yana mamaki ne ta yanda aka nemi Ammy ta wannan wayar gida, ya ɗauka wani sanarwa ne, tin da shine namiji yanzu a gidan, Abbah baya ƙasar....Sannan ya ji an furta sunansa...
Ammy zaro ido tayi jin muryar Salamatu...
Salamatu ta ci gaba da cewa.
"Hajiya ni bana jin ki, idan kina ji na to na ƙira wayarki baki ɗauka ba shiyasa na ƙira wayar gidan nakin, nasan yanzu ke kaɗai ce shiyasa....na je na samu malamin nan akan batun haɗa Maleekh da Farha sannan na bashi sunan Amal ɗin da photonta, insha Allahu ba za ta kai next week a raye ba, domin sai ta sha mungun jinya kafin ta mutu....."
Maleekh zaro ido waje ya yi yana kallon Ammy..
Islam buɗe baki tayi tare da toshe wa da hannayenta biyu..
Arfat kuwa tana kwance a sume bata san halin da ake ciki ba....
Ita kuwa Farha dake bakinsu ɗaya da Ammy saita sunkuyar da kanta ƙasi...
Ammy kuwa kasa motsi ta yi, haka zuciyarta ke bugawa ta kasa cewa komai...
Maleekh da yake riƙe da wayar sai ya ci gaba da sauraron matar tana faɗin...
"Malamin ya mun lissafin cewa, kuɗin kawar da Amal zai kai kimanin 1.5...Sannan kuɗin haɗa soyayyar Maleekh da Farha 2.5 ne domin yace zasu rayu ne har karshen rayuwa...domin Maleekh zai rinƙa bin Farha kamar raƙumi da akala, soyayya kuma mai ɗore wa, amma ya ce dole sai kin je ke da kan ki, abu ne mai muhimmanci idan har kina son burinki ya cika, jibi da asuba ki shirya zamu tafi, kafin nan ya gama haɗa mana komai...."
Ammy a fusace ta je ta fisge wayar daga hannun Maleekh... A tsawa ce take magana da matar cikin wayar..
"Ke wata iriyar jahila ce, jaka! Dabbiya, ai ko meye kya bari muyi waya ata wayata tin da private secret ne, ko kuma ki zo ki sameni a gida, amma saboda ke jaka ce shine za ki ƙira ni a public phone? ni kaɗai ce a gidan? ina da yara fa, shin kin san waye zai ɗauka a cikin su? ko kuma a misali idan mijina ya ɗauka fa?..."
Matar ta ce
"Kiyi haƙuri Hajiya ai nasan Alhaji baya Nigeria shiyasa na ƙira a wannan wayar gida..."
Ammy ta daka tsawa da cewa:
"Yi mun shiru dallah, ko ma menene ai kya bari mu haɗu kafin muyi wannan maganar.."
Matar ta ce
"Au kina nufin ki ce yanzu ba ke kaɗai kika ji wannan sirrin ba?.."
Ammy ta ja dogon tsaki tare da kashe wayar...
Ammy a wayen ce ta kalli Maleekh tana huci ta ce:
"Maleekh! Na ga alamar shaidan ya rufe maka ido koh? Kan ‘yan uwanka zaka yi musu irin wannan duka kamar dabbobi? Wlh yau ka wuce gona da iri! Kai ɗan banza ne, kai mara mutunci ne!!"
Maleekh idonsa Kan ta ya ce:
"Ni ɗan banza ne saboda na kare mutuncin matata? Ko saboda na hana su cin zarafin yarinyar da nake so? Ke kika ƙulla komai Ammy! Ke kika sa su zuwa gidansu Amal su yi mata dukan tsiya? Har kika kai ga haɗa baki da boka wajen zubar da jinin marainiya?! Wlh ki sani, a wannan karon baza ki taɓa cin nasara a kaina ba! Boka? Boka Ammy?..."
Ammy tana nuna shi da yatsa ta ce:
"Maleekh, ka saurareni da kyau, ni ce mahaifiyarka, ni ce na haife ka, ni ce na raine ka! Amma saboda wata ƙaramar yarinya matsiyaciyar ‘yar jarida zaka zubar da mutuncin ‘yan uwanka da ni kaina? Ka duba Arfat nan! Ka buga ta har ta suma! Farha nan jini ke zuba daga goshinta! Sannan ka tsaya a gabana kana faɗa mun maganganu son ranka, wai wannan shi ne mutumin da nake ƙira ɗana?!"
