulaƙanta, ita kuka ci zarafi! Ku tsaya ku nemi afuwarta…” Nan da nan suka ƙarasa wurin Amal ɗaya bayan ɗaya, suna ƙoƙarin lallashinta cikin ladabi: “Ki yafe mana Hajiya, wallahi ba mu san ƙarya akayi miki ba…” “Ki yi haƙuri, hakan ba zai sake faruwa ba.” Amal kuwa hawaye kawai take zubarwa tana jin ɗacin abinda aka yi mata. Maleekh ya kalli jami’an, muryarsa ta sake yin nauyi: “Ku sani, daga yau, ba wanda ya isa ya ɗaga mata yatsa a gabana. Ita ce matar da zan aura, kuma duk wanda ya kuskura ya sake tabata… sai na nuna masa babu wanda ya isa ya tauye mata daraja a wannan ƙasa.” Kowa ya sunkuyar da kai.. Da haka Maleekh ya kamo hannun Amal, ya taimaka mata ta miƙe da ƙyar, sannan ya ja ta har zuwa motarsa. Ya buɗe mata ƙofa da kansa ya tabbatar ta shiga, sai ya zagaya ya shiga driver’s seat. Ya kunna motar, zuciyarsa na cike da fushi da tausayinta lokaci guda. Ba tare da ɓata lokaci ba ya nufi hospital domin a duba jikinta, ganin yanda bakinta da hancinta suka fashe suna ɗigar da jini... Bayan sun isa hospital ɗin, motar Maleekh ta tsaya da ƙarfi har sai da mai gadin wurin ya zabura. Ba tare da ya tsaya ɓata lokaci ba ya fito ya buɗe ƙofar Amal, ya ɗaga ta kamar karamar yarinya ya shigar da ita cikin babban reception na hospital ɗin. “Doctor! Doctor!!” Ya ƙwalla ƙira, muryarsa na ɗaukar hankalin kowa. Ma’aikatan asibitin kamar ba su damu ba, suna ta dube-dube suna tambayar “card” da “payment” kafin su shiga aiki. Wani doctor ya ƙaraso da nutsuwa, yana faɗin: “Sir, please calm down, mu a nan muna bin order ne, dole sai an rubuta file kafin—” “Ka tsaya nan!” Maleekh ya katse shi da ƙarfi, idonsa ya ɗan firgita shi. “Kana ganin wannan yarinyar a wannan hali, baka da hankali ne, kace za a fara rubuce-rubuce kafin a taimaka mata? Wane irin rashin imani ne wannan?!” Nurse ɗin dake gefe ta ce a hankali: “Sir, rules ne, dole mu cike bayanai kafin—” “Rules ɗin ku ku watsar dasu!” Maleekh ya ɗaga hannu yana nuna Amal da hannunsa yana jijjiga. “Idan wani abu ya same ta saboda sakarci da rashin gaggawar ku, wallahi sai na rufe muku wannan hospital ɗin gaba ɗaya! Kun san ni da kyau! Ba zan bari wani ya ƙara wulaƙanta ta ba!” Dukan reception ɗin ya shiga ruɗewa, nurses da doctors suka fara ƙoƙarin haɗawa da sauri. Wani likita ya fito daga Emergency room, ya ga tashin hankalin, nan take ya umarci su: “Quick! Take her inside, emergency ward now!” Suka karɓi Amal daga hannun Maleekh a hankali suka ɗora ta kan gurneti. Duk da haka, Maleekh ya ci gaba da bin su har cikin hallway, yana rera musu magana da ƙarfi: “Kada wani ya kuskura ya yi wasa da rayuwar Amal! Duk wani abu da take buƙata, ku kawo yanzu! Ku tuna, idan wani abu ya same ta… kai ne na farko zan hukunta!” Doctors suka shiga yin gaggawa fiye da yadda suka saba, saboda kowa ya san irin tasirin Maleekh a ƙasar, babu wanda zai so ya shiga cikin fushinsa. Maleekh bai tsaya sauraron kowa ba. Duk wata nurse da ta ce masa ya tsaya a waje sai ya ɗaga hannu yana tsawatarwa. “Na ce bana son ji! Wannan hannunta zan riƙe har sai ta samu ƙarfin jiki! Ku dai kuyi aikin ku kawai!” Nurse ɗin da ke kusa da shi ta girgiza kai, tana faɗin: “Sir, please, ka tsaya a waje mana, ai ba manyan ciwuka bane—” “Ki yi mun shiru anan!” Maleekh ya dakatar da ita da murya mai cike da izza. “Kin ce ba ciwo bane? To kina ganin wannan jinin da yake fita a hancinta da lebenta wasa ne? Wannan ita ce rayuwata! Ki shiga ki kula da ita kafin na maka ƙarar ki cewa kina sakarci da aikinki..!” Likitan da yake tsaye ya kasa ɗaga kai ya kalle shi kawai, zuciyarsa na cewa: “Ai wannan fa ƙaramin rauni ne, amma yana wani rikicewa kamar wacce tayi accident da ya tawarwatsa ta.” Amal kuwa tana kwance tana ɗan