Maleekh ya matso kusa da ita, muryarsa na rawa da fushi ya ce:
"Idan kina so ki sani Ammy, kina gab da zubar da mutuncin mahaifiya a idona in har kika ci gaba da zuwa wurin waɗancan dabbobin bokaye, wallahi ban taɓa jin haushin ki irin yau ba. Kin yi amfani ta hanyar boka wurin niyyar zubar da jinin mutum, zaki biya boka akan ya cutar da rayuwar yarinya, sannan kike so in auri wacce take son jefa rayuwarki cikin haɗari? Ta sanadiyyar wannan ballagazar ƴar shaye-shaye kike son ki tarwatsa rayuwarki saboda ita, Ammy?...To wallahi sai dai ranar mutuwata na ƙarshe zan bar Amal ta shiga cikin sharrin ku...!"
Ammy ta buge ƙirjinsa da hannuwa, tana ihun takaici tare da faɗin;
"Wayyo Allah! Kai ne kaɗai ɗan da na haifa zai zama abin kunya a duniya? kai ne kaɗai ka bijire mun, ka zubar da darajata saboda wata zabiyar yarinya? To ka ji da kyau, wallahi tallahi gobe za’a ɗaura aurenka da Farha, ko ka so ko kar ka so. Wannan magana ta ƙare!"
Maleekh ya ce:
"Wallahi sai dai a ɗaura auren da gawa ta!! Ke da Farha da kowa duka ku ji da kyau, wallahi bazan aure ta ba! Bana son ta, bana son ta, bana buƙatar ta! Idan kin nace, to ki shirya zaman makoki!!"
Ammy ta girgiza kai, tana hawaye na fushi ta ce:
"Ka faɗi haka ko Maleekh? To ka sani, daga yau kai ba ɗana bane! Kai ba daga cikina ka fito ba! Nayi Allah wadai da haihuwarka, wlh sai na nuna maka babu wanda zai fi ƙarfina! Amal zata zama gawa a hannuna, kuma zaka dawo hannuna ciki kuka!!"..
Maleekh girgiza kai ya yi cikin kuka ya ce:
“Ki ci gaba da shirinki, Ammy! Ban yi mamaki dan kin ce ni ba ɗanki bane, sannan kin yi Allah wadai da haihuwana, zuciyarki ta riga da ta dusashe, boka ya ɓata miki imanin ki, tausayina ya dusashe a ranki, kin nuna cewa Allah bashi da ikon komai sai boka, kin nuna cewa boka yafi Allah wanda ya halicce ki, a duniya kika tarar da boka, Allah kuma baki ma san yanayinsa ba, baki taɓa ganinsa ba ko a mafarki, ƙarfin ikonsa kawai kike ji da kuma abubuwan da yake aiwatar wa ba tare da ganinsa ba, amma duk da hakan baki ɗauki hakan a matsayin darasi ba....gaskiya ne, saboda Allah ya baki lafiya, wadata, dukiya shiyasa zaki saka masa ta hanyar yin shirka da kuma tsine wa ɗanki wanda ya halitta a cikin cikinki, ni ɗin fa kyauta ne wanda Allah ya baki Ammy..."
Haka yake kuka yana magana, gaba ɗaya ya fita hayyacinsa, idanuwansa kamar jini tsabar jan da suka yi..
Ya ci gaba da cewa:
"Ammy! Wasu fa haka suke neman haihuwa amma Allah bai basu ba, sun nemi magani har sun gaji, sun roƙi Allah amma saboda ba wannan a cikin kaddararsu basu samu ba, amma ke Allah ya baki ni kuma iya nine namijin da Allah ya baki shine zaki yi watsi dani?...
Soyayyata da Amal kaddara ce ta Ubangiji, Allah ne ya ɗora mun sonta...
Idan na zaɓi matar aure bisa halal, ba tare da sa6a wa dokokin Musulunci ba, ba laifi nayi ba. Idan uwa ta tsine saboda haka, wannan tsinuwa bata da tushe, kuma zata iya dawo wa gare ta kamar yadda hadisi ya nuna...
Manzon Allah ﷺ ya ce:
“Ku guji tsinuwar iyaye, domin tsinuwarsu tana komawa ga wanda aka tsinewa kamar yadda kibiyar da aka harba take komawa ga mai harbawa.”..
Wannan yana nuna cewa, idan uwa ta tsine wa ɗa ba bisa hujja ba, Allah na iya karɓa saboda girman matsayin iyaye, amma kuma hakan na iya jawo mata alhakin da ba zata iya ɗauka ba..
Allah baya karɓar addu’a ta zalunci. Kuma wannan tsinuwa ba zata hana ƙaddarar Allah ba, domin aure da wanda ake so hukuncin Allah ne, ba wanda zai canza shi...
Ayar Qur’ani, Allah yana cewa:
“Babu wata masifar da za ta same ku face da izinin Allah. Kuma wanda ya yi imani da Allah, Allah zai shiryar da zuciyarsa. Kuma Allah ne Masani akan dukkan abubuwa.”
(Surat At-Taghabun: 11)
A Hadisi
Manzon Allah ﷺ ya ce:
“Ka yi imani cewa abin da ya same ka, ba zai wuce ka ba, kuma abin da ya wuce ka, ba zai same ka ba. Alkalami ya riga ya bushe da abin da aka rubuta.”
(Tirmidhi Sahih)
Maleekh yana kai wannan kalaman, ya juya cikin sanyin rai, Ya bar falon, ya wuce part ɗinsa ba tare da ya waiwayi kowa ba.
Ammy, kama kanta tayi tare da dokuwa akan kujera tana kuka...
☆
Maleekh ya shige ɗakinsa. Zuciyarsa tana bugawa kamar zata fito. Kalaman Ammy suna maimaituwa a kunnensa..
Voice echo a cikin kwakwalwarsa:
"Kai ba ɗana bane… Kai ba daga cikin jikina ka fito ba… Nayi Allah wadai da haihuwarka!"..
Maleekh dafe kansa ya yi yana girgiza shi da ƙarfi.
Murya na rawa yake faɗin:
"Why Ammy…? 😭 Why Ammy!! Why Ammy!!!"
(Ciwon kai ya tsananta, a ruɗe ya miƙe tare da ɗaukar ƙarfen flower vase ya fasa babban mirror ɗinsa.. Glass ya tarwatse a ƙasa. Ya ci gaba da farfasa duk wani abu na glass a ɗakin, yana ihu kamar mahaukaci.)
Maleekh yana ihu, yana zubar da hawayen da ba zai iya hanawa ba, yana faɗin:
"Idan ban kasance ɗanki ba, to ɗan wa nake?? Me yasa kika ce haka a kaina, mahaifiyata?? Wane ne ni yanzu…?!"
Ƙarar fashewar glass da ihunsa suka kai ga falon ƙasa. Ammy ta tsaya tana kallon Arfat da Farha, ko ta saurari yanda ihun yake fitowa, ta nuna kamar bata ji ba, sai ɗaukan ruwan sanyi da tayi a frig tana yayyafawa Arfat..
Islam kuwa ba ta iya jurewa ba, da gudu ta haura upstairs...
Cikin ɗakin Maleekh ta shige...
Islam ta shigo cikin razana, ta tarar da ɗakin a hargitse. Maleekh yana tsaye cikin kuka, hannunsa sai ɗigar da jini yake yanda glass ɗin mirror ya tsatstsaga masa fata... haka yake cakurkud'e sumar kansa yana ihu...
Ganin Islam yasa ya fara gurnanin cewa:
"Ammy ta kore ni daga zuciyarta, ta ce ni ba ɗanta bane… Islam, to ni ɗan wa ne in ba ɗanta ba?! Ina zan dosa yanzu??"
Islam ta ƙaraso cikin kuka, ta rungume shi da ƙarfi..
Itama kukan take tana faɗin:
"Dan Allah Yaya ka dakata haka. Ka yi haƙuri. Wallahi kai ɗan Ammy ne, kai ɗan gidanmu ne! Kada ka bari kalamanta su hallaka maka zuciya. Ka yi haƙuri dan Allah!"
Maleekh yana sakin nannauyar zuciya cikin kuka ya durƙusa ƙasa, ya jingina da bangon ɗaki, Islam itama zama tayi a tare da shi, ta rungume shi sosai. Dukansu suna kuka...
Maleekh a raunane cikin rawar murya ya ce:
"Islam… zuciyata ta karye. Na fi jin zafin wannan kalaman fiye da duk abinda aka taɓa mun a rayuwa. Ni ɗan waye yanzu, idan ba ɗan mahaifiyata ba?"