motsa idanu. Tana jin yadda Maleekh yake ƙara tada hankalin kowa a asibitin saboda ita. Duk da zafin da take ji a hancinta da lebenta, dariya na ƙoƙarin ƙwace mata saboda irin yadda yake nuna tsantsar ƙauna... Sai dai ita ta kasa furta komai, sai ta matse hannunsa wanda yake riƙe da nata. “Amal,” ya faɗa cikin rawar murya, yana lumshe ido, “wallahi babu wani da zai sake cutar da ke a gabana. Ko ƙwayar jini ɗaya naga ya zubo, sai na tabbatar da an biya mun kuɗin ta da rayuwarsa.” Nurses suka kalli juna da murmushi marar sauti, ɗaya tana faɗi a ƙasan baki: “Wannan ai soyayyar da ta wuce ƙa’ida ce. Don lips da hanci sun ɗan fashe, sai kamar za'a tashi duniya...” Amal bata san lokacin da dariya ya kuɓce mata ba. Duk ciwon da take ji, sai ta kasa daurewa ganin yadda Maleekh yake ta surutai yana korafi ga doctors da nurses tamkar an kawo mace da tayi mummunan accident. Ɗaya daga cikin nurses ta kalli Amal tana murmushi tace: “Kin ga dole kiyi dariya, wannan ciwon naki fa bai wuce aje chemist a ɗauko maganin hanci da lips balm ba. Amma gashi an tada mana hankali.” Doctors ma suka murmusa, suka shiga kallon Maleekh da mamaki. Maleekh ya yi saurin hararar Amal yana faɗin: “Au, dariya ma kike yi ko? To ki ci gaba, amma wallahi idan baki warke ba, sai nayi wa dukkan likitocin nan rigima.” Amal ta cigaba da dariyar cikin hawaye, zuciyarta na ƙara narkewa da yadda yake nuna tsantsar damuwa da ƙauna. Bayan sun goge mata jinin hanci da lips ɗinta da auduga, aka ɗora mata maganin ointment kaɗan, suka ce shikenan. Maleekh ya zuba musu ido yana faɗin: “Shikenan fa ku ka ce? Wannan kawai kuka iya yiwa matar da zuciyata take kanta? Wallahi bana jin daɗin yadda kuke sakaci da aikin ku.” Doctors suka yi shiru suka cigaba da rubuta prescription ɗin magungunan da za a siya. Amal kuwa ta tashi tana dariya tana riƙe da hannunsa. Haka suka fita daga ɗakin emergency kamar wacce aka yiwa babban tiyata. 😅 Maleekh da Amal suna fita daga emergency suka hangi Ammy tana nufar wani side na marasa lafiya, women ward. Suka zuba mata ido, tare da bin bayanta, domin sun tabbatar Farha tana kwance a cikin wannan hospital. Bayan Ammy ta shiga room ɗin da aka kwantar da Farha, sai ga Maleekh da Amal suma suka shigo. Farha a wannan lokacin tana zaune akan gado, jikinta ya ɗan warware sosai. Ganin Maleekh ya sa ta tsure, jikinta ya fara rawa, zuciyarta ta faɗi rasss. Tasan ba ƙaramin hukunci zai yi mata ba kan laifin kulle shi da tayi har tsawon sati uku. Ammy kuwa ganin Amal yasa ta tunzura, ta ɗaga murya cikin fushi tana faɗin: “Waye ya bada izinin sako ki daga police station?..” Maleekh ya yi saurin cewa cikin tsawa: “Nine!” Ammy ta zuba masa ido cike da mamaki, zuciyarta cike da takaici. Ba ta taɓa tsammanin ɗanta zai tsaya a gaban idonta ya kare wata mace irin haka ba. Sai kuma ya juyo da hancin fushinsa kan Farha. Kallo ɗaya ya yi mata, sai jikinta ya fara rawa. A tsawace ya ce. “Wa ya baki izinin kulle ni a ɗaki?” Shiru tayi, tana sunkuyar da kai. Maleekh ya darara mata tsawa, har Ammy da Amal suka zabura da tsoro. “Magana nake miki! Ko baki da kunne?!” Cikin rawar murya, Farha ta ce da kyar: “Babu…” Maleekh ya ci gaba da magana, zuciyarsa kamar wuta: “Amma ban taɓa sanin ke daƙiƙiya, jahila, banza jaka marar class ba, sai yau. Wacce kwakwalwarta datti ya cika. Shin a tunaninki, a haka zan aure ki? To wallahi ko mata sun ƙare a duniya, bazan taɓa aure ballagaza irinki ba. Na tsane ki Farha, na tsane ki da zuciya ta gaba ɗaya! Kuma ki tabbata, daga yau zaki tattara ki koma can gaban iyayenki. Bazaki cigaba da zama a gidan mu ba!” Farha ta riƙe ƙirjinta tana rawar jiki, hawaye suka fara sauƙa a idonta. Ammy ta tsaya dafe

Chapter 19 of 62