Islam ta share masa hawaye ta ce:
"Yaya, kai ɗan daraja ne. Kai ɗan halak ne. Kai ɗan da Allah ya ba a wannan gidan ne. Kada ka taɓa mantawa da hakan."
Maleekh ya rungumi Islam da ƙarfi, hawayensa na digowa a kafaɗarta, suna kuka tare. Ɗakin ya cika da ƙarar hargitsewar zuciya....
Suna zaune a wannan lokacin har dare yayi sosai, suna zaune rungume da juna, haka Islam take jin yanda jikin Yayanta Maleekh yake kakkarwa kamar wanda yake jin tsananin sanyi... ga jikinsa ya yi mungun ɗaukan zafi, alamun tsananin zazzabi ne ke damunsa..
Ga wani irin fitar da deep breathing da yake kamar last breathing ɗinsa kenam..
A tsorace ce Islam ta kokarta ɗaga shi, ta tallafa masa zuwa kan gadonsa ta kwantar da shi...
Da gudu ta fita daga ɗakin ta nufi down stairs, ba kowa a falon domin a lokacin misalin ƙarfe 12 na dare ne..
Kai tsaye medicines room ta nufa domin ɗauko first aid box..
Tana ɗauka ta koma part ɗin Maleekh dake itama Islam ɗin ɓangare likitanci ta karanta..
Tana aiki a wani babban hospital...
Tana zuwa tayi saurin masa allurar zazzabi sannan ta ɗaura masa drip a ɗakin, dake suna da komai da komai na emergency...
Sannan ta jiko ƙaramin towel da ruwan ɗumi tana matsa masa jiki da kan goshinsa gaba ɗaya...
A wannan ranar Islam bata samu yin bacci ba har asuba...
Da jin ƙiran sallah Maleekh ya buɗe ido, a hankali ya tashi zaune yana bin Islam da kallo wanda bacci bai daɗe da ɗaukar ta ba, tana zaune akan ƙarami chair a bakin gado, ta kwantar da kanta a bakin gadon..
Murmushi ya yi ganin yanda ta bashi kulawa, ɗaga kansa ya yi yaga drip na ruwa har leda uku duk ya ƙarar, ya samu an cire masa, ga alluran da ta masa ciki har da na Anxiety (damuwa)..
Yana ƙoƙarin tashi a zabure Islam ta buɗe ido tare da ɗago wa tana kallonsa, ta ce
"Yaya ya jikin dai? Yanzu me kake ji a jikinka?..."
Maleekh ya ce
"Ba komai Sweet Sis, normal.."
Murmushi tayi tare da faɗin
"To bari naje na haɗa maka breakfast sai na kawo maka ko?..."
Ta fice, shi kuwa ya bita da kallon Murmushi, daga bisani ya miƙe ya shiga toilet domin ɗauro alwala...
☆ _This Morning_ ☆
Gida gaba ɗaya ya yi shiru, kamar gidan da aka gudanar da jana’iza. Ba kowa ya yi bacci da kyau ba.
Farha na zaune a kujera tana duba wayanta..
Arfat kuwa har yanzu tana jin ciwon marin da Maleekh ya riƙa mata jiya, tana zaune itama tana game a wayarta...
Islam ce ta sauƙo daga part ɗin Maleekh zata wuce kitchen baya yi wa kowa magana ba..
Farha ta tsayar da ita da cewa.
"Kin ga Islam, zo ki taya ni zaɓan kayan ɗakin da aka turo mun daga Malaysian, kin san yau ne auren kuma a yau za'a kawo mun kayan....
Islam harararta tayi tare da faɗin.
"Wai ke kin ɗauka da gaske za'ayi auren yau ne?..."
Ammy wacce shigowar ta kenam falon ta ce:
"Ku saurara da kyau. Wallahi ban ga dalilin da zai hana a ɗaura auren Maleekh da Farha yau ba. A shirye nake. Ni uwa ba zan ƙi ganin auren ɗana ba. Idan kuwa shi yaron ya raina ni, to sai dai ya kashe kansa da ƙiyayya. Ba zan canja ra’ayina ba!"
Islam tana tsaye ta kasa magana, zuciyarta cike da tausayi. Ta tuna halin da ta ga Maleekh a ɗakinsa jiya. Ta kalli Ammy tana hawaye ta ce:
"Ammy… ki ji tausayin Yaya. Kalamanki sun yi masa ciwo sosai jiya. Wallahi ban taɓa ganin shi cikin wannan hali ba. Don Allah ki yi haƙuri da shi, kar ki tilasta masa wannan aure…"
Ammy ta kalli Islam da idanunta masu zafi..ta ce:
"Ke ma ko? To yanzu kin fara goyon bayan waccan yarinyar kenam? Ki saurara mun sosai Islam, ni ce mahaifiyar ku! Duk abin da zan ce kuyi, dole kuyi shi! Kuma wallahi sai na ga auren nan ya tabbata, ko Maleekh ya so, ko kar ya so wannan ya rage nasa.!"
Farha tana yatsina fuska ta ce:
"Ya yanzu Ya Maleekh ya soni ne?..."
Ammy ta ce da ita:
"Ke dai kiyi shiru! ki bar ni da shi. Idan har ya zama mijinki, to dole ya koyi yanda zai zauna dake. Ba son zuciyarsa nake nema ba, abin da nake nema shi ne buri na ya cika. Kuma sai ya cika, wallahi sai ya cika!"
Arfat ta turo baki tana shafar kumcinta ta ce:
"Ammy, gaskiya Yaya Maleekh ya yi mun tsauri sosai. Zai iya kasheni wallahi, jiya ya kusan hallaka ni da duka…dan Allah a haƙura da auren nan, wallahi tsoro nake ji..."
Ammy ta wurga mata ido cikin tsawa ta ce:
"Ke wato kin ji tsoro saboda ɗan marin da aka yi miki kenan? Idan ba ki shirya ba, sai ki fita daga harkata kema! Wallahi ba zan bar Farha ta zauna haka babu aure ba. Ko da duniya zata guje ni auren nan sai ya tabbata!"..
Tana faɗin haka ta miƙe tsaye ta bar falon.. Zuciyarta cike da tsananin fushi...
Bayan ya idar da sallah.
Idanunsa sun kumbura saboda kuka. Ya tuna da kalaman Ammy na jiya:
“Kai ba ɗana bane… Ba daga cikin jikina ka fito ba!” Sai zuciyarsa ta sake karyewa. Ya dafe kansa da hannaye biyu...
Yana magana shi kaɗai, da murya mai sanyi:
"Ammy… yau kike son ɗaura auren da Farha? To wallahi… idan wannan aure ya tabbata, sai dai a ɗaura shi ne da gawa ta…Domin nasan zuciyata ne zata buga, ga nauyin kalamanki ga nauyin ƙiyayyar Farha.."
Ya nufi window yana kallon rana wacce ta fito da haske, amma a zuciyarsa babu haske. Zuciyarsa ta cika da ƙiyayya, ciwo, da rashin bege...
Anata shirye-shiryen ɗaurin aure. An kawata falo da flowers da ƙananan kayan ado. Farha tana zaune cikin wani sabon gown mai tsada, tana cike da ƙyashi da girman kai. Arfat da Islam da wasu ƙawaye suna kusa da ita...
Sai ga Amal ta shigo cikin ruɗani, idanunta a kumbure da kuka. Ta shigo falon kamar wacce take neman mafaka, tana ƙiran suna da rawar murya...
"Maleeeekh! Maleeeekh!! Ina Yaya Maleekh ɗi naaa??"
ƴan mata a falon suka tsaya kallonta. Farha kuwa ta tashi da sauri, ta sha gabanta kafin ta nufi stairs ɗin...
A tsawace, tana hararar ta ta ce:
"Ke tsaya nan! Yau ranar aurensa da ni, ba zaki taɓa ganinsa ba. Domin mijina mai tsada ne, ba kowace kucaka bace zata iya ganinsa..."
Amal ta fashe da kuka, tana ƙoƙarin turata ta wuce tare da faɗin:
"Don Allah ki barni, ki barni na ganshi, ki barni kawai na ganshi…"
Da ƙyar Amal ke tura hannun Farha, sai kuma suka ji muryar Ammy daga sama, muryar da ta tsinke zuciya da ƙarfi kamar tsawa...
"KEEEE!! Dakata nan nace!!"
Amal ta tsaya cak! Ta juya a zabure tana kallon Ammy wacce ta sauƙo daga stairs ɗin part ɗinsa, fuskarta cike da ɗaci da fushi...ta ce:
"Me ya kawo ki gidan nan?!"
Amal tana kuka sosai ta ce:
"Ammy… wallahi ni Yaya Maleekh nake nema…"
Ammy ta katseta da tsawa cewa:
"Kin ji labarin aurensa kenam!? Ko shi ya gaya miki? To Da ke da Maleekh ɗin kunci kutumar buro uban ku! Kina jina kooo?!! Maza kama hanya ki barmun gida kafin in sa gadawa su fita mun dake..!!"
Amal ta gudu ta ƙaraso gabanta, ta durƙusa, ta riƙe ƙafar Ammy tana kuka da rawar murya.
"Dan Allah Ammy! Dan Allah kar ki rabani da shi! Wallahi inasonsa da zuciyata gaba ɗaya. Ki taimake mu, ki ji tausayinmu Ammy. Idan ma zaki aura masa Farha, to don Allah ki saka sunana a matsayin mata ta biyu. Ki haɗa aurenmu gaba ɗaya, dan Allah! Zan iya jure komai domin kawai na kasance da Maleekh…"
Ammy ta zare ƙafarta daga hannunta, ta ɗaga Amal da ƙarfi ta zabga mata mari! Mari har sau biyar a jere, tana huci.
Ta ce:
"Ke! Ki rabu da yarona. Kin hallaka shi da hauka saboda soyayyarki marar mutunci. Wace irin mayyar yarinya ce ke? Jarababbiya mara zuciya!"
Amal tana kuka tana riƙe da kumcinta ta ce:
"Ammy, idan auren ne… wallahi na yarda ki yi mun duk wani hukunci. Ki saka ni a cikin masu gasar shad'i idan haka ne. Zan iya jure bulala ɗari biyu kawai don na auri Maleekh…"
Ammy ta ja dogon tsaki tare da faɗin:
"Ni bani da lokacinki! Kafin minti biyu, ki bar min gida, kafin na ƙira maza su fitar dake da ƙarfin tsiya!"
Daga nan Ammy ta juya a fusace..
Amal ta juya zata tafi.
Farha ta sha gabanta, tana dariya cikin kyashi ta ce:
"Na gaya miki hanyar da zaki samu Maleekh? To ki tafi gidan club. Ki je can zaki same shi, kuyi bankwana na ƙarshe."
Farha ta ci gaba da yi mata dariya tana faɗin address ɗin wani club sananne a Abuja, inda aka fi cusa mata ƴan iska da masu shaye-shaye. Amal ba tare da ta yi tunani ba ta ɗauka da gaske ne. Da gudu ta fita daga gidan, ta shiga mota kai tsaye ta nufi wurin da aka faɗa mata...
Maleekh kuwa a wannan lokacin yana ɗakinsa, yana kwance cikin damuwa, bai san komai daga abin da ke faruwa a ƙasa ba. Islam tana falo, zuciyarta na tafasa da tausayin Amal da Yayan nata, amma ta kasa yin komai....
Kafin Amal ta isa.
Farha ta ƙira wasu kawayenta a waya tana sanar da su cewa:
“Ku saurara da kyau! Amal za ta shigo club, ka da ku bata damar shan iska. Ku dabaibayeta, ku tilastata ta shan kwayar maye. Idan ta fara rikicewa, sai ku mata injection, da zaran ta fara maye sai ku kaita toilet na maza, ku kwantar da ita, ku yayyaga mata kayan jikinta. Ku zuba mata jini a ƙasan wandonta, ku tabbatar ya gangaro har ƙafarta. Za a ɗauka cikin da take da shi ta zubar ne.
Bayan nan, ku ajiye kwayoyin zubar da ciki kusa da ita don a tabbatar da sharrin. Sai ku gudu ku bar ta can… Zan tabbatar duniya ta tsane ta!”..
Dariyar mugunta suka yi kowacce ta ɗauki nata aikin da za ta yi.
Farha kuwa ta ci gaba da zaman jiran saƙon kammala aiki...ɗaurin aure kuwa an ɗan taru a gidan ana jiran isowar Abbah kafin a shafa Fatiha....
Amal ta isa Club
Amal ta shigo club ɗin a ruɗe, tana duba ko za ta hangi Maleekh. Idonta ya rufe saboda tashin hankali da ruɗewa.
Cikin mintuna, kawayen Farha suka iso kanta. Ɗaya daga cikinsu ta yi kamar tana yi mata sannu da zuwa..
Amal kallonsu tayi tare da faɗin
"Ku ɗin su waye ne?.."
Suka sanar da ita cewa, su ɗin ƙawayen Maleekh ne..
Suka zaunar da ita tare da bata juice wanda suka sanya kwaya a ciki, sun sanar mata cewa.
"Ta jira Maleekh yana nan zuwa.."
Amal bata zargi komai ba, ta karɓi drink ɗin. Da ta sha, jikinta ya fara sanyi. Idonta ya fara juyawa, zuciyarta na bugawa da sauri.
“Me ke faruwa da ni haka…?” Ta furta da rawar murya.
Wata daga cikinsu ne ta watsa masa ruwan lemo ta nuna rashin sani ne, Amal ta zabura ta miƙe tana karkade ruwan jikinta, anan suka tura ta toilet akan ta je ta gyara jikinta, suka mata kwatancen toilet ɗin maza, ai kuwa nan Amal ta je..
Tana zuwa kuwa kanta yayi wani irin sarawa, maganin ya fara mata aiki..
Anan ta faɗi...
A cikin male’s toilet suka tarar da ita, suka kulle ƙofa. Wata ta riƙe hannunta, wata ta cire mata hijab ɗinta. Suka buɗe mata jiki da karfi, suka yi mata injection.
Amal ta fara rawar jiki, idanunta sun yi nauyi, numfashinta na sauƙa a wahale.
Suka yayyaga rigarta da ƙarfin tsiya, sannan ɗaya ta zuba mata jini da suka riga suka tanada a cikin kwalban roba. Jinin ya biyo ƙafafunta ya watse a tiles ɗin toilet.
“Hahaha yanzu duniya zata ɗauka ciki ta zubar. Muna da tabbaci wannan yarinyar ta lalace!”
Suka ajiye kwayoyin zubar da ciki kusa da ita, suka gama mata video sannan suka fice da gudu suna dariya, suka tura wa Farha video yanda suka yi mata daga farko har ƙarshe..
Misalin ƙarfe 10 na dare aka samu Amal a kwance a cikin male’s toilet. Tana kwance a cikin jini, idonta a rufe, numfashinta ya tsaya..
Mutane suka taru, suka fara ihu. Wani ya ɗauki hoton ta, ya saka a social media...
Aka ƙira an jarida..
Ƴan jarida suka isa, suna video da cewa:
“Abun mamaki, Amal Abdulsamaad shahararriyar ƴar jaridar nan, ga ta a gidan club a male's toilet kwance cikin jini, abin da bamu sani ba shine 'shin wani ne ya mata fyade ko kuwa?' Amma bisa alamun ciki ta zubar, domin ga kwayoyin zubda ciki a gefenta...."
Ƴan sanda suka shiga cikin hayaniya suna ƙoƙarin ƙiran motar asibiti, amma kafin hakan hotunan da bidiyon suka baza a duniya.
Maleekh yana kwance yana tunani. Wayarsa ta yi ting. Ya duba WhatsApp ya ga hoton Amal kwance a jini!
Message ya biyo baya:
“Idan baka yarda ba, kunna TV.”
Zuciyarsa ta buga, jini ya hau kai. Ya kunna TV sai ya ga rahoton kai tsaye na club ɗin, Amal kwance a jini, mutane suna ta kallonta, ƴan jarida suna ta yayata zancen
“Amal!!” Ya furta sunan a ruɗe..
Ya fice da gudu daga ɗakin sanye da farar jallabiya. Bai tsaya sauraron kowa a falon ba. Farha ta bishi da kallo tana tauna lebenta cikin shauƙin mugunta.
A wannan rana kuma, daidai da lokacin bikin Maleekh da Farha, Abbah ya dawo daga Amurka. Cikin fushi ya dawo zuciyarsa na harzuka, yana zuwa daman ya wargaza taron bikin, ya kori kowa a gidansa sannan ya ƙira iyayen su Farha ya sanar da su cewa kada su zo, an fasa bikin...
A wannan ranar wuni Abbah ya yi yana balbale Ammy da masifa..
"Akan me zaki yanke bikin ɗana ba tare da sanina ba? Saboda kin mayar ni mahaukaci bansan me nake yi ba?..."
A falon akwai wata tsohuwa wato mahaifiyar Abbah da Mahaifiyar Ammy duk suna zaune har da Mahaifin Ammy...
Jin wannan al'amari yasa duk suka zo...
Wannan bikin an soke shi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 27 Chapter of 62